Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 6
musamman irin nata na SON MASO WANIDY ana tausaya mata yadda ta ke cikin komar makauniyar soyayya da ba a sani ba za a haife ta da rai ko matacciya ce? Ya dan yi murmushi, ya ce. "Kanwas; ya dai?HS CL Ba tare da ta saki fuska ba ta tura masa 78 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah takardun da ke hannunta a gabansa, ta cc. "Da ma assignment din da ka ba ni jiya ne na shigo kawo maka". Sai ya ji ba dadi a ransa, yadda ta yi masa maganar. Ya sa hannu ya dauki zungureriyar takardar yana magana cikin sigar zolaya. "Da kyau kanwas, himma ba ta ga raggo! Haka na ke son falibi da maida han..." Bai Karasa maganarsa ba ganin ta mike ta soma tafiya, ya ce. "Ah! Saurin me ki ke yi ne haka?"? A takaice ta amsa masa da cewa. "Zan koma gida, Umma za ta unguwa". je Ya dago kai ya dube ta sosai, tare da dora hannayensa a saman tebur ya ce. "Ga shi yau ina son mu tattauna wasu muhimman maganganu game da lamarin bikina, ya ke nan?" Ba tare da ta juyo ba ta ce. "Kada ka damu, za mu tattauna idan an samu lokaci". 79 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Ya lura tana cikin damuwa, watakila masoyin nata ne ya hado mata zafi. don haka sai ya kyale ta, ya се. "Shi ke nan, ki gaishe min da Umman. kwana biyu ma ban je na gaishe ta ba. Karashe maganarsa Karashewar ficewar Bintu daga ofishin nasa. Ya yi zugum cike' da nazari, wace irin yarinya ce Bintu da ta dauki rayuwa da zafi haka? Ya jima yana nazarinta kafin daga bisani ya soma duba aikin da ya ba ta. Kokarin Bintu na kayatar da shi. da a ce ba ta da damuwa da ta fi gaka hazaka. Da yammaci ya kai gyaran motarsa da ta ke dan ba shi matsala, yana tsaye ana gyaran, wayarsa ta yi kara kafin ya ciro ta daga aljihu kiran ya katse, don haka sai bai bi ta kanta ba, ya ci gaba da kallon bakaniken. Zuwa can kuma ya ji kara alamar sako ya shigo wayar. Wannan dole ya duba don ya san sakon ba zai wuce daga Rufa'atu ba. Cikin nutsuwa ya ciro wayar. "Yar halak!" Ya ambata a ransa lokacin 80 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah da ya tabbatar da ita din ce a sabuwar lambarta. Murmushi ya soma yi kafin ya soma karanta abin da sakon ya kunsa kamar haka:- 'Da zan iya da na tsaga kirjina na cire soyayyarka a raina ko na huta da azabar da na ke sha. Amma sai dai kash na makara, ba ni da jaruntar da zan yi amfani da karfi na tsaga kirjin nawa, watakila rashin tabbaci ne da na ke da shi idan na tsaga Kirjin zan iya cire soyayyar ko ba zan iya ba, shin a kirjin ma kadai sovavyar ta ke da muhalli ko a gabadava gangar jikina ce? Amma dai tabbas Kokari yana bude kofar da ke rufe, don haka zan yi wani yunkuri ko da zan kusanta da kushewa, kai da mutanen duniya ku tabbatar an taba yin wata mahaukaciya a soyayya, ko na ce mai yin mataccen so a rayuwarta'. Iyakar nan sakon ya tsaya. Matukar damuwa Hafiz ya shige ta, shin wane yunkuri Rufa'atu ke son yi? Ta shiga duniya ko ta kashe kanta duk a kan soyayya? Lallai cikin biyu 81 SADAUKARWA-2 Múmmyn Faanah daya zai iya faruwa idanthaka ne mene ne abin yi? Yaushé zá tá yi yunkurin? Yanzu? Anjima? Gobe? Ko har ma ta yi-bayan tà turo da sakon? Ya fan ja tsaki, a sarari ya furta. Soyayya mä ba ta yi ba à rayüwa". Daidai kunnen danfulanin bakaniken da ke fama da sifanu, ya yi murimüshi ya cc. sde "Yahaj, ai kuwa soyayya ta yi sošaina rayuwa". SKHafiz ya dan kafe shi da idanu yayin da bakaniken ya bude bakin famfon koro jawabi. o "Yahaj. soyayya fa ita ce jigon zamän. lafiya isakanin alumm. kowace arin al ng kuwa. Da soyayya ake Raunar juna har ayi aure a zauna lafiya. Da soyayya a ke kulla abota Da 133 ...soyayya ل Hafiz-ya katse shi lura da ya yi, watakila bakaniken yana cikin inuwar yan ga-ni-kashenin soyayya, ya ce. Ni ma ai ba zagin soyayya na yi ba, cewa na yi ba ta yi ba a rayuwa". aDH awrn Bakaniken ya bangare da dariya yana carafke da sifanu уа сe. 22 SIHE SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Bakaniken ya bangare da dariya yana carafke da sifanu ya cе. "Ai Yahaj kanin zagin soyayyar ka yi". Hafiz ya yi tunanin da alama zai iya samun wata shawara daga bakaniken, tunda ya yi zurfi a kare hakkin soyayya, don haka ya ce. "Yauwa to, tunda na lura kana kare hakkin soyayya, ko za ka taimake ni da shawara?" Yahaj". Bakaniken ya ce, "To, ina saurarenka Hafiz ya mirgina kai da fadin. "Misali, budurwa ce na ke so ta ke sona, sai wani shamaki ya ratsa tsakaninmu da ba za mu iya aure ba, ta bangaren kin amincewa daga magabatanmu. To sai budurwar ta ci alwaşhi idan ban aure ta ba, za ta kashe kanta ko ta shiga duniya, a shawarce ta wace hanya zan bi na rabu da ita lafiya ba tare da ta aikata abu daya cikin biyun ba?" Shiru bakaniken ya fara yi, hatta da aikin da ya ke a gaban motar sai da ya dakata, da alama yana zanta abin da zai fada wa Hafiz ne 83 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah a zuciyarsa. Zuwa can ya yi dan malalacin murmushi, ya ce. "E to, a hakikanin gaskiya idan ni ne kai hanyoyi biyu zan bi. Hanya ta farko, zan iya ce. mata zan aure ta domin na samu ta dakatar da aikata wa kanta daya daga cikin biyun da ta ke yunkurin aikawata. Inyaso sai na dinga janue jikina daga gare ta, na yi kokarin cusa mata tsanata a zuciyarta, ta yadda za ta ji ba ta sha'awar aurena sam. Ko kuma na bi hanya ta biyu, wato na ce mata mu je a yi gwajin jini, idan har ya kasance ni da ita babu mai dauke da wasu kwayoyin cuta to za mu yi aure. Ka san hikimar yin hakan?" Yadda kalaman bakaniken suke ratsá zuciyar Hafiz, hakan ya sa shi zakwadin son jin karashen fatawar tasa, don haka da sauri ya girgiza kai. Bakaniken yana dan murmushi ya се. "Hikimar ba ta wuce ta za a dasa wa budurwar zargi a zuciyarta ba, ta yi tunanin ko da ma kana bibiyar wasu matan banza ne, watakila kana dauke da kwayar cutar kanjamau 84 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah ma ka rasa hanyar da za ka bayyana mata, shi ya sa ka 6illo mata da hakan. Ko kuma ta yi tunanin kana zarginta da bibiyar wasu mazan. Ka ga ke nan wasi-wasi zai shiga zuciyarta, a hankali sai ta dinga jin sonka yana ficewa a zuciyarta". Hafiz ya dinga gyada kai cikin gamsuwa da jin dadin bayanin bakaniken. Yana rufe baki ya dora da cewa. "Lallai matambayi ba ya bata, haka ilimi kogi ne idan ka shige shi sai ka zama kamar allura a cikin ruwa. Don Allah ya sunanka?"" Bakaniken ya fashe da dariya, ya сe. "Sunana Nura Baban Soyayya". Hafiz ya yi dariya da gyada kai, ya ce. "Tabbas ka cancanta da sunanka. Don Allah a ina ka koyo soyayya haka?" Nura yana dariya har yanzu ya ce.2 "Tabdijan! Ai labarin mai tsawo ne, amma ka sa a ranka duk fadin duniyar nan ba ni da malami a bangaren soyayya da ya wuce sahibar raina Naja'atu. Ita ce mafari da jigon zamana zakwakuri a soyayya. Ai in gaya maka 85 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Yahaj, har ranaku na ware wa masoya don kawai su zo su kwankwadi romon dimokaradiyyar soyayya" Su duka suka yi dariya, Hafiz ya dora da fadin. "Kai dai dan ban dariya ne, in ban da haka ga abubuwa nan da yawa da suka addabi mutane, yaushe za a tsaya daukar wani abu wai darasin soyayya?" Nura ya hangame baki yana kallon Hafiz jin yana neman ya raina fasahar da ya ke tinkaho da ita. Ya ce. "A tunaninka soyayya ba ta cikin abubuwa masu muhimmanci da suka damu al'umma a wannan marrar da muke ciki? To wallahi ba ka bi na bashin rantsuwa ka zo nan garejin duk ranar lahadi da yammaci ka ga yadda samari da 'yammata ke taruwa... Kai Yahaj, soyayya fa hm!" Murmushi Hafiz ya yi, ya ce. "A takaice dai kana yi min tallar makarantar soyayyarka ko?" Daidai lokacin da Nura ya ke rufe gaban 86 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah soyayya, ina ku ina karamar makaranta irin tamu da ba ta wuce cikin cokali ba?" Hafiz ya ce, "Na yi digirin zan tambaye ka abin da na tambaye ka? Yanzu ba ga shi ba ka ba ni shawara, wanda dole a ciki zan yi amfani da daya?" Nura bai tsaya- sake yin wata magana ba ya shiga cikin motar, ya tayar ya ba ta wuta, sannan ya ja ya yi gaba. Ya je karshen garejin ya juyo, yana fitowa ya сe. "Yahaj, mota dai ta gama kammaluwa" Hafiz ya ce. "Alhamdu lillahi malamin sovayya. Nawa ne kudin gyaran?" ne?" Ya yi dariya ya ce. "Dubu biyu da dari biyar". Hafiz ya ec. "Kudin form kuma nawa Nura ya zakuda kafada, ya ce. "Wani ikon Allah, kwandalar mutum ba na karba in dai zai zo daukar darasina, ni dai burina a daina ha'inci a soyayya, a dinga wanzar da zaman lafiya da yalwata zukata da annashuwa. Saboda ina takaici inga namiji ko 87 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah mace wani na babakere da nuna zamba a lamarin soyayya. idan na ga haka har zubar da Kwalla na ke, na dinga jin tausayin mai wannan hali a raina" Hafiz ya dinga Kyalkyala dariya, ya ciro Jubu biyar ya ba shi. ya се. "To na gode, ka rike sauran canjin ka sha rüwa, don na sani makoshinka na bushewa saboda bayar da darasi. Allah ya Kara yaukaka Kwalwa. Ya sa kuma daliban suna amfani da abin da suke koya". Nura ya cê. “Amin. ni ma na gode Yahaj. Allah ya kyaija geba Hafiz yana tafiya don shiga mota ya cc. "Amin Ya Allah". Da haka suka yi şallama. Yana tafe cikin mota yana zanta maganganun Nura Baban soyayya mai dumbin hikima da zalaka. Ya so matuka su yi rabuwar arziki da Rufa'atu, yana sonta tana sonsa ba tare da yin wani yunkurin da zai wanzar da kiyayya a zukatansu ba kamar yadda suke yanzu, sai dai dole ne ya dauki hanya daya a cikin biyun da Nura Baban 88 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Soyayya ya karanto masa, domin ba ya so ta rinjaye shi ya bijire wa umarnin mahaifinsa. Har ya isa gida yana zanta wannan kudiri. *** *** *** Da ya ke yau ranar hutu ce, kamar yadda ya saba more baccinsa a irin ranakun, yau din ma hakan take. Yana kwance daidai a kan gado yana sharbar baccinsa, kiran da a ka yi masa a waya ne ba gaggautawa, da kiran ya katse wani ya sake shigowa shi ya tayar da shi. Cikin magagin bacci ya kai hannu ya rarumi wayar. ganin lambar Abbansa ya sa shi mikewa zaune yana murza idanu, tare da kara wayar a kunne. Bayan ya yi sallama, Alhaji Atiku ya ce. "Hala kana wannan sababben baccin ne? Na ga ranar da ka yi iyali, haka za ka kwance mata a gida kamar kasa?" Duk suka yi dariya, sannan Alhaji Atiku ya ci gaba da cewa. "Yauwa, ka je maza-maza ka ciri kudi dubu hamsin ka kai wa Alhaji Umar, suna jira 89 7 SADAUKARWA-2 za su tafi sa ranar aurenka Mummyn Faanah Mamaki da farin ciki suka lulluße shi, ya сe. "Yau za a sa ranar ne?" Alhaji Atikú ya ce, "Mai garinku! Ko kunyata ba ka ji?" Sannan ya farga da rashin alkunyar da ya yi, yana dariya mai bayyanar da kunya ya ce. "Ка yi hakuri Abba... Ya katse shi da fadin. "Ka yi sauri fa, kada ka wuce minti talatin, domin sha biyun rana za a sa ranar". Bai ma jiraci cewar Hafiz din ba ya kashe wayar. Baccin da bai sake komawa ba ke nan, da sauri ya shiga bandaki ya watsa ruwa tare da yin brush ya fito. Bai Gata mintina goma ba ya gama shiryawa tsaf, ya saka fararen kaya, ya yi kyau ainun. Manufarsa idan ya je kai wa Alhaji Umar kudin sai ya bi su a sa ranar a gabansa. Kai tsaye banki ya nufa bai damu da rashin karin kumallonsa ba, ya ciri kudin sannan ya nufi gidan Alhaji Umar. 90 C SADAUKARWA-2 Mummyn Faangh Ya tarar da su su uku duk sun shirya, đa alama "shi kadai suke jira. Bayan ya gama gaishe da su ya ba su kudin. Da za su tafi bai nuna binsu zai yi ba don kada su ga rashin kunyarsa, sai ya bi su a baya yana tafiya a hankali har suka isa unguwar, ya samu guri can inda ba za su hango shi ba ya lafe. A gaban idonsa a ka yi komai, yau dai ta tabbata an sa ranar auren Hafiz, amma ba da Rufa'atu ba, da Fadimar da ke lugwigwita masa zuciya. Wani irin sanyin dadi ya dinga ji yana kwarara a kalbinsa. Ya daga hannu murya cike da nishadi ya ce. "Ya Ubangiji, yadda Ka nuna min wannan rana Ka nuna min ranar da za a daura aurena da Fadima lafiya". A take ya dinga kiran abokansa yana shaida musu sa ranar, amma duk wanda ya tambaye shi yaushe ne bikin sai ya ce sai an jima ya sanar da su, saboda bai ji da kunnensa lokacin da a ka sa ranar bа. Sai da ya ga iyayen nasa na haramar baro kofar gidan su Fadima din tukunna ya tayar da 91 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah motarsa, da ma sun yi waya da Habib ya kuma shaida masa ba ya cikin unguwar, Larab ne ma ya yi ta neman lambarsa ba ta shiga ba, shi ya sa da ya bar nan kai tsaye unguwar su Larab din ya nufa. Daidai lokacin da ya kashe mota zai fito daga motar shi kuma Larab ya danno layin hannunsa rike da bakar leda. Cikin murna da doki Hafiz ya fito daga cikin motar yana faman fara'a ya doshi Larab wanda yanayinsa ya nuna kamar bai kula da shi ba. "Larab! Larab!! Hafiz ya ambata ganin da gaske bai lura da shi din ba. Larab ya dan juyo a kaikaice fuskarsa kadaran kadahan ya cе. "Ah Malam Hafiz ya garin ne?" Yadda ya yi maganar ya shayar da Hafiz matukar mamaki, sai ya yi saurin duban hannun Larab din, haka nan ya ji bai gamsu ba, duk yadda a ka yi akwai wani kulli a kasa, ma'ana akwai wanda ba shi da lafiya wanda ya zautar da Larab din har ya sauya masa haka. Cikin rashin kuzari ya ce. 92 SADAUKARWA-2 Mummyn Faunah "Alhamdu lillahi. lafiya ina ta neman Jay inka a kashe? Suna tsaye a Rofar gidan su ba su shiga ba. haka ba su yi baya ba: Larab ya dan yatsina fuska yace. "Wallahi tun da safe na yi cilli da ita ban Kara bi ta kanta ba Sai ya jure damuwarsa a kan sauyawar yanayin abokin nasa. ya dan washe fuska ya сс. To albishirinka. vau fa an sa ranar aurena da Fadimatu Wani irin bahagon kallo Larab va watsa "Aure kuma? Ashe har maganar ta nuna haka ba ni da labari? Ganin kamar labarin bai yi masa dadi ba sai Hafiz ya dan yi dariya tare da dáfa kafadarsa duk da shi din yana kokarin ture hannun nasa, ya ce. "Ka yi hakuri abokina, wallahi ni ma ban san maganar ta yi karli haka ba, ka san Abba yana Lagos sai Baba Umar ya wakilta a kan komai, saboda haka ba ni da masaniya a kan 93 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah abin da suke ciki, ni ma sai dazun da safe Abban ya kira ni ya ce na je na kai musu kudi". Larab ya ce. "To Allah ya sanya alkhairi, Ya kuma kai mu lokacin lafiya". Tun kafin Hafiz ya amsa masa tuni ya juya zai shige ciki, Hafiz ya dan tako da nufin binsa cikin gidan. Larab ya juyo fuskarsa babu fara'a, ya се. "Don Allah ka fan yi hakuri Hafiz, maigidan ya ce kada wani baligi ya Kara shigar masa gida idan ba 'ya yansa ba". Mamaki va gama kashe Hafiz. sai va vi tsave fuskarsa da damuwa va ce. "Wai don Allah mai ya faru ne?" Larab ya ce, "Me fa? Umarnin maigidan ne dai wannan, ka san kuma da ma hakan ya kamata ko a addinance, tunda akwai 'yammata a gidan?" Hafiz ya girgiza da kalaman Larab, bai yarda ba akwai abin da ya ke faruwa. Larab zai shige cikin gidan. ya yi saurin riko hannunsa ya juyo da shi suka fuskanci juna, ya ce. "Don girman Ubangiji ka tsaya ka fada SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah juyo da shi suka fuskanci juna, ya cе. "Don girman Ubangiji ka tsaya ka fada min gaskiyar abin da ya faru. Wani abu na yi maka ne?" Larab ya girgiza kai, ya сe. "Na fada maka babu abin da ya faru". "To ina Bintu?" Ya tambaya bayan ya yi zargi biyu a zuciyarsa, wato ko ita ya yi wa laifin, ko kuma ta rasu ne, watakila mutuwar ce ta zauta Larab din har ya koma haka. Larab ya cuna masa baki. "Tana ciki mana Ya ce, "To don Allah taimaka ka kira min ita". Wani rudadden kallo ya sake watsa masa, kafin daga bisani ya ce. "Ba ka da labarin Baba ya hana ta fita gabadaya, saboda za a daura aurenta ranar asabar mai zuwa?" Wani irin lugude kirjinsa ya yi. Ya zaro idanu waje alamun mamaki zayyane a fuskarsa, tabbas wannan dalilin ne ya sa Bintu ta je 95 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah ofishinsa cikin rashin sukuni. Wannan dalilin nc ya sauya Larab daga yadda ya sanshi tunda ya san akwai. shakuwa da soyayya tsakanin Larab da Bintu. Da kuma wannan dalilin ne zai gamsu cewa mahaifin su Larab din ya kafa dokar hana shigar masa gida. Kafin ya samu abin fada, tuni Larab ya shige ciki ya barshi hangame da baki da dumbin mamakin yadda a ka mutu a ragaya. u Ya jima yana jiran tsammani ko Larab zai sake fitowa, amma shiru. Yana kokarin shiga motarsa ke nan ya hango Alhaji Shu'aibu mahaifin su Larab ya doso kofar gidan, don haka sai ya dakata har ya karaso. Ya risina yana gaishe da shi, Alhaji Shu'aibu ya amsa cikin yalwar fuska yana fadin. "Ya kuma na ga ka tsaya a kofar gida?" Wannan shi ne hagu da dama! Yanzu ba jimawa Larab ke maida masa martanin mahaifinsu ya hana maza shiga gidansa, amma ga shi mahaifin ya dawo yana mamakin rashin shigarsa cikin gidan. Ya kai 'hannunsa ga keya bai yi magana ba, Alhaji Shu'aibun ya sake 96 SADAUKARWA-2 cewa. Mummyn Faanah "Ko ba dubiya ka zo ba? In ce Larabi ya fada maka dalibar taka ba ta lafiya?" Ya ji maganar ta sake shigarsa, ya girgiza kai ya ce. "Wallahi bai fada min ba". Alhaji Shu'aibu ya ce, "Ayya, ai tun jiya da ta dawo gurin darasin ta ke haraswa, mu shiga ciki". Ya karashe maganar tare da dosar gidan. Hafiz ya mike ya bi shi a baya. A tsakar gida suka ci karo da Umma tana matse kayan da ta wanke. Ta amsa sallamar da maigidan nata ya yi, tare da yi masa sannu da zuwa. Ganin Hafiz a bayansa ya sa ta daure fuska, hka nan sai ya ji ya tsargu, me ya yi wa wadannan bayin Allah suka dauke shi da zafi haka? Ya dan risina yana gaishe ta, fuska babu walwala ta amsa masa. Alhaji Shu'aibu ya ce, "Na dawo ke nan na tarar da shi a kofar gida, ashe bai samu labarin Bintu ba ta lafiya ba?" Ta basar kamar ba ta ji abin da ya ce ba, 97 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah ta soma dauraye hannunta yayin da Alhaji Shu'aibu ya soma tafiya yana fadın. "Zo mu shiga dakin". Jiki ba kwari Hafiz ya bi Alhaji Shu'aibu yana nazartar laifin da ya aikata wa Umma da Larab. Turus Alhajin ya ja ya tsaya bayan ya shiga dakin sun yi ido hudu da Larab, ya ce. "Da ma kana cikin gidan amma ba ka san abokinka na waje ba?" Larab ya hade fuska sosai, ya ce. "Ban san ya zo ba". Hafiz ya dube shi da mamakin furucinsa, amma sai ya basar ya mika masa hannu kamar da gaske ba su hadun ba. Larab ya miko masa nasa hannun don babu yadda zai yi, suka yi musabiha.. Bintu na kwance idanunta a bude, amma ta ki duban inda Hafiz ya ke. Alhaji Shu'aibu ya ce. ki". "Ke Bintu, ga malaminki nan ya zo duba Ta dan motsa jikinta kadan alamun ta ji ०२ SADAUKARWA-2 ba?" Mummyn Faanah Ba ta amsa ba, Alhajin ya cc. "Yana yi miki magana fa?" Larab ya yi karaf ya се. "Baba ta ji fa, ka san yanayin ciwon dole sai an yi mata uzuri" Alhaji Shu'aibu ya dubi Larab da Bintu, sannan ya dubi Hafiz sai kawai ya girgiza kai, ya fice daga dakin. Hafiz ya yi tsuru-tsuru, ya rasa ta inda zai kamo don shigar da tuhumarsa. Bayan 'yan mintoci da fitar Alhajin, Larab ya dubi Hafiz ya ce. "Hafiz. ka san dai ni ne abokinka a gidan nan ko? To don Allah daga yau ba na bukatar ka zo gurina, abotar ma na yanke ta!" Gaban Hafiz ya sake hauhawar faduwa. "Larab, don Allah me na yi maka?" Wani dogon tsaki ya ja, kafin daga bisani ya girgiza kai, ya ce. "Babu bukatar jin abin da ka yi min, amma ka sa a ranka kusantarka a gare ni bala'i ne mai mugun muni, don Allah ka taimake ni 99 SADAUKARWA-2 ka janye jikinka daga gare ni Mummyn Faanah Babu yadda Hafiz zai yi, tunda shi ma mutum ne mai jini a jiki da zuciya, yasan ciwon kansa bai kamata ya tsaya a ci zarafinsa ba a kan abin da bai sanaya yi ba, saboda haka ya gyada kai ya ce. "Shi ke nan Larab, na gode. Amma wallahi ban taba tunanin akwai abin da zai faru tsakanina da kai ka kasa zaunar da ni ka fada min don mu fahinci juna ba" Larab ya kyabe baki. ya ce. "Ai da ya ke kai makaho ne sai ka tsaya nå rike hannunka na vi maka jagora ka dinga fahintar lamuran duniya!" Kwarai Haliz ya shaka, duk da bải kasance mai saurin fushi ba. ko duban inda suke bai kara yi ba. ya juya ya fice daga dakin. Daidai lokacin Umma ta fito daga dakin Alhaji Shu'aibu, ta auna masa harara ko amsa sallamar da ya ke yi mata ba ta yi ba, ta wuce, shi ma ya fice. Da ya ke ranar yau din ta kasance ta farin ciki a gare shi, saboda hawa mizanin da ya jima 100 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah yana fatan hawa, sai ta kasance mai sirkin abu biyu, wato farin cikin sa ranar aurensa da kuma damuwar abin da ya faru tsakaninsa da su Larab, wanda har zuwa yanzu ya kasa canko abin da ya haddasa wannan jin zafin nasa da suka yi. Ya yi kokarin ture abin amma ya kasa. Da yammacin washegarin ranar Alhaji Umar ya zo gidan ya kawo wa Hajiya Asiya kayan sa ranar Hafiz, ya kuma sanar da ita an sa za a yi bikin sati biyar masu zuwa, Ta vi farin ciki sosai, don tana son a aurar da Hatis saboda tana sane da har yanzu bai dayaye daga radadin rasa Rufa atu ba. Hafiz na shigowa gidan. da wannan albishir din ta tare shi, don ta yi tunanin bai samu labarin halin da a ke ciki ba. Ya zauna a kujera ya dinga kyalkyala mata dariya, ya ce. "Haba Aunty, ai a gabana a ka yi komai, ranar ce dai kawai ban ji ba sai yanzu". Та се, "То alhamdu lillahi, tafiya Dubai da Saudi hado lefe ya kama mu" Ya ce, "Wane lefe kuma bayan wanda Abba ya hado tun tuni?" 101 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah Ta yatsina fuska, ta cс. "Ai na zaci nasa ne. ko ba ka san da nasa auren ba?" Ya yi murmushi, ya се. "Aunty ke nan! Ba na tsammanin fa akwai maganar auren nan". Та се, "Мe ya sa ka fadi haka?" Ya ce, "To ni dai tun kafin ya koma Lagos bai sake yi min maganar ba, har gara wancan zuwan da ya yi na dan tuntube shi, amma dariya kawai ya yi bai dora ni a kan komai ba. Kin ga kuwa da akwai maganar ai da va ce wani abu ko?" Ta sake kyabe baki ta ce. "Hmn! Kai dai a yi sha'ani wai dogari ya mari. Sarki, amma in ka ga Alhaji ya fasa auren nan to mutuwa ya yi". Ya dube ta da mamaki, zai yi magana wayarsa ta yi kara alamar shigowar sako, ya ciro ya duba, ya ga lambar Rufa'atu ce, kai tsaye abin da ya fara fado masa a rai shi ne, shawarwarin da Nura Baban Soyayya ya ba shi, wanda tuni ya yanke hukuncin yin amfani da 102 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanáh shawarwarin da Nura Baban Soyayya ya ba shi, wanda tuni ya yanke hukuncin yin amfani da hanya ta farko. Cike da karsashi ya soma karanta sakon. 'Yau na nutsu na yi wa kaina tambayoyi, wai shin ni wace irin mace ce da na kasa tsayar da alkibla ta a guri daya? Me ya sa na ke son abin da bai dace da ni nawa ra'ayin ba? Amsar da na samu ita ce, da ma can ni Allah ya halicce ni da zazzafar jarabta shi ya sa ba ni da juriyar kauda kaina ga abin da na ke so. Babban dalilin ankarar da ni hakan shi ne, cin zarafin da magabatana suka yi min, ya hada da kafa min sharadin idan ban cire ka daga zuciyata ba za su bar rayuwata ta kare a wahalce. To na amsa musu na hakura da kai, amma sonka da kaunarka har abada ba za su taba tumbuke jijiyoyinsu da suka kafu a raina ba in ba Allah ne yà cire min ba. Daga yau, ina yi maka albishir zan koyi juriyar rashi, ba zan sake kiranka ko turo maka sako ba. Ba za a sake samuna a duniyar waya 103 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah ba, zan yi gangami domin binne mataccen sona da ya dade da mutuwa a cikina ban sani ba. Zan jarraba nesanta kaina da kai watakila na samu sauki daga radadin da na ke ji. kada ka manta da an taba yin mahaukaciya a makauniyar soyayyarka! Sai watarana!! Ya yi shiru yana kallon madubin wayar, batutuwan da ta zana mafita ce a gare shi wanda ba sai ya yi amfani da waccan hanyar ta Nura Baban Soyayya ba, sai dai fa zuciyarsa ta cunkushe da tsananin tausayin rayuwar Rufa'atu, wato bayan wahala da soyayyarsa da ke nukurkusar gabban jikinta, ba ta huta ba a 6angaren mahaifanta? Hajiya Asiya tunda ya soma karanta sakon wayar ta ke binsa da ido, kafin ya gama kuma ta shige dakinta yin wasu bukatun. Ba ta fito ba har ya gama zamansa ya fice. *** *** *** Bai yi mamakin daina zuwan Bintu daukar darasi ba saboda tana fama da rashin 104 1 SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah lafiya, da kuma abin da ya faru tsakaninsa da yayanta, wanda shi ya kawo ta kamfanin. Don haka ya cire ta a cikin jerin daliban da ya ke tunanin kaifin kwalwarsu ya kai tsaikon da zai dauke ta aiki a kamfanin nasa. Yanzu abin da ke gabansa bai wuce shirye-shiryen aurensa da Fadima ba, wanda saura mako biyu kacal. Duk wata bukata ta kudi Hafiz ba shi da matsalarta, domin bayan nasa kudin da ke cikin asusunsa na banki wanda a ké samunsu ta 6angaren

Chapter 4 of 6