Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 5
bude da zage zagen hakora, sai shugaba ya sake bada oda da cewa "Animo Vuelo lo Cielo Willow ma'ana ruhinsu yai fiffike zuwa duniyar tsutsa dajini. Shike nan to fa duk wadda aka ambaci sunansa a daren nan to babu shi sai in yana tare da abinda basa so kamar warin albasa, tafarnuwa, ko kayan yaji, ko kuma ambaton Allah da karatun Al-kurani. Sannan basu son dumin wuta da hayaki. Basu kuma son barkono da kamshin zaitun. Haka basu samun wadda yake farke don idonsu bai iya ganin su. Suna ganin mai barci ne don shima ya shiga duniyar linkaya ta mafarki. To anan suke haduwa a tsotse jini, shike nan sai kaga mutum ya wuce ta can ko ya kamu da cuta, sukai ta shan wadda suka samu a wannan dare. To Rufa'i dai gudun mawarsa bata samu ba don sunje gidan Alhajin amma sai kamshin zaitun na carbin da Alhajin yake ja a lokacin ya hana su shiga, gashi kuma yana ta lazimi domin abinda ya saba yi kenan kullum dare. Sannan yana da niyar addu'a ga Rufa'i akan Allah ya juyo zuciyarsa akan kar ya basu kunya. Badon kome ba sai don kawai son da yake masa, ya 42 A dauke shi tamkar shine ya haifeshi don bashi da da. Suka zaga suka zaga amma ina? Rufa'i ya leka ya duba babu alamar Alhaji sai dai ya kan ga kamar ya wulga to sai ya bace to ashe gyangyadi Alhaji yakeyi. Rufa'i kuma baiga iyayensa ba, saboda ba suyi barci ba. Yai fushi, yai wani gunji wadda uban har ya sunkuya zai masa tofi sai da ya tsorita. Mahaifiyarsa sai idonta ya fara hawaye tana ta shafansa, tana al'ajabi. To a ka'idarsu in akai fita uku ba'asha jinin abinda ka bayar ba to za'a shanye naka ne. To Rufa'i anyi fita biyu da shi kenan. Don haka shine yai fushi. Nan da nan sai shugaba yace "vueta mundo"wato mukoma duniya. Nan da nan sai kowa ya bode ido" shugaba ya ce kuma "Despido comrades ir" ma'ana abokai sai wata rana sai an jima kowa sai yace "Good Dious" sai ya fado daga sama, kamarsa kuma ta dawo amma cikin wannan fuskar robar yana ta iyo a sarari kamar tsuntsu, kan hanyar komawa daga yadda suka taso, suna cewa ga junansu, "Diu Diu Onioly" wato hankali da albasa fa! Kowa sai ya koma gurbin da yake fara tasowa, a ko ina ne kuma kome nisa cikin lakaci kadan zai isa. To sai anan ne Rufa'i ya gane Quiranan, shikenan sai suka sauko suka kama hanyar gida, sai take ce masa haba Rufa'i yaya kake magana biyu ne? da, kace babanka, kuma ka dawo cewa abokinshi, wannan ya jawo maka faduwa fa, nan gaba in bamu kama ba kaga zamu rabu da kai kenan, sai ya ce ba kome zamu kama, Quirana tace wa din? Sai yace Usamatu, nan ma sai uban yaji an ambaci Usamatu, sai yace, "Rufa'i! Rufa'i!!" ya girgizashi sai akai sa'a Rufa'i ya dawo sai ya tashi firgigi sai yaga mahaifinsa a tsaye a kansa da carbi, uwarsa kuma tana zaune a bisa kujera tana gyangyadi, sai ya tsorita, zuciyarsa ta yanke, idanuwansa sunyi jazur, sai uban yace 'yaya ka kara ji? uwar tace dan nan ka bamu tsoro. Sannu, yace "sannu". 43 KASHI NA TAKWAS Anan ne dai Rufa'i ya basu labarin irin halinda yake ciki tun daga farko har karshe. Uban yai ta mamakin irin wannan al'amari uwar ma ta tambayi ko menene kuma kungiyar asiri. Dukkaninsu suka la'anci irin wannan ta'ada. A ka'idar wannan kungiya ta su Rufa'i kuwa ba'a fada ma wani ko nuna alamar al'amuran kungiyar, in kuma kayi daya daga ciki to a bakin ranka ne. To sai gashi Rufa'i dangane da irin tambayoyi irin na hikima da takurawa da mahaifinsa ya masa shine bai san lokacin da ya fede biri har wutsiyarba. Saboda uban ya tsorita kan cewa in mayu ne suka kamashi kamar yadda uwar tace, to yaya zai rinka kiran Alhaji Usamatu? bayan haka kuma in cuta ce ai jikinsa babu zazzabi, in kuma kwaya ya sha yaya haka farat zai mike, kuma cikin hankalinsa? To wannan shi ya baiwa uban damar sai ya tsaya ya bincike shi, nan ne sukai tayi har akai assalatu ya tafi masallaci. To uwar ma ta gamsu da taji yadda abin yake sai ta tuna cewa akwai lokacin da yaci albasa yayi amai saboda haka fur ya hanata yin abinci da albasa. Sannan kuma tana ganin yana kinyin salla akan kari kuma yakan yi wani yare jifa jifa. Da dai abubuwa iri-iri, sukai ta al'ajabin wannan al'amari. Sannan da tunanin hanyar da za'a fito ayi maganin hakan. Rufa'i kuma sai zulumi, me zai faru dashi nan gaba yake yi, tsakaninsa da jama'arsa. Duk abinda daya yayi a ko inane sauran zasu sani, saboda sun sha jinin juna kuma sun zama daya. Cikin daren sha hudu nako wane wata dama suke fita don haka sai wani watan zasu zo mar ke nan. Alhaji dai haka ya kwashe duk wannan labari ya kaiwa Alhaji Usamatu. Shima yai mamaki kuma yai addu'ar Allah ya kawo 44 sauki. To sai dai kuma basu san raayin Rufa'i akan batun auren ba, shi yasa Mallam Ibrahim bai ji ko duriyar su ba. Kuma shima bai tuntube su ba. Wataran da daddare, Alhaji ya kira Rufa'i ya tursa shi kan sai ya yarda da batun auren Zainab, shiko sai ya fito ya bashi labarin tsakaninsa da Quirana da alkawarin da sukayi. Alhaji ya shure wannan magana. Kuma yai masa tankiyar kar ya sake alaka do ita har abada. Kuma in yayi to zasu sa kafar wando guda, yai barazanar zai tsine masa. Rufa'i da ya ga ran uban ya baci sai yace ya yarda. Amma a gaskiya zuciyar sa bata yarda ba. To a daren ne fa Quirana ta zomasa kamar yadda ta saba. Rufa'i dai ga ci ga rashi, yana tuna managar uban kuma yana tuna Quirana, da ya tuna cewa ai kuma yanzu ya zama nama ga sauran 'yan kungiyar sai ya baiyana mata cewa yanzu tayi hakuri don ya canza shawara. Jin haka sai Quirana ranta ya baci ta juya kamar zata tafi sai ta waigo da wata irin mummunar fuskar da Rufa'i bai taba gani ba koda a can duniyarsu ta tsafi. Saboda hancinta da ya zazzabo kai kace liko take furawa, kumatunta kuwa sunyi fulu fulu kamar balobalo, sannan wuya kamar sillen kara; sai katon kai da yafi tulu kuma ba gashi, tace ani ko'? Zaka gani! Kasancewar Rufa'i bai shiga sulke ba irin nasu wato wannan fuska da suke sawa a can duniyar sai ya tsorita. Wannan shi yasa yai lhu mai tsanani, kawai sai ta juya ta tafi. Ihun da Rufa'i yai shi ya tada uwar sai ta fito da sauri ta nufi dakinsa. Dama dakin yana can kusurwar gidan ta barin yamma, kuma an kewaye gaban da 'yar katanga wadda sai an za gaya ta sannan a shiga dakin. Da 'yan shuke shuken fulawa da furaini irinsu biribis, Barbados da ros a gaban dakin. Balki da ta shiga sai 45 ta tarar da shi yana motsi bisa gado tai kira shiru sai ta tabashi sannan ya firgita, zubur ya mike. Uwar tace 'yaya, sai ya gaya mata abinda ya faru. To ashe uban ma yaji fitarta da Ihun sai yazo, sai yace da shi ya karanta Salatin Annabi uku, Inna Lillahi goma sha daya, La'ilaha Illa Lahu goma sha daya sannan ya karanta kula'uzai da qul huwa uku, ya kwanta. Kuma kullum kar ya rabu da karanta wannan abu iya gwargwado, kuma a ko'ina yake. To haka dai Rufa'i yai tayi, kuma sai ya shiga cin tafarnuwa da albasa lokaci, lokaci har ya saba. Zikiri kuwa kamar Liman. Shiko Taja da yaji abinda ya faru da Rufa'i sai yai ta masa Addu'a kuma ya bar abin a cikinsa bai furtawa kowa ba shima. Haka dai har lokaci mai tsawo. Tajan yana matsawa akan suje ido da ido gun Quirana amma Rufa'i yaki. Dangane da yardar Rufa'i akan auren Zainab sai aka sanar da Baban ta Mallam Ibrahim. Shikuma ya bada dama ga Rufa'i akan duk lokacin da yaje zance to ya shiga cikin gidan abinsa. Shiko Alhaji Usamatu tuni har ya fara tunanin gidan da zai bashi a gidajensa dake kusa, to babu, don duk a gefen garin suke, shima kuma Alhaji Mai Wake yana tunanin ko ya gyara masa dakinsa ne koko ya saya masa wani a kusa domin gina wani zai dauki lokaci, kuma ga dukkan alamu Mallam Ibrahim a shirye yake. To akarshe dai suka zantu sai Alhaji Usamatu ya hakura akan Mai wake ya sai gidan. hakanne ta faru, amma sabon gidan da aka saya na da dan nisa da ainihin gidan nasu. Gidane dan karami na maigida daya da matarsa. Domin dakuna biyu ne kawai a hade, ciki da falo. gami da bandaki hade da falo wadda kofarsa ta cikin falon take, sai kuma 'yan zauruka biyu na kicin da dakin ajiya. To amma a kwai fili mai dan fadi wadda za'a'iya gina wasu dakuna guda biyu manya daidai da nada. Akwai fanfo, wuta 46 da kome na kawa, kai harda ma alamar mashukar fulawa kewaye da katanga. Sai kuma irin matarar ruwa (tanki obahed) da akan dora sama da daki domin amfanin cikin gida da sarga irin ta sink da shawa ta wanka. Rufa'i bai san da wannan gida ba, ammam mahaifiyarsa taji cewa an saya masa. Yana nan yana tunanin yadda zai fito wa wannan matsala, ga shawarar Taja dai yaje gun Zainab yai ta zance kawai, yayi yayi dashi suje amma yaki. Ga shawarar uwarsa kuwa ya cigaba da zuwa amma zata san yadda za'a raba abin koda malamai, kuma tana son Binta don shi Rufa'i ya bata labarin Bintar da abinda ya faru tsakaninsu. Rufa'i sai ya dauki ra'ayin uwarsa. Ranar nan da la'asar sai yai tunanin da ya fara zuwa gun Zainab, ita ma ta san kome dama. Tunda uwarta ta gaya mata cewa babanta yace ya nema mata miji sai ta yarda. Harma tace da uwar ai akwai Hadisin da yake cewa bazawara ita ke da Hakkin kanta, budurwa kuma iyayenta. Dadin dadawa kuma dama ta gaji da zaman gida, tana son auren amma Allah bai kawo shi ba. Sannan kuma da taji Rufa'i ne sai ta amince Hani'an ba gardama, kuma sauraron zuwansa takeyi kullum amma shiru. To da yaje sai yaki shiga kamar yadda akai masa izini ya tura yaro. Zainab sai tace yaron yazo yace wai baza ta zoba. Rufa'i da yaji haka sai yai mamaki, yace da yaron yakoma yace inji dai Rufa'i ne, sai ta aiko da cewa ai dama ta sani, bata da lokaci ne kawai, Rufa'i yai shiru yace to! Wato wannan taji nace bana sontane take so ta min walakanci, ko kuma taji labarin da na shiga kungiyar asirine. Haka dai yana tunani, sai ya ce "kai bata isa ba" sai ta soni sai ya kada kai ya tafi. bayan kwana biyu ya koma Zainab dai bata canza 47 ra'ayinta ba, ta bada amsa irinta rannan. Rufa'i fa sai hankali ya tashi, ya koma gida sai tunanin wannan al'amari yake yi. Yanzu ya manta da itane? to amma ai taci nasara akansa kenan, to yaya zasu hadu ya ga karyarta yana ta tunani. Duk da haka bai sanar da kowa abinda ke faruwa ba. Duk kowa na ganin cewa yana zuwa suna hira sosai da Zainab. Rannan yaje unguwar su Taja gun da suke zama sai ga Zainab da wasu abokanta sun wuce, Rufa'i ya ganta amma ita bata ganshiba saboda yana daga karshen kudune a zaune. Shiko Taja bai santa bama sosai bare ya ganeta. Suna nan har kusan magrib Rufa'i na cewa zai tafi gida Taja na cewa ya tsaya suyi sallah tukun, sai ga can Zainab ta bullo ita daya, Rufa'i da ya hangota sai yace da Taja ka ganta nan tafe"Taja yace wace fa?" Rufa'i yace "Zainab din mana 'yar yawa" Taja sai ya sake hangota yace kodai dan 'yawa, ai wallahi wannan in kabarta kabar banza, hadaddiyar dem irin wannan, ai ban san haka take ba. Don Allah kayi mata magana', Rufa'i yace haba, ai bazata sauraren ba don naje sau biyu ta bonsa ni. Taja yace To wallahi ni zammata". Sauran abokansu sai dariya suke tayi, suna dan hangen Zainab tana tafowa, Rufa'i zuciyarsa tana ta bugawa. To ita ko kafin ta iso ta fahimci akwai wani abu don taga kallon yai yawa, har ma tai sassarfa. Yuu da tayi da ido sai taga Rufa'i sukai cul da cul sai ta kauda kai ta wuce. Dama ta can gefen hanya take. Taja sai ya tashi ya bita Rufa'i ya biyoshi, yace Hajiya Zainab"kamar dama tasan suna zuwa sai tace "a'a, Zainab din dai. Sai ta tsaya. Su kuma sauran duk suna ta kallonsu. Taja yace ai im ba busa sai a daga hannu", Zainab tace ana me? Rufa'i sai ya karbe, yace ana zumunci, mutunci da kuma......"sai tace kuma me? Fadi man muji, sai yace soyanci" Zainab tace "banga ne ba soyanci? 48 wani yare ne? ko karatu? Sai yace eh yare ne na soyayya kuma karatu ne na biyayya? Sai tace, iunda yaren masoyane ai sai a gayawa masoya? Anan Taja sai yace Hakika ai masoyanne yan zuma suke yarawa?"Zainab sai tace uhm makiya dai", Rufa'i sai yace sai dai inke ce mai ki ni masoyine! Sai tace na wa"? Rufa'i yace naki' Taja sai ya ce "kwarai tunda ya furta, Zainab tace to ai ni banga alama ba', Rufa'i yace, eh! to! baki zoba shiyasa aida kingani kuma koda yau zaki zo in rnunje, to zaki ga alamar? Zainab tai murmushi a ranta tana cewa ha! kace ba kai ba, da saura ma tukun! Sai tace Allah ya kaimu", suka ce amin'. Ta kama hanya zata tafi sai ta juyo tace da Taja "Mallam baka gayamin sunanka ba, Rufa'i sai yai farat yace eh don Allah kiyi hakuri, ban gabatar miki da shi ba sunansa Tajuddeen Tijani ko kuma T.T" sai tai murmushi tace sai an jima ta tafi. Su Rufa'i aka tafa hannu ana dariya tuni kuma har anyi sallar Magrib suna hira. Sukai sallah suka ci abinci ya dan afa tafarnuwa, kamar yadda ya saba. Suka nufo unguwarsu Rufa'i tare. 49 KASHI NA TARA Anan kofar gidansu Zainab, Rufa'i da Taja suna jiranta ta fito, Taja sai yace da Rufa'i "ah! kaga da muntafo da katin nan, koda yake ma ya wuce, kasan su Binta ma sai washe garin Valentin din na basu?" Rufa'i sai yace "kai kuwa! ina ruwan kifi da rigar ruwa? me ya hada eli da valentin? Ta san maka amfanin katin? Taja yace "ai wai dan tukwici ne", Suna cikin haka sai ga Zainab ta fito tare daʼyar yarinya, kafin ta nufo su sai kamshin turaren da ta sa ya bugesu, Taja sai yace "uhm! lalle!" Zainab dai sanin cewa zatayi baki, hatta kayan da tasa da la'asar ta canzasu. Ta sako irin duguwar rigarnan mai suna Hijab da kuma farin gyale ta yafashi a kafardarta ya rufe kirjinta. Dan kwalinta kuwa tayi masa daurin kimar wato hannayensa ta dauresu ta karkashin habarta. Sai ta nufosu, tai sallama suka amsa. Ta zauna. Bayan duk tabi su da daddaya sun gaisa sai akai dan shiru na dan lokaci. Can Rufa'i sai yace, "mun cika alkawari?" Zainab sai ta amsa masa da cewa kadan ba!" Taja sai yace "ea! Zainab yaya kadan? Zainab tace "ah! kabarni da shi mana", Rufa'i sai yace "to ya barmun mana, nidai nasan alkawari na na cikashi, sai dai kece ma baki cikashi sosai ba". Zainab sai tace "to naji abar wannan zancen". Taja sai yace to wane zancen za'ayidaya fi wannan din. Haka dai sukaita zancen shega kai kaсе calikawa ne irin na fin din Indiya. Ba suyi wani zancen soyayyaba har dare yayi sukai sallama. Rufa'i yai mata kyauta, sai taki karba, yayi, yayi taki, sai ya dan baiwa yarinyar da ta rako ta. Yayin da Rufa'i ya dan yi tattaki ga Taja sai suka tsaya suna tattaunawa, Taja yace "na tabbatar wannan yarinyar tana sonka kwarai", Rufa'i yace "ai nima yanzu naji kuma gaba daya tana shiga raina wallahi". Taja yace "ai kayi 50 스 sa'ar mata don agaskiya bata da makusa. Ga kyau, ga hali ga ilmi to kuma me yarage? Arziki kuwa na Allah ne". Nan dai suka rabu kowa ya tafi gida. Haka nan dai Rufa'i yai ta zuwa gidan su Zainab suna hira wata rana da Taja wata rana shi kaďai ko kuma da sauran abokansa dake unguwarsu, har dai aka aiko gidansu Rufa'ї cewa ambashi Zainab, amma za'asa ranar biki nan gaba, saboda shi Mallam Ibrahim ya sanar da Alhaji Usamatu cewa kar su aiko kome da ake yi. Bukata dai son yaro da yarinya, to ga dukkan alamu sun shirya. Shiya sa aka aiko cewa am bashi ita. Ita ko Quirana, ganin Rufa'i ya shiga mata duhu saboda tsabar tasbihi da Hailala da zikiri da yakeyi ga kuma dan karen cin albasa da tafarnuwa da shike dama da niyar hakan yake yi sai ta hakura. Suma 'yan uwanta sun rasa hanyar da zasu fito masa, saboda foton da ke manne a dakinsa ya cire ya kona, dama shine kamar shaidar mambarsu., sannan kuma a zahiri ya kaurace mata baya zuwa gidansu, dake unguwar 'yan sanda. Ita ma kuma sai ta fara tsorita dashi. Allah gatan kowa. Kai in gajarce maka labari Quirana dai barin garin Fatara tayi kwata-kwata, saboda tasan abin zai komo kanta tunda itace musabbabin shigar Rufa'i wannan kungiya. Haka ta kare, domin kashet. za suyi. Rabuwar Rufa'i da muguwa Quirana kenan. Labari ya bazu cewa Rufa'i zai auri Zainab, har ya kai kunnen, Binta wadda ita bata san ma akwai wata mace da Rufa'i yake kulawa ba. Da taji wannan labari tayi bakin ciki matua, saboda burinta bai cika ba. Dama haka yake duk wadda yake da mungun nufi ga wani, koda Allah ya bashi sa'a, a karshe 51 sai ya koma kansa. Ko kuma Allah ya kiyaye wadda aka nufa din. To ita Binta dai ashe juna ne da ita. Tun lokacin da ta tabbatar ta samu ciki sai ta gayawa shi Sekiap cewa ga halin da take ciki. Dama tun lokacin da suka sadu a 'me and you photo studio yayin da taje daukan photo lokacin sallar idi ya sa aka dauketa kyauta, kai har ma ya bata damar duk lokacin da taken son dauka kawai tazo ta dauka, a matsayinsa na abokin mai daukan photon. To shi Sekiap wadda akafi sani da eskep mutumin jihar Bayelsa ne dan yaren tsigira. Dama Binta kan je gidansa. Ta fura zuwa gidan ne ta sanadin karbowa photo da ta dauka, shi kuma ya karba da nufin in tazo a turata gidan nasa. Tun daga wannan ranar eskep ya san Binta 'ya mace, a takaice ma dai shine ya kawar mata da budurci. Ya aza harsashi bata mata rayuwa. Kuda wajen kwadayi akan mutu. Haka Binta ta dinga satan jiki tana zuwa domin ta samo irin abinda yake bata na bajinta. Da ta gaya masa nefa cewa tayi ciki sai yai mata alkawarin zai aureta, ina! kan kace me, ya tattara'yan kayan gyaransa ya gudu. Dama bakanike ne na babur. To daga nan ne fa Binta ta rasa makama, har taci karo da Rufa'i. Ta so ta rufeshi. Mahaifiyarta ta sani amma uban bai san kome a game da maganar ba. Zaliha ma tasan kome amma saboda kunya, kawaici da zumunci irin na mata sai ta bakam kuma ake hada baki da ita. Binta dai bakin cikin ta, asirinta sai ya tonu, tunda shi kadai din da take gadara dashi gashi ya kubuce A duk lokacin da tazo kwanciya sai tayi kuka da hawaye tana mai nada mar abinda tayi. Kuma tana ta sake saken hanyar da zata bi. Ta gudu ne! kashe kanta zatayi? a'a zubarwane? duk abinda ta tuna sai taga ai tamkar ta tona asirine da kanta. 52 Allahu Akbar, Allah mai yin yadda yaso, har an sanya ranar bikin Zainab da Rufa'i, duk wadda abin ya shafeshi na dokin lokacin yazo, shi kansa Rufa'i yama fi kowa dokin abin, saboda dunbin son daya kwarara masa na Zainab cikin zuciyarsa. Kash, abinda Allah ya kaddara hakika ya kaddaru, cikin lokaci kankane sai masifar anobar wata cuta amai da gudawa mai suna "Gastro entritis' ta barke a yankin gaba daya. Duk wadda ya kamu in har ya wuce kwana uku to ana tsammata masa tashi. Mutane da dama, manya da yara, maza da mata an rabu dasu. Allah Sarkin kudura, Rufa'i da aka gaya masa cewa Zainab bata da lafiya, waiyo, yadda kasan an harbo masa kibyar da aka zaro a wuta ta soki zuciyarsa. Tunda ya kamo hanya ya nufo gidansu Zainab bai san da wa yake kiliya ba, har ya kutsa kansa cikin gidan. Shigarsa na farko kenan gidan sai ya rasa inda zai nufa. Daso sai tace dashi "shigo gata a daki", sai ya shiga bayan sun gaisa, da uwar, ya ga Zainab, ya kura mata ido sai ta bude ido ta ganshi sukai ido hudu sai tai murmushi ta yunkuro zata dago ina! babu karfi duk ta zabge ta rame cikin awoyin da basu kai ashirin ba. Rufa'i dai ya rasa ma me zai ce. Idanuwan sa sun ciko da hawaye saboda yanayin da ya ganta. Zainab tace da shi da sauki dai karka damu, to anan ne fa yai mata magana da cewa "ai asibiti ya kamata aje" sai Daso tana daga waje tace, ai anje, Mallam ya sayo mata maganin kuma yai mata allura. Yanzu ma shi muke jira ya dawo don a saka mata karin ruwa." Taci gaba da cewa, "ai wannan al'amari sai dai mu barwa Allah, domin asibitin ma cike yake da bayin Allah. Kuma ga babu maganin sai dai saye." Rufa'i yace "sai a dinga bata ko dan kunu ma", sai Zainab tace "bazan sha ba". Daso itama tace "ai ko ambata to yanzu zai fito". Sai ta fashe ta kuka don tausayi. Haba zuciyar Rufa'i sai ta kara bugawa idonsa yana zubda hawaye, sai yai 53 ta maza yace gwaggo hakuri zakiyi Allah zai sauwake mata. Suna haka sai ga Mallam Ibrahim sun shigo da wani saurayi da fararen kaya. Ga alamu nas ne, da yaga tana kuka sai yai turus yace "ke ni halinki kenan, to ame kike yin kukan? inma mutuwane, kullu natsin zayikatil maut ko? Kawai ki mata addu'ar neman sauki, in ko ciwon ajali ne ki yafeta, Allah ya yafeta, amma kya rinka kuka wadda ma bashi da kyau". Wannan nas shima yace "ai sai hakuri, Allah ya sauwake mata" duk suka ce amin. Mallam Ibrahim suka gaisa da Rufa'i sai ya shige daki nas ya bishi. Shiko Rufa'i ya ce zai je gida ya gaya musu, ya fita. Daya isa gidansu magriba tayi, sai yai alwala yai sallah, yai ta yiwa Zainab addu'ar neman sauki, sannan ya dauko abincinsa yana ci sai yana tunani ko ya gayawa Balki ne. ko da yake ma ita Balki bata cika son Zainab ba sosai, haka dai ya samu, ya sanar da Balki, sai tai alkawarin in Alhaji ya shigo zata tambayeshi taje ta ganta. haka kuwa akayi. Shiko cikin daren ya tafi gidansu Taja ya tarar da shi da wasu abokansu guda uku sunzo gunsa. Taja yace kaga ango sha kanshi, Ruta'i sai yace yanzu kam sha wari ne, ai Zainab ba lafiya Taja sai yace subhanallahi. meya sameta? Rufa'i sai yace ah banda Gastro! sauran sai suka ce cab! Allah ya sauwake mata, duk suka ce amin. Taja sai yace "ai sai ku tashi muje mu ganta, a wane daki suke?" Rufa'i sai ya ce "a'a, suna gida, ai kasan aľ'amarin wani daga cikinsu yace "kai abinfa ya zama azimin sai dai addu'a don ana matukar yin wannan cutar". Na biyun sai yace "babban abin ma mutuwa", Rufa'i yace "ai nima yanzu 54 duk hankalina wallahi ya tashi ganin Zainab cikin irin halinda take, duk fa ta zagbe Mallam". Suna al'ajabin abin har suka iso kantin 'Jibo stores,' Rufa'i ya shiga ya sayo Treetop da Ribena, da kuma gwangwanayen Madara da sauransu, suka nufi gidansu Zainab. Duk suka shiga gidan. Tuni har Mahalfiyarsa Balki itama, tazo nan dai sukai carko carko shiru kowa na alĽajabin wannan abu. Suka gaisa sai Rufa'i ya mika kayan. Zainab da taji muryar Rufa'i sai tai yunkuri zata tashi sai uwartace a'a kiyi hakuri ki kwanta, Zainab ga dukkan alamu tana son ta kira Rufa'i amma bakin ba zai iyaba sai ta bude baki amma murya bata fito ba. Ta daga hannu ina' sai ya koma. Da Balki ta lura da haka sai ta kiransa dama suna daga waje ne, sai ya shigo cikin dakin. Dakin na da fadi kuma falone 'yan kayan dake ciki ba wasu masu yawa bane dama. Kuma an tare su gefe guda. Daso na rike da hannun Zainab da aka daura mata Dirip wato karin ruwa a jiki, shi kuma Rufa'i sai ya tsuguna kusa da Zainab, idonta yana rufe. Daso sai tace da Zainab gashi nan yazo, Zainab dai bata bude ido ba. Can sai ta bude ta dan waigo taga Rufa'i sai ta sake yi mishi murmushi, Rufa'i yace da ita sannu Zainab, Allah ya sauwake miki. Tai kamar ta dago amma ina babu, ta bude baki ba murya, sai ta dan gyada kai a hankali Rufa'i dai ta maza yake yi, amma abin kamar yayi kuka ne. Zainab ta dan matso da hannunta don ta dafa jikinsa amma hannun bai iso ba da Rufa'i ya lura sai ya miko hannun sa ya dora akan nata. Taba jikinta na biyu kenan tun marinda yai mata tana yarinya. Anan nefa ya tuna irin abinda ya faru da su a wancan lokaci, arashi, ita ma mahaifiyarsa da taganshi yayi zugum a gaban Zainab sai tana tunanın abinda ya faru tsakanin iyayen akansu Rufa'i da Zainab. 55 Shiru ne dan loakci Zainab sai ta janye hannun ta, ta kuma yi murmushi ga Rufa'i shima anan ne yai mata murmushi sai ta rufe idonta. Mahaifiyarshi tace dashi ai sai ka tashi kutafi dare yayi. Sukai sallama, suka tafi. Balki tana nan wannan suzo, su tafi wancan suzo har wajen karfe sha biyu na dare bata tafiba tana tausayawa Zainab da kuma taimakawa Daso

Chapter 4 of 5