Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 6
yi wa wannan ranar ba ne shi ya sa ki ke fadin haka". ooti Wani ciwo mai zafi ya mintsini Fadima, har wayar ta kusa kubuce mata. Ta daure tana jin ciwon ta ce. Hum! Haka dai ka ke fad..." Ta kasa Karasa maganar sakamakon fizgar cibiyarta da a ka yi, ta sa salati tare da sakin wayar. Yana ta faman hello-hello bai ji amsarta ba, sai salatin da ta ke yi. Hankalinsa ya yi kololuwar tashi, ya kashe wayar ya sake kira, amma ta kasa kai hannu ta dauka, sai madodowa 131 1 1 SADAUKARWA-2 ta ke. Mummyn Faanah Daidai lokacin Ladi mai dakin ta shigo da niyyar daukar wani abu ta tarar da halin da Fadima ke ciki, ta nufe ta da sauri tana jera mata tambayoyin me ke faruwa? Tuni Fadima ta fita hayyacinta, don haka da sauri Ladi ta tallabe ta suka fito daga dakin tana kwalawa kawayen Fadiman kira. Duk suka fito, ganin halin da ta ke ciki ya kidima su, suka yi dafifi kowace na fadar albarkacin bakinta, kafin daga bisani Jummai daya matar gidan ta lulluba hijabinta ta shiga gidan Malam Abdullahi ta sanar da su halin da a ke ciki. InnaBaida'u da wasu mata suka shigo suka tafi da Fadima, a na jiran karasowar Isma'i! wanda Malam Abdullahi ya kira a waya ya zo a kai ta asibiti, sai ga Hafiz a sukwane. Tun bayan gama wayar da ya yita kira ba ta dauka ba ya biyo hanyar gidana Ya iso gidan cikin kidima yana tambayar abin da ke faruwa, tausayin Fadima ya narkar da zuciyarsayen tvAllah ya sani yana jin tausayin wannan yanayin da ta ke fuskanta da ya san fokacin SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah al'adarta ya yi da tuni an matso da bikin don ya magance mata matsalar kamar yadda likita ya fada masa. Bai bata lokaci ba ko jin kunya, tunda yanzu ta zamo mallakinsa, halaliyarsa da ya ke ikon yin komai da ita, haka ya runtse ido ya dauki matarsa a kafada ya sa a mota. Fuskantar da Malam Abdullahi ya yi Hafiz kokarin tafiya da Fadima shi kadai ya ke yi,ya sa da sauri ya ba wa Inna Baida'u umarnin ta shiga motar. Ba don haka ba kuwa da sai dai su shafa su ji ba komai, don yana shiga cikin motar da gudu ya ja ta, bai zame ko'ina ba sai Najnoor Private hospital, nan da nan a ka karbe ta a ka ba ta gado saboda fita hayyacin da ta yi. Wannan rashin lafiya ta Fadima ita ta rusa komai, domin har magariba ana kanta don samun saukin ciwon marar da ta ke rakin zai zamo ajalinta. Hafiz na zaune ya rafka tagumi cikin yanayin damuwa da fargaba kada Fadima ta rasa ranta a dalilin wannan ciwon marar, wayarsa ta yi kara. 133 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Yana dubawa ya ga lambar mahaifinsa ce, ya kara a kunne. Alhaji Atiku ya ce. "Wai ina ka shiga ne, tun dazu ina nemanka?" Hafiz ya ce, "Muna asibiti, Fadima ce ba ta lafiya".oi Alhajin ya ce, "Assha, me ya same ta?" sils) Ya ce, "Ciwon eiki ne" d BY "To Allah ya ba ta lafiya, ba maganar daukar amarya ke nan a yau?" uaa Tambaya ce mara bukatar amsa, amma sai da ya ba shi amsar da cewa. oseE tunda har yanzu ba ta cikin hayyacinta Ya ce, "Kuffia wane asibiti ne?"" zrHafiz ya ce, "Najnoor private hospital. Ya ce, "To ga ni nan zuwa om Bayan an gama sallar isha'i ne Alhaji Atiku ya iso asibitin, lokacin Fadima tana bacci, an samu al'adar ta zo mata don haka ciwon cikin ya lafa mata. i Tana kwance a kan gado dankwalinta ya dan zame, ana iya ganin daukar kitson da a ka yi 134 SADAUKARWA-2 Mummyn Fagnah mata, idon Alhaji Atiku a kanta zuciyarsa ta soma luguden uku-uku, wani irin yanayi ya dinga dawainiya da shi. Da kyar ya yi kokarim jan kafafunsa yay fita daga dakin da ta ke kwancе saboda zuciyarsa da ta ke karanta masa kada ya yarda da kaddarar rabuwa da matar da ya ke tsananin Kauna,led i as in ise shet" Walwalarsa ta gushe ya ki yarda ya hada idanu da Hafiz, domin yana ganin kamar idan sun yi musayar kallo Hafiz din zai ga zanen kaunar matarsa rado-rado a kan fuskar mahaifin nasa.2 Murya a cushe ya yi masa sannu da mai jiki, sannann ya yi masa sallama ya tafi gida,Н" Wani abin rudani da tashin hankali da yad riski Alhaji Atiku a wannan dare shi ne rashin nutsuwa, shaidan ya yi kane-kane azuciyarsad yana Kawata masa kyau da cikar halittar matar dansa BWAB0 ned Bb mi Ads saitim sb seeb shis sun s Yana zayyana masa bai dace ya hakura da matar da ta dace da shi ya bar wa dansa ba! Sam wannan ba mai yiwuwa ba ne, shi ya cancanta da auren Fadima. Sai dai anya bakin alkalami bai bushe ba? An fa taru daruruwan mutane kowa yaA shaida an daura auren Hafiz da Fadima, wane 135 a SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah yunkuri zai yi don kwatar matarsa daga hannun dansa? Kwance ya ke a kan gado lokacin da shaidan ke masa wannan kidan shan kabewar a kunnuwa, ya tashi zaune ya zuba tagumi da hannaye biyu, a sarari ya ce. "Hafiz, sai dai ka yi hakuri. Allah ya jarrabe ni da kaunar matarka!" Ya ci gaba da cewa. "Idan dai kai dan halak ne ya kamata ka sadaukar min da matarka, ta zama matata!" Ya karfafa zuciyarsa da wannan kudiri. "Hafiz da ne na halak, mai dumbin biyayya, zai iya yi min komai don ya san na yi masa kowace irin SADAUKARWA, tun daga haihuwarsa zuwa yanzu". Ya janyo wayarsa, ya fara duba lokaci da ya nuna karfe daya da mintina arba'in da bakwai na dare, kawai sai ya lalubo lambar Hafiz ya matsa masa kira. Hafiz yana zaune a gefen matarsa, sam ya kasa sukuni, addu'a kawai ya ke kwararowa Allah ya ba ta, lafiya. Tana kwance idanunta a lumshe tana 136 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Bai amsa masa ba, ya ci gaba da cewa. "Hafiz. ina son ganinka da safe". Hafiz ya ce, "Lafiya Abba?" Kashe wayar da ya yi ba tare da ya ba shi amsa ba ya tayar masa da hankali. Haka ya kwana cikin was-wasi, ko lokacin da bacci ya fauke shi mafarkai ya dinga yi masu razanarwa duk a dalilin kiran da mahaifin nasa ya yi masa da daddare, irin lokacin da bai taбa kiransa ba. Da safe bai bar asibitin ba, sai da a ka ba shi saliamar Fadima. Ya mayar da ita giuan mahaifinta da zummar sai bayan sallar isha'in ranar za su zo daukar amarya. Lokacm da ya shiga gidansu ya tarar da Abbansa zaune a falo, duk da akwai bakin biki. Kallo daya za ka yi masa ka gane yana cikin matsananciyar damuwa, domin fuskarsa ta zayyana yanayin da ya ke ciki. Hafiz ya karasa ya nemi guri ya zauna, ya gaishe shi. Alhaji Atiku ya dubi idanun Hafiz ya gå yadda suka yi jajir alamar bai samu wadataccen bacci ba a daren jiya, ya ce. "Wai a asibitin ka kwana ne?" 137 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Haka nan sai faduwar gaba ta samu Hafiz, tunda ya ke da mahaifinsa bai taba jin ya yi masa magana da irin muryar da ya yi masa magana da ita yanzu ba. Kunya ta kama shi ya kasa amsa masa a can asibitin ya kwana. Alhaji Atiku ya gyada kai, ya ce. "To, je ka ka kwanta ka rama baccin tukunna ka zo ina son magana da kaі”. Musu ba dabi'ar Hafiz ba ne, don haka jiki ba kuzari ya tashi ya nufi sashensa da zai yi masa baccin bankwana a safiyar yau din. Sai dai sam baccin da ya kamata ya yi ya faskara, nazari kawai ya ke, me ya ke faruwa ne? Karfe sha daya daidai ya fito daga sashen nasa, har yanzu Alhajin na falo, sai dai babu mutum ko daya a tare da shi. Abu na farko da ya fara dasa masa zargi shi ne, rashin ganin Hajiya Asiya daga dazu zuwa yanzu, to ko sun samu sabanin da ya sauwake mata din ne ya haifar masa da wannan sauyin yanayin? A darare ya zauna a kan kafet ya yi masa sannu da hutawa. Su duka suka yi shiru na.wani lokaci, kafin daga bisani Alhaji Atiku ya 138 A SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah in a Sa Ba a la ra m ка Ke a e. yi a 0 sa jagorance su su koma can bedroom dinsa, bayan sun zauna ya ambaci sunan Hafiz har sau uku, shi kuma yana amsawa cike da kaduwa. Alhajin ya dora da fadin. "Hafiz, na san a iya tsawon rayuwata na yi kokarin sauke nauyinka a kaina ko?"" Hafiz ya gyada kai. "Ko akwai abin da na kasa da shi?" Ya tambaya idonsa kafe a kan Hafiz. "Babu, ka yi mini komai Abba". Ya fada muryarsa na rawa. "Duk da haka ina yi maka albishir. Anjima zan saka maka kudi naira miliyan biyu a asusunka, sannan na mallaka maka gidajena guda biyu sun zamo SADAUKARWA a gare ka. An zuba komai na aiki a sabon kamfaninka, zan yi dauki nauyin albashin ma'aikata hamsin daga lokacin da suka fara aiki, zuwa wata biyar! Zuciyar Hafiz ta raunana, ba mamaki mahaifin nasa yana jin alamun kamar zai mutu ne a kwana kusa. Ya dago kai da niyyar yin magana, Abban ya riga shi cewa. "Duk abin da zan yi maka ba faduwa ba ce, domin kai kadai ne dana da na mallaka a 139 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah fadin duniyar nan, na san kuma kai mai biyayya ne, duk abin da zan bukata a gurinka za ka yi min shi, haka ne??" Da sauri Hafiz ya ce. "Abba alkawari ne babu abbin da za ka sa ni na kasa yi maka shi, muddin bai tsallake shingen addinin musulunci ba". Alhaji Atiku ya gyada kai yana jin dadin samun makamin da zai yaki dan nasa ya kwaci matarsa, ya сe. "Ka tabbata ina da wannan alfarmar?" Hafiz ya ce, "Ko alkur'ani zan iya dalawa a kan haka". Shiru Alhaji Atiku ya yi yana kallon Hafiz tare da nazarin ya dace ya biye masa ya kafa rantsuwakafin yá bayyanamasa Kudirinsa, domin abu ne mai nauyin gaske. A hankali ya tashi ya isa ga durowar da suke ajiye littattafan addini, ya dauko kur'ani ya ajiye a gaban Hafiz yana dan murmushi, ya ce. "Ba wai ban yarda da kai ba ne Hafizu, ina so dai kawai ka dauki alamarin haka Allah ya kaddara, ka dauki alkur'anin nan ka yi min rantsuwa da shi za ka yi duk abin da na sanya ka. 140 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah ASRANUAGA? "Ba wai ban yarda da kai ba ne Hafizu, ina so dai kawai ka dauki al'amarin haka Allah ya kaddara, ka dauki alkur anih nan ka yi min rantsuwa da shi za ka yi duk abin da ha sanya ka. Ka dai san matsayinsa a gare ka, da kuma illa kauce wa rantsuwar abin da za ka yi da shi" Jikin Hafiz ya yi sanyi kalau, tsoro yarle kama shi sosai, me ke shirin faruwa né da mahaifinsa zai gifta wannan shamakin? Sai kuma ya tuna duk duniya ba shi da kamar mabaifin nasa, haka yana da tabbacin ya yi zurfi auilimin addini, ba zai taßa sanya shi aikatas abin da baab daidai ba, don haka ya matsa ya sa hannu yans dauki alkur'anin yana kallon mahaifin nasa ya cё. "Na rantse da tsarkin mulkin Allah, da darajar da ya yi wa alkur'ani mai tsarkizansw dauwama ina bin'umarnin mahaifina muddin baiм saba wa Allah baoio utnla iy sy xtsH Alhaji Atiku ya gyada kai cikin gamsuwa da rantsuwar dan nasa, sannan ya се твпет в nseuk "Na gode da ka kasance dan, halak Ina sb rokon Ubangiji ya ba ka juriyar abin dai zan umarce ka da shi, Ya kuma musanya maka shi 141 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah da mafi alkhairi daga cikin alkhairanSa" Hafiz ya yi shiru jikinsa na kara sanyaya. "Shin jiya a ina ka kwana tsakaninka da Allah?" Kai tsaye ya yi masa wannan tambayar, shi ma ba tare da jinkiri ba ya amsa masa. "A asibiti wajen Fadima". Ya ce, "Wani abu ya gilma tsakaninku na auratayya? Duk da tambaya ce mai shayar da kunya da mameki, amma a hakan Hafiz ya ba shi arma "Wallahi babu abin da ya shiga tsakaninmu". Alhaji Atiku ya ce, "Za ka iya tuna watarana da muka je unguwar su Alhaji Mande?" Hafiz ya yi shiru cikin nazari. Tabbas ya tuna, a ranar ne ya gane unguwar su Fadima, kusan a ranar ne ma ya kafa tubalin soyayyarsa da ita bayan ya rasa masoyiyarsa Rufa'atu. Ya gyada kai da fadin. "Na tuna ranar". 142 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Alhaji Atiku ya ce, "To a ranar ne na fara ganin yarinyar da na fada maka zan aura, wadda na sha yin istihara ina ganin alheri tattare da ita. Sai dai matsalar da a ka samu lokacin da na tura a bincika min mahaifanta, sai a ka sanar da ni an bayar da ita ga wani..." Dukan kirjin Hafiz ya tsananta. "Duk da yadda na ke jin damuwar rashinta na daure na hakura, amma wani al'amari mai shayar da mamaki, sai ga shi ashe ba wata ba ce wannan yarinyar face matar da ka aura! Hafiz ba zan boye maka ba idan na rasa auren Fadima zan rasa abubuwa da yawa masu muhimmanci na cikar farin cikin rayuwata, don haka a matsayina na mahaifinka da ka fi kowa sanin rashin dacen da na yi na matan aure da ya sa a ke kirana AURI-SAKI, ina rokonka da girman Allah ka.daure ka sadaukar min da matarka. Ma'ana ka saki Fadima na aura!!!"l s Yadda maganganun suka razana Hafiz haka ya mike tsaye a razanen, yana maimaita. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un A umarnin da mahaifin nasa ya yi masa 143 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah bai saba wa shari'ar ubangiji ba, tunda bai kwanta da Fadima ba, ga shi ya gifta ransa da alkur'ani, sai dai fa abu ne mai matukar rudani ya saki matarsa mahaifinsa ya aura! Shi tunda ya ke bai taba jin jarabtaccen al'amari kwatankwacin wannan ba.. Nan da nan gumi ya karyo masa ta hanci ta goshi, har cikin riga ma, jirin da ke neman dibarsa ya tilasta masa komawa ya zauna jabar, yana jin kirjinsa kamar zai tsage saboda tsananin dukan da zuciyarsa ke masa! Tammat! Mu hadu a littafi na uku don jin warwarar wannan kullin, SADAUKARWAr za ta yiwu? Idan ta yiwu mene ne makomar hakan? Wace ce mai sakonnin wayar, da gaske ba Rufa'atun ba ce? Da ma wasu sauran tambayoyin duk sura cikin ci gaban labarin. Mai kaunarku koyaushe. Shagwaba6biyar Daddyn Yusuf 144 Littattafan marubuciyar: RASHIN JINI SADAUKARWA INA HUJJAR TA KE? KAZA DA HATSI WUTAR DAJI... SUNANMU DAYA BAHAGON HUKUNCI Bugawa da yadawa MADAKIN GINI BOOKSHOP Kasuwar Kurmi, Kano City. 08036527328, 07068361426, 07037690966. 08104059156 F Cover Graphics Anka-Graphics fagge 07030319787 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 6 of 6