An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
IDO UKIL..
Suleiman El-Ahmad Azare
SABATARWA
Wannan rubutu ba shagube, habaic: koko ba'o ga wan, wata, ko wata kungiya bane, ko kuma tarhin rayuwar wani, wata ko wata kungıya bane. Kage ne kawai. Duk wanı abu da yai daidai da na wani, wata ko wata kungiya to Arashi m
kawai. Ance kwa Arachi na rariya mai raba Auren wawa.
Hakkin Mallaka (H) Suieiman El-Ahmad996
An fara bugawa(19961
SADAUKARWA
Na sadaukar da wannan iittafi ga dukkan wadda ya
karantashi
DOKA
Ba'a yarda wani ko wasu su juya wannan littati, ko wan
bangarensa zuwa wani yare ko gyarashi ta ko wace hanye
ba tare da rubucecan izini daga marubucin littalin ba; dor
gudun batanci.
2
KASHI NA DAYA
"Kai! Kai! a'a, kada kai haka mana, ai rayuwa ta yau hakuri
akeyi da ita, inji Malam Mahe yake gayawa Rufai. Shi Malam
Mahe Malami ne a unguwar su Rufa'i, ana ce da ita kwana
bakwai, yana koyadda karatun allo. Shi kuwa Rufa'i dan gidan
Alhaji Mai Wake ne. Rufa'i sai bai kai marin ba, ya kyale. To
amma ina!, ita Zainab bata daina zagin sa ba. To shi Rufa'i
mai zuciya ne irin ta ubansa. Nan da nan bai san lokacin da
ya wanke ta da mari gaba da baya ba. Malam Mahe ya tsaya
yana ganinsa irin gani na mamaki. Zai ce wani abu sai dai ya danne. Tuni sai Rufa'i ya kada baki ya ce da Malam Mahe,
"zuciyar tawa ce ba mai jure irin wadannan tsawrin idon bace Malam, ka kyale mu". Tuni ita kuma Zainab sai taruga da gudu gida zata kira Muntaqa yayanta. Rufa'i sai ya tafi abinsa.
To tsakanin gun da suke da gidan su ba nisa sosai. Don a
unguwar tsakuwa suke.
Rufa'i yashiga gidansu har ma ya fito sai Zainab tare da
Muntaqa sun iso kofar Malam Mahe. Rufa'i, da ya hango su
sai ya nufo su, sai Zainab tace gashi can'! Sai suma suka nufi kansa. Isarsu ke da wuya sai Muntaqa yakai masa duka ba
magana. Sai Rufa'i ya kare da hannu. Ita ma Zainab sai takai
masa sura tana danna masa ashar. To ba nesa suke da gidan Malam Mahe ba, sai yaji su yafito da gaggawa yana
tsawa "kai! wai ni wannan wadanne irin yarane?" Kafin ya iso
har sun kai Rufa'i kasa suna ta duka. Malam Mahe yazo ya
kama Muntaqa yarike yana cewa ku tsaya, menene ya hada kune"? Ya juya kan Zainab, ke dai wannan yarinya baki da kirki. Tun dazu har yanzu baki hakuraba"? Shi kuwa Muntaqa
1
sai kokarin kwacewa yake yi, yana cewa "to ni Malam ka sake
ni, ina ruwan ka ne"? to ina ruwan ka". Suna cikin haka sai ga
Da'ado tazo wucewa sai ta tsaya tace "wanake gani kamar
Zainab? A'a! wannan ba Muntaqa bane? Me ya faru? Sai ta
waiga tana tambayar Malam Mahe "bawan Allah me ya
hada ku?" Malam Mahe ya saki Muntaqa yace "baiwar Allah
ni ma haka na gansu suna ta yi tun dazu shi wannan sun fara
da wannan yarinya, ya nuna Rufai, na rabasu, sai kuma naga
sun dawo da wannan saurayin shi ne nazo kuma nake sake
rabasu. Shi kuma harma yana neman yamin rashin albarka",
yacigaba da cewa, yanzu da kuka tarumar kuna jin in kukai
masa rauni uban sa zai yarda? Nan da nan sai Da'ado
kishiyar uwar su Zainab ta yi farat ta ce "wai shi wannan din
dan waye ne?" Shi kuma waye uban nasa?" Malam Mahe ya
amsa mata cewa "ai ba abin fada bane, yaran Alhaji Mai
Wake ne. Nan da nan Da'ado tace "wane mai waken? inji dai
ba wancan matsiyacin mutumin ba"? Ah! akwai wani bayan
shi ne? Inji Malam. Da'ado tace da Zainab ta kama hanya
suje gida ta kara da cewa "kai ma Muntaqa zamu tafi ai uban
nasa ma sai ya kwammace kida da karatu". Malam dai bai ce
uffan ba kawai dai ya tsaya yana kallon su. Kazalika shima
Rufai baice kome ba. Malam dai bai san musabbabin abin
ba. Shi kuwa Rufai bai gaya masaba. Sai dai kawai zuciyar sa
tana ta tafasa kamar tafashe, don bakin cikin ga fada amma
yafi karfin sa.
Isar su Da'ado gida kenan sai ta kwalla wa uwar su Zainab
kira"yaya!, yaya!" Ita kuwa Daso tana daki ta dan kishingida
tana futawa. Nan da nan sai ta zabura ta fito da sauri.
"Da'ado latiya? ko har wunin ya kare kenan"? taci gaba da
cewa yaya nagan ku tare da wadannan? Lafiya? Nan da nan
sai Muntaqa yai subut da baka yace "wai wani ne ya duka
2
Zainab shine muka je....." Uwar sai ta harare shi cikin fushi
tace "kuma kuka yi me da kukaje? kudai da baku son zaman
lafiya. Ke din menene ya hada ki da wanin? Wanene shi? Dan
gidan waye?" Da'ado tace mata "dan gidan Mai Wake ne", sai
Daso tace "inji dai ba Alhaji Mai Wake na kwana bakwai bа?"
Sai Zainab tare da Da'ado gaba daya suka amsa "shi fa".
Da'ado ta tambayi Zainab ainihin musabbain abin. Zainab
sao ta fara yin kwalla idonta duk suka ciko da hawaye tace
fatsa masa "wai don yana wuce wa naje tsallake kwata sai na
sai yace wai sai na wanke masa. Shine nace masa sannu sai
yace ko ubana ma bai isa ba. Shine nima na ce masa ko
ubansa bai isa na wanke masa ba. Shine sai na kama hanya
zan tafi sai ya biyo ni har wajen gidan Malamin nan yana
zagina. Shine nima na zageshi yazo zai mareni sai Malamin
nan ya hana shi, shi kuma yaki har yamareni. Shine na zo na
kira yaya". Banda marin ba abin da yayi miki? "inji Da'ado".
Wai waya war da uwar tayi sai taga babu sarkar Zainab a
wuyanta, ta tambayeta ina sarkar ki?" Sai Zainab ta kai hannu
wuyanta, sarka kuwa tace daukeni inda kika ajiye ni. Haba
Zainab ai sai ido ya fara zubda hawaye sosai, ta fara kuka
tana i'ina "ai..... ai.... shine ya cire min" Muntaqa kuwa tun da
yayi shiru saboda hararan uwar bai yi magana ba. Kuma
yace bazai komaba yayin da Da'ado tace yakoma gidansu
Rufa'i ya nemo sarkar, uwar kuwa wato Daso sai tace a'a
subari uban yazo. Muntaqa sai ya fice abinsa.
Shi kuma Rufa'i da Malam yaraba su sai ya tafi abinsa shima.
Amma bai nufi yaje gidansuba sai yabi wani wuri. Shikuma Malam Mahe yajuya zai tafi sai ya hangi sarkar wuya a kar,
sai ya zaci dai ta Zainab ce, saboda haka yaje ya dauka,
sannan ya kwallawa Rufa'i kira "Kai! yaro! zo ga sarkar nan
3
dama baiyi nisaba sai ya juyo yagani, yace "ba tawa bace".
Sai kawai ya juya ya tafi. Malam ya tsaya ya danyi shiru sai kawai ya shiga gida yana cewa ai masu ita sabiyo sawu.
Gari na waye wa Rufai ya tashi hannun sa a kumbure daman
yasan yaji ciwo to amma bai san cewa har abin yakai ga gurdewa ba. To ashe ya gurde. Ya zo dakin uwarsa Balki
yana shan kwakko dama su agidan abin karyawar su sukeyi
ba su saya sai dai kuma randa aka gadama a dan sayo
kosai. To uwar taga yatsansa a kumbure. To shi Rufai dai shi
kadai ne gareta, ya kai shekara kamar goma sha biyar amma
ana renonsa kamar jariri. Nan da nan sai tace me yasame ka
anan? na ganshi a kumbure yace da ita buguwa yayi", tace
"bana son karya. Kai dai in ma faduwar kayi a gun kwallan ku
ne ko kuma kukayi fada. Kagayamin gaskiya. Waya jima ka?"
Sai Rufai yace da ita wasu ne suka dukashi jiya. Tace "mekayi
musu zasu dukaka har suji maka ciwo haka?" Tashi muje gun
Alhaji" Yaya za'a jima ka ciwo haka kawai?" Suka fita daga
dakin ta sai turakar Alhaji Mai Wake. Tai sallama tace, "Alhaji
kaduba abinda akayi wa wannan dan jaririn namu". Uban
yace da ita "kedai Balki baki rabuwa da shashanci. Yaro yana
girma kina dada shagwabantar dashi. Menene ya same shi?
"Sai ta kama hannun Rufai ta nuna wa uban; sai yace "ina kaji
wannan ciwon. Rufai yace "nima ban san suba" Sai uban ya
bata fuska. "Ina cewa ina kaji kana cemin baka san suba,
suwaye?" Nan da nan sai Balki tace "anya dai wasu yara ne
sukai ta dukansa dai 'yan maza", su nawa ne? a'i na ne"? Ta
sunkuya tana tambayarsa, sai shi kuma Rufai yace "a'a wata
yarinya ce da wanta. Sarkar ta ma tana gun Malam". "Wane
Malam?" Inji Uban Rufai yace "Malam na can" Uban yace
"Malam Mahe?" sai uwar tace hala shi ne. Rufai yace "eh! shi".
Uwar tace me ya hada Mallam da sarkar ta? Rufa'i ya amsa
4
"lokacin da muke fadan ne sarkar ta fadi. Su kuma sai
matarnan ta wajen gidan Babata Sala ta tafida su gida harmа
tana zagin Baba. "Wane baban"? Inji uwar. "Babana", Rufai ya
amsa. Wai shin wadanne irin mutane ne wadannan? Kace
tawajen gidan Sala? Kodai gidan Malam Ibrahim Malamin
Dabbobi? Don nan ne da akwai yaro yadan fika da kuma
yarinya, ta kan kawo, talla nan; to wallahi Alhaji, kasan abinda
kayi akan wannan, kai din ma ai zasu duka ashe, in zasu
samu sarari, har da zagi? To wallahi in bazaka ba, ni zan rufe
kai na in tafi", yace "naji"! "A ina ne sarkar; a gun Malam"? "ai
zasu biyo sawu". Inji uban.
A can gidan su Zainab kuwa, Da'ado tariga ta gaya wa uban
su Zainab, wato Malam Ibrahim tun jiya da la'asar bayan
yadawo daga gun aiki. Dama yana shirin yazo neman sarka
da kuma dogaciya ga Rufai kada yasake shiga harkar
'ya'yansa. To shi dai Malam Ibrahim Allah yayi shi mai hakuri.
A saboda haka ya riga yazama (mijin Hajiya) wato marar iko a
gidansa, sai abinda sukace. Ita Daso bamai magana ce
kamar Da'ado ba. To Da'ado dai a takaice ta sa mai gida ya
tafi fada. Ya ta fo yazo daf da gidan Malam Mahe, Rufai can
shima uwarta turoshi yazo ya karbi sarkar saboda in Masu ita
sunzo sai suje can asan abinda za'ayi. Rufai ya iso sai Malam
Ibrahim ya kirashi dukan su ba wanda yasan wani a ciki, sai
Rufai yazo ya tsaya agunsa sai yace yaje yayi masa magana
da wani Malami a nan gidan, ai nan ne gidansa ko"? inji shi
Malam Ibrahim, sai Rufai yace eh! nan ne gidan Malami, Rufai
da ya shiga sai yai sallama Malam ya fito a cikin daki sai Rufai
yace dashi masu sarka ne sunje gidanmu shine akace in zo in
karba. Sai Malam yace da matar ke miko min wannan
sarkar akan buzun nan sai ta dauko ta bashi sai ya mika wa
Rufai, sai Rufai ya karba yace masa anayi maka kuma
5
lafiya kabiyo mun yaro? Menene yashiga tsakanin ka da yarona?
A'a, tsaya mana a gaya maKasassalar zance". Inji Malam Ibrahim
yaci gaba "ai biyo shin da nayi ba wai dukansa zanyi ko wani abu
ba, sarka ce ta 'yata a gunsa yaje wurin wancan Malamin ya karbo
to nima na biyo sawun sarkar ne to amma sai kawai naga yaje ya
karba.
To na kirashi a kan ya ban sai ya rufa a guje. Sai na biyo shi,
to kaji. Saboda haka koda yake tare sukai fada da yarinyar
amma meyasa zai dauki sarkarta. A kawo mun sarkar ni
kawai ita nazo karba". Alhaji dai da a fusace yake, to shirun
da yayi sai ya sauko, sai yace dashi to ai ba haka ba menene
dalilin da zai sa su yaranku zasu taru su duka shi. Ai dama ina
son in sameka inji dalili". "To banda kai ma wa zai biye fadan
yara"? Wani abinsu ya hadasu wanda bai kai ya kawo ba", inji
Malam Ibrahim kenan. Ai! haka ma zakace? bayan sun duka
shi har sunji masa ciwo zaka zo harka ce mun haka to ka
amsa kira a gun Alkali" inji Alhaji. "Kai Rufai", Rufai", Na'am' ya
amsa, zonan, inji Alhaji. Sai gashi. Alhaji ya kama hannun
Rufai yana nuna wa Malam Ibrahim yanzu a jimasa wannan
ciwon sannan kazo kana gaya mun wannan maganar banza.
To sarka ka karba agun Alhali. "Haba Alhaji me yasa zakayi
haka, kayi hakuri, ba'a biye yara", inji Malam Ibrahim. "eh ba'a
biye yara da yake kai naka nada yawa har suna taran tarume
su duka marasa yawa ko?" inji Alhaji kenan sai yajuya ya
shiga gida abinsa. Shi kuma Malam Ibrahim da yazo
dogaciya, yatafi abinsa shima. Ba dogaciya, ba sarka. Malam
Ibrahim dai bai ma sake wai wayar gida ba sai ya zarce gun hidimarsa.
Kashe gari Alhaji sai ya nufi kotun yanki, yaje kenan sai yatarar ana yin shari'ar wasu filani sai ya saurara domin a
hada musu sannan ya shigar da kara. Yana nan zaune sai
7
7
2
lafiya kabiyo mun yaro? Menene yashiga tsakanin ka da yarona?
A'a, tsaya mana a gaya maKasassalar zance". Inji Malam Ibrahim
yaci gaba "ai biyo shin da nayi ba wai dukansa zanyi ko wani abu
ba, sarka ce ta 'yata a gunsa yaje wurin wancan Malamin ya karbo
to nima na biyo sawun sarkar ne to amma sai kawai naga yaje ya
karba.
To na kirashi a kan ya ban sai ya rufa a guje. Sai na biyo shi,
to kaji. Saboda haka koda yake tare sukai fada da yarinyar
amma meyasa zai dauki sarkarta. A kawo mun sarkar ni
kawai ita nazo karba". Alhaji dai da a fusace yake, to shirun
da yayi sai ya sauko, sai yace dashi to ai ba haka ba menene
dalilin da zai sa su yaranku zasu taru su duka shi. Ai dama ina
son in sameka inji dalili". "To banda kai ma wa zai biye fadan
yara"? Wani abinsu ya hadasu wanda bai kai ya kawo ba", inji
Malam Ibrahim kenan. Ai! haka ma zakace? bayan sun duka
shi har sunji masa ciwo zaka zo harka ce mun haka to ka
amsa kira a gun Alkali" inji Alhaji. "Kai Rufai", Rufai", Na'am' ya
amsa, zonan, inji Alhaji. Sai gashi. Alhaji ya kama hannun
Rufai yana nuna wa Malam Ibrahim yanzu a jimasa wannan
ciwon sannan kazo kana gaya mun wannan maganar banza.
To sarka ka karba agun Alhali. "Haba Alhaji me yasa zakayi
haka, kayi hakuri, ba'a biye yara", inji Malam Ibrahim. "eh ba'a
biye yara da yake kai naka nada yawa har suna taran tarume
su duka marasa yawa ko?" inji Alhaji kenan sai yajuya ya
shiga gida abinsa. Shi kuma Malam Ibrahim da yazo
dogaciya, yatafi abinsa shima. Ba dogaciya, ba sarka. Malam
Ibrahim dai bai ma sake wai wayar gida ba sai ya zarce gun
hidimarsa.
Kashe gari Alhaji sai ya nufi kotun yanki, yaje kenan sai
yatarar ana yin shari'ar wasu filani sai ya saurara domin a
hada musu sannan ya shigar da kara. Yana nan zaune sai
7
can ya ga Malam Ibrahim ya shigo harabar kotun.
Ita harabar akwai katuna har guda uku ciki akwai magistare,
ta hannun dama sannan ta bayan ta akwai kotun masu laifi
wato (criminal court) sannan ta hannun hagu akwai kotun yanki. to shi Mallam Ibrahim daya shigo sai kawai yanufi kotun Majistare. Yaje sai ya tarar ana yi wa 'yan fashi shari'a to
tsammanin sa Alhaji bai iso ba sai kawai ya shige, ya zauna.
a
A can kuma Alhaji har an hada da shari'ar fulani, an saurari
karar sa. To ana rubuta sammaci sai ya sanar da Alkalin cewa
ai yaga mutumin anan. Saboda haka sai Alkali ya umurci
masinjansa da yakai wa Mallam Ibrahim sammaci. Sai suka tafo tare da Alhaji domin ya nuna masa shi. Suna dubawa
cikin dakin kotun sai Alhaji ya hango shi akan kujera ta
karshen baya. "Gashi can mai darar can na bay inji Alhaji sai
masinja ya kutsa kai cikin kotu. To ba wanda ya kula shi suna
ta sauraron lauyoyi suna cacar baki. Da isar masinja sai
Mallam Ibrahim ya juyo kai, don yaga ko wanene, sai yaga
ana mika masa takarda, zuciyarsa sai tayanke tana bugawa
dar dar. "Objection my lord"! wannan muryar sai ta dauki
hankalin Mallam Ibrahim, to amma ina! masinja sai ya jefa
masa ita akan cinyarsa sai yayi waje ya tsaya yana jiransa.
Shiru shiru Mallam Ibrahim bai fito ba, ya yi shiru yana ta
mamakin abin. Can sai ya tashi ya fito. To ai sai muje inji
masinja kenan. Shikuwa Alhaji dama bai tsaya anan ba sai
ya koma. Isar su Mallam Ibrahim kenan sai suka yi, sa'a ta su
shari'ar ta iso sai aka mika sammaci. Alkali ya karba yana
dubawa, su kuma Mallam Ibrahim da Alhaji sun kutsa kai ciki
har sun zauna a kan bencina. Alhaji sai ya zauna. Daga nan
bakin kofa kusa da taga shi kuma Mallam Ibrahim gashi can
ciki daf da kujerar dan sanda. Gefen Alkalin kuma
8
Magatakardar sane. Alkali na gama duba takardar sammaci,
sai ya mikawa magatakarda, shi kuma sai ya fara karantawa
"Ni Alhaji Mai Wake, unguwar kwana bakwai, cikin garin
Fatara, ina karar Mallam Ibrahim, Mallamin Dabbobi,
unguwar Tsakuwa, akan sammaci na Naira dari biyar". Duk
da Alhaji da Mallam Ibrahim suna sunkuye da kai, suna
saurare. Magatakarda ya cigaba. "Dalilin karar kuwa shine
yaran Mallam Ibrahim sun duka dana har sun gurdashi a
hannu". Rufe bakinsa keda wuya sai Alkali yace "ina Mallam
Ibrahim, kaji abinda akace ko?" Mallam Ibrahim ya daga kai
yace "naji"!. To kawo kudin sammaci tukun, sai Mallam
Ibrahim ya zaro kudi Naira dari biyar. Naira biyar - biyar guda
dari sai masinja ya taso ya karba ya mika wa magatakarda.
Alkali yace haka akayi? ka amsa"? "Eh! Ranka yadade", jiki
ya debi rawa. "Na amsa; to amma....... (yana EEna) ranka
yadade ina so a .... yi tuhuma domin a samu abinda ya hada
su yaran". Sai Alkali yace "Eh! gaskiyarka, to amma ai abinda
zamuyi, ba sai ka gayamana ba, ko"? Ya juya ga Alhaji "kai
Mallam mai kara menene ya sa yaran suka duka yaranka?"
"Me yai musu?" "Wallahi ranka yadade ni dai bana idar ba,
amma za'a iya kiran su yaran su fadi abin daya hadasu. Wato
Ranka yadade ni ba nada mu da ayi hukunci akan abinda ya
faru bane amma ayi dokaciya ga shi wannan Mallami tare da
yaransa akan sufita hanyar Rufai. Dalili kuwa shine, shi kadai
Allah ya bani". Alkali sai yace "Af to ai wannan mai sauki kenan.
Yanzu abinda akayi wa danka ka yafe kenan"? Inji Alkali yana tambayar Alhaji. "Eh ranka ya dade, ba kome". 'To saboda
haka ai kiran yaran ba kome zai dada ba illah wahal da ku
saboda haka kai Mallam Ibrahim, kana da abin fada? Shi kuma sai
yace "yallabai ni kam anan dai tunda Alhajin nan yamin hakanne
don yaci min mutunci to ina rokon kotu ta nema min mutunci
na daga gunsa. Domin ni nayi imani da Allah 'ya ta ba zata
9
kula wani yaro bama balle dan sa. Sai shi da yake yana
nunawa dansa gata to. Sannan kuma shi yaron bayan an rabasu sai ya dauke sarkar ita yar tawa,to ana me? Na bishi
zan karba sai kawai ya shiga gida sai ga Alhajin ya fito. Ba tambayar ko me ya kawoka sai ya hauni da fada, sai ya kawo
ni kara kawai. To anan ina so kotu tayi min kokari ta kwatar
min 'yanci na da kuma hakkin 'yata. Sannan kuma tayi hukunci akan batamin lokaci da Alhaji yayi". "Dirkashi, wata
sabuwa" inji Alkali kenan" To kai Alhaji kaji", ba haka bama ya dubi Mallam Ibrahim. Kai Mallam wakake"?"Ibrahim ranka ya
dade" ya amsa, shin ashe kananan yaran suke fada naji kace" "bayan an rabasu kabishi zaka karbi sarkar yarinyar da
yaron ya dauke", "a'a, Yalla-bai' kashe garine nake nufi, a
lokacin da suke fada ai shekaranjiya Talata ne. To jiya Laraba
sai aka gayamin gunda sukai fadan ni kuma sai na je dakai
na saboda na bada hakuri. Don maiyiwuwa in na aika yarona
wata sabuwa ta fito. To da naje ashe wani Mallami ne ya
dauka ya ajiye. Na je sai ga shi yaron, sai na aike shi akan ya
kira Mallamin, to ashe shi ko ya san sarkar naje karba sai
kawai ga Mallamin ina idarmasa, sai yace ai ga yaron da ya
karba can sai na biyo shi ina kiransa kawai sai ya ruga da
gudu, to nima sai na biyo shi kaji yadda akayi ranka ya dade".
Can gidan Mallam Ibrahim kuwa ba susan cewa an kaishi
kara ba domin ya bar gida akan zai je wurin aiki.
Gidan Alhaji Mai Wake kuwa Balki tana nan tana tunanin ko
yaya shari'a zata kaya. Tana ta zulumi
To a kotun kuwa lokacin da Mallam Ibrahim ya gama fada ma
Alkali yadda akayi sai Alkali ya juya ga Alhaji "to Alhaji kaji"!
me kace? Sai Alhaji yace ah-to! Ranka ya dade ai sai abinda
10
kotu tayi. Alkali yace "to yanzu ina sarkar"?Alhaji yace gata, ya daukota, yana cewa "dama an karbo ta ne domin in an biyo
sawu musan ko waye uban yaran saboda haka mun riga
mun sani amma sai dai abinda kayi ranka ya dade". "To
yanzu kotu zata nema maka gafara daga gunsa da a yafe
maka domin reshe ya riga ya juye da mujiya". "Kai Mallam
Ibrahim kotu na rokonka da ka yafe masa". Mallam Ibrahim
yai shiru sai ya nisa yace to ranka yadade naji, na kuma yafe,
amma bashi! bani!!" "A΄α, a'α, aί kartakai ga haka mana, αἰ
dama yara sukan hada zumunta ne ko kuma su hada
mugunta, to kudai kar ku yarda su hadaku mugunta" domin
Allah S.W.T. baya son mugu. Kuma mugunyar zama
mummuniyar rayuwace". Inji Alkali, musulmi kuma da
musulmi da suke fushi ga juna Allah ya tsine musu, har sai
sun fuce. Kuma duk musulmi yan uwan junane, sannan Allah
yana son masu hakuri."
Saboda haka kudai yi Sulhu a tsakaninku don Allah. Sai
wannan ya dubi idon wannan a tsakaninsu. Can sai Mallam
Ibrahim ya taso ya miko hannu ga Alhaji yace masa "Assalamu Alaikum" sai Alhaji ma ya mika masa hannu da
cewa "wa'alaikumu salam". Duk kotu sai aka dauka "Allah yayi muku gafara. Amin." To kotu dama lokacin tashi ya gabato. Sai duk suka tashi suka bi bayan Alkali, sukayi waje.
Mallam Ibrahim shi daya tashi sai ya wuce wurin aiki, yana ta sauri, saboda makaransa yayi yawa. Don ya sanar abinda ya tsai da shi.
Amma shi kuma Alhaji sai ya nufi gida. Domin ya je ya futa, kuma ya tafi harkokinsa. Shi Alhaji ba cikakken dan kasuwa
וו
bane, amma yana taba kasuwanci a tsatstsaye, dama kuma
yakan taba 'yar kwangila 'yar karama, domin shi ba wani Mai Kudi ne ba sai dai yana da dai dai gwargwado na rufin asiri.
A can gidan Alhaji kuwa dama matarsa tana jiran ko yaya
abin zai kasance. Tana ta zulumin abin ko yaya? Can sai taji tafiyarsa, yayi kaki dama ya saba kullum in ya shigo zai yi wani dan kaki wato shaidan yazo. To da jin kakinsa sai ta fito daga daki da dan murmushi "sannu da dawowa", "yaya dai?"
"Yawwa" "ai, "Bako me dai" "A,a Alhaji menene ya kasance,
kace ba kome? Inji dai reshe bai juye da mujiya ba? "Haba!"
"Allah ya kiyaye" inji Alhaji, "ai wato abu da yafaru dai.....".
sai yace "shigo dai", sai ya kutsa kai cikin