An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
Sadaukarwa2
Naja'atu Haruna Saleh (Matar Nura Sada Nasimat KT)
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
SHEKARAR BUGU
2015
GODIYA
na mika godiyata ga Ubangina,
mahaliccin kowa da komai, wanda Ya ba ni
dama da ikon rubuta wannan littafi nawa ba
don iyawata ba, sai don kudirarsa na
tabbatuwar rubutuna alkali a cikin al'umma.
GODIYA TA MUSAMMAN
Ga Mijina abin tinkahona, wanda ba ya
gajiya da bukatuna, ina fatan Allah Ubangiji Ya
saka masa da gidan aljanna Firdausi, Ya
daukaka, Ya kiyaye shi daga dukkan sharri,
Allahumma Amin.
SADAUKARWA
Wannan littafi nawa SADAUKARWA
ne ga mahaifiyata Marigayiya Rukayya Na'iya,
ina fatan Allah Ya kai haske a kabarinta, Ya şa
aljanna Firdausi ce makomarta.
2
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
JINJINA GA:-
Alhaji Haruna Sale (Abbana)
Alhaji Sada Isah Mani (Babana)
Alhaji Ibrahim Na'iya (Kawuna).
YABON GWANAYE
Makaranta littattafaina a duk inda ku ke.
bisa kokarin da ku ke yi na duba littafina, Allah
Ya saka muku da alkhairi. Ya bar kaunar da ke
tsakaninmu har zuwa aljanna Firdausi, amin
MUN HADE HAR KULLUM
Aisra Wada Abdullahi (Jini da tsoká)
Maimuna Idris Sani Beli2 Li
Sadiya Garba Yakasai
Fauziyya D. Sulaiman
Ummulkhairi Kabir-Aliyu
Khadija Sharubutu
Zulfa'u Jabir Abdullahi
Zulfa'a Aliyu Zango
A'isha Ali Dambatta
Farida Ado Gachi
3
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
Hauwa Abubakar Lawan Maiturare
Bilkisu Yusuf Ali
Nafisat Tasi'u Moh'd
Lu'ubatu Isah Lawan
Da sauransu, duk ina mana fatan alkhairi.
JINI DA TSOKА
Dana Kwallin Kwal Yusuf Nura Sada
(Faanah) Allah ya raya ka tare da sauran
'ya'yan musulmi bisa tafarki na gaskiya, amin.
KA CANCANCI YABO
Yahaya Mahi, Bookshop, da ke wurin
'Yan Awaki, Bakin Kasuwar Kauran Namoda,
Zamfara State.
TA'AZIYYA
Ga 'yan uwana musulmai wadanda
hatsarin rikicin addini ya rutsa da su suka rasa
rayukansu da kuma wadanda suka rasa
muhallansu da rashin nutsuwar zuciya. Allah ya
jikan rayukan da a ka rasa, Ya mayar da abin da
4
R
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
a ka rasa da mafi alkhairinSa, Ya zaunar da kasarmu lafiya, allahumma amin.
TSOKACI
Don Allah ina son a tsaya a fahimce ni,
kar ai saurin yanke min hukunci kamar yadda
wasu suka soma yi akan tallar littafin kawai da
suka gani kafin ma su karanta, wasu har kafirta
ni suka dinga yi. To ina neman alfarma a yi
hakuri a kammala labarin sannan ai sharhi.
Baya da haka, ina rokon duk wanda ya
ga kuskure a cikin littafi na daya da na biyu
bayan wancan maganar da na fada ną sakin
aure ga da uba ya aura, to a sanar min don
kiyayewa. Na gode.
GARGADI
Daukar wani 6angare na wannan littafi
ko sarrafa shi ta wata hanyar, laifi ne babba,
kuma hakan yana iya gurfanar da mu gaban kuliya. Neman izinin marubuciyar shi ne abu
mafi dacewa da samun salama a tsakani.
5
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
SADAUKARWA-2
afiz. ya yi shiru bai ce komai ba
da zan yi maka, shin da gaske
kake aure zaka yi?
da cewa.
Bai ba shi amsa ba, Habib din ya ci gaba
"Na tambaye ka ba ka bani amsa ba".
"Idan tambayar taka tana da amsa ai da
na baka".
"Ke nan kana nufin ba ka shirya aure
ba?" Inji Habib.
"Wannan kuma kai ta shafa". Ya ba shi
amsa cikin kulewa.
Ya jinjina kai, sannan ya ce.
"Ba laifi, ka ga tambaya ta biyu ba ta da
amfani, sai dai abin da zan yi maka matashiya
da shi shine, ka daina sanya kanka shirgin da ba
naka ba, a sanina kai ba mayaudari ba ne, to
don me yanzu za ka fara yaudar..."
Ya sake tare shi, wannan karon rai a
бace, "Wai wa ya ce maka ni mayaudari ne
6
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
kake ta dauko wannan batu kana dora min? Ko
na yi maka kama da irin samarin'nan 'yan shan
minti ne?"
Murmushi Habib ya yi sannan ya ce.
"Ai ba ni na ce ba, tambayarka na yi ka
ce min kuma ni ta shafa, ni kuwa a tunanina
duk mutumin da kyakkyawar niyya cе
zuciyarsa idan har aka tambaye shi ba ya maido
irin amsar da ka maido min ba".
Hafiz ya jinjina kai, ya ce.
a
"To ni ba haka nake ba, tun da nakе
rayuwata ban taßa duban wata 'ya mace da
wannan sigar ba, idan kuma ba aurė zan yi ba
babu dalilin da zai sanya ni shiga shirgin mata
bare na wahaľar da kaina har na dorawa kaina
hawan jini".
2F Habib ya sake yin murmushi, ya ce.
"Idan na fahimce ka ka bani amsata ta
farko, don haka tambayata ta biyu a gare ka,
shin zaka iya aure 'yar talakawa wadda ba su
da cin gobe a ajiye, kullum sai an fita an nemo?
Kuma diyar malamin makarantar allo, wadda
ba su waye da wayewar boko ba?"
7
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanoh
Ya kasa fahimtar inda wannan tambaya
ta sa a gaba, don haka sai ya zubawa Habib in
ido kawai yana nazarin ta inda zai kamo hax y
fahimci me yake nufi da wannan tambayar tasa
mai harshen damo.
Kamar Habib din ya fahimci abin da
Hafiz din yake tunani, sai ya murgina kai ya ce
"Kar ka rikita kanka mana, game da
matar auren da Allah Ya jarrabi zuciyarka da so
ne".
Daram! Gabansa ya kuma faduwa, ya dai
yi shirun yana kallonsa.
Habib ya gyara zama ya ce.
"Ka yi hakuri abokina na ruda tunaninka
kwanaki hudu da suka wuce, ba komai ya sa na
yi hakan ba, illa don na tantance wane irin so
ne kake wa Batula, kuma alhamdu lillah na
fahimta, amma maganar gaskiya Batula ba ta da
aure, budurwa ce 'yar talakawa diyar malamin
zaure...
Zuciyata tana raya min kamar don ba ka
san wace ce ita ba shi yasa ka ce kana sonta, sai
na kasa samun nutsuwa, hakan ya sa na ce
8
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
maka tana da auren don mu samu mu rabu
lafiya da kai. Na farko Yayanta abokina ne, kai
ma abokina ne, ga shi akwai sanayya
dukkanmu sai na ke ganin tarin kalubale a duk
lokacin da ka ce ba zaka aure ta ba don tana
'yar talakawa bayan kuma ka sa ni a tsakiya, ka
ga zan ji kúnya a gidan su. Sannan kai ma za
mu iya samun sabani a tsakaninmu, ka ga anyi
badi ba rai ke nan.
Wannan shi ne dalilina, to amma daga
shekaran jiya kawo wa jiya na yi istihara sai na
rasa gane kan lamarin, domin ina ganin alkhairi
a tarayyarku, haka ina ganin wani rudani da
ban san daga inda zai fito ba, saboda haka
kawai na ga dacewar na sanar da kai gaskiya,
na kuma tayaka da addu'a Allah Ya tabbatar da
abin da ya fi zama alkhairi a tsakaninku".
Hafiz ya rasa kwatanta irin dadin da ya ji
ya shige shi, fuskarsa ta yalwatu da fara'a sosai,
wai Fadima ta tabbatu ba ta da aure? Mamaki?
Al'ajabi? Farin ciki? Murna? Ko doki ya
kamata ya yi?
Habib ya mike tsaye daga inda yake
9
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
zaune, ya dawo gaban teburin da ya gilma
tsakaninsu, yana murmushi ya ce.
a
"Ka san me? Har na yi azarbabin
sanarwa Batula, kuma ta nuna min
amincewarta, sai dai kasan gidansu akwai
a'idoji da duk wanda yake neman 'yar gidan
ya ke bi kafin ya soma tunkarar mace, don haka
ta bayar da wannan damar. Ma'ana kana da
damar da zaka sami mahaifinta ka sanar da shi
cewar, kana sonta idan ya amince da kai zai ba
ka damar tsayawa da ita, idan kuma ya yi mata
miji ne duk zai sanar da kai".
Sai ya ke ganin kamar abin a mafarki ne.
amma yadda ya ga Habib yana maganar ya
samu yakinin hakan take. Shi ma mikewa
tsayen ya yi suna fuskantar juna ya ce.
"Don Allah da gaske ka ke Habib?"
Gira ya daga masa ba tare da ya yi
magana ba.
"Idan dai har da gaske ka ke, ina so ka
fada min me ya hanata zuwa nan kwanaki hudu
tun ranar da ka dauke ta?"
Ya yi murmushi, tukunna ya ce.
10
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanoh
3
"Allah Sarki! Wato ka yi tunanin mijin
nata ne ya hana ta zuwa? To sha kuruminka, ba
ta jin dadi ne tun daga ranar da na dauke ta, yau
ma da safe na shiga na duba ta".
"To yanzu ya za a yi ke nan?"
Habib ya dafa kafadarsa ya ce.
"Abin yi ya rage gare ka, sai ka fidda
lokacin da zamu je ga mahaifin nata idan har
zaka iya aurenta a bisa mizanin da ta ke kai".
Da fara'a a fuskar Hafiz ya ce.
"Kar ka damu Habib, wallahi ba ni da
wannan burin na cewar ba zan auri 'yar
talakawa ba sai 'yar masu kudi, domin a
rayuwar aurena babu abin da nake fata illa
Allah Ya hada ni da abokiyar zama ta gari.
Fadima kuwa ba na hasashen rashin dace a tare
da ita. Tun ranar da na soma tozali da ita, na
san ita kyautar Allah ce, wadda suka yi karanci
a wannan zamanin.
Zuciyata na raya min idan na samu
nasarar aurenta na yi dace da mace ta gari duk da dai su din ba tukwane ba ne bare a
kwankwasa a ji wacce ta fi kwari, amma ka san
11
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
an ce daga ganin juma'ar da zata yi kyau tun
daga Laraba ake gane ta.
Fadima tana da nutsuwa, hankali kai har
ilimi Fadima duk ta hada, yadda ta ke da
kamewa da kuma kwalwa na san ba zata rasa
wadataccen ilimin addini ba sai ga shi kuma
yanzu ka sanar da ni daga gidan da ta fito, wato
gidan da aka san alkur'ani ciki da bai, gidan da
koda yaushe rahama ta ke ziyartarsa. Alhamdu
lillah, ina matukar godiya ga Allah da Ya hada
ni da Fadima, kuma ina fatan Ya mallaka min
ita a matsayin matar aurena ПАПЧЕ
nitnoa janye hannun Habib da ke saman
kafadunsa, sannan ya zauna. Shi ma Habib din
ya zauna yana kallon yadda Hafiz duk ya cika
da farin ciki, nan da nan ya ji shi ma farin cikin
ya kama shi, saboda dukkansu ya san su, yasan
kuma sun dace da juna. Hafiz ya сe.
"Yanzu ya kake ganin za a yi?"
un Habib ya dan yi murmushin jin dadi ya
ce.
"Ba sai mun tsawaita lokaci ba, kamar
yadda na sanar da kai Fadima diyar malami ce,
12
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
३
ka san kuwa dole zaka same su da dokoki da sharudda, don haka da zafi-zafi akan bugi karfe, sai ka shirya anjima da daddare mu je gidansu mu nemi izinin ganin mahaifinta mu isar da muradinmu a gare shi".
Hafiz ya girgiza kai, yana fadin.
"Da wannan dan wannan wai an tura
tsohon banza biko ya ce idan ba a mayar masa
ba ina wa dana riko... Amma me zai hana mu
bari sai jibi Laraba, kasan duk abin da aka soma
shi ranar Laraba zai wahala bai zo da nasara ba,
manzon Allah (S.A.W) Ya yi mana nunin,
dumbin darajar da ranar Laraba ta ke da ita, har
ya yi mana hani da fifita ranar juma'a fiye da Laraba, saboda Yahudawa sun dauki Asabar
mafificiyar rana a gare su, Nasarawa kuma suka
dauki Lahadi, ka ga ke nan idan mu musulmi
muka dauki juma'a a matsayin mafificiyar rana
a gare mu, mun koma su ke nan, ma'ana mun bi
sahunsu. Saboda haka ina ganin mu je ranar Larabar".
Habib ya ce, "Lallai kam ka yi tunani
mai kyau, da a ce mutane da yawa za su dinga
13
LADANLAFWA;
ataha
uma 31
hutur
2
253ght
dи123 21а
7кabа ta at
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
tsinkaye irin naka su soma neman aure ranar
Laraba da sun ji dadi, to amma an biyewa
Yahudawa da Nasarawa wai hatta da daurin
aure sai a ce sai ranar Asabar za a yi shi, ba
kuma don komai ba wai sai don ranar ce ranar
hutun ma'aikata, shin a islamance wace rana cе
ranar hutu? Ina ce Alhamis da Juma'a sune
ranaku hutun musulmi, me yasa ba za a dinga
daurin aure a irin ranakun ba a matsayinmu na
musulmi? Duk da cewa yin daurin auren ma
Asabar ba aibu ba ne, amma kowa ya bar gida,
to kuwa gida zai barshi. Ba Karamin jin dadi
Yahudawa suke ji ba da wannan tsarin nasu da
muka dauka wai na daurin aure ranar asabar"
Da wannan shawarar suka rabu akan jibi
ranar laraba za su je wajen mahaifin Fadima.
*** ***
Kwance ya ke akan gadonsa yana bacci
bayan ya taso daga wajen aiki ke nan, wayarsa
ta ishe shi da tsuwwa, amma baccin da ke
idonsa ya hana ya kai hannu ya janyo ta.
Kiran ya katse, wani ya sake shigowa har
14
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
sai da aka kira ya fi sau biyar bai daga.
Karfe uku da mintina sha biyar ya farka
daga baccinsa, wayarsa ya soma dubawa don ya
ga karfe nawa, sai ya tarar da kiran da aka rasa
guda shida (6 missed calls). Ya mike zaune
yana dubawa, lambar Rufa'atu ya soma gani
mài kira biyar, sai daya lambar da babu suna.
Ya yi tsai da idanunsa akan lambar
Rufa'atu yana tünanin makasudin kiransa,
domin ya san tunda abin nan ya faru ta daina
amfani da layinta, a cewarta mahaifinta ne ya
amshe wayar gaba daya, yanzu kuma ga shi ta
kira shi da layin.
Kafin ya lalubo abin yi rubutaccen sako
(text massage) ya. shigo masa. Ya duba da
bakuwar lambar da aka yi masa missed call ne
aka turo sakon. A hankali ya soma karanta abin
da sakon ya kunsa.
Farin cikin rayuwata, da fatan ka wayi gari cikin koshin lafiya.
Bayan haka ina mai sanar da kai zuciyata ta kamu da matsanancin Kaunarka sai dai na
15
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
kasa sarrafa kaina ta yadda zan iya hakura ba
tare da na tuntube ka ba...
Iya abin da sakon ya kunsa ke nan, karo
na farko babu wadda zuciyar Hafiz ta hasaso
tana mallakar wannan rubutaccen sako sai
Rufa'atu, domin ita ce tauraruwar da ta ke
sonsa fiye da tunanin mai tunani. Bayan ita
babu wata budurwa da ya taba tunkara ya ce
yana sonta, don haka koda yaushe, zai ga irin
wadannan kalamai yasan daga gare ta ne, ko ba
ma don haka ba, yanzun nan ya gama duba
missed calls dinta guda biyar sai daya da
bakuwar lambar, ke nan hakan na nufin ita се
mallakar bakuwar da aka yi missed call da
kuma rubutaccen sakon.
Bai yi kasa a gwiwa ba, tunda zuciyarsa
ta gama yi masa amanna Rufa'atu ce, sai ya
soma kiran lambar da ke da sunanta, amma ya
tarar da ita a kashe. Ya bi waccan bakuwar
lambar, ita din ma a kashe ta ke. Ya jingina da
filo yana mai lumshe idanunsa, hakika har
kullum yana tausayin Rufa'atu, yasan son da ta
16
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
ke masa ba irin wanda zai yi fitar burgu ba ne a
gare ta, amma shi a ganinsá son da babu aure
me ye amfaninsa? Ita da kanta ta fada masa
zata yi hakuri da shi don ta taya shi biyayya ga
mahaifansa, kuma ita ma ta yi tata biyayyar ga
mahaifinta da ya'ce ba ta ba shi, to ammá ya
lura Karfin son da ta ke masa žai haifar da
raunin yin hakan a gare ta.
Abin da zuciyarsa ta ayyana masa idan
har yana son zama lafiya, ya kuma yi biyayya
ga mahaifinsa har ita ma ta samu damar yin tata
biyayyar ga nata mahaifin dole ne ya saúya layi
don su yi nesa da juna. Ya yi amanna da
wannan shawarar dari bisa dari, sauya layi shi
ya fi dacewa a gare shi.
Bayan ya yi wanka ya shirya, kai tsaye
cikin gida ya shiga, ya tarar da Hajiya Asiya
zaune akan doguwar kujera, fuskar nan tata a
daure. ga dukkan alamu wani abu ne ke
damunta.
Ilai kuwa Hafiz na zama a kan kujera ko
gaishe ta ba ta bari ya yi ba ta hau furta
munanan kalaman da ta kunsa.
17
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
"Haka kawai ina hakuri da mutum ba ya
gani, to wallahi alo tsiya alo danja. ba a isa a
kawo min wata bankadaddiyar yarinya ba".
Jin wannan furucin nata ya sa Hafiz ya
dago dalilin fushin, wato Abba ya sanar da ita
zai kara aure, shin maganar har ta tabbata ke
nan? Rashin dacewar magantuwa ya gani shi
yasa ya mike tsam zuwa bedroom din
mahaifinsa, ya tarar da shi yana kidaya kudi.
Ya nemi guri ya zauna kusa da kafafun
Abban nasa, yayin da Alhaji Atiku ya dago kai
ya dube shi, ya ce, "Ka shigo?"
A' yanayin fuskar Alhaji Atikun bai ga
wata damuwa ba game da halin da Hajiya
Asiya ta ke ciki, ya san hakan ba ya rasa nasaba
da maganar Hausawa, inda sabo kifi ya saba da
ruwa. Ya се.
"Eh, dama game da maganar da muka yi
da kai jiya ne, yau da daddare za mu je gidan su
yarinyar wajen mahaifinta".
Alhaji Atiku ya tsayar da nutsuwarsa
akan Hafiz fuskarsa cike da yalwa ya ce.
"Na yi murna matuka, Allah Ya sa a fara
18
SADAUKARWA-2
neman a saa
Hafiz ya ce, "Amin"
Mummyn Faanah
Alhaji Atiku ya ce, "Bude lokar can ka
dauki daurin 'yan hamsin guda biyu ka yi dük
abin da ya dace".
Ya ce, "To Abba, na gode Allah Ya kara
girma".
Ya mike ya bude lokar ya dauko kudin,
dai-dai lokacin da yake shirin fita Hajiya Asiya
ta shigo dakin, tana fadin.
"Magana fa nake maka ka kyale ni, mene
ne manufarka a Kaina?"
Hafiz ya sa kai ya fice daga dakin, ita
kuma ta karasa shiga ciki tana zuba ruwan
masifarta, shi dai ya yi shiru ya kyale ta tamkar
bai san da zamanta a gurin ba.
Kai tsaye Hafiz na fitowa daga gidan,
motarsa ya shiga ya zauna sannan ya kira
lambar Larab, ba jimawa ya dauka.
"Hello Larab kana ina ne?"
Larab ya ce, "Uhummm! Na san arina,
yanzu kuma ta nan ka billo wai kidan farauta a
kasuwa".
19
SADAUKARWA-2
Hafiz ya yi dariya. yaа се.
Mummyn Faanah
"To nuna min kana digiri a fannin Hausa,
ni ba wannan ne sanadin kiranka ba. Kana ina
ne? Ina so zaka yi mana rakiya ni da wani
abokina zuwa gaido surukai".
"Surukai?"
Larab ya maimaita cike da tsananin
mamaki, zuciyarsa kuma na isananta bugawa.
Yaushe ka samu surukan har da zamu
gaishe da su?"
Maimakon Hafiz ya amsa masa tambayar
da ya yi masa, sai ya се.
Kai dai kana ina ne, ina sauri karfe
biyar muka yi zamu je"
eer Larab ya ce, "To'yanzu dai ga ni nan
gidanmu".
Ya ce, "To ka jira nina karaso".
Yana kashe wayar ya nuti gidan su Larab
din. Tafiyar mintina ashirin suka sadar da shi
gidan, lokacin ana ta haramar shiga masallaci
sallar la'asar, don haka gaisawa kadai suka yi
da Larab ko cikin gidan bai shiga ba sai suka
wuce masallaci, ya yi alwała a can sannan suka
20
SADAUKARWA-2
gabatar da sallar.
Mummyn Faanah
Suna gamawa suka nufi cikin gidan.
Umma ta gama tata sallar sai Bintu ce ke yi.
Ya durkusa kasa ya gaishe da Umman, ta
amsa cike da jin dadi.
Ya ce, "Ya mai jiki?"
Ta kyabe baki tana fadin.
"Ai ciwon Bintu yadda ka san ciwon
jinnu, yanzun nan za ka ji ta da lafiya an jima
ka ji ba lafiya. Tun dai da muka dawo asibiti
lafiya kalau babu wani abu da ya ke damunta,
illa rashin kuzari na wanda ya tashi daga ciwo".
Ya ce, "To Allah Ya kara inganta mata
lafiya, amma ni kaina ciwonta na ba ni mamaki,
ko dai har da aljannun ne?"
h Larab ya yi karaf ya сe.
"Ba wani aljannu, illa jarabar soyayya da
ta saka wa ranta...
Sai kuma ya kasa karasa fadar abin da ya
ke shirin fada, ya sunkuyar da kansa kasa. Shi
kuma Hafiz ya yi saurin duban Larab din yana
maimaita kalmar.
"Soyayya? Da ma soyayya ce jigon
21
SADAUKARWA-2
rashin lafiyarta?"
"Yaya barka da yini
Mummyn Faanah
Wannan itaice amsar da ya samu daga
bakin Bintu wadda ta sallame. sallar tana
murmushi. Ya juyo yana kallonta ya amsa
mata.
"Yauwa Bintu, sannu da jiki"
Ya maida kallonsa ga Larab yana fadin.
"Laifinka nake gani; domin kai ne ka cе
Bintu ba zata tsayá da saurayi ba wai ta yi
Karanta, yanzu wa gari ya waya?"
Ya dubi Umma ya cс.
"Wallahi Umma kar ki yarda Larab ya
nakasa miki 'ya, kiobar yarinya ta kula wanda
ke sonta, wannan takurar ta Larab ban san inda
ya koyo ta ba, sammutum ba ya uzuri da duban
abin da ya dace saboda mugun son kai".
Su duka biyun Umma daLarab suka yi
dariya, yayin das Bintu ta sunkuyar da kai
Kwalla na zubo mata cikin idanu.
Hafiz ya lura da kwalan dansuka zubo
mata a kumatu, tausayinta yaokama shi, ina
dalilin wannan zalunci da Larab ya yi mata?
22
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
3
Shi kam a yanzu ya san zali da radadin rabuwa
da masoyi. don haka a duk inda masoya suke
suna ba shi tausayi, dole ne kuma ya Karfafa
musu gwiwa rike junansu bisa gaskiya da
amana, an ce ruwan da ya dake ka shi ne ruwa.
Larab yana dariya ya CC.
"Soyayya ko shirme? In bącin hauka me
ye a cikinta?"
Sai Umman ta mike ta fita ta ba su guri,
jin sun tabo shafin da ya girme tunaninta. Hafiz
ya auna masa harara yana fadin.
"Kai ka ga hauka a soyayya, ni kam ina
ganin muhimmancinta da darajarta, shi yasan
kake ba ni haushi Larab, wani lokaci kai mugu
ne, ba ka da tausayí sam a rayuwarka
Larab ya tamke fuska, ya сe. "Tausayi? Ai kana tausayawa masoyan
da suka san me ye soyayyar har suke yinta, wadanda ba su santa ba me ye amfanin ka
tausaya musu? Kai ni fa wallahi duk wanda ya
ce zai jawo kansa azal to ba ya ba ni tausayi..." Hafiz ya katse shi da fadin.
"Me ye azal? Kuma idan ba a koya an
23
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
samu Rwararru? Ko ka manta duk wanda ya
shahara a soyayyar sai ya fara zama falibi kafin
ya zama shahararren?"
Bintu dai Kwallanta ta ke shara. Hirar
kuma tana burge ta, a kalla zata samu sassaucin
matsin lambar da yayan nata ya mata.
Larab ya girgiza kai, ya сe.
"Da kake wannan hakilon, shin me ye
amfanin SON MASO WANI?"
A nan sai Hafiz ya yi jagale yana kallon
Larab, a fahimtarsa son maso wani koshin
wahała ne, domin ba lallai wanda kake son ya
tausaya maka ba har ya kulaka ya tallafe ka da
muhalli ko da na wucin gadi ba ne, duk da dai
ba duka aka taru aka zama daya ba, wasu suna
da adalcin musamman idan suka dubi wanda ke
son nasu yana cikin halin kunci da damuwa mai
tsanani...
"Ba ka ba ni amsata ba"
Larab ya katse masa tunani.
Hafiz ya kai dubanshi ga Bintu, sannan
ya dawo da duban ga Larab, ya сe.
"Ba shi da amfani kam, amma ya kamata
24
SADAUKARWA-2 Mummyn Faanah
duk wanda ya samu kansa a wannan gurbi a
tausaya masa, zafafa masa ba shi zai kawo
maslaha a gare shi ba...""
Larab ya daga masa hannu.
"Don haka ne ba na jin tausayinta, tunda
ta dorawa kanta dala da gwauron dutse ba sai ta
nemi mai sauke mata su ba, na me mu kullum
zata sa mu dinga asarar lokaci da kudadenmu a
wajen nema mata magani? Ni fa wallahi kullum
ji nake kamar na kamata na yi ta jibga don
takaici..."
Bintu ta dago kai ta dubi Larab, mamaki
ta ke na rashin tausayinsa. Harara ya auna mata,
sai ta maida kan kasa. Hafiz ya ce da shi.
"To ba sai ka maida niyya ba, tunda kai
ka haife ta? Ah! Ji ni da mutum da karfin hali...
Amma na san. maganinka, addu'a zan ta yi
Allah Ya sa ka hadu da wadda kake tsananin so
amma ba ta sonka"
Larab ya ce, "Ba bakinka ba, sai dai kai
دو zan yi addu'a kar ka dace da samun...
Sai kuma ya sauya zancen da fadin.
"Ka ga na sha'afa, ya kamata mu san na
25
SADAUKARWA-2
yi kada lokaci ya kure mana ko?
Mummyn Faanah
Hafiz ya ce. "Eh, tunda ka san ba ka da
hujja ba".
Suka yunkura su biyun, Bintu ta zuba
musu idanu kawai har suka fice daga dakin,
suka yi wa Umma sallama sannan suka fice
zuwa inda Hafiz ya ajiye motarsa.
Bayan sun soma tafiya ne, Larab ya dago
kai ya dubi Hafiz yana fadin.
"Ka ce gaisuwar surukai za mu je, shin
ya maganar ta ke ne?"
Hafiz ya yi murmushi cikin zumudi, ya
ce da shi.
"Haka zancen ya ke, na samu matar da
zan aura ne a unguwar su wani abokina Habib,
to ya fada min