Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 6
ina ganin za ki gyara wannan matsalar shi ya sa na ke zaune da ke". b つ SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah "Malam! Kawai kana son labewa da guzuma ne ka harbi karsana, ka rasahujjar da za. ka kafa gudun kada a maimaita sababben sunan naka na AURI-SAKI shi ya sa... To ina yi maka albishiri wannan karon ba 'yar iskar yarinyar da ta isa ta shigo gidan nan ta raina min hankali... a bar ni ma da zafin rashin ganin kwaina a duniya ba za a yi ba, sai an kawo min annoba". Ya dinga murmushi jin ta hau sama, ita kuma abin da ya kular da ita ke nan, ta ce. "Sannan maganar tafiyarka Lagos, na ji kana cewa wai a nan za ka bar ni. Ban gane wannan wankan kura da sabulun ba?" Ya ce, "Asiya matsala! Asiya mita! Asiya korafi! Ni yanzu na zauna don na huta a cikin gidana amma kin hana ni". Cikin tsiwa ta ce. "Ai kai ne ba ka so hutawar ba. A bugi kuturu a hana shi zuciya?" Ya ce, "To yanzu me ki ke so a yi?" Та се, "Ка fi ni sani!" Ya yi dariya yana gyada yatsa. "Hmn, aure dai babu fashi in Allah ya 53 SADAUKARWA-2 Mummyn Faangh 711 ha S ke an ka A ka : ka 111 3S ki di la bi yarda. Lagos kuma ni kadai zan je idan kin ji za ki iya zama a nan ki zauna, idan ba za ki iya ba ki yi duk abin da za ki yi". Ta ce, "Kana nufin ko tafiya gidanmu na yi ba damuwarka ba се?" Ya zakuda kafada cikin tabbatarwa. "Kwarai kuwa, don na fita hakkinki. Don zan tafi Lagos wajen aiki saboda ni ne lalle sarkin aure sai na ce sai na tafi da ke?" Ta mike tsaye tana sobare baki. "Da ma na sani ba sona ka ke ba, bakin zalunci ne ya hana ka sauwake min..." Ta kai kofa za ta fita ya daka mata tsawa ransa a matukar Gace, dole ta ja ta tsaya. Ya ce, "Idan kina cin kasa ki kiyayi ta shuri Asiya, bari ganin ina biye miki za ki raina min hankali. Ki fada min kin gaji da zama ki gani idan ban sauwake miki ba, sakaryar banza kawai, ana hakurin zama da ke amma sai kin kai mutum bango? Bace min da gani". Ya Karashe cikin hasala. Ta wuce dakinta tana jin takaici a ranta, wannan danniya ce kawai a ke nuna mata, sarai 54 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah 4 ya sani zaman hakuri ta ke da shi. amma bai duba hakan. bai nuna mata kulawar da kowace mace ke muradi a gidan aurenta, ta yi hakuri ta zauna da shi a hakan amma zai dinga gasa mata maganganu yadda ya ga dama? Kudinsa ne ya sa ta'ke zaune da shi har kawo wa yanzu, ba don haka ba da a yau za ta nemi takardarta ko ita ma ta je ta haihu a wani gurin kamar yadda ta samu labarin Hajiya Suwaiba ta haihu a inda ta yi aure. Bayan fitarta ya ja wayarsa ya lalubo lambar Alhaji Mande. ya kira ringin biyu va dauka: Suka gaisa. sannan ya cc. "Alhaji Mande, game da maganar yarinyar nan ne. Ina fatan ka samu zama da mahaifin nata?" Alhaji Mande ya ce, "E, jiya na je na same shi. Amma an samu matsala, domin bayanin da ya yi min a cikin satin nan ya karbi bakuncin wani yaro da ke sonta, har ya ba shi aurenta" Alhaji Atiku ya ji maganar kamar saukar mashi a zuciyarsa. Da sauri ya ce. 55 ce. SADAUKARWA-2 "Subhanallahi". Mummyn Faanah Alhaji Mande ya kwantar da murya, ya "Wallahi abin babu dadin ji, ga shi na san shi mutum ne kaifi daya, ba don haka ba da יי mun bi ta wata hanyar..." ya ce. Alhaji Atiku cikin bayyanar da dauriya "Kada ka samu damuwa, Allah ya sa haka shi ya fi zama alkhairi, amina kwarai na so auren yarinyar nan saboda na hangi alkhairai da yawa a tare da ita. Kuma tun ranar da na fara ganinta na ke istihara a kanta, alkhairin dai na gani". Alhaji Mande ya ce, "Ai ko yanzu ba fidda rai za mu yi ba, domin ba a aurar da ita ba. Addu'a za a dage yi idan da rabon aure a tsakaninku sai ka ga Allah ya tabbatar". Alhaji Atiku ya ce, "Na gode, gobc idan Allah ya kai mu zan yi fakin Lagos din fa". Alhaji Mande ya de, "Tow! Ashe tafiyar har ta zo? Allah ya sa alkhairi, Ya sa kana dawowa a ba ka damar yin ritayar 56 SADAUKARWA 2 Mummyn Faanah Alhaji- Atiku ya yi murmushi, ya cc. "Amin dai". Ya kashe wayar damuwa ta dabaibaye shi, tun ranar da ya soma ganin Fadima ya kasancecikin fata da burin ta zamo matar aurensa, saboda a kallon da ya yi mata ya hango abubuwan da ya rasa a sauran matan da ya aura. Yanzu shi ke nan ya ga samu ya ga rashi? nes Har dare yana cikin wannan yanayi, Hafiz ya same shi a harabar gidan suna magana da maigadi. Alhaji Atiku ya dubi Hafiz cikin damuwa. ya сe. "Yauwa Hafizu, ka kai masa sakon?" Hafiz ya ce, "E, na kai. Amma ban tarar da shi ba sai da na jira shi ya dawo. Ya ce a yi maka godiya, Allah ya kai ka lafiya ya dawo da kai lafiya. foskod Alhaji Atiku ya ce, "Amin... don Allah a shirya min mota don da wuri zan tafi". s Hafiz yana sosa kai ya се. "To Abba, kuma..." Sai ya yi shiru. 57 SADAUKARWA-2 cikin gidan, ya ce. Mummyn Faanoh Alhaji Atiku ya senm aaku don nuf "Kuma me? Zo mu jesesciki ka fada min", Suka karasa cikin falonAlhaji Atiku ya zauna a kan kujera, yayin da shikuma ya zauna a kan kafet kansa a kasa. "Ina saurarenka" Cikin sanyin murya ya се. "Da ma cewa na yr no yi zaton kafin ka tafi za a tura gidan su Fadima Alhaji Atiku ya ji gahonse ya fadi saboda tunowa da ya vi da tasa usalar. ya dan kafe Hafiz da ido, ya ces "Sun bukaci hakan ne?" r.Hafiz ya ce, "A'a, gani na yi daí ya daçe a tura din ba sai sun nema ba". Ee dz se Alhaji Atiku ya ce, "To shi ko nan. Lokaci ya kure min, amma zan wakilta Alhaji Umar ya bincika min nasabar yarinyar kafin a .tura وو Hafiz ya yi mamaki kwarai, don ya san wancan lokacin tare da Alhajin a ka je Katsina gidan su Rufa'atu neman aurensa, kodayake 58 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah yanzu bai kamata ya yi mamaki ba idan ya yi la'akari da Alhajin zai tafi Lagos ne, kuma babu lokaci saboda aiki ko ya dawo ba zai wuce hutun karshen mako ba, sai dai duk da haka ya yi tunanin zai ce sai ya dawo din zai bincika da kansa. Alhaji Atiku ya katse masa tunani da fadin. "Na so a ce ni zan yi wannan binciken, domin ina son ka auri 'yar gidan kwarai, 'yar manyan mutane da suka san mutuncin kansu da wanda ya rabe su, amma yanayin tafiyar da zan vi dole zan wakilta Alhaji Umar din..." Hafiz ya tare shi cikin girmamawa. "To Abba, ko dai a bari sai ka dawo?" Da sauri Alhaji Atiku ya girgiza kai. "A'a. Kada ka damu, na san insha Allah yadda zan yi binciken shi ma zai iya. Allah dai ya sa a dace da wadda a ke nema". Murya kasa-Kasa Hafiz ya ce, "Amin”. Alhaji Atiku ya ce, "Sai ka je ka same shi ka yi masa bayanin gidan nasu". Yadda ya yi maganar kamar cikin 6acin 59 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah rai ya daga wa Hafiz hankali, sai ya ga kamar ya yi masa abin da bai dace ba, wato rashin alkunya! Har ga Allah bai yi masa maganar don rashin kunya ba, illa kosawa da ya yi Fadima ta shigo gidansa, yana tsoron jinkirin ya haifar da rashi kamar yadda ya rasa Rufa'atu. Cikin sanyin murya da rashin kuzari ya се. "Don Allah ka yi hakuri Abba idan na ata maka rai". Alhaji Atiku ya yi murmushin yake. "Me ka gani?" Hafiz ya ce; "Na ga kamar ranka ya Басі". Alhaji Atiku ya girgiza kai ya ce. "Ko daya Hafizu, ba ka fata min rai ba. Ai ni babban farin cikina na ga ka yi aure. Wallahi ba zan iya fasalta maka murna ta a kan wannan lamarin ba... kaina ne kawai ke ciwo shi ya sa ka gan ni haka". Hafiz ya yarda da abin da mahaifin nasa ya fada, saboda ya sanshi da fadar gaskiya. Duk abin da Hafiz ya yi masa cikin kuskure ko rashin sani kai tsaye ya ke zaunar da shi ya 60 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah nusar da shi. Sai ya yarda ciwon kan ne ya sauya shi haka, ya ce. "To Allah ya ba da lafiya Alhaji Atiku ya ce, "Amin" Ya mike tsaye alamar yana son Hafiz din ya ba shi guri. Fahintar hakan da ya yi ya sa tun kafin Alhajin ya soma taku ya yi saurin mikewa ya ce. "Bari na fara shirya kayan" Alhaji Atiku ya ce, "Ba laifi". Don kada Hafiz ya gane korarsa ya yi sai ya nufi dakinsa. Hafiz yana cikin shirva kayan mahaifin nasa wayarsa ta yi kara. Ya ciro ta daga aljihu ya ga sabuwar lambar Rufa'atu ce wadda yawan turo sakon da ta ke masa ya sa dole ya adana ta a cikin jerin lambobin da ke kan wayarsa. Yana kallon wayar yana tunanin ya dauka ko kada ya dauka, har kiran ya katse. Yana kokarin mayar da ita aljihu wani kiran ya sake shigowa, ya danna malatsin amsawa, sannan ya kara a kunne tare da yin sallama. Ba a amsa masa ba illa shesshekar 61 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah kukanta da ya jiyo. Hankalinsa ya yi matukar tashi, komai ya kunce masá, nan da nan ya kidime yа се. "Don girman Allah ki daina kukan nan haka, wallahi kina daga min hankali. Ya kamata mu yi hakuri mu mika wa Ubangiji lamarinmu". Ya dan saurara don jin ko za ta ce wani abu, amma ba ta ce din ba, ba ta kuma daina shesshekar kukan ba. Ya buda baki zai yi magana ta ji ta kashe wayar. Rufa'atu tana da babban matsayi a rayuwarsa. ba ya iya tsallake uzurinta. don haka a take va bi ta da nasa kiran. Tana ta kara wayar ba a daga ba, ya kira ya fi sau hudu ba amsa. Ransa ya baci, yana mamakin halinta, ta kasa hakuri da shi, idan ya kira ta kuma ba ta daga wayarsa, ta ya zai shawo kanta? Ya ja tsaki ya mayar da wayar cikin aljihu ya ci gaba da aikinsa. Yana jin Karar, wayar tasa alamar shigowar sako ya yi biris, don ya san daga Rufa'atun ne. Sai da ya kammala komai ya shiga dakinsa, ya sauya kayan bacci ya zauna a gefen 62 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah gadonsa, ya janyo wayar ya duba. Lambar ce dai tata, kamar ba zai karanta ba sai kuma ya daure ya soma karantawa. 'Na rasa yadda zan sanar da kai son da na ke maka Hafiz da ke tafiya a duk wata gaba da ke jikina. Ka yi hakuri ka daina damuwa da damuwata, domin na san ni kaina ban yi wa rayuwata adalci ba da na kasa cire ka a raina. Ka yi hakuri! Ka yi hakuri!! Ni na san sonka shi ne ajalina! Don Allah ka yi min addu'a Allah ya sa na yi kyakkyawan karshe, don ina ji a jikina kamar ni ba mai sa'a ba ce a duniya!" Ya ji zuciyarsa ta karye matuka, tsananin tausayinta ya lugwigwita masa zuciya, ya kasa jurewa sai da ya mayar mata da martani. 'Ko ba ki fasalta min a fatar baki ba na sani kina sona matuka. Kuma ni ma din ina sonki fiye da yadda ki ke tsammani, sai dai shamakin da ya gilma a tsakaninmu shi za ти dinga hanga. Kada ki damu, dole ne damuwarki 63 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah ta dame ni don idan na ce ban damu da damuwarki ba, ban yi wa so adalci ba Insha Allah sona ba zai zamo ajalinki ba, ke dai ki dage addu'a Allah ya kawo mana mafita'. Ya tura sakon tare da tsura wa wayar idanu kamar ita ce a gabansa, dole ne ya samu lokaci ya je Katsina duk da shamakin da ke tsakaninsu, to amma ba soyayya ce za ta kai shi ba ballantana a ce ya tsallake umarnin mahaifin nasa. Yana cikin wannan hali ta sake turo masa sakon. 'Hafiz, ba ka gane abin da na ke nufi ba! Ba za ka gamsu da uzurina ba a lokacin da na bayyana maka sirrin zuciyata, wannan shi ke damuna da sa ni fargaba. Wallahi na sadaukar da raina a kanka, don gabadaya rayuwata babu wani da namiji da na ke so da Kauna, na ke kuma fatan ya zamo mijina sai kai. Na sani duk namijin da zan aura bayan kai sai dai na yi biyayya, amma ni da shi za mu takura, don ba zan taba dubansa a matsayin masoyi ba, sai 64 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah wanda ya yi soyayya ta karan tsaye'. Ya dauke idanunsa daga kan wayar, abin da ba ya so na son tabbatuwa, wato ya sauya layin waya a dalilinta, ya kwana da wannan kudiri. Sai dai kafin safe komai ya subuce masa na son sauya layin, musamman dogon nazarin da ya yi, idan har ya sauya layin bai zama lallai ya samu lambobin wasu mutanen da suke mu'amala ba. Bayan haka lambar tasa da ita ya ke amfani ga wadanda ya ke koya wa ilimin na'ura mai kwalwa. wanda tana like a takardar shaidar karbar dalibi "(form), don haka ya hakura kawai, zai ci gaba da amfani da layin, amma zai yi kokarin isa Katsina a dan tsukin kafin Abbansa ya dawo daga Lagos. Lokacin da ya fito falon gidan, ya tarar da mahaifinsa ya gama karin kumallonsa, Hajiya Asiya na zaune cikin tattara fuska da Kawatata da tsantsar damuwa. Haka ta kwana jiya cikin kunci tana, ganin mijin nata mara adalci, don a ganinta ya daina sonta shi ya sa ya ke mata kora da hali. 65 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Hafiz ya gaishe ta bayan sun gama gaisawa da mahaifinsa, ta amsa masa ba yabo ba fallasa, sannan ya dawo da dubansa ga Alhaji Atiku yana fadin. "Abba, yanzu za ka tafi ko sai anjima?" Alhaji Atiku ya ce. "Yanzu zan tafi, da ma kai na ke jira ka fito". Ya ce, "To, ina waje ina jiranka" Ya fito zuwa harabar gidan ya barsu zaune don su yi sallama a nutse. Cikin kwantar da murya Alhaji Atiku ya ce. "Asiya. don Allab ki kwantar da hankalinki, wannan tafiyar fa ba wadda ya kamata mu rabu a haka ba ne, idan ki ka yi la'akari da tsayin kwanakin wata daya zan yi kafin na dawo hutu. a kalla muna bukatar rabuwa cikin salama don ba mu sani ba ko rabuwar ke nan" Ta ce, "Ni ba tafiyarka ce ta dame ni ba, maganar aurenka ita ta dame ni Ya yi murmushi yana duba agogon hannunsa, ya ce. 66 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah "Lokaci ya kure ballantana na tsaya mu yi wannan maganar, sai dai ina tunatar da ke, tun can baya ba ke kadai ce a gidan nan ba, ya kamata yanzu ma ki kwana da sanin zan iya kara aure koyaushe". Ta tattaro wani korafin, amma kafin ta samu damar saukewa ya rigata magantuwa bayan ya mike tsaye. "Don Allah a bar maganar nan, ki yi mana addu'ar sauka lafiya. Duk abin da ki ke bukata na sauke miki shi, bayan haka ga Hafiz nan ko da akwai wata bukatar a uzurce. Ta kyabe baki, murya a cushe ta се. "Allah ya kiyaye hanya". Bai damu da rashin rakiyarta ba ya fice, ya tarar da Hafiz yana jiransa. *** *** *** Larab ya dago kai ya dubi Hafiz ya ce. "Malam, ni fa ba hirar Fadima ta kawo ni gurinka ba, za ka wani dame ni da zancenta. Na zo ne musamman don sayen form". Hafiz ya yi murmushi, ya ce. 67 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah "To na ji, wa zai yi training ne?" Kai tsaye Larab ya amsa masa. "Kanwarka Bintu, wai tana son koyon na'ura mai kwalwa". Hafiz ya gyada kai, ya ce. "E, hakan yana da kyau, ta warware ke nan?" Larab ya се, "Е". Hafiz ya ce, "To, ai ba sai ka saya ba. Tunda kanwa guda ce ai ko bude kwalwarta sai a yi a zuba mata". Su duka suka yi dariya, Hafiz ya dora da fadin. "Koyaushe ta shirya zta zo za ta zama cikakkiyar daliba". Larab ya ce, "Ai ita a shirya ta ke, ko yanzu a ka ba ta umarni da gudu za ta zo. Hmn yadda Bintu ke son karatun nan, ina jin ko lokacin da ta samu gurbin karatun sakandire ba ta yi dokinsa ba". Hafiz ya yi murmushi, ya ce. "Ai karatun kwamfita dadi gare shi... yaushe za ka raka ni Katsina?" 68 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah "Ai karatun kwamfita dadi gare shi... yaushe za ka raka ni Katsina?" Ya jefo masa wannan tambayar gatsal, Larab ya yamutsa fuska, ya ce. "Katsina? Me kuma za ka yo?" Hafiz ya ce, "Zan je wajen Rufa'atu ne, wato tun rabuwarmu har zuwa yanzu fa ta kasa kwantar da hankalinta, koyaushe cikin turo min sakonni ta ke, wai ba za ta iya rabuwa da ni ba, shi ne na ke son zuwa". Larab ya yi shiru na wani lokaci, kafin daga bisani ya girgiza kai ya ce. "Kada ka yi wannan gangancin Hafiz, ka bi umarnin mahaifinka ka rabu da sha'anin Rufa'atu..." Hafiz ya tare shi da fadin. "Wallahi na hakura da ita, kawai ina son dai na je na kara kwantar mata da hankali ne, don ba na so a dalilina ta shiga wani hali, ka san mata rauni ne da su musamman a sha'anin soyayya". Larab ya ce, "Ka san Allah ka rufa wa kanka asiri, duk halin da Rufa'atu za ta shiga 69 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah bai kai naka ba don na tabbata ba karamin 6acin rai mahaifinka zai yi ba idan ya samu labarin ka bijire wa umarminsa ka je gurin Rufa'atu, ka yi mata addu'a da kuma ci gaba da kwatanta mata muhimmancin yarda da Kaddara". Hafiz ya yarfa hannaye ya ce. "Ai inda matsalar ta ke ba ta daukar wayata, idan ma ta dauka ba ta ce min komai sai kuka. Ni kuma abin da ya ke ci mini rai ke nan, shi ya sa na yanke hukuncin zuwa can Katsinan" Larab ya yi shiru na wani lokaci. "Ka yi hakuri Hafiz, ni dai ba na ba ka goyon bayan zuwa Katsinan nan, sai dai zan yi maka addu'ar Allah ya kai ka lafiya ya dawo da kai lafiya. Daga karshe ina tunasar da kai, mahaifa ba ababen wasa ba ne, umarninsu muddin bai shiga shingen shari'a ba binsa ya zamo lazim, ballantana ga bayanin da mahaifinka ya yi maka game da nasabarta. Wallahi ka gode wa Allah da ka samu uba mai sonka da zai guje maka auren macen da za ka 70 SADAUKARWA-2 dawo kana nadama". Mummyn Faanah Sam bai ji zafin maganganun Larab ba, bai kuma ji haushin rashin samun rakiyarsa ba, haka suka rabu yana ayyana wa a ransa zuwan shi ne mafi a'ala, domin ko daren jiya ta kira shi tana kukan, ta kuma turo masa sakon tana cikin wani hali na kunci a dalilin kaunar da ta ke masa. A lokacin sun yi musayar sakonni, amma yadda ya lura ta yi zurfin da zuwan nasa Katsina ne kadai zai rage mata radadi. A bangare daya kuma ga lamarin Fadima da ya tunkaro shi gadan-gadan, tun bayan zuwan Alhaji Umar gidan su Fadimanya dawo da fadin dumbin karamcin mahaifinta, wanda kai tsaye Malam Abdullahi ya ce ba ya bukatar komai daga gare su illa sadaki, kuma idan yau sun shirya ma su zo a daura aure, don da ma koyaushe cikin jiran aurar da Fadiman ya ke. Tun ranar da a ka yi hakan a ka dakatar da Fadima zuwa daukar karatun, amma dai yana samun damar ganinta idan ya je gidan. Abin da ya sa shi damuwa shi ne, da a ka sanar wa Alhaji Atiku abin da suka ce, kai tsaye ya ce 71 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah a jira shi dai, ba za a yi gaggawa ba. A ganin Hafiz kamar jinkitin ba zai yi fa'ida ba, tunda sun nuna halin dattako bai kamata a jinkirta ba nidan dai su ma suna son su dauke su manyan smutanevil ns ok ni gtsi noKamar yadda Alhaji Atikun ya sanar da shitzai dawo bayan wata daya, yau saura mako daya, don haka ya ke cikin zumudin dawowar tasa don cikar burinsa, sai kuma ga sha'anin Rufa'atu da ya ke hauhawa farashi a zuciyarsa, ba dai yana son dawo da bara bana ba, ko nuna karfi ya kwato soyayyar da ya ke ganin an yi wa karan-tsaye ba, illa tausayin halin da ta ke ciki a dalilinsa, wanda ya ke ganin shamakin da a ka shata musu ya yi tsauri, akalla dai a barsu su dinga haduwa har Allah ya zaba mata miji. sm sb Bayan barin Larab ofis din nasa ya dade cikin saka da warwara, a wani bigiren yana tauna bayanan Larab a mahangar hankali da kyautuwar a yi amfani da su don kore wancan tarnakin, sai dai raunin da dayan bigiren ya ke da shisyana sa shi rudani, har ya ji kamar yana ci gaba da zalunci ne! Tun kusan wata daya da 721 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah lokacin ba, sai don bai san dalili ba. Bayan ya tashi daga aiki ya koma gida ya yi wanka ya dauki hanyar gidan su Fadima kamar yadda ya saba duk bayan kwanaki biyu ya kan jc. Yana isa kofar gidan ya tarar da abin da ya kada hankalinsa., Fadima ce a ka fito da ita ranga-ranga cikin halin fita hayyaci, gefe ga mai tasi ya bude kofa yana jiran a sakata. Hankalin Hafiz ya yi kololuwar tashi, da sauri ya fito daga mota ya tunkari Malam Abdullahi da ya ke ba da umarnin a saka ta a : ciki, ya cе. ne. "Malam lafiya? Malam Abdullahi ya ce, "Ba ta jin dadi Hafiz ya ce, "To ku shiga motata mana". Kafin ma Malam Abdullahin ya yi wata magana tuni Hafiz ya isa ga mai tasin ya ba shi dari biyar, sannan ya hanzarta bude wa su Inna Baida'u motarsa, a ka sa Fadima a ciki, Malam Abdullahi ya shiga motar suka nufi asibiti. A kan hanyarsu ta tafiyar ne Hafiz ya ke tambayar ba'asin rashin lafiyar tata. A dunkule 73 SADAUKARWA-2 Malam Abdullahi ya сс. Mummyn Faanah "Kada ka samu damuwa, da ma tana yin haka duk karshen lokacinta, sai dai na yanzu ne ya yi muni". Sam Hafiz bai gane abin da ya ke nufi ba, amma ba ya son tsawaita magana a tsakaninsa da surukin nasa saboda kunya. Sai da Karin suka isa asibitin ya samu bayanin, duk lokacin da za ta yi al'ada tana shan wuya. Tausayinta ya kama shi ainun. An ba ta gado saboda ta sha wahala sosai a wannan karon. Hafiz ya dinga zarya tsakanin harabar asibitin saboda an yi mata allura ta samu bacci. Yadda ya kidime ya rasa kwanciyar hankali ya sa Malam Abdullahi ya gamsu lallai ba karamin so Hafiz ya ke yi wa gudan jininsa ba. Har magriba ba shi da niyyar barin asibitin, sai da Malam Abdullahi ya ji tausayinsa sosai ya сe. "Malam Hafizu, ya kamata ka tafi haka nan, na san kana da sabgogi, ga shi sun yi mata allura muna sa ran zuwa anjima idan ta farka su 74 SADAUKARWA-2 sallame mu Mummyn Faanah Kansa a kasa cikin girmamawa ya ce. "Ko da ta farkan a yi hakuri ta kwana Malam, za ta fi samun sauki" Malam Abdullahi ya ce, "E, ai dama ba mu za mu nemi sallamar ba, sai yadda jikin ya bayar. Kada ka damu, Bintu za ta tashi da yardar Allah". Hafiz ya ce, "Allah ya sa" Kai tsaye ofishin likita ya nufa ya yi masa bayanin ko da Fatima ta farka kada ya ba su sallama. ya barta ta kwana a asibitin. sannan daga bisani ya tambayi likitan wại dole ne duk lokacin da za ta yi al'ada sai ta yi wannan ciwon ba wani tallafi da za a yi mata don rigakafi? Likitan ya ce. "Akwai tallafin mana. idan za a aurar da ita, namiji ya kusance ta ai abin zai zo da sauki. Akwai irin nau'in mata da suke kasancewa a haka yayin al'adarsu, da zarar an yi musu aure suna samun sauki". Ya bar asibitin da wannan maganar ta likita, wato idan a ka aurar da Fadima ana da 75 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah yakinin za ta tsira da wannan wahalar? Idan haka ne lallai ya kyautu a gaggauta yin aurensu. don ba zai iya jure ganinta cikin wannan azabar ciwon ba. Báyan an sallaci isha'i wajen tara saura, ya sake komawa asibitin ya tarar ta farko, ruwan da a ka sa mata saura kadan ya kare. Ya dan zauna ana jimamin da shi, sannan Karfe goma ya bar asibitin. Rashin lafiyar Fadima shi ya dauke masa hankalin zuwa Katsina, musamman da ya kasance a kwanaki ukun ba tà turo masa sakon da zai iva tunawa da shä'aninia ba. An sallami Fadima daga asibitin a washegarin da a ka kawo ta, ba laifi ta dawo hayyacinta, sai dai kana kallon fuskarta ka san ka ga mara lafiya. A kullum Hafiz ya zo gidan sau biyu ko sau uku, ban da kiran wayar Isma'il da ya kan yi don jin yanayin lafiyarta. Ita kanta Fadiman ta yarda da ba karamin so Hafiz ya ke yi mata ba, duba da yadda hankalinsa ya tashi game da rashin lafiyarta, barin ma irin dawainiyar da ya ke yi musu, duk zuwan da zai 76 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah yi sai ya shigo mata da ‘ya'yan itatuwa, wani abin ma sai a dalilinsa ta taba cinsa, misali inibi da suturo beri. Yana zaune a ofishinsa cike da nishadi saboda wayar da ya ke yi da Fadima ta wayar yayanta Isma'il suna more hirarsu cikin shauki da kaunar juna. A hankali a ka kwankwasa kofar, ba tare da ya damu da ko waye ba ya ba da umarnin a shigo, bai sauke wayar daga kunnensa ba. Bintu ce ta shigo sanye da yaluwar atamfa ta sha kwalliyarta mai kayatarwa, komai iri daya (too much) ta saka kalar ja da fari, sai shigar ta kayatar da ma abu ga fara sol. Ya yi mata nuni da yatsa ta zauna kujerar da ke gabansa, yana ci gaba da cewa a wayar. "Allah ba ni da wani burin da ya wuce na faranta miki, don haka kada ki damu da duk wata hidima da zan yi a gare ki. Ba na duban hakan a matsayin takuwara illa fita hakkinki a matsayinki na wadda za ta maye min guraban da ke tattare a zuciyata da ma rayuwar gabadaya". 77 SADAUKARWA-2 Mummyn Faánah Ya tsagaita da maganar da alama raddi ya ke saurare, yadda fuškarsa ta sake washewa da murmushi alama ce ta yana jin dadin abin da à ke fada masa. Bintu ta ci gaba da zuba masa idanu, yayin da ya fora da fadin! "Hmn, Fadima ke nan, ke dai Allah ya raya min ke mu yi tsawon rai, kuma Ya kai mu ranar aurenmu... Bayan ya yi shiru na wani lokaci, sannan ya ce. "To shi ke nan, sai na sake kiray amma fa ki kula. kin san tukin tiwo akwai wahala" Ya sa dariya tare dà kashe wayar ya dawo daodubansa ga Bintu wadda ya ga yanayinta babu walwala, koyaushe ya ganta cikin yanayin damuwa tausayinta kan kama shi, ya san zafin so

Chapter 3 of 6