yi ga wani irin shi ba...
"Babban suna ne a wuri na ba na iya fadar sunan ...
Na soma Karanta mishi Ina Jin kamar Zan daburce don idon shi a kaina har na Gama shima yayi kabbara Yana min ADDU AR Allah yasa Al kur ani ya CeCe Ni . ADDU AR shi tayi min Dadi matuka Gaya na Kuma Amsa da ameen ya Rabbi
Ya sa fito da kudi daga aljuhu Yana Fadin
"Nima ga tawa sadakar...
Na kasa Musa mishi na karba Ina godiya muka wuce Ina Jin idanun sa a kaina .
Sai da muka Shiga gidan su Ziyada ne Naga Ashe Dubu biyar ce farin mutumin Nan ya bani . Na nunawa Ziyada wacce take cewa
"Gaskiya gayen Nan ya iya wanka Halimatu....
Naja tsaki na wuce zuwa dakin mama wacce take ta min ADDU A Bayan na Karanta Mata Allo itama Dubu biyu ta bani kafin muka Shiga zaga gidajen Yan Uwa da abokan arziki sai gani da kudi masu yawa. Wanda ake ta bani.
Sai kusan la asar muka dawo gida Ina gaban Dada Ina Karanta Mata adadin mutanen da suka bani kudi da masu yi min fatan alheri har na Kare kafin Dada tace
"Banji abinda Dubu ta Baki ba ?
Na dubi Dada Ina Fadin
"Bata bani komai ba Dada sai ma cewa da tayi Wai nayi Zuk'u....
"Ahaf ai Ni na San jauhara tana iya Baki komai ma Amma Dubu fatan alheri ma bakin ciki ba zai Bari ta iya ba....
"Kyale ta kawai Dada Allah ai shaida ne Kuma ba gashi ba Wanda ban sani ba ma yabani Dubu biyar.
Dada ta jawo langar wacce ta dafe kazar Nan da daddawa da albasa Tasha attarugu ta Miko min tana Fadin
"Ga kazar ki Ziyada Taya ta ku cinye ta ....
Nace
"Ai tare dake Dada zamu ci ....
"Kuci in kun rage zanci in Kuma kun cinye ba komai Bari na yiwa jauhara godiyar alherin da tayi Miki...
Ta fice zuwa kofar su goggo Dubu
"Jauhara kun cika Halima da abin arziki allah ya biya ya saka da alheri....
Goggo Dubu tace
"Wai Dada Anya karatun Nan na Halima Babu Zuk'u a ciki? ....
"To Dubu in ma da Zuk'un ai ta dai yi duk gidan Nan waye yayi Zuk'un Nan irin na Halima? Ina ce har su jummai sukayi aure ko saukar Zuk'un basuyi ba? Ashe ko ko Babu komai Halima ta kafa tarihin sauka Koda ta Zuk'u ce ....
"A a dada kice magana dama Kika kullo tunda har da gori da Gaya magana Amma Ina ce saukar kawai Halima zata nunawa su jummai Amma ba nagarta ba tunda su har gobe Basu da wani bakin fenti bari mugun tabon da in magana ta bugi magana za ayi Indo ina Ai....
Wannan maganar ta sauka akan kunne na na bakin fenti da mugun tabon da in ya bayyana....
"Dubu nafi karfin na kullo magana Akan ki . Mijin ki ma Dole yayi abinda nake so bare har na kullawa suruka magana. Kuma kin yi na farko kinyi na karshe Akan wannan maganar na Rantse Miki da Allah duk Ranar da Kika Kuma kwata irin ta Zaki hadu da fishi na ....
Goggo jauhara ta taso tana Fadin
"Gaskiya Dubu babu tsinkaye a cikin abinda kikeyi . Dada ba tsarar ki bace tunda Wanda ya San darajar manyan sa shine Yake mutunta na wani....
"Barta jauhara in ita ban Isa da ita ba ai na Isa da mijin ta....
"Kiyi hakuri don Allah Dada....
Na kamo Hannun Dada Ina Fadin
"Yi hakuri Dada ta taho muje....
Muka wuce inda Kuma goggo Dubu ta mayar da tijarar ta Kan goggo jauhara tana Fadin
"Ni fa in ban kasa da mutum ba Banga dalilin da zai dauka ba in ba munafunci ba sai a zage Ni a dake Ni kuma ace ba zan koka ba? In takamar ta haifi miji na sai ta gayan zancen banza na kyale ta? In ta zubar da girman ta sai na kasa saka kafa na murje shi ?to bana gayyar munafunci ban kasa da mutum ba bare ya dauka Kuma tsohuwar can tace min kulle Zan ce Mata casss ta Rike girman ta ta daina yada min magana da arashi har tana neman zagin Ya'ya na akan wata karere can Marar tsarki? To in ta haifi Mai gidan sai akace Nima ta Haife Ni?
Goggo Dubu tayi ta tijara tana sakin maganganu Amma goggo jauhara ko Tak Bata ce Mata ba sai ma Kira ar karatun Al kur ani da ta saka wayar ta ya soma karade tsakiyar gidan abinda ya Kuma fusata goggo Dubu kenan Amma iyakar abinda zata iya kenan don jauhara dai ba zata daku ba don ta taba Rufe gida Wai zata Bata Kashi sai gashi reshe ya juye da mujiya jauhara ta lakada Mata dukan da har sai da tayi barin ciki tun daga wannan Rana Bata Kuma gigin cewa zata dake ta ba.......
To fa kaji wani Abu. Bari muji Yaya wannan tafiyar take Mai taken _*LINZAMI DA WUTA*_
✍🏻 Alkalamin GIDAN IKO
[8/20, 10:53 AM] Gidan Iko: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
🧆 *_LINZMI DA WUTA_*🧆
Pages
3️⃣//4️⃣
NA
GIDAN IKO💖
*_Kirkirarren labari ne da Bai shafi Rayuwar kowa ba kuskure ne babba danganta kai ko wani dashi babu mafi cancantar suyi suka akan labarin irin taurarun cikin labarin Wanda kuka San Babu su a zahiri to kar wanda ba cikin jaruman labarin Yake ba yace don shi ko don wani akayi Hakan jaruman cikin labarin ne kadai suke da damar sukar marubuci akan don me zai fallasaww duniya sirrin_.*
_WULAKANCI_
...............Babu abinda Yake Amsa kuwwa a kunnuwa na da zuciya ta face kalaman goggo Dubu. Meye bak'in fentin da Yake gareni ? Wane irin mugun tabo ne Dani Wanda har in magana ta bugi magana za ayi Indo ina A i?
Kaina ya shiga wani irin mugun duhu duk da ba yau ne Ranar farko da na soma Jin hakan a bakin goggo Dubu ba Amma a yau din naji Ina son sanin ma anar kalaman nata gareni.
Dada da take ta tijara da masifa Akan dai kalaman goggo Dubu ban iya ce Mata Tak ba bare na Bata hakuri har aka Kira sallar magaruba Dada Bata yi shiru ba .
Na mike na figi buta na Shiga bandaki na fito na jawo kujera Yar tsuguno na Zauna ina alwala Ina Jin zafin kalaman goggo Dubu Wanda nake son a yau na tambayi Dada meye bak'in fentin da Yake jiki na ? Meye Kuma mugun tabo a tare Dani?
Na Gama daura alwala na mike na wuce Dada tana ta fadan ta duk dai akan goggo Dubu da abinda tayi mini...
Duk da ban juyo ba Amma naji kallon dada a jikina Wanda bana ko tantama na shirun da nayi ne ban kuma tankawa ba har kawo yanzu.
Ina salla zuciya ta cike fall da tunanin Al Amarin da ya Zama bak'in fentin a gareni.
Hakika gata da kulawar Dada ta Bai iya bude min kofar da Zan tuhumi Ni wacece ba . Tunda kaf ahalin da suke gidan mu Ni din Yar gata ce ta nunawa a jarida . Dada ta kore min dukkan wani Abu da zai nuna Ni din na tawaya ko a nakashe nake. Amma a yau kalaman goggo Dubu sun nuna min Ni din wata musaka ce ko tauyayyiya wacce ta Rasa wani Abu da zatayi dukan kirjin da cikakkun Ya'ya sukeyi....
Ban San nayi zurfi a tunani ba har idaniya ta Bata iya Boye zafin da zuciyar tawa take ciki ba har na soma zubar da hawayen tausayawa Kai sai dai ji nayi Dada tana Fadin....
"Subhanallahi me ya faru ne Halima?
Na dago da sauri ina goge hawaye na nace Mata
"Ba komai.
Ta bi Ni da kallon tuhuma na mike na wuce Uwar dakin na Zauna a gefen gado Ina Kara jin zafin kaddarar da ta hau Ni har abin ya Zama abin gori gareni wurin goggo Dubu. Shin MENENE? Me ya faru har Al Amari na ya Zama a goranta min don Raina ya baci a ji Dadi?
Ina jin lokacin da goggo Dubu ta kawowa Dada abinci har Dada tana Kuma Rufe ta da masifa duk dai akan abinda ya farun Amma banji goggo Dubu ta tanka ba me yuwuwa tayi nadamar abinda tayi Amma Kuma banji ta bayar da hakuri ba.
Dada ta dauko kwanon abincin ta biyo Ni Uwar dakin tana kallo na ta aje abincin tana Zama kusa Dani ganin idanu na da Ruwan hawaye kaca kace yasa ta jawo Ni tana Fadin
"Halima yanzu akwai wani Abu da zai same ki Amma ki Boye min ki kasa sanar Dani? Don Allah ci abinci ki fada min abinda ya Dame ki....
"Na koshi Dada. Babu Kuma abinda Yake damu na sai kalaman goggo Dubu. Meye bak'in fentin da nake dashi Dada? Meye mugun tabon da ake tsoron ya fito mini?....
Sai kawai Naga Dada ta fashe da kuka tana Fadin
"Ni Dubu zata wulakanta? Ni zakiyiwa wannan wulakancin? Sai Kuma ta mike da Sauri har zanin ta Yana Shirin faduwa ta fice daga dakin Ina kallon ta fice zuwa kofar su goggo Dubu. Ina ji tana Fadin
"Jauhara sa adu na Nan?
Banji abinda goggo jauhara ta fada ba sai Naga Dada ta wuce cikin gidan
Baba sa adu Wanda suke cewa Baba Headmaster Yana Zaune saman kujerar sa da redio Yana sauraren Shirin idon mikiya ya Rage karar Radio Yana mikewa don Jin Kiran mahaifiyar sa inda Kuma goggo Dubu gaba ya fara Mata balli balli....
"Gani Nan Dada lafiya dai ko?..
"Ina fa lafiya? Ba nice nace kayiwa matar ka iyaka da Halima ba? Shin a me kuka dauke Ni ne Kai da ita? Raining da kayi min ne har ka Bawa matar ka damar ta Raina Ni? To zan Kai karar ka ga Ubangiji don Allah ya sani Kuna cutar Dani kuna kunsa min bakin ciki...
Sai ta Kuma fashewa da kuka ta koma kofar ta....
Goggo jauhara ce ta ta biyo ta tana fadin
"Kiyi hakuri don girman Allah Dada ayi hakuri in Sha Allah ba zata sake ba....
"Za a sake Mana jauhara? Ba shi ya Bata kofar da ta Raina Ni ba? Inda Ina da mutunci a wurin shi yaushe Dubu zata kalli idona tayi min Rashin kunya? Ni da kaina nace mishi ya jawa matar shi kunne ta fita harkar Halima tunda ba kishiyar ta bace Ni Banga abinda yarinyar Nan tayi mata ba.....
Baba Headmaster ya biyo Bayan dada Hankalin say tashe yana Fadin
"Kiyi hakuri Dada wallahi ban San abinda Yake faruwa ba....
Dada ta soma share hawayen ta tana fadin
"Ai Ni na Gama magana sa adu saura kiris na hada kayana na bar maku gidan Nan ....
"Kiyi hakuri don girman Allah
Ya dubi goggo jauhara Yana Fadin
"Jauhara Kira min Dubu taxo...
Goggo jauhara ta fice Kiran goggo Dubu inda Baba Headmaster Yake ta rarrashi da ban hakuri har goggo Dubu ta iso....
"Me kikayiwa Dada?
Ya watsa Mata tambayar ta dube shi tana duban Dada....
"Me fa tayi Banda son ketawa Halimatu Rigar mutunci? Ni na Rasa abinda yarinyar Nan ta tsarewa baiwar Allah Nan tamkar taji ance kana Shirin auren ta ta Zama kishiyar ta. To a yau na gaji da hakuri wallahi yadda ta saka Halimatu kuka itama sai tayi nata kukan. Dama na fada Miki tab'a mutuncin Halima daidai Yake da tab'a mutuncin igiyar auren ki don wallahi kinji na Rantse matukar dai Kika ce Halima ce kishiyar ki fiye da jauhara to ina Mai tabbatar miki da wallahi zaman ki ya zo karshe a gidan Nan don sa adu ma yace zai tab'a mutuncin Halima to zai ga abinda zanyi mishi bare ke da aure ya kawo . Tun yarinyar Nan Bata kula da kalaman ki ba har a yau tana neman sanin meye abinda Kika fada Mata? Sai Kuma Dada ta Kuma rushewa da kuka .....
"Don girman Allah kiyi hakuri Dada....
"Ba inyi hakuri nake son ji ba sa adu. Mataki kawai nake so ka dauka akan matar ka kafin nan da zuwa Safiya don wallahi ba zanyi rantsuwar banza tunda Dubu Bata ji kashedin da nayi Mata ba to kun kaini kwano ...
Baba Headmaster ya juya inda goggo Dubu take tana kallon Dada cike da Haushi da takaici....
"Wato Dubu na Gama Gane kece ke son Shiga tsakani na da mahaifiya ta ko? Dukkan wani Abu da Ranta zai baci kece ke jswo min shi . To bari kiji Akan ki ba Zan yarda na fusata mahaifiya ta ba wallahi Duka ki bata hakuri ki Kuma tabbatar Mata da wannan shine karon karshe da Zaki sake tofa wani Abu akan Halima....
Goggo Dubu ta motse Baki tana fadin
"Ikon Allah Ni fa Babu abinda nace daga ta kawo Allon Zayyana nace Anya Babu Zuk'u a cikin wanna sauka shikenan fa cibi ya Zama Kari Kari Kuma ya Zama kababa Allah ya Baki hakuri ...
Tana fadar hakan ta juya Bata Kuma sauraren su ba.
Baba Headmaster ya dubi Dada Yana Fadin
"Kiyi hakuri don Allah Dada nayi Miki Alkawarin daga wannan ba zata sake ba....
Dada ta dube shi ba tare da ta tanka ba ya Gama jera Mata kalaman Rarrashi ya mike Yana Mata sallama ta dube shi tana fadin
"Iyakar matakin da zaka dauka kenan sa adu?....
"Zan Kara wani Dada musamman idan Dubu ta Kuma Shiga harkar Halima....
Dada ta shigo dakin ta same Ni don naji duk abinda ya faru inda Kuma na Gane Tayar da Hankalin da nayi to tamkar Tayar da Hankalin Dada ne nata ma yafi nawa ....
"Kiyi hakuri Dada ki rabu da goggo Dubu abinda ya faru Kuma ya wuce....
"Kinci abincin?
Ta tambaya nace Mata eh duk da kuwa ko bude shi banyi ba don Sam bana Jin yunwar...
Ina Gama sallar isha I na kwanta don kaina sai ciwo Yake ga zazzabi da nake ji
Kafin wayewar gari sai gani Sharkaf cikin Rashin lafiya zazzabi da ciwon Kai har da haraswa
Dada ta Rikice tana ta jawo min magunguna na samu paracetamol na Sha na koma na kwanta....
Dada ta nufi wurin jauhara ta samo min maganin ciwon Kai inda ta ci Karo da goggo Dubu tana hada kullun wainar ta ...
"Kai Usman maza Shiga makaranta ka kiro min sa adu kace maza maza yazo
Yaron ya fice Kiran baban su sai ga su a tare da Baba Headmaster....
"Wannan shine matakin da ka dauka Akan matar Nan? To in ma baka Gane abinda nake nufi Bari in bude maka bana son ganin matar Nan a yanzu ta matsa daga Nan har zuwa lokacin da Zan huce in Kuma ba Haka ba Ni zan matsa...
Baba Headmaster ya dubi goggo Dubu Yana Fadin
"Zo ki shige Dubu kije sai lokacin da Dada ta huce ...
Dada ta wuce wurin jauhara tana Fadin
"Jauhara don Allah bani maganin ciwon Kai in kina da shi Halima ce kwance riris...
Goggo Dubu ta mike ta tsallake kullun wainar ta ta wuce Uwar Daki duk da batayi zaton wannan hukuncin ba Amma Dole ta tsallake ta bar gidan zuwa Nasu gidan da Yake can karamar hukumar jibia...
Goggo jauhara ta karasa kwabin kullun wainar goggo Dubu ta Kuma toya Mata don gudun Kar ayi asara . Ta toya Mata ta Kuma siyar Mata t Adana Mata kudin ta ....
Kwana na uku a kwance kafin na warware na shiga harkokina inda Kuma goggo Dubu sai da tayi wata biyu a gidan su Inda iyayen ta suka shiga zaryar zuwa Bawa Dada hakuri Amma Dada tace Bata huce su Mara hakuri har zuwa lokacin da zata huce
Sai da goggo Dubu tayi wata hudu cur Bata gidan kafin goggo jauhara ta iso wurin Dada tana fadin
"Dada don Allah Nazo kiyi mini wata alfarma don ANNABI. ....
"S A W jauhara nayi Miki ita tun kafin naji ta tunda Kika ce ANNABI ai karshen magana ne...
"Yauwa dada Nagode . Don Allah dama cewa zanyi kiyi hakuri dubu ta dawo ko ba don komai sai don Yan yaran ta Kuma kuskure ne abinda tayi yanzu in ta dawo tunda kin hora ta ba zata yarda ta sake ba. Na duba yaran ta ne suna bani tausayi wallahi ga Kuma iyayen ta da suke ta Zarya kin san shi zaman gida in mutum ya wuce shi to ya wuce shi Babu Kuma uwar da take so ta Kai yarta dakin aure ta dawo Mata bare Dubu da har suruki gareta abun Babu Dadi surukin ta yayi ta zuwa Yana Tara's da Bata Nan tun Bai Gane ba zai Gane shine Nazo kiyi min alfarma don Allah kiyi hakuri ta dawo dakin ta...
"To jauhara na yarda Amma ba don ita ba sai don ke da na Gane ba irin Dubu bace zuciyar ki tana da kyau in sa adun ya dawo ki fada mishi na huce ya dawo da matar sa...
"To Nagode Dada Allah ya Kara sutura da lafiya...
Washe gari sai ga goggo Dubu ta dawo goggo jauhara ta Bata kudin cinikin wainar ta ta Kuma Bata shawarar ta kawar da idon ta daga Halimatu Kuma Yana da kyau taje ta Kara Bawa Dada hakuri don komai ya wuce....
Wani mugun kallo da goggo Dubu ta jefawa goggo jauhara tare da Jan tsaki shi ya nunawa goggo jauhara Dubu Bata rusuna ba don Haka Bata Kuma bi ta kanta ba tayi mata ADDU AR shiriya kawai
Kwana biyu da dawowar goggo Dubu sai ga kawar ta goggo tabawa ta iso gidan tana Fadin
"Kai barka barka aminiya ta hasken gidan headmaster duk sadda zanzo gidan Nan na Tara's da dakin ki a Rufe sai naji wani Abu har Mai gidan na Samu Ina Rokon alfarma yace min Babu yadda zaiyi ne a Nan na Gane yafi kowa damuwa da Rashin ki a gidan ............
To ke kuma Haka kike tabawa? Anya kuwa za a kulla abin arziki? Muje zuwa tukuna
✍🏻 Alkalamin GIDAN IKO💖
[8/20, 10:53 AM] Gidan Iko: 🧆 *_LINZAMI DA WUTA_*🧆
Pages
5️⃣//6️⃣
GIDAN IKO💖
*_WATA MAGANAR_*
..............Goggo jauhara ta dago kanta saboda Jin Arashin da tabawa take saki Wanda ta tabbatar da ita take.
Goggo ta mike tana fadin
"Yar Halak kink'i ambato yanzu nake zancen ki a Raina Ashe kina tafe. Muje daki akwai magana dama ko Baki zo ba Ni Zan zo shiyyar ta ku...
Ta figi hannun tabawa suka nufi Daki yayin da Goggo jauhara tace da tabawar
"Tabawa Ina yini ya gida?
Tabawa ta juyo tana yamutsa fuska tamkar taga tutun da yasha kashin Ruwa tana Fadin
"Lafiya Lau Amarya ya kasuwa?
Ta shige Daki ta zauna tana Fadin
"Kai Dubu kina ganin lukutar masifa wannan Mata akwai kisisina da son iyawa....
Goggo Dubu ta katse ta tana fadin
"Ke me kika gani a Kan kisisina? Wai fa shegiyar tsohuwar can har arashi tazo ta yada min wai jauhara ba kishiya ta bace Yar Uwa ce wai ita ta bayar da hakurin da aka dawo Dani.?.....
"Tasa aka dawo da ke ko dai tasa aka fidda ke? Tuni nake fada Miki matar Nan asiri take tana hayewa tana barin ki Amma kina ganin kamar Zaki iya da ita ....
"Na yarda wallahi tabawa don in ban yarda tayi min asiri Akan miji ba yanzu Dole na yarda tayi min Akan Sana a ta....
"To Bari ma kiji in fito miki a mutum Dubu Ranar da sa adu ya Kora ki gida ai wani tarkon ne ya Kama meye don kin zagi waccan lauyayyar tsohuwar? Ina Abun Kora a Nan? To don ma in Kara fita daga zargi wurin malam Mai gafukka naje na Zayyana mishi komai sai ga magana ta fito asirin dai ne Kuma daga kishiya....
Goggo Dubu ta zubawa tabawa idanu cike da tsoro don Allah yayi Mata mugun tsoron asiri shiyasa ma Bata tab'a taka wurin wani malami ko Dan tsubbu ba don gudun Kar ta jawo abinda zai ishe ta duk da aminiyar tata tabawa Tasha fada Mata akwai asirin da kishiyar ta jauhara ke auno Mata Amma Bata tab'a Jin zata mayar da martani ba...
"To in da ban yarda ba tabawa yanzu ai na yarda wallahi . Tunda na dawo gidan Nan tabawa komai na Sana a ta yaja baya kullum sai nayi kwantan waina tamkar wacce take siyar da mugun Abu Amma ita sau biyu ma kwanan nan take dafa taliya Yara kuwa Yan Tara Babu Mai duban inda nake bare ace waccan shegiyar Mai take kasawa? Kowa ya shigo zakiji yace a bashi taliya abada taliya dai har na yanke shawarar Nima taliyar Nan Zan koma tun abin saidawa Bai gagareni ba tunda kullum cikin asara nake sai dai na Bawa Yara da almajirai kayan kudi na Ina ji Ina gani...
"Ahab ai wannan tafiyar da kikayi Dubu Nan aka samu damar binne binnen da akayi Miki . Ba kince har da wata kinaya akayi Miki ba Wai an Toya Miki kullun wainar ki don Kar ya lalace an siyar Miki ba? To da Zaki lalube inda kike kafa kayan Sana ar ki da kinsha mamaki don Babu abinda ba Zaki gani ba ....
"To yanzu dai ga wainar can bokiti fall Ina Jin Duka dukan cinikin da nayi Bai wuce dari takwas ba ita Kam har sake dafa taliyar tayi ta Kuma siyar.....
"Ai wannan karon Dubu Dole ki aje tsoron ki gefe mu je gun malam Mai gafukka wallahi in ba fidda matar Nan kikayi a gidan Nan ba to itace zata fidda ki don shi macuci kafin ya cuce ka ne ya kamata ka fara cutar shege don shima burin da Yake da shi kenan Akan ka. To in har kin ji kin gani Zaki iya Zama da ita to sai ki kasa a kassara Mata Sana ar ta ko a kassara Mata lafiyar da zata yi Sana ar da ita Amma in nice ke wallahi da tsiya Zan sa Mai gafukkar ya fidda min ita in yaso Ni nake yin Sana ar tata Duka na hade ita Kuma Allah ya hada ta da mijin Mai tsautsayi Amma yaushe kana da kishiya ka Kama hannu ka Rungume? Ai Dole sai kana Dan motsawa....
"Ya zama Dole wannan karon nayi motsi tabawa musamman da na Gane yadda ake so na Zama . Na Gane anyi nufin yi min kisan mummuke ta yadda Zan ta narka kudi na wurin Sana suna narkewa Kinga idan na Zama bani da komai to burin ya cika ayi mini homa da barazana har ma ya Zama Ya'ya na ma sai abinda aka Basu sai dai Allah ya Sani Ina tsoron dakin Nan na malam Mai gafukka tabawa yadda kike fada cewa har Kan Rauhanai ake gani da yadda macizai suke kawo magani shine abinda Yake tsorata Ni wallahi ....
"Kinji matsalar ki wallahi Dubu . Ban fada Miki Aikin malam Mai gafukka Sha yanzu ne magani yanzu ba? Shi fa da kinje kafin kice mishi komai shine zai ce sunan ki wance Kuma akan Abu kaza Kika zo . Kan kice me? Sai dai kiga Mai kawo magani tsakanin Rauhani ko bakin aljani ko macizai ko wani Abu daban....
"Yanzu Babu yadda za ayi tabawa ba bada Sak'o ki isar mishi ba sai naje ba?....
"Ai shi baya karbar Sak'on wane yaji ga wane? Yafi son kazo da kanka in kace sako ne aka Aiko ka zai ce koma in Mai Sak'on Yana son biyan bukatar sa yazo da kanshi . Ai da Yana karbar Sak'on Dubu ai da tuni na zube kudi na na karbo Miki magani sai sai dai ki gan shi kawai....
"Wallahi Ina tsoron ganowa kaina janhurun masifa ne tabawa.....
"To sai ki Zauna in aka mayar da ke yadda ake so ai bukatar ki ta biya ko?
Cewar tabawa wacce ta dankara baka...
"Ba ma za ayi haka ba Zan Rufe Ido muje sai dai yanzu Babu wasu kudin kirki wuri na sai na Dan tattale su tukuna ...
*** *** ***
"This is love at first sight?
Ya fada da karamin sauti tamkar Mai yin rad'a...
Ya mike daga kwancen da yake ya dubi agogon wayar sa da take nuni da