Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
10 / 10
ba son mu dinga samun sabani a ko wani lokaci ba haka na aurokine sin in samu farin ciki da gamsuwa a wurin ki sai gashi tun yanzu kin fara min da hakan. Idan kika bi dokana zamu zauna lafiya dake zakiji dadina fiye da zaton ki wasila sai kukan munafunci wai tayi kuskure ba zata kara hakan ba insha Allahu. Mikewa yayi yana fadin kin mayi wanka kuwa kinga hakan na cikin abinda zai dinga sakani fada dake don bana son ganin mace a haka. Mikewa tayi itama tana fadin yanzun nan idan na karasa aikin nan nake son nayi wanka sai gaka ka dawo ya girgiza mata kai ya shige ciki shi da kanshi ya gyaro dakin nasa don yasan ko tayi ba tsayawa zatayi gyara masa yadda yakeso ba tunda alama ya nuna bata iya komai ba tun a gida. Lailai bariki tayi bakin yan iska duk suyar awarane da za a bakin hayaki da wanan kwalliyan haka maman biyuce ke fadin hakan daga kofanta inda take zaune. Fita nake da kayan aikina don yanzu na rage zuwa islamiya sosai tunda na sauka amma akwai ranakun dana ware nake shiga daukan karatu. Don hakane yanzu na kara fadada karfin sana,ata inda mukeyin shi tare da wasu matasan unguwarmu da basu da girman kai suna dan samun kwabon kashi suma ta wanan hanyar. Zakice wata yar kasuwace a wurin yadda wurin ke cika yanzu da jama,a masu sayar da abubuwa da dama don unguwar ta rayu sosai yanzu ba sai kayi wahalan zuwa wani wuri sayen kayan miya ba duk akwaishi a wanan wajen. Motoci ko har daga wani unguwa suke zuwa saya awaran mu da soya milk mai dadin hadi ga kunnun ayya da zobo da ruwan sanyi sai sauran kayayakin da wasu ke ajewa suma a waje. Zubin farkone yunusa ya zuba ina kokarin ganin wurin ya natsu min wata mota ja tazo ta parker a gaban mu wasu matane a cikin motan suka fito. Naji dayan na fadin lalai wurin nada kyau sosai kuma ga tsabta tana zuwa ta tsaya saitin kaskon suyana daga can inda nake tsaye na dago ina masu sannu da zuwa. Suka amsa dayan ke fadin don Allah ina me wurin nan ace muna macece ko na amsa da nice ai tow takara min kallo kafin tace ikon Allah dama ashe ma yarinyace karama haka na dauka wata babban mace zangani idan munzo don Allah munzo muna son wani alfarma a wurin ki. Nan muke kasan layin nan bamu dade da dawo ba garin nan to akwai wani yaron mu dayake sayo muna wanan awaran shine muke so da yawa in ba damu muna da buki da zamuyi dashi. Dan murmushi nayi har duple dina yana dan lutsawa nace zaikai na kwano nawa sai naga sun kalli junan su kamar ta ashirin haka ko fiye ko da sauri nace aikin ashema ba mai yawa bane sosai zamu iya in Allah ya yarda. Kamar wani rana kuke sonshi ke nan tace zuwa ranan jumma,am nan mai zuwa insha Allah nace to sai ki ban lamban wayan dayanku don muyi communicate daku muji inda za,a kawo maku. Baida matsala hakan karfe sha biyun rana zamu iya samu nace insha Allahu ok nawa zamu baki dan tunane nayi kafin na fada masu kudin sai naga sunyi dariya kawai abin ma ai ba tsada yadda muka zata. Na dai raga makune don farkon haduwan mu ke nan daku sukace sun gode manyan yanka za ayi ko kanana mai yawan maganan a ciki tace min kingane zaki munashine irin dai yankan da zai karrama bako din nan don Allah yajin yayi dadi sosai nace baki da matsala suka ciro kudin suka ban mukayi sallama dasu. Har sun juya dayan tace min son Allah ko kinsan wani gida da aka iya abincin buki mai kyau na gani na alfarma da zai fitar da mutum a kuya. Nace kwarai kuwa wanan gidan ma sunayi sosai kuwa da cewa gidan mu nace ai sai kowa ya yaba insha Allah suna alala na gwagwani dana leda suna tuwo duk na,uin da kukeso sai fadi kalan miyan da kakeso ka kabar masu zabi suyi ma. Wai masha Allah wallahi naji dadi har ina tunanen inda zamu je mu samu masu aikin nan nace Allah ya yanke maku wahala to kinga abinda zamuyi shi wanan tuwon na kwana shidane za a dinga muna saidai muzo mu dauka. Kinga zai fara daga ranan wanan alhamis din ko jumma,a zuwa dai asabar har lahadi kilama amma zamu kawo maku shinkafa da abin miya kullun kuma zamu dinga waya dake sai a fada maki abinda akeso . Don Allah amana yayi dadi sosai don bakin mu na kunya da zasuzo muna haba hajiya kada ki samu matsala insha Allahu komai zaiyi daidai. Kudi ta ciro wrapper yan dubu dubu ta miko min tana fadin wanan zaku sai kayan miya abinda babu cikinsa wanan kuma dai sai abawa masu aiki su fara tabawa kafin mu hadu. Suka tafi suna min godiya ina masu sai da suka bace min da gani na fada cikin gida ina kwalawa su mama kira da mama uwa ku fito yau ta samu fa. Na dauko maku rigama da rana tsaka kowa ya fito na fara basu labari ina kyalkyatar dariya suma haka wai bintu wanan bakin wayau naki a ina kika gajeshine ? Ai in batayi ba Allah zai tambayeta kun manta haka malam yake da wanan wayau neman kudin a baya muka juya da mamaki haka maryama take da neman kudi shima kuma malam kun gani abin yasata tsakiya ke nan ai. Karo na farko da mama ta kira sunan mahaifiyata da sunan kwarai bata aibanta ta agabana ba jin hakan yasa nasan yan arzikin nata suna kusa lokacin. Nace mama da wanan abin akaishi wani gida a gara a kawo nan ko dan dubu biyar biyar muka samu kan wanan harkan kinga ai mun karu ko gashi kuma ko banza zamuci mu koshi har yan kannena. Ai kinyi dabara keda tuka tuwone aiki kome a garemu yanzu barin dawo a zauna ai kasafi muji yadda za a tsara abin but hassana ta fito daga dakinsu tace dani a ciki saiga hussai na fadin wa za a bari a baya har ni wallahi dani ciki. Nace barin gama mu san ya za ayi idan nashigo na fice na barsu suna magana na koma wurin sana,ata mukaci gaba da aiki sai karfe takwas na kwashe kayan muka dawo gida. Dukkansu suna zaune suna kallo a kofana alwala nayi nayi sallah isha,i kafin na fito da kudi wrapper guda nace yanzu mama yaya za ayi sai a fara lissafi ke Samira dauko littafi ki rubuta. Nan suka fara lissafo abinda za a saya duk na dangin miya dana amfani zamu kashe wurin dubu sittin akalla don muna son ayisa yayi kyau don gobe. Ku ban yin malmalan tuwo mukaji maman biyu ta fada a bayan mu nace mama da wahala fa zaki iya ke kadai kuwa tace ai dole wani ya kama min amma ku barni a duba yanzu dai mama kece zaki kula da komai keda mama uwa mu sai muyi aikim ku duba mana ko ? Ina magana ina kirgan kudi na cire goma na fara bawa mama na kirgo wasu goman muka ba mama uwa hakama mama Lanto. Su kuma yan matan na basu biyar biyar yara kuma na bisu da dubu dubu har kananan sai samarin danabawa dubu biyu biyu nan gida ya dauki murna sosai. Washegari wanan aikin ya dauke muna hankali sai masu aikina suka tsaya sukai sana,a din ni saida yamma sosai muka dawo gida kamar jiran mu sukeyi su masu bukin sai gasu sun iso muna da kayan abincin irin shinkafa fara dana dahuwa da bag din semo masu yawa sai da aka gama shigowa da kayan matan suka shigo har cikin gida aka gaisa dasu mama suka kumayi masu alheri suka tafi na rakosu zuwa bakin motar su nidasu samira sukai ta zuba muna godiya zakice kyautane zamuyi masu aikin. Babane ya fito yana fadin wai meke faruwa sai kowa yayi shiru maman biyuce take fadin mallam alherine fa yarka ta dauko muna muna zaune nan dai ta fada mai yadda na labarta masu komai. Saida baba ya gama saurare yace to nidai gaskiya rikicine bani son amma ai wanan hanyar samune da kuma karuwa da hadin kai in za a tsaya ai masu shi babu hayaniya ko ha,inci walillahi hamdu. Tsegumine banso ya biyo baya don Allah a kula ya juya ya shiga daki koda muka dawo mun samu har ya gama ya shiga dakin shi yasaya. Komai mun shirya mun kuma tanadi abubuwan amfani har tukwane hassana taje da mota ta aro lokaci kawai muke jira Allah ya kaimu. ZAINAB IDRIS MAKAWA An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 10 of 10