Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 6
tsarin gidan ba a fara zuwa gurin 'yar gidan sai an nemi izini daga maigidan, shi ne za mu je gaisuwa da rokon iri". Larab ya yi shiru yana wani tunani, kafin daga bisani ya yi murmushin yake, ya ce. "To me ka shirya game da zuwan?" Hafiz ya dube shi, ya сe. "Ban gane me na shirya ba?" 26 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Larab ya cc, "Ah, kana nufin hannu rabbana za mu je?" Hafiz ya yi dariya, ya сe. "To me za mu kai musu?" Larab ya amsa masa da cewa. "Kamata ya yi mu sayi ko dan lemo da abarba ne ko?" Hafiz ya ce, "Ba matsala". Kafin su isa unguwar suka tsaya wajen mai sayar da kayan marmari suka cika ledar viva da su lemo da ayaba, sannan suka doshi unguwar. Gidan su Habib suka fara zuwa, don shi zai yi musu jagoranci. Habib ya dinga dariya, ya ce da Hafiz. "Kai mutumina akwai ka da zumudi, to ai Malam din ba ya zama a irin wannan ranar' Hafiz ya dan harare shi. "Tsiya ta da da kai kenan ba ka cika ba wa komai muhimmanci ba, don Allah ka daina wannan halin naka, sam ba shi da kyau wallahi". Habib ya de, "Daga fadin gaskiya sai ka yi min wannan fassarar? To shi kenan mu je 27 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah idan an tarar ba ya nan kai ka jiyo Hafiz ya ce, "Eh, na ji mu je". Suka doshi gidan a motar Hafiz, da yake layi daya ne a tsakani shi ya sa ba su bata lokaci ba suka isa. Yaro suka samu ya yi musu sallama da Malam Abdullahi, jim kadan ya fito yana ganin Habib fuskarsa ta yalwatu da fara'a, yá ce. "A'ah malam Habibu ku ne tafe?" Su duka suka rusuna don gaishe da shi, ya amsa musu cikin jin dadi. Habib ya ce. "Malam wani sha'ani ne ya zo da mu: game da wannan abokin nawa mai suna Hafiz" Ya Karashe yana nuna Hafiza da ya sunkuyar da kansa kasa. Malam ya ce. "To, ina zuwa" Ya shiga cikin gida ya sa Tahir ya shimfida tabarma a soron gidan, sannan ya dawo waje ya ce su shiga. Suka shiga suka zauna a ladabce. Malam ya ce, "Ina jinka malam Habib". Habib ya gyara zama ya soma da cewa. "Malam wannan abokina ne, ko kuma na 28 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah ce aminina, domin mun dade da shi, na san halinsa da yawa sunansa Hafiz, to shi ne Allah ya hada shi da Batula a inda ta ke koyon na'ura mai kwakwalwa, ya ji yana sonta da aure. Ya same ni da maganar na sanar da shi ka'idar gidan nan, shi ne muka zo maka da zancen" Malam Abdullahi ya yi shiru idonsa a kanCELERT Hafiz, tun da ya ga yaron ya ke jin ya kwanta amasa a rar domin a kallo daya ya gamsu da kamewarsa, sai kuma ga shi ya gurfana a gabansa da sunan ya zo neman izinin tsayuwa da yarsa, wannan ya isa shaidar da Ka gaske yana sonta. Domin a wannan zamanin ba a cika samun matashi kamarsa ya amince da zuwa neman izini don yana son yarinya ba. Amma duk da haka bai yi garajen yanke hukunci ba, illa ya nuna jin dadinsa da faruwar hakan, sannan ya doara da fadin.w sD "Na ji dadi kwarai da wannan karamcin naka, amma wani hanzari ba gudu ba, zan ba Hafizu damar tsayawa da Fadimatu ya nemi soyayya a gurinta don ba na yi wa ya'yana aure da wanda ba sa so, amma hakan za ta 29 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah tabbata bayan bincike da zan gudanar na nasaba kamar yadda ma'aiki (S.A.W) ya koyar da mu" Hafiz ya ji tsananin dadi ya kwaranya a zuciyarsa, domin alamu dun kara tabbatar masa da ya yi dace da 'yar kwarai, wadda Hausawa kan ce mai son IRI NA GARI ya duba gidan Kwarai. Haka suka baro gidan da alkawarin Malam Abdullahi zai tuntu6i Habib lokacin da ya gama bincike a kansa, ya karfi cikakken adireshin mahaifinsa. Da za su tafi suka ba shi dubu biyar, da farko ya ki karba saboda ya nuná musu ba don kudi zai ba su Fadimatu ba. Larab ya nuna masa su ma ba don haka suka ba shi ba, kyauta ce suka yi masa a matsayinsa na mahaifinsu. Ko bai ba su Fadimatu ba a yadda, ya karbi lamarinsu ma ya gode. Da wannan farin ciki Hafiz ya shigo gidan, ya sami Alhaji Atiku a falo yana kallon labaran kasa. A gefe guda kuma Hajiya Asiya na zaune tana ta hura hanci alamun har yanzu ba ta huce ba. Hafiz ya zauna a kusa da kafafun mahaifin nasa, yayin da Alhaji Atiku ya rage 30 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah sautin talabijin din ya dubi Hafiz ya ce. "Ĝa dukkan alamu an samu nasarar abin da aka fita nema ko?" Murmushi ya kara bayyana a fuskar Hafiz ya cе. "Kwarai Abba, an dade. Amma ya сe mu jira shi ya gama bincike". Alhaji Atiku ya dafa kan Hafiz ya ce. "Ina tayaka murna Hafiz, hakika alamu na nuna ka dace da surukin kwarai, Allah ya tabbatar da lamarin" Hafiz ya amsa da, "Amin Abba. Ya ce, "To ni yaushe za a kai ni na gaida surukin nawa?" Kunya ta kama Hafiz ya kasa magana. Alhaji Atiku ya ankare da hakan, ya ce. "Ko don da ya ke a bari sai nan gaba idan tafiya ta yi nisa, wato idan ya gama binciken ya ba ka damar tsayawa da yarinyar... Wai mene ne sunanta ma?" Murya kasa-Kasa Hafiz ya ce. "Fadimatuz Zahra" Alhaji Atiku ya yi dariya ya ce. 31 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah "Ka ga mun yi anko ke nan, don ni ma sunan sabuwar uwar taka ke nan Hajiya Asiya ta ja dogon tsaki tana fadin. "Sabon salo busa usur da asuba". Ba wanda ya kulata yayin da Alhaji Atiku ya ce da Hafiz. "Sai ka dage addu'a dare da rana kana neman zabin Allah, ka kuma yi tawakkali duk abin da ya same ka daga Allah ne, idan ya hukunta matarka ce falillahi hamdihi, idan ma akasin haka aka samu don Allah kar ka zafafa ka yi tawakkali kamar yadda ka yi game da Rufa'atu". Ya salam! Da Alhaji Atiku ya sani bai tabo wa Hafiz zancen Rufa'atu ba, domin da ya koma dakinsa kasa sukuni ya yi. Sakon da ta turo masa dazun ya yi masa tsaye a zuciya, wanda ta ke nufin har yanzu ba ta hakura da shi ba, tana hangen wani sanadi zai dauwamar da su a inuwa daya. Da damuwa ta yi masa yawa ya kasa jurewa sai ya dau wayarsa ya dinga kiran layinta ana sanar da shi a kashe wayar ta ke. Karshe ya tuna da sabuwar lambar da ta yi 32 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah amfani da ita wajen turo masa sakon ya kira, ita kuma ya yi nasarar samunta a kunne amma har ta karaci kararta ba a daga ba. Ba a jima ba kuma sai ga rubutaccen sako ya shigo wayarsa da lambar. Ya soma karantawa kamar haka. "Hafiz ina sonka sosai fiye da yadda baki zai furta, sai dai na rasa yadda za a yi ka gane irin son da nake maka. Wannan dalilin ke sa ni fargaba a duk lokacin da na ji muryarka. Ka yi hakuri ba zan iya daga wayarka ba, ka dai sani ina sonka har karshen rayuwata". Ya sauke ajiyar zuciya lokacin da ya gama karanta sakon. Tausayi mai tsanani ya shige shi, sai yaushe ne Rufa'atu za ta gane ba laifinsa ba ne? Ya takarkare shi ma ya rubuta mata amsa. "Na yarda da kina sona, domin ko halin da ki ke yanzu a ciki na kasa juriya ya tabbatar min da zurfin Kaunarki. To amma ya za mu yi 33 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah da ikon Allah? Mu yi tawakkali mu mikà lamarinmu ga Sarki Allah, idan da rabon za шп zauna a inwa daya sai ki ga wani sanadi ya assasa hakan, domin Allah ba Ya bacci, ba Ya mantuwa a kan komai. Don Allah ki daure ki sanyaya zuciyarki kin ji? Yawan damuwarki na daga min hankali matuka". Bayan ya tura sakon ya dade yana kallon wayar, a bangare daya kuma yana jin kaunarta na kara shiga jinin jikinsa. Har kullum yana hango wa kansu zama a muhalli daya, yana hango Rufa'atu a wani matsayi na rayuwarsa marar gushewa. Samun Fadima a gare shi hanya ce ta kawo sassauci ga dumbin damuwar da ya ke cikina rashin Rufa'atu har ya kan yi kokarin goge shafin soyayyarta a zuciyarsa,amma a wannan lokacin komai ya kunce wa Hafiz, burinsa bai wuce ya ji zazzakar muryarta tana ambata masa yawan kaunarta a gare shi. Burinsa bai wuce yau mahaifinsa ya ce ya amince ya koma wa Rufa'atu domin kulla mu'amalar aure ba. 34 C SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Haka Hafiz ya yi ta juyi yana kallon hotunan Rufa'atu da fatan maido bara zuwa bana. Washegari ya shiga gaida mahaifinsa bayan sun gama gaisawa, Alhaji Atiku ya dubi Hafiz a nazarce ya hango damuwa a tare da shi, tausayinsa ya kama shi. Ko kadan ba ya so ya ga Hafiz cikin halin damuwa yana ji a jikinsa duk lokacin da Hafiz ya shiga damuwa, to Allah zai kama shi da laifin hakan, domin yana ganin kamar ya tauye wa Hafiz hakki ne, amma dole tasa ya hana Hafiz.mu'amala da Rufa'atu. Cikin nutsuwa Alhaji Atiku ya ce. "Hafiz me ke damunka?" Hafiz ya yi malalacin murmushi ya сe. "Ba komai Abba, jiya ne dai na kwana da ciwon kai". Alhaji Atiku ya ce, "Hala ka yi tunani ne? Don Allah Hafiz ka daina sanya damuwa a ranka, kar ka so ka ji yadda nake kasancewa a duk lokacin da na ganka cikin damuwa, sai na ga kamar na kasance mugun uba...." Da sauri Hafiz ya ce. 35 : SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah "Ko daya Abba, ka daina tunanin ba ka yin adalci a gare ni. Wallahi babu hukuncin da za ka yanke min ya zamo cuta". ka ji?" Alhaji Atiku ya ce, "To ka daina damuwa Ya ce, "Insha Allah". Alhaji Atiku ya ce, "Yauwa, da ma ina son sanar da kai an kammala ginin kamfanin nan yaushe za ka je ka gani?" Hafiz ya dago kai da murmushi ya ce. "Kai amma aikin ya yi sauri. Ina ga ko zuwa gobe sai na je ko?" Alhaji Atiku ya jinjina kai ya ce. "Eh hakan na da : na da kyau, amma fa na yi abin da ba ka so, wato na mallaka maka shi halak malak, ba ya cikin kadarorina da idan na mutu za a raba gado da shi" Hafiz ya dan daure füska ya ce. "Kai Abba, wai me ya sa ka ke haka ne komai mai muhimmanci sai ka ce ka mallaka min shi?" Alhaji Atiku ya yi dariya ya ce. "To ai kai ma din mai muhimmanci ne 36 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah shi ya sa na ke SADAUKAR maka da duk abu mai muhimmanci" Ya ce. "Duk da haka Abba ka daina. ka dinga barin kadarorinka a hannunka..." Alhaji Atiku ya tare shi da fadin. "Saboda me? Ka sani ko yau na fadi na mutu 'yan uwana su yi sama da fadi da dukiyata? Amma idan tun ina raye kowa ya shaida na ba ka kadarorina ka ga ko da ta Allah ta kasance bå mai tunanin ya yi sama da fadi da su. Hafiz ya ce, "Haba dai Abba, ai su Baba Aliyu ba za su yi haka ba, don Allah ni ka ma daina kawo mutuwa kusa, ba na son na rasa ka. don idan na rasa ka zan yi kukan gatana ya Kare". Alhaji Atiku ya kai hannu ya dan bugi kafadar Hafiz ya ce. Dan lelen Abbansa. Allah ya sa mu yi tsawon rai mai amfani". Hafiz ya amsa, "Amin" Yana barin gurin Abban nasa wayarsa ta yi kara, ya duba sunan Habib ne ya gani. Cikin 37 SADAUKARWA-2 Muňmmyn Faarlah zumidi ya fauka don yana kyautata zaton bayani ne zai ji game da abar kaunarsa. "Habib. va a ke ciki?" Habib ya ce. "Zumudi sarkin tabargaza ke nan, wato ko gaisuwą ba za ka barimu yi ba. anya Hafiz yarinyar nan ba ta soma zautar da kai ba?" Hafiz ya ce. Tolsarkin jayc-jaye, don Allah kai min bayanin abin da keda akwai, kar ka bata min lokaci. Habib ya ce, "Ah to shi ke nan sai anjima. don ni'ma ina tattalin nawa Hokacin kamar baturen ingila.. Da sauri kuma cikin sarewa Hafiz ya tari numfashinsa da fadin "Kai fa matsalata da kai ke nan. komai sai ka vi masa waśar don Alah be serious. me ka ke son fada min? Habib ya yi dariyayá ce."Ja'iriCidan ba da irin wannan damarBasyausher (zaka langwabe min kamar marayathaka? Hafiz ya yi dariyar da ba tá kai har ciki ba, ya ce. 38 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah "O.K, shi ya sa ka ke gara ni? Mhm, to ni dai na ji na zubda makaman, yauwa Yaya Habib ina saurarenka". Habib ya kyalkyale da dariya, ya сe. "To ai ka san gwamnati ta hana aikin banza, don haka ka kira ni tunda ka san kudina a ke ci ba kuma kai ke turo min katin ba, ko..." Kafin ma ya karasa doki da gajiyawa ya sa Hafiz ya datse kiran, ya kuma bi shi da nasa. Yana dauka bai tsaya jinkiri ba ya ce. "Albishir zan maka, dazun surukinka ya kira ni ya sanar da ni ya ba ka damar ka zo ka nemi soyayya a gurin Batulu..." Dadin da ya shigi Hafiz ba don yana jingine da bango ba hakika da tafiya ya ke ya fadi, idan tuki ya ke da ya kai wa abin hawan da ke gabansa karo. Farin ciki ya sa shi fashewa da dariya sosai. Habib ya ce, "Kai dan tsaya mana, kar ka kashe min dodon kunne, ba auren a ka ce an daura ba. Dama kawai a ka ba ka ka nemi soyayya, idan kuma ba ta amince ba yaro sai a rungumi na Annabawa". 39 SADA SADAUKARWA-2 Cikin dariyar Hafiz уa сс. Mummyn Faanah "Wannan albishir din ya fi daura auren ami gardi a gare ni, domin na san tunda na samu ayar amincewar mahaifinta, samun soyayyarta ma zai zamo abu sassauka, ko ka manta bayanin da ka yi min da ya fitö daga bakin Fadima?" e na iya ai b Allal a 6: njin ám Habib ya ce, "Ban manta ba, saura goron albishir don ungulu ba ta jewar banza". Hafiz ya yi dariya, ya сс. "Oho dai, ai aikin gama ya gama, da dai ba ka fara sanar da ni ba ne ka zo da wannan fatawar, wata kila ka samu 1,500 recharge card... Habib ya katse shi da cewa. Wallahi yanzu ma ba ka isa ba, ko na 750 ne ka turo min, ai na yi kokari ma a haka da na bata lokacina, da kudina na sanar'maka" Hafiz ya ce, "Hmm! Sai ka gan ni anjima ai da daddare..." Ka 341 Habib ya ce; "Tsaya, su fa gidansu ba a tadin 'yan shan minti ato, sai a zo da yamma Ja. idan ba haka ba murna sai ta koma ciki" an Hafiz ya се, "Ко da asuba ma a ka ba 40 3 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah kayyade min zan zo karshen yamma" Yana Karashe fadar hakan ya kashe wayarsa. Ya dade tsaye a gurin yana maimaita kalmar godiya ga Allah da Ya kawo masa lamarin a saukake. Bai san son da ya ke wa Fadima ya kai girman mizanin kasa fasaltawa ba sai a wannan lokacin. Tabbas bayan Rufa'atu bai so wata 'ya mace kamar yadda ya ke jin karfin son Fadima na kutsawa da karfin gaske a cikin zuciyarsa. Ana gama sallar la'asar Hafiz ya shilla wanka, ya murza mai akwai wani dinkinsa da ya karbo jiya na wani farin yadi, tunda yau rana ce mai muhimmanci ya zabi ya saka shi, da so ya yi sai juma'a mai zuwa, to amma zuwa gurin Fadima da kayan abu ne da zai faranta masa rai, a kalla duk ranar da zai dubi kayan zai dinga tunawa da su a ka soma ginin tubalin soyayyarsa da Fadima, Bintu Zahra, Batulu Abdullahi. Da farin ciki sosai ya saka kayan, ya kawo hular zanna bukar wadda a ka yi dinkinta 41 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah da farin zare da baki, haka takalman kafarsa bakake ne, da ya ke aikin jikin tagguwar fari da bakin zare ne, sai komai ya yi cas a jikinsa, ko da ma Hafiz ba daga baya ba wajen faukar ado, ya ko hadu ainun. Hummer Jeep ya dauka daya daga cikin motocin da Abbansa ke ji da su. Gidan su Habib ya fara zuwa, a kofar gida ya tarar da shi zaune a majalissar da sukan zauna shi da abokansa duk yammaci. Habib na hango Hafiz ya mike da sauri ya ba shi hannu suka yi musabiha ya ce. "Yau shi ne farko kuma karshe, ka dai san Zahra kanwa ce a gare ni, ba zan juri zuwa tadi gurinta ba". Hafiz ya ce, "Na ji, mu je don Allah". Suka shiga mota suka zagaya baya zuwa gidan su Fadima. Suna tsayawa da motar, Malam Abdullagi ya fito daga soron gidan da alama wani gurin za shi. Habib da Hafiz suka rusuna suna gaishe da shi, ya amsa tare da cewa. "Malam Hafizu ka samu sakona ke nan? SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah と Na bincika nasabarka, alhamdu lillahi na tarar da mahaifinka mutum nc kamili da a ka ba da shaidarsa, don haka na yarje maka ka cí gaba da zuwa gurin Batulu har ku daidaita junanku" Hafiz ya ji dadi da wannan bayani, su duka suka yi wa Malam Abdullahi godiya, sannan ya koma cikin gidan don sanar da Fadima tana da baki. Suna nan tsaye, wani yaro ya fito daga cikin gidan dauke da tabarma, ya shimfida a kofar gidan sannan ya ce su zauna. Suka zauna jim kadan Fadima ta fito cikin yalwatacciyar shigarta ta kamala. fuskarta kadaran-kadahan ta gaishe da su. Habib ne gaba wajen amsawa, sannan ya се. "Malama Fadima, kamar yadda" na yi miki bayanin abokina, ga 'shi nan na rako shi. na kuma fada masa yadda muka yi da ke, don haka daga yanzu din nan ba zan kuma zama dan rakiyarsa ba". 'Fadima ta yi murmushi ba tare da ta ce komai bá. Hafiz ya ce. "Wallahi ko me za ka ce godiya dai ce 43 SADAUKARWA-2 tsakaninmu". Habib ya mike. ya ce. Mummyn Faanah "Idan ka gama ka same ni gida". Bayan tafiyarsa sai duk su duka suka yi shiru, Hafiz yana kallonta cikin shauki, ita kuma kanta a kasa kunya duk ta lullube ta saboda wannan ne karo na farko da ta taba tsayawa da saurayi tunda ta ke. "Malama Fadima, ina fatan Baba ya yi miki bayanin abin da ke tafe da ni?" Ta yi shiru, ya ce. "Ko da yake bai kamata ma na vi miki wannan tambayar ba tunda shi ya turo min ke. Don Allah ina rokon alfarmarki, kada ki 6oye min sirrin zuciyarki game da ni, idan kin aminta da ni zan yi farin ciki, haka idan akasin haka ma aka samu zan yi farin cikin". Ta dai yi shiru ta kasa magana. Ya ce, "Don Allah ki yi min magana, bana so na shiga hakkinki, ni dai Allah ya sani na kamu da matsananciyar kaunarki, wadda na ke fatan ta kai mu ga aure ban sani ba ko ke kina da wani ra'ayi game da aurenki". 44 SADAUKARWA 2 Cikin sanyin muryarta ta ce. Mummyn Faanah "Ba ni da wani ra'ayi a game da aurena. sai abin da Allah ya za6a min". Ya ce, "Ke nan kin aminta da ni?" Та сс, "Ko da ban aminta da kai don ra'ayin zuciyata ba, zan aminta da kai don cikar nasabarka wadda mahaifina ya bincika ya tarar Ya girgiza kai, ya ce. "A'a Fadima, na fi so ki fada min gaskiya, kar ki so ni don dole, idan kina sona har cikin zuciyarki ki fada min. wallahi ba zan ji haushi ba idan kin ce ba kya sona, sai dai ba zan yi fatan hakan ba, don a zahirin gaskiya ina miki kaunar da ba zan so ki kubuce min ba". Ta dago kai kadan ta dube shi cikin sanyayyen 'kałlonta, kafin daga bisani ta maida kan Kasa saboda ba ta iya jurewa kallonsa, ta ce. "Bayanin ke nan, na amince da kai da zuciya daya bisa dalilai guda biyu da na hanga". Ya gyara zama yana kallonta ya ce. 45 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah "Ina jinki, fada min dalilan". Ta yi shiru kamar ba za ta yi magana ba, Ya lura halayyarta ne haka, kafin ta yi doguwar magana tana sararawa. bai takura mata sai ta yi maganar a dole ba, illa kafe ta da idanu da ya yi yana jin farin ciki sosai a ransa. Ta ce, "Dalili na farko da na amilnce maka shi ne, cancantarka. Don a rayuwata ina son namiji kamili wanda a kallo daya da na yi maka na fuskanci haka. Na biyu, ka cika sharuddan da Ma'aiki (S.A.W) ya koyar mana, wato idan saurayi ya ga budurwa yana so kafin ya tunkare ta ya soma zuwa gurin mahaifinta neman izini. Wadannan dalilai su suka sa na amince da soyayyarka a gare ni". Tana kammala fadar haka ta yi shiru tana murza yatsun Kafarta. Ya yi murmushi ya ce. "Na ji dadi, kuma na gode da wannan karamci da ki ka nunan. Allah ya barmu tare". Can kasan makoshi kamar ba tason maganar ta fito ta amsa, "Amin". Ya ce, "Kin san wani abu, da gaske fa na 46 SADAUKARWA-2 shiga rudani a kanki". Mummyn Faanah Ta dan dago cikin rashin fahimta ta ce. "A kan me?" Yana murmushi ya се. "Ai na yi zaton wanda ke kawo ki mijinki ne, sai da Habib ya ke sanar da ni yayanki ne". Ta yi murmushi, ta се. "Auho! Yaya Isma'il ne, shi ne babban yayanmu". Ya ce, "Haka Habib ya fada min... Yanzu Fadima yaushe ki ke ganin ya dace na dinga zuwa?" Та сc, "Eh to duk lokacin da ka zo ma daidai ne". Ya ce, "Na dauka kina zuwa islamiyya?" Ta ce, "A gida malam ke biya mana duk bayan sallar asuba da isha'i". Ya jinjina kai cikin jin dadi, ya се. "Masha Allah, gobe ai za ki je daukar dárasi ko?" Ta ce, "Insha Allah". Sun tattauna cikin fahimtar juna kafin 47 SADAUKARWA-2 daga bisani su yi sallama. Mummyn Faanah Abin da Hafiz ya lura game da Fadima mace ce mai zurfin ilimin addini, da nutsuw sosai. Wannan ya armasa masa zuciya, yakuma sa shi tunanin ya yi dacen samun mace ta gar ba kwashi kwarab irin wafanda mahaifinsa ya aura ba. WACE CE FADIМА? Malam Abdullahi mai almajirai haifaffen garin Bauchi ne a karamar hukumar Jama'are, neman ilimin addini ya dawo da shi cikin birnin Bauchin, inda daga nan ya soma yin dako a kasuwanni yana dan samun abin kashe, lokacin da ya girma zaman Bauchi ya kama shi tsakaninsa da Jama'are sai dai ziyara. Ya samu ilimin addini mai zurfi, na bokon ne ko A.B.C.D bai taba zuwa koyo ba. Zurfin iliminsa ya sa malamin da ya ke zaune a gidansa tun yana yaro ya wanke 'ya sukutum ya ba shi, wato Hajara ya kuma hada masa da inda za su zauna a cikin gidan nasa, don gidan babba ne akwai bangaren da irin Abdullahi ke zama, 48 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah za su zauna a cikin gidan nasa, don gidan babba ne akwai bangaren da irin Abdullahi ke zama, wato sabbin aure za su zauna kafin Allah ya hore musu nasu, ko kuma su samu karfin kama gidan haya su tashi a saka wasu. s sbbe Tun can baya malam Abdullahi ya kan aTID E) Б zauna wa malaminsa a makaranta, ma'ana yana koyar da daliban makarantar idan malamin na da wani uzuri, don Abdullahi tuni ya sauke alkur'ani da sauran littattafai, don haka ko bayan aurensa ma bai yı kasa a gwiwa ba ya kan yi hakan, sannan ya kan fita neman dari da Sobab ups ase dub na etisd si so a sma 182 a haka Hhar Allah ya albarkace su. da sd wudisd st sd isd dsIIA samun da namiji, wanda suka sa wa Isma'il. USTSU Kudin sunan da Hajara ta samu suna da yawa, ta damkawa mijinta su, lokacin yana da wasu kudın da ya ke tarawa, ya hada ya sai musu (2SIKI fili.LUST sionsIdan ya samu sa faragar kud kdi ya kan je da sun 20 synnisy SS Su almajiran Malam su dan taba ginin gurin har ya ssisM рт ву li s kammala. Lokacin da suka koma gidan da shekaru biyu Hajara ta kuma haihuwa, wannan karon ma namiji ne ta haifa Sablu, bayan shi a 49 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah ハ k al ká A ki dl ki 1 k P la b ka haifi Fadima. Tana da wani cikin ne ciwon sankarar mama ya kamata, wanda cikin lokaci Kankani Allah ya yi mata rasuwa. Wannan rashi ba karamin tashin hankali ya jefa zuri'ar Malam Abdullahi ba, babu wadda a ke tausaya wa kamar Fadima wadda a lokacin ba a jima da cire ta daga mama ba, ga shi Allah ya sako mata kwallafar uwa. Bayan an yi sadakar arba'in a ka wanke Kanwar Hajara mai suna Baida'u a ka ba wa Malam Abdullahi aurenta. Ita ma din dai mai hakuri ce kamar 'yan uwanta, ta rike su Fadima kamar ita ce ta haife su, duk wani abu da uwa ke yi wa 'ya'yanta Inna Baida'u na yi musu, sai dai ita Allah bai ba ta haihuwa ba har kawo wa yanzu. Fadima ta samu tarbiyya sosai, tun tana ;yar shekaru goma sha uku ta sauke alkur'ani mai tsarki. Ta yi karatun firamare da sakandire. Da ya ke yarinya ce mara kula samari don haka da Isma'il ya roki Malam Abdullahi alfarmar a barta ta yi difloma a Gangaren na'ura mai kwalwa bai hana ba, sai dai ya kafa sharadin da 50 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah ta samu miji za ta yi aure, ko ba ta kammala karatun ba, kuma a haka a ke har yanzu. *** *** *** Kafin mako daya soyayya ta kankama tsakanin Hafiz da Fadima, sun fahinci juna sosai duk da dai zuwansa biyu a gidan nasu, amma dai sukan zanta idan ta zo daukar darasi. Abota ta kullu tsakaninsa da Isma'il ta haka ne ma Isma'il din ke dan daga musu kafa idan ya zo daukarta ya tarar suna hira, sai ya jira su zuwa mintoci kafin daga bisani su tafi. Farin ciki na kama Hafiz duk lokacin da ya kasance da Fadima, yanzu ya ture batun Rufa'atu, ya sa wa zuciyarsa dangana don samun lafiyarsa da kwanciyar hankali, duk da ba ta tsagaita da yi masa atisayen sakonnin jaddada ba za ta iya daina sonsa ba har abada. Alhaji Atiku na zaune a falonsa, Hajiya Asiya na gefensa fuskarta ba walwala ta ce. "Alhaji, don Allah ka tsaya ka saurare n1. Ya dago kai ya dube ta, ya ce. 51 S 11 a kc an ka A ka al ki 11 S k d la از SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah "Karshen tsayawa ma a zaune na ke. Ina saurarenki sarkin korafi". Ta ce, "Maganar auren da ka ke shewar za ka kara, da me na rage ka da ba za ka iya hakurin zama da ni kadai ba?" Yana murmushin yake ya ce. "Da abubuwa da yawa Asiya. Idan zan zayyano miki illolinki ke kanki sai kin ji kunya bare ni”. Ta ce, "Lissafo su". Ya ba da nutsuwarsa gabadaya a kanta. "Kin ga na farko kina da matsalar yawan korafi, wanda kin sani ba na son haka amma kullum bakinki ba ya hutawa. Sannan ga ki kazama ke kanki kin san ba Kazafi na yi mi" ni ba?" Ta katse shi cikin jin haushi. "Idan ni Kazama ce to ba sai ka rabu da Ya ce, "Ai na so yin hakan da ki ka kasa gyarawa, amma da na tuna Manzo (S.A.W) bai yi mana umarni da yawan saki ba shi ya sa na kyale ki. Kullum

Chapter 2 of 6