kamfaninsa, to mahaifinsa ma ya turo
masa ko kuma na ce yana kan turo masa wasu
kudaden, shi ya sa ta nan bangaren ba shi da
matsala. Wani abin kayatarwa, tun sauran sati
biyu bikin odar kayan amarya da Alhaji Atiku
ya yi daga Dubai suka iso, don ya ce yana da
halin da zai tallafa wa iyayen matar da da daya
tilo da ya ke da shi a duniya zai aura, bayan
Alhaji Umar ya bayyana masa iyayen Fadima
masu karamin karfi ne.
Tsallen badakaren da a ke yi ke nan da
Malam Abdullahi mai almajirai, wanda ya ke
rokon Allah-Annabi a taimaka a barshi ya yi
105
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
wa 'yarsa aure da abin da ya ke da shi, inyaso
can idan an gama bikin lafiya abin da ya kasa
da shi na amfanin yau da kullum sai a yi. Yayin
da shi kuma Hafiz ya ke ta magiya a yi hakuri a
yi amfani da kayan da a ka siyo din.
Har yanzu ba a tsayar da matsaya a kan
haka ba, amma dai an shirya gidan amarya da
ke Muwinti, Gamji street, duk wanda ya ga
gidan sai ya burge shi, musamman Larabawan
da suka kawo kayan su suka shirya komai a
gidan. Ko a nan kudade ne masu yawa a ka
narka, wannan kadai ya isa gamsar da mutum
bikin dan gata a ke yi.
Saura kwanaki goma bikin, Hafiz yana
gidan nasa shi da Habib suna kara kallon yadda
a ka shirya gidan tsaf, waya kare a kunnensa
yana magana da Abbansa. Ya dafa hangar
sarkafe kaya da ke cikin dakin da a ka ware
musamman domin ajiye suturu, ya ce.
"Wallahi komai ya yi daidai Abba, sai
mutanen nan karshe ne".
Ya dan saurara sannan ya yi murmushi,
ya ce.
106
a
SADAUKARWA-2
ya ce.
Mummyn Faanah
Yana dan sosa keya kamar yana gabansa,
"A'a, kawai dai na yi kewarka ne... Allah
da gaske... to Allah ya lamunce Ya kai mu
juma'ar rai da lafiya"
Ya sauke wayar daga kunnensa tare da
sauke idonsa ga Habib ya ce.
"Yauwa abokina, tafiya Katsina ta tashi
gobe idan Allah ya kai mu, Abba sai ranar
juma'a zai dawo".
Cikin dariyar zolaya Habib ya ce.
"Misali idan mun je: Katsinar sai
Rufa'atu ta burkuce lallai sai ka aure ta. ya za
ka vi?
Ya ce, "Da ma can a burkucenta ta ke..."
Habib ya tare shi.
"To me zai sa mu je?"
Ya ce, "Kawai ina son na ganta. Wallahi
Habib ban taba yin soyayya mai tsayawa a rai
kamar ta Rufa'atu ba, ka ga dai a zahiri na
hakura da auenta tunda Abba ya hana ni, amma
ina jin kaunarta har yanzu a zuciyata"
Habib ya mirgina kai ya ce.
107
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
"Yanzu goben za mu tafi ke nan?"
Ya gyada kai. "Insha Allah".
"To amma kafin mu tafi ya kamata yau
mu leka Fadima. mu ji yadda za mu yi da
'yammatan ko?"
Hafiz ya girgiza kai, ya се.
"Ba dole sai mun je ba. zan wakilta
Sultan ya ba wa 'yammatan dubu hamsin".
Tun kafin ya Karasa Habib ya ke girgiza
kai, ya cc.
"Gaskiya idan ka yi haka ba ka kyauta
ba. domin sai ta ga kamar ka raina matsayin
Raway enta shi va sa ka ti Karlin ka gaa da u
sai ab akinka Iden dai son samu no'ke je
ko yanzu ne zai fi girma da mutunci.
Hafiz ya vi shiru. kafin ya ce.
"Shi ke nan. bari na kira Sultan din sai ya
zo mu je tare ko".
"Ya kamata Larab ma ka kira shi. ko ba
ya gari ne na ga duk hidimar da a ke yi ban da
shi?"
Nan da nan walwalar Hafiz ta gushe, ya
се.
108
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
"Rabu da shi, mun dan samu rashin
fahinta ne”.
Cikin yanayin mamaki Habib ya сe.
"Ban gane ba?"
Nan Hafiz ya kwashe duk abin ya faru ya
fada wa Habib, shi ma ya yi mamaki, ya ce. "Tofa! Kai mutane suna da wuyar
sha'ani, yadda na ke ganin Larab kamar mai
dogon tsinkaye bai kamata in wani abu ka yi
masa ya kasa sanar da kai ba".
Hafiz ya ce, "Ni ma dai abin da na gani
ke nan... Mu je"
Suka fice daga gidan, a hanya Hafiz ya
kira Sultan ya tambaye shi inda ya ke, ya sanar
masa, ya ce to ya jira su za su tarar da shi.
109
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
:
B
KATSINA
abu wanda ya san da tafiyar Hafiz
birnin na Katsina, daga shi sai
Habib gudun kada a samu wani ya
kwarmata wa Abbansa ko Hajiya
Asiya bai sanarwa ba, domin ya san ransa ba zai
so ba, don zai ga kamar ya ki bin umarninsa ne.
Suna tafe suna hira har suka iso Kano, a
nan suka yada zango wajen wani abokin Habib
din suka yi karin kumallo. sannan suka dau
hanyar Katsina.
Karfe dayan rana a Goruba Road unguwar
su Rufa'atu ta yi musu. Sun tsayar da motarsu
nesa kadan da gidan, sun fi kusa da gidan su
Zubaida kawarta. Suna zaune cikin motar
kowanne ya yi shiru, da alama akwai abin da
suke zantawa a zukatansu. Zuwa can Habib ya
се.
"Hafiz, ka ce mun iso unguwarsu, amma
ka barmu a nan, kuma kana sane sarai yau za mu
juya".
110
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
Hafiz ya sauke ajiyar zuciya, ya се.
"Ka san wani abu Habib? Duk lokacin da
zan zo gidan su Rufa'atu sai gabana ya dinga
faduwa, na dinga jin wani irin tsoro mai tsanani
na shiga ta".
Habib ya ce, "Dalilin ya wuce sanar da kai
da Abba ya yi mahaifinta ba shi da nagartar da za
a haďa jini da shi?"
Sam Hafiz bai ji dadin amsar da Habib ya
ba shi ba, amma ya mazance ganin shi ya ja
Habib din ya samu damar furta abin da ya furta.
Ya dan ja tsaki ya bude murfin motar ya fita, ya
nemi wani yaro ya tura ya yi masa kiran Zubaida.
Yaron ya shiga jim kadan ya lito tare da kanwar
Zubaidan mai suna Sadiya 'yar shekaru goma. Ta
risina ta gaida shi ya amsa yana tambayarta.
waye".
"Zubaida kuwa na nan?"
Ta ce, "E, ita ce ma ta ce na zo na tambayi
Ya yi murmushi, ya се.
"Ki je ki ce mata Hafiz ne daga Bauchi".
Sadiya ta koma cikin gidan. Cikin dan
gajeren lokaci Zubaida ta fito fuskarta kunshe da
tsananin mamaki. Tun daga bakin kofar ta ke
111
SADAUKARWA-2
fadin.
Mummyn Faanah
"Hafiz? Yau kai ne a garinmu?"
Shi ma ya tare ta da murmushin, Habib ya
fito suka jera shi da Hafiz suka isa inda ta ke, har
lokacin bakinta a bude. Ta gaishe su, suka amsa
sannan Hafiz ya dora da fadin.
"Kin yi mamakin zuwana ko?"
Ta gyaďa kai tana fadin.
"Sosai kuwa, don lokacin da na tsammaci
zuwanka ba ka zo ba".
Ya ce, "Haka lamarin Ubangiji ya ke. Ki
taimaka ki kira mana Rufa'atu cikin hikima, na
san idan na aika gidansu ba za'a barta ta fito ba".
ba
Ta ce, "Yanzu ına ba zai barta ta fito din
Ya ce, "Shi wa?"
Kai tsaye ta amsa masa.
"Mijinta maná... ai tuni a ka yi wa
Rufa'atu aure, a yanzu haka tana Abuja, ko jiya
mun yi waya da ita na yi mata sannu da jiki
saboda tana fama da laulayi"
Ta karashe maganar cikin yalwata fuskarta
da murmushi. Kallon-kallo a ka shiga yi tsakanin
Hafiz da Habib, kowane yanayinsa ya nuna
112
SADAUKARWA-2
mamaki. Hafiz ya ce.
Mummyn Faanah
"Wai kina nufin tana gidan mijinta ta ke
turo min sakonnin soyayya?"
Walwalar Zubaida ta gushe, ta се.
"Rufa'atun? Kai amma kuwa da ta bata
wayonta. Matar aure da soyayya da wani ba
mijinta ba?"
Da sauri Hafiz ya ciro wayarsa daga aljihu,
ya lalubo ire-iren sakonnin Rufa'atu ya mika wa
Zubaida, ya сe.
"Duba ki gani.
Hannunta har kyarma ya ke ta karba, ta
karanta sakonnin, sannan ta sake karanta lambar
da a ka turo sakonnin. Ta dago kai ta dubi Haliz
ta ce.
"A bayanan cikin sakonnin sam babu
maraba da Rufa'atu, saboda bayan an fasa
aurenka da ita ta jima tana jin radadin rashinka,
ko bayan tsayar da maganar aurenta da Shureim
sai da mahaifanta suka hada da yi mata rokon
Allah. Da kyar a ka samu ta hakura da kai, ta kai
ta kawo ma gabadaya ta maida akalarta ga
Shureim. Wallahi ba ka bi na ba shi rantsuwa
Hafiz, ka ga dai Rufa'atu ba ta da kawar da ta fi
113
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
ni ko? To wallahi Allah har a ka yi bikinta wata
uku da suka shude kai har kawo wa yanzu ba ta
Rara ambata min sunanka ba. Don lokacin da
muke hidimar bikinta ma akwai wata kawarmu
Wasila Aminu da ta san soyayyarku, ta ke
tambayar Rufa'atun ya ta ga haka za ta auri wani
ba kai ba? Idan ka ga yadda ta yi kicin-kicin har
ta fada mata magana mara dadi sai ka tsammaci
da dai duniya ba ta taßa saninka ba. To amma ka
san shi so kamar hawainiya ya ke, yanzu ne zai
juyo. Sai dai ka san wani abu? Wallahi ban taba
sanin Rufaatu da wannan layin ba, layukanta
daga Glo sai Etisalat"
се.
Hafiz ya dauke wuta, yayin da Habib ya
"Babu mamaki ko shi wannan layin daban
ta ajiye shi... Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, kai
jama'a ina za mu da duniya ne?"
Zubaida ta girgiza kai tana fadin.
"Har yanzu ina shakkar Rufa'atu za ta iya
ha'intar mijinta ta yi soyayya da wani bayan ta
san'da auren wani a kantabamma ina zuwa".
Tamika wa Hafiz wayarsa, sannan ta
shiga cikin gidansu. Jim kadan ta dawo rike da
114
SADAUKARWA-2 Mummyn Faunah
Ta mika wa Hafiz wayarsa, sannan ta
shiga cikin gidansu. Jim kadan ta dawo rike da
wayarta, ta ce.
"Karanto min lambar na kirata da tawa, ka
ga sai mu fita shakku ko?"
Bai musa ba ya karanto mata lambar ta
shigar a tata, ta kira. Sai dai wayar a kashe ta ke,
ya ce.
"Ai tun bayan turo min sakonta na karshe
ban kara samunta a wayar ba".
Та се, "To bari na kirata da wancan
layukan nata".
Nan da nan ta kamo Rufa'atu, ta fitar da
maganar yadda za su ji (handsfree), suka gaisa,
sannan ta dora cikin sigar bugun ciki.
"Ashe kin sake yin layin MTN amma ba
labari?"
Rufa'atu ta ce, "Ke kuma matsalarki tada
zaune tsaye. Mijina ya ce ba ya son MTN don
tsabar taurin kai sai na yi amfani da shi?"
Zubaida ta ce, "A'ah to ke dai fadi gaskiya
yarinya, ko wannan ba lambarki ba ce?"
Ta karanto mata wancan layin da a ke tura
wa Hafiz sakonni da shi.
115
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
Dariya kawai Rufa'atu ta ke yi, har
Zubaida ta gama karanto lambar.
"Wai shin na tambaye ki, a mafarki wani
ya ce miki ina amfani da wannan layin ne?"
Zubaida ta ce, "Don Allah ki cire batun
wasa, wannan ba layinki ba ne?"
ne?"
Cikin mayar da nutsuwa Rufa'atu ta ce.
"Wallahi ba tawa ba ce, me ke faruwa
Sanin idan ta ambaci sunan Hafiz ba za su
wanye kalau ba ya sa ta ce.
"Ba komai, zan sake kiranki an jima
Ba ta jira cewar Rufa'atun ba ta kashe
wayar, tare da sauke ajiyar zuciya tana duban
Hafiz ta се.
s0"To kun dai ji abin da ta ce, wallahi ni da
ma na zargi ba ita ba ce, saboda Rufa'atu tana da
hankali da ilimin addini, ta san hakan keta dokar
Ubangiji ne".
Hafiz ya gyada kai ya ce.
"Tabbas al'amarin da ban mamaki... kuma
na yarda ba ita din ba ce"
Habib ya ce, "To wace ce?"
Hafiz ya ce, "Wannan kuma aikin nutsuwa
116
SADAUKARWA-2
ne.
Mummyn Faanah
Zubaida ta ce, "Ahaf! Don Allah ku yi
hakuri na bar ku a tsaye, bari na kawo muku abin
zama
Su duka suka yi murmushi, Habib ya ce.
"Ai zama bai ganmu ba tunda yau muke
son komawa, kuma mun gama abin da ya kawo
mu.
Та се, "Тofa! Amma ko ruwa ai kwa bari
na kawo muku ko"
Ba ta jira wani ya yi magana ba ta fada
cikin gida.
Ta shiga ke nan sai ga Mustapha kanin
Rufa'atu ya fito daga gidansu. Hafiz na hango shi
ya kira shi, Mustapha ya iso da sauri yana fadın.
"Yaya Hafizm barka da rana
Hafiz ya amsa.
"Lafiya lau Musty, ya su Ummanmu?"
Ya ce, "Tana lafiya, ko na koma na sanar
da ita ka zo?"
Sai da ya dubi Habib wanda ya girgiza
masa kai alamar a'a, sannan ya dawo da dubansa
ga Mustaphan ya ce.
"Yanzu ba aikenka a ka yi ba?"
117
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
Ya ce, "E, kati zan karbo mata can
shagon".
"To je ka dawo tukunna".
Zubaida ta fito musu da ruwan, suna sha
Mustapha ya wuce su, don haka da sauri Hafiz ya
ce.
"Zubaida mun wuce, sai wani lokacin"
Suka shiga mota tana yi musu godiya.
Suna gab da fita layin Mustapha ya dawo
daga cikin gidan don ya shaida musu Umman ta
ce su shiga a gaisa, ya tarar da wayam, sai hango
motarsu ya yi tana ficewa daga layin. Hafiz ya
hango shi ta cikin madubin motar, ya yi dariya,
ya ce.
"Ga shi can ya fito, na san cewa za ta yi
mu shiga ciki".
Habib ya ce, "Da kuwa ka yi babban
ganganci, dön na tabbata idan muka shiga sai ta
fada wa mijinta, shi kuma zai iya kalubalantar
mun shiga gidansa ba da izini ba, ka ga komai zai
iya faruwa”.
Hafiz ya ce, "E to, ban ki ta taka ba,
halayya na juyawa a koyaushe, amma dai sanin
soyayyar da Umman Rufa'atu ke min ba na
118
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
Habib ya ce. "Maganim dai kar a yi, tơ
kada a fara
BAUCНІ.
Ihaji Atiku yana zaune a falonsa, A
Hajiya Asiya a gefe ta cada ado
da dandasheshen leshi, wannan
a sabon salon da ta koyo ne bayan
kawayenta sun nuna mata mafita don dakusar da
auren da maigidan nata ke yunkurin yi. Sun ce
tunda babban Kalubalen da ya ke kokawa game
da zamansu rashin tsafta ne, to ta dage ta cike
wadanman guraban don su samu ko ya ya ne su
dauke hankalinsa daga kan wasu matan. Saboda
haka kafin ya iso garin jiya da daren juma'a ta
kimtsa gidan bisa jagorancin Kannenta da ta
gayyato.5e ei
Matuka Alhaji Atiku ya yi mamakin
sauyin da a ka samu, kuma ya ji dadi kwarai da
gaske a ransa, domin yana son zama da Asiya,
matsalar da ma ita ce rashin tsaftarta, idan kuwa
ta gyara ai shi ke nän.
119
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
S
N
C
n
gi
fa
m
iy
ha
SO
Kudade ne a gabansa masu yawan gaske,
yana ta kasafi, ita kuma tana binsa da ido, ta san
dole dai ta tashi da nata kason ko da na wucin
gadi ne da za a samu a rarar cefane ko wani abun
na daban.
Alhaji Umar ya yi sallama da fara'a ya ke
amsa sallamar, yana fadin.
"Yauwa karaso".
Hajiya Asiya ta mike tana yi masa sannu
da zuwa. Ya karasa yana amsa gaisuwar Hajiya
Asiyan.
Bayan ya zauna suka sake gaisawa, sannan
Alhaji Atiku ya cc.
"Da ma yanzu na ke ware kudaden,
wancan (ya nuna gurin), dubu dari da hamsin ne
وو kudin sadaki, wancan...
din".
Alhaji Umar ya katse shi.
"Ai dubu ashirin suka ce za a bayar".
Ya ce, "Na sani, amma a ba su wannan
Girgiza kai Alhaji Umar ya yi, ya сe.
"Ba a haka Alhaji, ya kamata ka dinga
nazari, zamanin nan fa ba irin na da ba ne, an bar
kiwon dabba sai na mutane...
120
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
nazari, zamanin nan fa ba irin na da ba ne, an bar
kiwon dabba sai na mutane..."
Shi ma ya tare shi da cewa.
"Mene ne a ciki don na biya sadakin Hafiz
dubu dari da hamsin?"
a
Alhaji Umar ya ce, "Babu wani aibu, sai
dai ka lura, mutumin nan malami ne, kuma ya zo
da yakana bai kamata a nuna masa iyakarsa ba,
nuna masa auren kudi za a yi da 'yarsa ba. Ka ga
yanzu ma da kyar muka shawo kansa game da
kayan dakin yarinyar, kuma sai a je masa da
linkin balinkin sadakin da ya yanka wa 'yarsa?
Gaskiya hakan bai dace ba, ai sai ya ga kamar
sayen 'yar za mu yi".
Alhaji Atiku ya yi shiru na wani lokaci
yana nazari, kafin daga bisani ya се.
"Shi ke nan, za a cire dubu ashirin din
sadaki, sauran kuma sai a ba shi kyauta ya kara a
hidima".
Alhaji Umar ya yi takaitaccen murmushi,
"Alhaji ke nan, duk inda a ka 6illo maka
دو sai ka zame
Shi ma yana murmushin ya ke cewa.
"To saboda Allah bayan Hafiz wa na ke da
121
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
shi? Shi fa kaďai ne kwallin kwal dana a duniya,
don haka duk abin da na mallaka
,י SADAUKARWA ne ga rayuwarsa
Alhaji Umar ya mirgina kai.
"Da wannan kam, amma dai wasu
abubuwan sai a dinga tsagaitawa saboda akwai
sauran masu hakki a kanka"
Ya karashe maganar yana duban Hajiya Asiya da ta yi zugum tana jin tsantsar takaicin
rashin haihuwa, har maigidan nata ya ke kasaftar
da dukiyarsa don ya nuna mata iyakarta.
Alhaji Atiku ba tare da ya dube ta ba, ya
сe.
"Kada ka damu, duk wanda ke da hakki a
kaina ina sane da shi (ya nuna wani daurin
kudin), wancan dubu dari ne na Asiya ne ta yi
hidimar biki (ya sake nuna wani daurin), can
kuma dubu dari biyu da hamsin ne na abinci da
abin sha da za a ci. (Ya nuna na gabansa), nan
kuma dubu dari biyu ne kai da su Yaya Aliyu,
kowa dubu hamsin-hamsin".
Alhaji Umar ya ce.
"To mun gode, Allah ya kara arziki, Ya
jikan tsaffi da rahama".
122
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
Su duka suka amsa da, "Amin".
Ya ce, "An jima zan aiko muku da naku
katin gayyatar".
"Ba laifi, idan ka shirya muna iya tafiya
gidan surukan namu".
Ya ce, "A shirye na ke, Asiya ki dauki
kasonki da kudin cefanen ku je kasuwa da direba
da su Hajiya Rabi ku sayo duk abin da a ke
bukata".
Ta ji dadin wannan umarnin, ko banza nan
ma za ta kara cika jakar tata da 'yan ragowar
kudin siyayyar.
Suka fito daga gidan suka nufi unguwar su
Fadima. Suna tafe suna labari, Alhaji Umar na
koda yakana da cikar haibar mahaifin Fadima.
Gaban Alhaji Atiku ya dinga faduwa sakamakon
tunawa da tasa Fadimar da ya yi wadda wani ya
kasa shi lokacin da Alhaji Abubakar ke bayyana
masa sun iso unguwar surukan Hafiz, wadda ita
ce unguwar da Alhaji Mande abokinsa ya ke.
Kofar gidan damkan da almajirai, duk da
cewa sun tashi daga karaţu, sai dai wasu na nan
cikin rumfar kofar gidan da ke jibge da alluna
Tun a nan farin ciki ya kama Alhaji Atiku,
123
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
AXUADAR saboda yana ganin da alama Hafiz zai dace da
'yar kwarai, ba irin matan da ya aura ba.
5 Har cikin soron gidan dattijo mai cikar
kamala Malam Abdullahi ya sauki su AlhajiR
Atiku, sai haba-haba ya ke da su, da alama
mutum ne shi mai son mutane da sanin darajarsu.
Ya zauna a ka gaisa a mutunce, ya tura almajirai
cikin gida suka kawo musu ruwa mai sanyi, sukak
sha babu nuna kyama. Abin da ya burge Malam
Abdullahi ke nan. stud
re0 Bayan sun dan taba hira, Alhaji Umar ya
ce.swogST HSY
"Malam Abdullahi, wannanshi ne
mahaifin Hafizu, ya zo ku gaisa, sannan mụn
kawo kudin sadakin Fadima"e ets suuesmios
Malam Abdullahi ya ce, "Masha Allah, na
ji dadin sada zumunci da ku ka yi, Allah ya yi
albarka a cikin lamarin".
Se Su duka suka amsa da, "Amin". Sanna
suka gabatar da sadaki da kuma kyautar da Alhaji
Atiku ya yi masa, wanda sai da suka kai ruwa
rana kafin yа катба, skneh nebig OK
ប
Suna zaune suna dada zantawa ke nan
Fadima ta shigo soron ita da kawayenta guda ulia is A B ay ills Rit Den T
24
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
Wani irin tashin hankali Alhaji Atiku ya
tsinci kansa a ciki lokacin da idanunsa suka yi
arba da na Fadima, kada dai a ce ita ce matar da
dansa Hafiz zaj aura?
Malam Abdullahi ya zo masa da amsar
tambayar da ya yi wa kansa.
"Yauwa, ai ga ma surukar taku nan. Batula
wannan shi ya haifi Hafiz".
Wata irin kunya ta lullube Fadima, har ta
kasa motsin kirki, muryarta Kasa-Kasa ta sake
gaishe da su. Rudanin da Alhaji Atiku ke ciki ya
hana shi amsa gaisuwar, idanunsa kyam a kan
Fadima, ya aksa kawar då dubansa daga gare ta.
Damuwa da fargaba suka dinga dabaibaye shi
kamar huhun goro.
Fadima suka tashi don shiga cikin gidan,
Malam Abdullahi ya dan dubi Alhaji Atiku, haka
nan sai ya tsargu da irin kallon da ya ga yana yi
wa 'yar tasa, ko yana nazartar ba ta dace ta shiga
cikin zuri'arsa ba ne? Ya dan muskuta da fadin.
"Ai Alhaji ba zan iya fasalta muku
tsananin farin cikina ba. Kun yi mana dukkan
halacci, a wannan zamanin duk mutumin da zai
so hada jini da naka ai ba ka da kamarsa".
125
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
Alhaji Umar shi ya ke amsa masa, yayin
da uban gayyar ya tafi kololuwar nazari, ta
tabbata Hafiz shi ne jarumin da ya ba shi kaye ga
wadda ya kwallafa rai da ita. Fadar ma ya shiga
tasku bai taso ba, domin abu ne da ya zo masa a
bazata. Ko a mafarki bai taba tunanin yarinyar da
ya gani yana so ba ita ce talliron dansa zai aura
ba.
Ya dan muskuta kaďan ya kalli Malam
Abdullahi, amma kallo daya za ka yi masa ka
fahinci rudanin da ya ke ciki, sai dai da ya ke
jarumin gaske ne da ya dade yana gwagwarmaya
a duniya, sai ya sakaye damuwarsa a iya
fuskarsa, muryarsa ba ta nuna damuwar ba, ya ce.
"Ni kaina na ji dadin yadda Hafizu ya yi
dogon nazari yayin fidda matar aure. Allah ya
jagoranci lamarin".
Su duka suka amsa da, "Amin".
Sannan suka yi yunkurin tafiya.
Hår wajen mota Malam Abdullahi ya rako
su, suka tafi Alhaji Atiku ya yi tsam da ransa
yana nazarin hanyar da zai 6illo wa lamarin.
***
126
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
Duk yadda Alhaji Atiku ya dauki lamarin
ya, wuce nan, domin tun a ranar da suka dawo
daga gidan su Fadima ya tsinci kansa dumudumu cikin sabunta soyayyarta, bacci sam ya
kaurace wa idaniyarsa. Tun yana 6oyon
damuwarsa shi kadai, har sai da ta kai ta kawo
Hajiya Asiya ta fahinci akwai abin dá ke
damunsa, ta shiga damuwa sosai saboda ta san
damuwarsa ba za ta rasa nasaba da auren da ya ke
son yi ba, domin har yanzu ba ta yarda ya janye
maganar auren ba, tunda ba ta ji daga bakinsa ba.
Saboda haka, funda ta fuskanci yanayin da
ya ke ciki ta ke ayyana auren ne ya ke son vi shi
ya sa ya ke ta yi mata kunci, wannan dalilin ne ya
kassara zaman lafiyarsu, duk da da farko ta
kwantar da kai da bin yarima don shan kida ta
yashi rabonta a dalilin auren Hafiz din.
Ya yi biris da atisayen da ta ke masa na
bakaken maganganu, don ba damuwarta ce a
gabansa ba.
Hafiz kuwa, hidimar aurensa ce ta dauke
hankalinsa, ba wai bai fahinci akwai abin da ke
damunsa ba, a'a yana ganin kamar duk hidimar
bikin ce ta sauya shi haka.
127
1
1
1
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
A bangare daya har ana gobe daurin aure
bai rabu da tunanin wace mace ce ta dinga yawo
da hankalinsa ta hanyar zarge zuciyarsa da
sakonnin soyayya ba. Abin yana. shayar da shi
dumbin mamaki, shi dai ba tarkacen 'yammata
gare shi ba ballantana ya ce a cikinsu ne wata ta
kasa shanye dafin sonsa ta ke masa wannan
makauniyar soyayyar ba.
Haka ya yi nazari a cikin 'ya'yan dangin
Abbansa babu wadda ya canko da za ta iya yi
masa wannan basajar soyayyar, ciki kuwa har da
Nusaiba yar Alhaji Aliyu, don haka ya zubar da
lamarin a kwandon shara bisa hujjar tunda dai ya
samu tabbacin ba Rufa'atu ce ke cikin matsatsi
ba da sauki, koma wace mace ce ita ta ji za ta-iya
dora wa kanta dala ba gamə tunda ta ki bayyana
kanta. Dadin da ya ke jin ma bai wuce idan ya
tuna sakonta na karshe ba, da ta yi alkawarin
2 Gacewa a duniyarsa, hakan na nufin ya kwashi
f matacciyar soyayyar da ba ta zo gare shi da
n numfashi ba ya kai ta kushewa.
P
h
Tabbas ya tausaya wa kowace ce, amma
bai kai ya tausayin kansa na rabuwa da lissafin
dokin ranonsa ba.
S 128
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
bai kai ya tausayin kansa na rabuwa da lissafin
dokin ranonsa ba.
Da ya ke Fadima da shi kansa ustazai ne,
sai ba su shirya wani abin ku zo ku gani na bidi'a
ba, kamu kawai a ka yi, sai wa'azi da saukar
Fadima, amma dai duk wanda ya halacci bikin
.sai abin ya kayatar da shi, saboda zamani ya
wuce na auren matashi mai abin hannunsa kamar
Hafiz da a ka yi aurensa ba tare da bidi'o'i ba.
Wannan kam ya kafa tarihi a duk fadin jihar
Bauchin,Yakubu, abin koyi ma ga sauran matasa.
Misalin karfe biyu da rabi na ranar asabar
a ka daura auren Hafiz Atiku Bauchi, da
amaryarsa Fadima Abdullahi Mai almajirai,
daurin auren da ya samu halartar manyan mutane
daga Gangaren Alhaji Atiku zuwa ga ango shakurukundum! Ana ta hada-hadar arziki, kowa
na taya Hafiz murnar ganin wannan rana ta
aurensa.
Amarya Fadima na cikin kawayenta bayan
sallar la'asar ke nan a gidan makotansu, inda
suke zaman amarci, wayar da tuni Isma'il ya
129
SADAUKARWA-2 Mummyn Faangh -АТЛАНИAGAZ
sallama mata ita duk da Hafizya so-mallaka mata
waya a Ra auJT FRFidansa tukunna ce ya bari
wayar ta soma 6urari alamar ana kira. Ko ba ta
duba ba ta sansenel ine eb u BY B
wanda ya kira, wato angonta, farin
Alainia sa insg ul os is mids insW BYTO ve bo the
yi murmushi tana satar kallon.
Kawayenta da sukabawம் üba mata idanu, kunya ta 165, காமகா
ebodez ide, eb E x os t2
hana ta daga wayar a gabansu, dole ta fice zuwa
dakin dayarud matar don ba za ta sake a gaban nide isra idastsm дзз вD СCПM
kawayen nata ba. Suka bi ta da kallo suna dariyar
tsantsar kunya irin ta "Fadima kamar ba yar
zamanı ba.
287L δς ως κολι spτ Sκρπ' X BRnCμI!
"Haba Zuhuriyyah, duk kin daga min
hankali, ina ta kira ba ki daga ba?"
160a€ikin sanyin muryarta gilsaiM da ke kassara duk
wani tanadi nasa ta ce susH
EULGO
ii idelubdA. soibe
SLUSD
BZISVISNIS
"Ka yr hakuri. Ina
pai
cikin
23 mutane AS GS neLCD
shi
ya சார் பிசி
sa kaca ga ban daga ba
ognn yaceu syeh
Krce kawai za a jigatar min da ke 18bed-sha BI SIழாமிde yadda idan n 6ki iya moro ba? 8818BH BVI Kunyaubeta, a yt shiru. 80
BRIDIUS
Ya ce, "Allah ina girmama wannan ranar,
saboda ta zamo min daya daga cikin ranakun
farin cikina. Yanzu haka ba ki ji yadda na ke i
AT li'amel imn ab RVEW JOIems nernBs Sue
חבז
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
ba, wallahi ban ki na bude idanuna na ga an
kawo min ke ba yanzu... don Allah me zai hana a
sassauta lokacin maimakon bayan isha'i a kawo
ki karfe shida?"rut
Ta daure cikin jin nauyi, ta ce.
VAa Kila ma sai gobe"
Da sauri ya се.
"Haba dai! Na yi ya ya ke nan da zuciyata
da ta kasa hutawa a kanki?"
tenTa ce,"Sai ka yi yadda ka ke yi da".
ngida Ya ce, "Ke ma wasa ki ke, ba ki san
dumbin tanadin da na