Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 5
wajen juya Zainab da goje irin abinda ya fito daga gareta na Amai da Gudawa. Kai saida Mallam İbrahim yace da ita ta tafi kar Alhaji ya ga shiru bai ganta ba hankalinsa ya tashi. Sukai sallama ta tafi. Da ta isa, ta baiwa Alhaji labarin halin da Zainab ke ciki, yai Aľ'ajabi da niyar da safe zai je ya gaisheta. Da gari ya waye sai ga Mallam Ibrahim yana sallama a gidan Alhaji Mai Waken, Allahu Akbar, Alhaji daga jin muryar sai ya saida, to amma yau ba sarka aka zo karba ba kuma ba tankiya aka zo yiba, Alkawarin Allah ne ya cika. Bayan da Alhaji ya fito suka gaisa Mallam Ibrahim ya sanar mar da cewa niyarsu kyakkyawa dai yanzu Allah bai yi ba saboda kuwa Zainab Rai yai halinsa misalin karfe hudu na dare. Yanzu ma am fara taruwa don jana'iza. Mallam Ibrahim ya koma, shi ko Alhaji ya shiga cikin gida ya kira Rufa'i ga Balki tana zaune ya sanar da su, haba nan da nan sai Balki ta fashe da kuka, sai daki, ta dauko zani, Alhaji yace da ita to haka zaki bi titi kina ihu sai kace wadda kura ta koro, mutuwa fa kowa zai dandanata, na menene zakirinka haka. Kije sai munzo. Ta tafi. Shiko Rufa'i Alhaji yace dashi kayi hakuri kar ka daga hankalinka. Duk abinda Allah yayi shine daidai, mahaifiya kan 56 1 α e iyilaια이 ih mutu tabar jaririn da bai ko shekara ba, miji kan mutu ya bar matarsa da ciki da 'ya'ya masu yawa, Sarki kan mutu ya bar sarauta, don haka kayi hakuri, ka dinga yi mata addu'a, Allah ya jikanta ya yafeta. Kuka kuma kan kara tsanani ne ga mamaci, don haka kar ma ka fara kana namiji. Sai ya umarce shi da ya tafi gidan Alhaji Usamatu ya sanar da shi. Yaje ya biyo ta gidan kanwar uwar ya gaya mata. Shiko Taja tun a unguwarsu yaji saboda akwai kanin uban Zainab din acan don haka sai ya tafo. Nan dai aka taru aka sallaci gawa aka je makabarta aka sitirta ta. Rufa'i na daga cikin wadda suka sanya gawar Zainab cikin kabari. Aka dawo zaman makoki. Duk wadda ya san Rufa'i sai yai masa taziya ta musamman saboda rashinda yayi baya ga iyayenta. Akai zama har na sati aka watse. Anan ne Taja yake gayawa Rufa'i cewa Quirana ta bar garin. Rufa yaii yoi murna da haka. Kuma ya fara tunanin Binta. Ita ko Binta jhar ta riga ta yanke shawarar tafiya can gun wata kanivar warta da ke aure a wani gari. Saboda kar asirinta ya tond in thje can in da halin zubarwa sai a zubar. To duk Rufa'i da qja basu da labarin haka. Amma Zaliha ta san kome. Bayan lokaci mai tsawo, sai Alhaji Usamatu ya kira Rufa'i don ya tun tube shi batun yarinyar da yaji labarin yana nema ada, wato Binta. To a nan ne Rufa'i ya sanar da shi cewa sai ya zo ya bincika. To da yazo ya sanar da Taja batun wannan magana sai suka je gidan su Zatiha saboda tun da tazo tai masa ta'aziyya basu sake sadpwa ba, bare ma suyi zancen. Anan ne suka ji cewa 57 Binta tayi tafiya. Taja ya tambayi Zaliha batun auren Binta da Rufa'i, sai Zaliha tai ajiyar zuciya, wannan sai ya baiwa Rufa'i wani irin tunanin ko menene ya faru? Zaliha ta nuna babu kome amma dal akwai wani abu a yadda suka fahinceta. Sukai sallama akan sai in Binta ta dawo. To labarin dai da Rufa'i ya sanar a gidansu kenan cewa sai Binta ta dawo. 58 KASHI NA GOMA Daga cikin wadda suka zo ta aziyyar Zainab har akwai wani abokin Rufa'i wadda yake can wani Birni na Uku mafi girma a kasar, yana aiki a wata ma'aikatar harkokin kasashen waje. To shine yake tun tubar Rufa'i batun kome yakeyi yanzu? Ya bashi duk labarin halin da yake ciki na rashin aiki, sai shi abokin nasa ya nemi da ya rubuta takardar neman aiki ya hada da takardunsa na shaidar kare karatu don ya tafi dasu. Don akwai wani kamfanin gine-gine da sauran aiyuka, na kokarin kara ma'aikata saboda wata kwangila da ya samu ta gina tagwayen hanyoyi a kasar. Haka akayi, Rufa'i ya rubuta, ya bashi, shi kuma ya tafi dasu. Rufa'i dai na nan yana jiran dawo war Binta, sai wata rana Taja yake dan tsokala masa labarin da yajikishin kishin dinsa a cikin gari game da Binta. Cewa Eskep ya gudu ne saboda caiki da yai wa wata yarinya, har ma ya tafi da wasu kayan jama'a. Taja da yai bincike sai yaji ashe Binta ce. To amma bai yarda ba, akan sai ya tambayi Zaliha. Rufa'i da yaji haka sai ya tuna lokacin da suka je gun Zaliha, wannan magana ta sa Rufa'i cikin zulumi da tunanin yaya matsayin rayuwarsa ne? Menene rashin nasararsa akan aľamuransa ne? Yanzu me zai fada a gida in har an tabbatar Binta tayi ciki, wace hanya zai bi, yana cikin irin wannan tunani, sai Taja yace dashi "yau muje gun Zaliha!' Rufa'i ya yarda, Sai Suka tafi dare yayi suje gidan su Zaliha. Da isarsu kofar gidan su Zaliha sai sukai sa'a ga mahaifin ta ya dawo daga unguwa zai shiga gida, to dama yana ganin Taja a wurin da suka gaisa sai ya shige ciki. Kawai sai ga Zaliha ta fito ya turo ta. 59 Suka gaisą aka fara tadi kamar yadda aka saba. Can sai Taja ya ce "Zaliha a gaskiya, ranar wanka ba boyon cibi,kuma duk mutumin daya taka ka gaya mar cewa ka takani, to abinda nake so dake, tunda tsakaninmu akwai cin amana da rufa, to fa ba zamu je ko ina ba. Kuma tsakanin mu sai dai sakayyar Allah". Zaliha sai tai farat ta dafa kirji tace me ya faru? Rufa'i ya sa baki yace "Batun Binta ne kuma kin san kome amma kika rufe mu, to amma alhamdu lil lahi tunda Allah ya buda mana mum ji, kuma mun gani", Taja ya kara da cewa "kuma bamu.baku". Zaliha kanta ya kulle duk ta fahimci manufarsu. To amma sai tai tawili ta dage tace, "kash! ana dara ga dare yayi, ni baku cemin ga irin abinda mukai muku ba kawai sai fada haka, ai sai kuce munyi muku kaza da kaza amma kuna magana a fakaice sai kace kuna tsoro. Taja sai ransa ya baci ya ce a fusace "Tsoron wa? Allah ya sauwake, saya wa ne kawai muke yi saboda kin san kome duk abinda muke nufi, amma bari ai miki gwari gwari; Binta cikine daita tun wata uku da suka wuce, shiya sa ma ta bar garin yanzu. Kuma munsan wadda yai mata. Kuma in gayamiki gaskiya, tunda abokin barawo, barowo ne to ni kema gari zamu raba, Rufa'i sai yace "a'a ba za'ayi haka ba. Kai dai tunda mun nuna mata laifinta sai ai hakuri". Binta tace "to wai ni ina ma zansan wannan abu, ba gaya mun za tayi ba, ba gani nayi ba, to ina zan sani?" Taja sai ya kauda kai yace "kya gayawa yaran gidaku ko zasu yarda. Amma ba mu ba! Nan dai sukai sallama, suka tafi. Suna tafiya suna mahawara Rufa'i yace da Taja na tabbatar ta sani, saboda ai kaga bata karya ta ba, sai kawai ta nuna 60 bata sani ba. Kuma ba tai mamakin jin cewa Binta tayi ciki ba. Kuma abinda nake so da kai kar ka kuskura kace zaka rabu da ita in ma tana iskancin dai to ya rage nata, duk tsuntsun da kaja ruwa shi ruwa kan doka, kuma wannan ya isheta ishara, in kace wata zaka nema ma to duk dai gautar jace, matsalar wahalar auren nan saboda tsarabe tsarabe da kage kage da sai nayl irin na wane suke hana auren, rashin auren kuma ya haifar da zinace zinacen, Allah ya sauwake", Taja yace "Amin", sukon tun daga nan dai Rufa'i yai ta ko karin sasanta tsakanin Taja da Zalita har ya ci našara. Shikuma ya sharar da batun Binta, kai koma tunanin ta baya yi. Kuma ya sanar da mahaifiyarsa labarin itama tai bakin ciki da wannan al'amari. Shi kuma Rufai ya kudiri aniya ba zai sake neman aure a wannan gari nasu ba, sai ko in kar yai auren kwata kwata. Bisa wannan ra'ayi ko niya ta Rufa'i sai Taja yai ta bashi shawara da Nasiha kan cewa ya dau hakuri da duk abinda ya faru saboda yárda da kaddara wani rukuni ne na imani.to duk da haka dai kuttum tunanin Rufa'i Allah ya kawo hanyar da zai bar garinma, kullum yai sallah bayan yayi addu'a ga iyayensa, addu'arsa, wani alheri yazo ga fiddashi daga garin, kuma ya sami wata matar a can ta gari. Allah maji roko a karshe dai wannan kamfani da aka kai takardunsa suka nemi da yaje ganawa linterview). Bayan kamar wata biyu sai ga takardar daukan aiki da albashi mai tsoka. lyayen sa, 'yan'uwa da abokan arziki sukai ta masa murnar samun aiki ya tafi. A karshe dai a can Rufa'i yai aurensa da wata mai suna Sa'a cikinsa'a. 61 TSOKACI Kai! kai! a'a kada kai haka mana ai rayuwa ta yau hakuri akeyi da ita....... Rufa'i sai bai kai marin ba ya kyale. To amma ina ita Zainab bata daina zagin saba....... Nan da nan bai san lokacin da ya wanke ta da mari gaba da baya ba. Rannan Mallam Ibrahim suna kwance a daki da matarsa Daso sai ya tuntube ta akan yaya ta gani akan ya aurar wa dan Alhaji Mai Wake Zainab wato Rufa'i.? To shi dai Rufa'i sai ya shiga cikin wata irin dimuwa ta me ya kamata yayi a wannan hali na raguwarsa. Shiko Dious' shine suke jin mai basu abin da suke so na duniya na daga Arziki, sarauta, shugabanci, ilmi, farin jini, kwarjini, da dai duk irin abinda suke da niyya a zuciyar kowannen su 'yan kungiyar. ...Shiga kungiyar sai an sadaukar da wani abu da mutum yafi so fiye da kome. Kamar Uba, Uwa, da ko kai ko kuma mata. α a U li C C ג 1 62 ב 느 FASSARAR YAREN DA KUNGIYAR ASIRI TA KU KLUX KLAN KE Y Ilamor Hora Dunga/Dene Dia Dia Caida Bajo Hurra Good DiousDious Kada boka centro palour Kamar Sallama ce Wanene? Inkiya ce Barka dai Ku shigo Barka da zuwa da kyau diyos Sunan babban abinda suke wa biyayya - (jagoransu) Kada tenermala vestido piernaless Kowa ya shigo ciki falon shiri. Vestido blanco piernaless figuras difanto Mezclar bloo de vinor Vinor Kada Vra Vaso Alegrar! Agua Nor kada alma kambiar Diabla Lete cualquira cengeri Kowa ya canza kaya rabi da rabi Fararen kaya da takalmi daya, kuma mu dauka muma mace. Ku gauraya jininku da vinor Ruwan jiri (kamar giyace rin ta wiski) Kowa ya dauki kofi Hada kofi da na dan uwanka ana shewa in za'a sha wani abiu (turawane kanyi) wato fos. Yanzu kowa ya zama dodo (abin tsoro) a iya wake gaba daya, kada comida willow hehe, kada Agua ra baber hehe'-'Kowa yaci tsutsarsa da farin ciki, kowa ya sha abinshan sa da farin ciki (waka ce) Lete praya wisho Ciego - ma iya addu'a ido rufe (ta abin da muke so) Secre Buenos A bayar abin sadaka (cikin addu'ar) kenan Madre - uwa, Los - da, Marido - mata, hamono - aboki hijo - uba 63 Kada nadar gymnasia domir - kowa ya makale (kamar jemage) ayi barci (barcin fita shan jini). A mino Vuelo lo cielo willow - Ruhin (kurwa) ya fita zuwa duniyar jini Vueta mundo - Mu koma Despido comrades ir Diu Diu onoinly da tsutsa Abokai mu watse sai wata rana Hankali da Albasa fa. Mu hadu a littafi na uku In da zamu ji yadda Rufa'i ya kare da sauran rayuwarsa a can Abuja da abokanan aikinsa gami da iyalansa da sauran mutanen da ya saba da su a Abujan. Da yadda a chan garinsu ya share tsakaninsa da su. Dadin dadawa da kuma tsohuwar dangantakarsa da 'yan kungiyar asiri. 69 Printed by:- ADAMU NAMAAJ PRINTING PRESS 173 Ita Waziri Rd., Brd Lane Off Zoo Rd.. P. O. Воx 1395. Kano. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 5 of 5