na Shiga uku?...
Dada ta zuba min ido tana Fadin
"Ai na saka Allah Gaba Kuma shi zai tsare ni ba ke ko wata mariya ba..
Na kafe akan ban yarda ta tafi ba in Kuma tace sai taje to Zan fadawa Baba Headmaster. Abunda Kuma Bata so kenan har Al amarin ya kusa Zama bacin Rai tace Babu wanda zai Hana ta tafiya in ta so tafiyar ta abunda Kuma Ni ya Tayar min da Hankali kenan nayi ta Mata kuka har tace ta fasa kafin hankali na ya kwanta
Kwanaki da yawa Dada Bata kuma tada maganar tafiya ba Amma fa Bata fasa maganar shirun baba na ba. Ranar asabar Ina makarantar islamiya sai dawowa nayi na iske Dada Bata Nan . Na tambayi fiddausi wacce take bani Sak'on da Dada ta Bata ta aje min na kudi .....
"Ina ta tafi fiddausi?
Fiddausi ta dube Ni tana fadin
"Naga dai ta hada Kaya a Jakar ta Kuma ta gwada min wasu fakardu Wanda tace na duba Mata na Gaya Mata sunan wata unguwa da Naga Ni an Rubuta A kamaru.....
Shikenan Dada ta tafi kamaru.....
To Dada Allah ya Kai ki lafiya ya Kuma sa lafiya ta Boye hamzan Nan mu Kam mun Matsu a fiddo mu daga cikin duhu har yanzu Kam a lullube muke tafiya.....
Saura page daya mu kammala book one kuma book one din shine free amma 2 @3 4 paid ne mai bukatar su zai tura 1k ne account 1780003378 Eco banks ko kuma Katin MTN akan 08035191669
Gidan iko 08035191669
✍🏻 Alkalamin GIDAN IKO💖
[8/20, 10:53 AM] Gidan Iko: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅
🧆 *_LINZAMI DA WUTA_*🧆
Pages
2️⃣9️⃣/30️⃣
NA
GIDAN IKO💖
_Hakkin mallakar littafin ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne kowane Abu Yana da mamallakin sa Babu Kuma Mai son a daukar mishi kayan sa ba tare da izinin sa ba mu kiyaye hakkin juna sai mu Zauna lafiya_
_ADDU A ne ga RUHIN dukkan musulmin duniya masu NUMFASHI da Wanda Ubangiji ya yanke NUMFASHIn su Allah ta ala da Kai mukai imani da Kai muke dogaro Allah ka Rahamtaww musulmi da Rahamar ka don Wanda ka k'agi duniya da lahira domin sa_
_TA FARU TA K'ARE_
💖
............... "Inna lillahi wa Inna ilaihir Raju un ! Ita nake ta fada ina maimaitawa cike da tashin Hankali kafin na fashe da kuka ina fadin
'Na shiga uku na fiddausi shikenan shikenan tawa ta same ni'
Fiddausi ta dube Ni a rikice cikin tashin hankali tana fadin
"Me Yake faruwa ne wai Halimatu? Me Dada ta tafi yi kamarun?...
Ban iya Gane abinda fiddausi take tambaya ta ba tamkar ba da hausa tayi tambayar ba . Babu abinda nake hangowa sai Dada a garin da ita kanta Bata yarda da kanta akan zuwan sa ba. Ban Manta ba Ni kaina da Baba na yace zai tafi Dani cewa tayi ba zanje ba. Haka Kuma tace tayi kuskure da ta Bari baba na ya tafi shi kadai gashi itama ta tafi Ni babban tashin Hankali na ma yadda Rayuwa ta Zama a yanzu da ake cike da tashe tashen Hankula da yadda in ka San wuri a da yanzy ba Haka Yake ba Kar taje ma ta bace shine damuwa ta....
"Me zatayo a kamarun?
Fiddausi ta kuma katse Ni da wannan tambayar...
"Wai baba na zata bi bayan shi gashi ma Ashe ko sunan inda Yake Bata Rike ba sai da ta tambaye ki na Kuma tabbatar da kafin ta Isa kamarun ta manta garin da tace duk arna ne waye ma ya iya hausar da zata tambaya?
Mukayi shiru Ni da fiddausi cike da tashin Hankali ga Dada ko waya Bata da ita bare na Kira ta naji inda ake ko Halin da take ciki
Wani matsiyacin tashin Hankali da ya mamaye Ni har na soma Jin zazzabi Yana kada Ni Dole na kwanta ina makyarkyata
Da yamma na nufi kofar Baba Headmaster na same shi ina gaishe shi ya Amsa min kamar yadda ya Saba amsa min ba yabo ba fallasa Don tun lokacin da Dada ta kora Goggo Dubu gida akan abinda tayi min na kula Baba Headmaster ya Kara tsana ta duk da dama can ba wani yi na Yake ba to Amma maganganun da ya fada ne suka nuna min ya ji haushin abun don ji nayi Yana Fadin
"Wannan yarinyar an shagwaba ta tana tatawa matan mu Rashin kirki kuma ace laifin su ne kana kallon idon ta kasan ja ira ce ...
Tunda naji wannan maganar na San yaji Haushi Amma ban yarda Dada ta Sani ba....
Na gaishe shi Ina Fadin
"Baba Dada fa ta tafi kamaru ita Daya Ni kuma Ina Jin tsoron Kar wani Abu ya faru don Naga ita da kanta Bata yarda da wani ya tafi ba Amma ita fa ko sunan unguwar da zataje Bata Sani ba sai da ta tambaye fiddausi......
"Me ta tafi yi kamarun? Ko ance wani Abu ya sake faruwa ne?...
"Wai bin Bayan baba na tayi taji shirun shi yayi yawa shine tabi Bayan shi .....
"Yanzu har Dada ta iya tafiya kamarun Amma Bata sanar da Dayan mu ba?
Ya fada Yana Mai nuna fushi inda na Gane Kai dangin mahaifi na dai mutuncin su ba wani yawan kirki ne da shi ba....
"Ni yanzu da kika zo kika fada min me kike nufin nayi?
Ya tambaya Yana tsattsare Ni da manyan idanun shi cike da masifa...
"Baba don Abi bayan ta tunda ba Sanin inda zataje tayi ba ita da kanta fa a tsorace take da garin Nan Baba gara abi Bayan ta a dawo da ita kamaru fa ba Nan bace....
"Ni dai ba zanbi Bayan ta ba tunda har ta tafi ban sani ba zanyi Mata ADDU AR Allah ya tsare hanya Amma Ni Ina Naga kudin da Zan bi hanyar kamaru a yanzu ? Allah ya maido ta lafiya ai Ina ganin cikin mu ya kamata ta tada wani ko Ni ko Bello tace mubi Mata Bayan hamzan tunda Kuma ta fidda mu daga cikin lamarin me zai kai mu Shiga? Dama ta fara Fadin saaboda munga yadda ya Zama . Tun yaushe Dada take nuna Mana Hamza ne kawai Dan ta ko wanda take so? Inda ta dauke mu kamar shi yaushe zata tafi bamu Sani ba? Ni ko kudin zuwan ma ne da Ni ba zanje ba tunda ba a saka Dani ba ....
Na mike ina Jin Ashe ba Rashin kirki ne da su Baba Headmaster ba Rashin mutunci ne . To Rashin mutunci Mana? In sunyiwa Baba na bakin Hali shine Rashin kirki Amma tunda abun Nasu Bai bar Uwar su ba ya je ga Dada Rashin mutunci ne....
Na mike ban iya ce mishi komai ba Yana ta sababi Yana tijara yayin da Goggo jauhara tace
"Amma kuwa in kace Haka kamar Babu GIRMA da biyayya ai Dada ko makotaka take da ku ta wuce abinda kake fada Mata gaskiya Babu D'a A acikin abinda kayi Amma kayi hakuri in tawa tayi zafi....
Ban iya tsayawa naji karshen abinda Goggo jauhara take fada mishi ba na wuce na barshi Yana ta tijara har Goggo Dubu na Fadin
"Ai kuwa a makotakar akace ka sanar da makocinka Halin tafiya ko ciwo don shine Wanda zai fara taimakon ka kafin wani naka yazo ma Amma sai fa yanzu muke Jin ta tafi kamaru....
Na wuce ban tssya ba inda koma kofar mu na Rufe na nufi gidan yakumbo mariya wacce na Zayyanewa komai akan tafiyar Dada kamaru Amma itama yadda kuka San sun hada Baki da Baba Headmaster itama tace ai Dada ta Gama mutuwa Akan son Hamza fiye da su don Haka ADDU A zasu Mata Allah ya tsare hanya
Na fito ina cike da tashin Hankali Anya kuwa Dada ce uwar su Yakumbo mariya da Baba Headmaster? Kai ban zaci hakan ba Amma Kuma ko Rukon su tayi ai ta zarta wannan wulakancin a gare su...
Na iso bakin titi don na tsayar da Napep amma fetal Babu su na kafa tsayuwar jira....
Dr Anam da ya taho daga asibiti zuwa gida ya soma hango ta tsaye cikin hijabi da kyakkyawar Shiga ta Kamala Amma ya cika da mamaki me ya kawo ta garin Nan? Kuma duk cikin salon barikin ne ya ganta da hijabi?...
Ya taka burki a gaban ta Yana sauke gilas din motar....
Na ja da baya da sauri ganin mota ta faka a gaba na ya sauke gilas din Yana kallo na cike da mamaki har Yana murmushi...
"Kai Ranki ya Dade helengabros yau kece a garin namu ?
Na dube shi cike da Mamakin sunan da ya Kira mini Wai Helen gabros....
"Wace Haka Kuma Helen gabros?...
Yayi murmushi Yana Fadin
"Oh Sorry Queen nake so tunda Haka kowa ya San sunan ko?
Na Kuma duban shi ina Fadin
"Don Allah kayi hakuri ina Jin ba wacce ka Sani ba ce kace Helen kace Queen in ma cinke kake to Duka Babu suna na a ciki wallahi....
Kafin ya tanka nayi maza na tsayar da Napep da Hannu na Mai dauke da waya ta inda yabi hannun da wayar shi da ya gani wacce ta nuna mishi Halin bariki kawai ake son nuna mishi....
Yana kokarin fitowa Daga motar na fada Napep ya ja muka shilla a guje kamar Mai Napep din ya San hakan nake bukata. Ga Alama Kuma Dan arufta ne wanda Yake Aikin a Haka....
Dr Anam ya koma motar da sauri ya tashi motar ya marawa Napep din baya don Bai tab'a Jin Yana son Helen ba sai yanzu da ya ganta cikin shiga ta mutunci wacce yake fatan ace ta musulunta Kuma ta Kame kanta shi Kam da yafi kowa murna ....
Yadda yake gudu da son ya cimma su inda Kuma Mai Napep ya wuce mishi fintinkau Amma tabbacci da hakika Yana nuna mishi zai iya taddo su.
Sai dai ina ! Ko kyallin su bai hango ba har ya iso bakin traffic light Amma Babu wata Napep ma bare yayi zaton tana ciki...
Ya koma baya Yana dukan sitiyarin motar Yana cizon lebe da Jin wani irin so da bege ga yarinya Helen gabros...
Ko da na iso gida Ni tuni ma na manta da babin wani Mai mota don tun a can na Gane Yan latsi ne Ni Kuma basa gaba na. Abinda kawai Yake a Raina shine yadda su Baba Headmaster da Yakumbo mariya suka nuna min akan Dada ko Rukon su tayi ai ta wuce da wannan wulakancin Daga gare su. Na San Baba Bello yafi su Rashin kirki shiyasa ma ban nufe shi ba na fara da babban Nasu Baba Headmaster to karamar tasu ma ba kirkin gare ta ba ga abunda tayi min .
Da dare sai ga Baba Bello ya iso nan suka shigo shi da Baba Headmaster Yana Fadin
"Ai Ni Bata zo gida na ba Allah ne ma ya kure ta da Bata zo ba don da sai na Zane kafira saboda Uban ta ne zata tsoma mu cikin balaki? Mutanen can ita Dada da kanta ta San yadda suka Rabu wurin tahowa da Yar Nan Kuma ta San ba ta Dadi za a kwashe ba meye ya kaita kwasar jiki ta tafi? Ai don ta San in ta fada Mana gaskiya zamu fada Mata shiyasa Ai Bata fada Mana ba ....
"To ai Ni da nace Kai Bello kabi Bayan ta tunda har jauhara ta soma nuna min dacewa da Rashin dacewa sai kace Uwar ta ce ba tawa ba sai gashi dazu ma ana cewa Wai munyi abun kunya Uwar mu ta gudu Amma bamu damu ba to tunda duniya ta soma zagin mu kawai ka Rufe ido ka bi Bayan ta na San Kai ba zaka yarda ka kwana ciki ba in yaso in na Samu kudi Zan mayar maka da na zuwa sai kayi na dawowa tunda Kai dai kana da kudi a yanzu Napep din ka uku Kuma kowace tana kawo wuta ....
"Yo in don zagin duniya ne sa adu ai baka iyawa Dan Adam Kuma Dada Bata son mu Shiga lamarin Dan ta sai ta ganni a kamarun? Ai kawai muyi Mata ADDU AR Allah ya tsare ya maido ta lafiya....
"A a Bello tafiya fa ta Kama ka tun yanzu an soma ga zance ga magana ina ga Kuma wani Abu ya faru? Ai duk shiyyar Nan Babu mu Babu sauran zaman lafiya Ni in ka dawo nace Zan mayar maka da kudin zuwa Amma ai kaima ka San in suka ga zuwan ta garin Nan wallahi Rike Dada zasuyi kaga wata Shiga ukun ce ta same mu in bamu bi Bayan Hamza ba ai zamu Bayan dada .....
A Haka dai Baba Headmaster ya ci karfin baba Bello har ya shirya tafiya kamarun. Kwana biyu da yin hakan Baba Bello ya dauki hanyar kamaru...
Tunda Baba Bello ya tafi na Samu Dan sauki sauki don na San ba Zai dawo ba sai da Dada Kuma ko ba komai duk Rashin mutuncin sa dai ba zai Bari Dada tayi mishi Bataan dabo ba
Na samu sauki kad'an Amma Kuma zuwa yanzy ji nake Babu abinda nake so irin sanin ta yadda kaddarorin Baba na suka fara har kaddarar ta Kara Hawa da mahaifiya ta
Kwanaki bakwai cur kafin baba Bello ya iso garin katsina Amma Kuma shi kadai ya taho Babu Dada Babu wani labarin ta...
Na tarbe shi ina mishi sannu da zuwa Bai Amsa ba sai faman Jan tsaki Yake tamkar zai tsinke hsrshen sa
Ban Isa na tambayi damuwar shi ba bare nabi kadin tsakin bare kuma nace Dada zan tambaya ...
Ina makure naji Baba Headmaster ya shigo Yana Fadin
"Yo Bello ya Nagan ka Kai Daya? Ina dadar ne ko tace ba zata taho bane?
Baba Bello ya Kuma Jan tsaki Yana Fadin
" Sai da nace ba zanje garin Nan ba sa adu ka matsa min kaja nayi asarar kudin mota ta to gashi Nan naje da kyar na iya lalubo muhallin Hamza Wanda nasha da kyar dock nima da kafuran nan sun kula dani da ban tsira ba sai kuma gashi wai Amma Dada Bata je can ba matar sa kahira kawai na Samu a gidan Amma shi hamzan Yana can wurin iyayen matar sa wai ana mishi magani ciwon kafar sa ne ya dawo Amma kuma Wai Dada Bata je ba Ni kuma na san iyayen matar Hamza ne zasu hada da Dada da Hamza su Rike kuma kunga dole suyi hakan tunda namu ne ya jawo mana. Wannan bala in Allah kadai ya San Halin da suke ciki a yanzu....
Na mike tsaye cike da wani matsiyacin tashin Hankali na Dora hannaye na saman kaina ina Shirin kwarara ihu Amma tamkar wacce aka sakawa padlock aka datsewa Baki Haka na kasa ko motsi....
Kan kace me?. Sai ga Yakumbo mariya ta iso tana kuka tana fadin
"Ni Kam Hamza ne ya cuce Ni wallahi kuma ba zan taba yafe mishi ba gashi Nan ina Shirin Rasa Uwa ta
Gida ya rude ana ta koke koke yayin da Baba Headmaster shi da Yakumbo mariya sukayi Shirin wucewa kamarun Don a yanzu kam Basu ga ta Zama ba
Washe gari kuwa Baba Headmaster da Yakumbo mariya suka dauki hanyar kamaru duk da Baba Headmaster yaso su koma da baba Bello Amma yace ba zai je ba su dai suje
Isar su Baba Headmaster da Yakumbo mariya kamarun Kai tsaye Suka Isa gidan Hamza inda Suka same shi kwance karkashin cikin ciwo yayin da dayar kafar da batayi ciwon ba itace ta kamu da ciwon ga Kuma Halin Rashi Hamza Yana cikin jinya matuka Gaya Amma da Yake ba ta shi din suke ba sai suka shiga tuhumar Dada da son Sanin inda ta lakafe...
Sophia wacce take ta kuka musamman da taga Halin da mijin nata Yake sai Kuma tsoro yayi matukar Kama ta tunda taga zuwan baba Bello taji tashin Hankali Mai tsanani ya kamata don in har akwai abinda take tsoro to Bai wuce Yan Uwan Hamza ba don gani take kashe ta zasuyi sai Kuma gashi yanzu taga wasu daga cikin dangin nashi sun Kuma zuwa kwanaki kad'an da zuwan wancan ta tabbatar da ba lafiya ba
Hamza da Yake cikin Halin jinya ya Rame sosai ga Halin Babu ga ciwo ga Kuma wani tashin Hankalin na tahowar Dada Kuma Bata zo ba sai Al Amarin ya dugunzuma shi yaji ina ma Yana da lafiya? Da a yau duk inda dada take sai ya Nemo ta a cikin garin kamarun Amma ina ! Kafa Bata takuwa sai da hikima sai da dabara ...
Sophia kuwa tunda taga fadan da Yakumbo mariya ta iso take ta lafe ta kasa ko motsi Mai karfi don tsoro gare ta matuka Gaya
Wani makocin Hamza ne da Yake da tsananin kirki shi ya Shiga gaba da su baba sa adu aka shiga cigiyar Dada har a kafafen yada labarai na babban birnin yawunde aka Shiga cigiya Babu ji Babu gani Amma shiru Wai Mai kalangu ya fada Ruwa
Kwanaki goma Sha hudu su Baba Headmaster da Yakumbo mariya sukayi a kamaru Babu wani labari Dole suka juyo gida Nigeria suka Kuma baro Hamza bawan Allah cikin Halin jinya Kuma Babu wani tartabin taimako ko saka lalurar shi ta Zama ta su Babu ma Wanda ya Kuma bi ta Kan shi bare tuna Yaya zai Kare ?
Yakumbo mariya kam kuka ta iso gidan tana Fadin
"Na Shiga uku na lalace Hamza yaja Mana janhurun masifa Dada na can ta bace a garin kamarun Kuma Babu ko shakka siddabarun arnan Nan ne da ya dafewa Yar su
Kan kace me ? Gida ya cika dankam da mutane ana ta faman jajantawa juna dada ta b'ace Dada ta b'ace shine kawai abinda ake ta shelantawa Amma maganar su tuna da Halin da bawan Allah baba na Hamza Yake ciki ma Babu don suna ganin shine ma yaja musu hakan don Haka Babu tausayin Halin da Yake ciki bare ayi nufin taimakon sa sai ma kullata da Jin ciwon batan dada da abinda zai faru Kuma da ita .........
Ikon Ubangijin musulunci Kuma Haka kuke? To Allah na Nan Hamza Allah ya kawo maka sauki don alfarmar ANNABI da Al kur ani Amma zumunci Kam ya Zama abinda ya Zama a wannan marrar Dada ina kika makale ke kuwa?
Wannan shine karshen book one kuma karshen free Page sai dai mai bukatar ci gaban 2 3 @ 4 zai tura 1k akan wannan account din 1780003378 Eco bank ko kuma katin MTN akan wannan layin 08035191669
Gidan iko 08035191669
✍🏻 Alkalamin GIDAN IKO💖
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels