Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 6
wajenta da wajen mahaitinta. Duk wannan magana da yake yi banda hawaye babu abunda ke zuba daga fuskarsa. "Nafisa ke ma ki Xafe mini dan Allah. in Allah ya so zaki gane mahäifinki ko da wannan tsagu da ke wuyanki ko da sarkar hannun da muka tsince ki da shi. tana wajen Hajiva ga shi kuma yadda al'amari ya kasance na Bat Karasa ba ya fashe da kuka yana mai daga muryat kamar fan yaro "Allah ka yafe min, ubangiji ka yafe minı zunubaina. Üzaif dan Allah ku yafe mini. Ku yafe mini Nafisa.... Banda kuka babu abinda muke yi, na kasa ua bude baki in yi masa magana. "Astagfirillah, Astagfirillah. Astagtirillah. Allah ka yafe mini, Allah ka yafe Bai Rarasa ba wani dan sanda ya shigo wajan. Da shigowarsa na san cewa lokacin tafiyarmu ya ki. Kan ka ce Kala tuni yavana ya mike tsaye yana,fadin "Ku gafarce....." bai Karasa ba va fadi Kasa wanavas ran yayi halinsa. 51 ** * Allah ya raya Maryam, da gama radin suna bayan sallar Asuba sai aka nemo masu hada gawa. Kamar Karfe bakwai na safe aka yi jana'izarsa. Bayan "yan karbar zaman makoki sun taru a kayi masa addu da sauran musulmi da suka riga mu gidan gaskiya, daga nan jama'a suka watse. Mun jima kwarai kafin juyayin mace-macen da aka yi mana hade da fargaba ya sake mu. Yau kusan wata uku kenan. Dukkan su suka futo suna murmushi hade da fadin "La! har ka maida Hajiyar gida?" Na: amsa musu a yayin da suka zazzauna akan makekiyar kujerar da ke falon "Tun dazu na dawo, ai in fada muku kafin Hajiya Inna ta bar ni na taho sai da nayi da kyar tukunna, ban da kuka babu abin da take yi mini. Ta ce dai kun hana ta bebi Maryam." Moda tayi dariya sanían ta ce "Haba Uzaif ya za a yi mu ba wa wannan tsohuwar wannan tsaleliyar yarinyar? Uzaifat ta dauka "Wallahi gaskiyarki gara dai ta zauna a wajenmu." Nafisat da ke zaune a hannun kujera tayi ajiyar zuciya hade da fadin "Ni wallahi duk rashin saduwa da mahaifana shi ya dame ni, domin kuwa bacin yawon da muke yi da ku a nemansu ni ma na yi har na gaji, kuma na gane kwatançen da Hajiya tayi mini, na je har gidan aka ce mai man kulin ta rasu, Sannan bolar bayan gidan naku an yi gidaje a wajen. Wallahi ni ban san inda zan sa kaina ba. a 52 Na nisa na ce da ita "Kar ki samu damuwa Insha Allahu zamu kasance masu kara baki kwarin guiwa domin kuwa farin cikinki shi ne namu." Na lura cewa maganata ta faranta mata rai, don haka sai na ci gaba "Zamu sake komawa gidan mai man kuli mu yi bincike akan ta dalla-dalla." Na mika hannu na amshi bebi Maryam daga hannun Uzaifat. "Bebi Maryam how are you today?" Ta bamale baki tana dariya a yayin da nayi mata wannan tambaya. Gaba daya muka kwashe da dariya. "Kawo ta ka gani za ta yi dariyar da tafi haka idan nayi mata rawa da waka." Na mikawa Nafisa ita a yayin da na mike ina mai tambayar Uzaifat lafiyar mahaifinmu. "Eh, ya samu sauki kwarai da gaske har labari fa yake ba ni." Ta amsa tana mini murmushi mai kara kwarin soyayya. * * * Nafisat ta kalli 'yan tsagun da ke wuyanta a madubi ta ce "Kun san wani ikon Allah? Wallahi ban taba lura da wadannan tsagun ba fa." Uzaifat ta ce "Haba ai ñi tuni na san da su, domin suna daga cikin abubuwan da suka karawa wuyanki kyau." Tayi murmushin yabonta da aka yi. Na ce "Sai mu hanzarta zuwa can gurin gaida baban namu daga nan sai mu karasa gidan mai man kuli." Na sa hannu na amshi bebi Maryam wacce ta ci ado da jeans complete sannan tayi bulbul abinta kamar 53 mai shan mama, ai dole tayi bulbul in ba haka ba kuwa mene ne amfanin Dr. Uzaifat? Kana kallon ta ma ba zaka ce da ita bakwai ni ba. Bacin fitarmu daga gidansu Uzaifat ne muka dauki hanya zuwa 'Faltinga'. Da isarmu gidan muka riske wani tsoho a zaune akan tabarma. Bayan mun yi masa sallama sai muka yi masa tambaya cewar muna bukatar ganin daya daga cikin yaran da mai man kuli ta rika. Ya sanar da mu cewa da daya kawai ta rika wato jikanta. "Baba dan Allah ko zamu san inda wannan jika nata yake?" "Eh to". Yayi tari hade da kaki. Bayan ya tofar sai ya ci gaba "Shi wannan jika nata yana can Abuja da zama, amma kuma ya kanzo nan duk bayan sati, domin duba lafiyar mahaifiyarsa. Bayan sauraron bayaninsa saia na yi masa tambaya da cewa "Idan ba zaka damu ba dan Allah ina son ka sanar da mu ranar da zai zo.' Yayi tari mai tsayi sannan ya gutsiri goro ya tauna "Gaskiya ba na ce ga ranar da zai zo ba, domin kuwa ya kwana biyu bai bullo wajena ba." Cikin garaje Nafisat ta dauka da "To yanzun dan Allah idan zai yiwu kayi mana kwatancen gidan יי mahaifiyar tasa." * ** * Mun yi fakin a kofar gidan wanda yayi matukar dace wa fantin da akayi masa. Bayan sallama da muka yi. mai gadin wanda a zahiri bahause ne amma yayi kama då bafillatani. 54 "Don Allah Hajiya-Mai-Duka muke nema." Na fada a lokacin da yake gyara tsaiwarsa. "Eh babu mai duka sai Allah." Ya fada yana dariya "To ta san da zuwanku ne ko kuwa?" Nafisat ta gyara mayafin da ta rataya a kafadarta sannan ta ce "Ba ta san da zuwanmu ba, amma ka iya sanar da ita cewa daga gidan mahaifiyar mijinta muke wato Faltingo." "A sannunku da zuwa ku shigo mana, ai shi ma Hafiz din ya zo dazun nan amma ya dan zaga gurin abokai." Mun yi farin ciki kwarai sosai da jin wannan albishir. "Shakka babu wannan Hafiz din means alot to us." Na fada a bayane wanda hakan ya sa mai gadin yayi mini wani kallo wanda yake bukatar in fahimtar da shi wani abu game da turancin da nayi. Nayi masa kallon kai magulmaci ne, sannan na kau da kaina daga kallonsa. Mun zazzauna akan kujeru da aka shirya a falon kasa, a yayin da mai gadi ya sauko daga matattakalar "Ku jirata minti biyu tana zuwa." Bayan godiya da muka yi masa ne ya fice waje. Kyakkyawar kafarta ce ta fara yi mana sallama sannan sauran jikinta. Fara ce gajeriya wacce goshinta ya sha fashi siriri wanda yayi matukar kara mata kyau. "Sunnunku bayan Allah." Ta fada tana kokarin zama. "Yawwa sannu ina yini?" Nafisat ta fada tana fadada bakinta zuwa murmushi. Bacin sauran gaishe-gaishe, ta nemi ta san ko su waye mu? Na nisa na ce da ita "Da yake abu mai wuya 55 ( ne ki kasa ganc bayaninmu in dai har kin sauraremu sosai. Ba zamuce mun sanki ba, domin kuwa babu wanda ya taba ganinki a cikinmu. Amma idan baki manta ba shekaru ashirin da foriya da suka wuce kin yi wata kawa Hajiya Ubaida wacce take kamar aminiya a gareki." Na tsaya a lokacin da nake kallon kwayar idonta. Ta dan yamutse fuska wanda hakan ya sanar da ni ta zurfafa cikin tunani. Ganin zata 6ata mana lokaci yasa na kudiri niyyar fahimtar da ita cikin sauki. "Hajiya kada mu saki a duhu, bari in sanar da ke abun da ke tafe damu dalla-dalla. Kamar yadda na sanar da ke cewa kin yi aminiya a da H.Ubaida wacce kika canja mata suna da Kawas a wannanlokaci......." Ban Karasa ba ta zaro idanu ta dakatar da ni "Af! Kawas kake nufi matar A.M. Sadiku?" "Shakka babu ita." "Au ai Allah yayi mata rasuwa." "Subhanallahi." Gaba dayamu muka fada. A gaskiya ban ji dadin wannan zance ba, domin kuwa na so a ce tana raye domin ta ga abinda Allah ya maida Nafisat. "Allah ya jikanta." Na fada, sannan na ci gaba "ko da yake dama ba saboda ita muka zo wajen ki ba, mun zo ne domin kiyi mana kwatancen gidanta. Ko da yake ya kamata idan har da dama mu tafi tare da ke. Nayi mamaki da ba ki tambaye mu wanda ya turo mu wajeki ba, amma duk da haka zan yi miki bayani yanzun. Idan ba ki manta da Hajiya Maryam sirikar Alhaji Mubarak matar Alhaji Yusuf ba, to zaki iya tuno 56 da duk wani bayani da zan nema daga wajenki." Na ja na tsaya, domin na ba ta damar magana. Bayan ta nisa sai ta ce "Haba ni kuwa na san Hajiya Maryam farin sani, dama tana nan garin?" "Tana nan garin mana, amma ita ma Allah yayi mata rasuwa. "What" Ta fada a yayin da hawaye suka bakunci kuncinta "Allah sarki matar arziki, kai Allah ya jikanta da rahama." Ta fada tana sharar hawaye. "To tun kafin ta rasu ta bar mana wasika mai kunshe da yanayinki, sannan tayi mana-kwatancen gidan sirikar ki wato mai man Kuli wanda tana ganin cewa ta hanyar wannan mata zamu fi saurin saduwa da ke. Tayi mana bayani cewa ke da Kawas aminan juna ne, sannan kuma kuna mutunci dà ita kwarai da gaske. Hajiya idan ba ki manta ba a baya dillanci kike yi wanda hakan ya sa kike zuwa gidanta talla. Wanda hakan yasa wata rana bayan zuwanki wajenta kika ci karo da wata jaririya, a wannan rana kun yi rigima sosai akan jaririyar sannan daga baya kun shirya akan wasn makudan kudi da tayi miki alkawarin zata baki. Kafin ta baki sai da kika shaida mata cewa wannan jaririya 'yar A.M. Sadiku ce sannan kuma Kawas ce ta sa danki Hafis ya kashe ta a yayin da ke kuma kika hana shi sannan kika sanar da shi cewa ya je bolar da ke bayan gidan mahaifina ya ajiye sannan ya san yadda yayi ma gadi ya fito ya ga wannan jaririya. "Babu shakka anyi haka." Ta fada tana mat ba da gaskiyar ta akan maganar. 57 Ba ni ba har su Uzaifat sai da suka ji dadin rashin musawarta. Na ce "Ta sanar da mu ccwar da farko ta ba ki Naira dubu dari uku sannan kika dada dawo mata da nufin ta kara miki. Kafin ta ba ki sai da kika kika yi mata alkawarin ba zaki kara dawo mata ba, kuma ba zaki taba fadawa kowa ba hatta Kawas. Bayan haka ne ta kara miki Naira dubu dari biyu. Daga sannan ba ki kara dawo mata ba, ita ma kuma ba ta kara ganinki ba, wannan sirri ne a tsakaninki da ita a wannan lokaci, amma yanzun ya zama open secret domin kuwa yarinya ta gane cewa ba mahaifanta ba ne, saboda haka yanzun muke son dan Allah ki kai mu gurin mahaifanta. "Babu komai, yanzu ina yarinyar take?" Tа tambaya. "Gata nan." Na yi mata nuni da Nafisat. "Sannu 'yan mata, ya sunanki?" Nafisat ta kalle ta hawaye na zuba daga fuskarta "Sunana Nafisat, na gode kwarai da taimakon da kika yi mini a rashin bari a kashe ni." Hajiya Mai-Duka ta tashi ta je gaban Nafisat idonta na zubda hawaye ta ce "Don Allah ki gafarta mini domin kuwa da ni aka hada komai, sannan kuma cetonki da nayi ba wai tsakani da Allah na yi ba, nayi shi ne domin na samu kudi wato kenan na butulcėwa Kawas, kuma ba komai ya sa tayi miki haka ba sai don tsananin kishin da ke tsakanin mahaifiyarki da ita. "Ni kuwa mai ya sa kishin mahaifiyata ya shafe ni?" Nafisat ta tambaya. "Yanzun kuwa zaki ji komai." 58 * ** * Bayan ta koma kan kujera ta zauna, sai ta fara ba mu labari da cewa "Duk da zafina da iya kissata wannan bai hana na ji tsoron H. Ubaida ba, domin kuwa mace ce mai zaifin bala'i tare da saurin fushi. Ya kasance cewa mahaifiyarki ita ce amaryarta. Mahaifinki ya dade yana neman 'ya mace a sakamakon duk 'ya'yansa-maza ne. Ita Kawas ta haifi maza biyar amma uku sun rasu saura biyu Haruna da Kabir, sannan mahaifiyarki ta haifi 'ya'ya hudu duk da ke. To amma kafin ta haife ki ta dade sosai har hakan ya sa mahaifinki ya zata haihuwa ta tsaya musu ne. Kwatsam sai ga mahaifiyarki ta fara laulayin ciki da ganin haka sai gaba mai tsanani ta kullu a tsakaninsu har ta kai sun daina wa juna magana. Kawaş tayi-tayi ta zubda cikin amma abun ya gaga, har Allah ya sauki mahaifiyarki lafiya. A ranar da ta haife ki wanki wanda kike bi ya rasu a sakamakon wawan marin da ya sha a wajen Kawas, don ya je da gudu ya fada mata cewa an haifarwa baba yarinya kyakkyawa. Tayi masa marin ne har sai da ya fada kan tebir din da gilas da ke falon, fuskarsa ta yanyanke а sakamakon farfashewar da gilas din yayi wanda yasa hakan ya zo da karar kwana." Ta dakata sannan ta cі gaba "Tun ranar da aka haife ki Alhaji ya dauki ransa gaba daya ya dora kanki. Hakazalika ya rinka kashe kudi kamar daga sama ya same su. Hakan ya bakantawa Kawas rai sosai har ta neme ni da shawarar yadda zata yi. Ban yi niyyar ba ta muguwar shawara ba, amma ganin yadda take kallona kamar wacce na azurta 59 mahaitinki da 'ya mace ya sa na ji tsoron ta na ce da ita a sace ki kawai a kashe. Hakan ya faranta mata rai matuka har va sa tayi mini kyautar da ba ta taba yi mini ba. Ana sauran kwana biyu a rada suna mahaifiyarki ta Kamu da matsanancin ciwon eiki wanda ya sa ta fita hayyacinta. Bayan an kaita asibiti sai aka ba ta gado. Dan tsananin son da Alhaji ke yiwa wannan jaririya sai ya ki bawa kowa ita ya rike a barsa. A wannan rana sai da Kawas tayi kirana ta sannar da ni cewa wannan ita ce damarta ta Karshe idan kuwa ta wuce ta to ba zata samu wata damar ba. Dan haka muka yanke shawarar cewa mu hada baki da Doctor din asibitin a karbi 'yar a sanar da shi cewa idan ba tana kusa da babarta tana ba ta nono ba to ita ma 'yar zata samu illa, jin hakan shi ya sa Alhaji bayar da jaririyar. Bayan barin mahaifinki asibiti ne Kawas ta bani jaririyar ta ce na kaita da daddare in sa dana Hafiz da abokan shashancinsa su kai ta can wurin katon kwalbati su kashe ta su jefa ta ciki. Ta kawo kudi dubu talatin ta ba ni, ta baiva likitan ma dubu ashirin da biyar bayan yayi mata alkawarin zai bata motacciyar jaririya. Bayan tafiyarta likitan ya ba ta jaririyar, take ta zarce gida ta sai likkafani ta sanya yarinya a ciki ta ajiye gefe guda. Da Alhaji ya dawo ya ji labarin mutuwar 'yarsa yayi bakin ciki sosai kai har da kuka. Ni kuwa bayan na je gida sai na nemi Hafiz da yake Allah ya hada ni da sangartaccen da mugu marar jin Magana, sai na sanar da shi abin da nake so yayi mini. To kin ji dalilin da ya sa Hajiya Maryam ta same ki. Da ma sai da na yi masa kwatance da gidan sosai, kuma na yi masa kashedin 60 kada ya kuskura ya bari ki mutu, kuma ya tabbata ya ga sanda ya dauke ki sannan ya bar wajen. Nayi haka ne domin samun wasu kudi daga wajen Hajiya Maryam sakamakon yawaita fadin tana sha'awar ta ga ta haihu. Bayan ta gama sai ta kalli falonta sama da kasa ta ce "Ga shi kuma Alhamdulillahi kudin Hajiya Maryam ya zame mini gata, ya canja mini rayuwa gaba daya, domin da su na gyara dana Hafiz shi ma ya zama mutum sannan kuma ya zama babban masana'anci a sakamakon makarantar da na komar da shi da rokon Allah. Sannan da su ni ma na dinga kasuwanci ina juya su har suka zama miliyoyi. Dalilin da ya sa na kaurace mata a wannan lokacin shi ne kada ganina ya dinga zame mata tashin hankali, Allah ya ji kanta, sb "Amin" Duk muka amsa. Daga nan ta sanar da mu cewa tana zuwa ta raka mu. Bayan hawanta sama da kamar minti hudu, ta fito hannunta rike da mayafi. Tana saukowa aka yi sallama aka shigo falon. Wani farin saurayi mai matukar kama da ita ne ya shigo. Af Hafiz har ka dawo?" Ta tambaye shi a yayin da take kokarin yafa mayafinta. "Na dawo Hajiya, baki kika yi ne?" Shi ma ya tambaya. 'Ya'yana ne." Ta fada tana murmushi Bayan yayi mana sallama sai muka gaggaisa, Baila "Hafiz ba zama zaka yi ba, ina so ka kaimu gidan A.M. Sadiku yanzun." Ta ce da shi. "A.M. Sadiku dai wanda na sani a da? Ya tambaya, "Ba shakka shi." "Anya suna cikin gidan nan na shi har yanzun?" Ya sake tambaya. s neb ainided ingеd "Ina zaton hakan." Ta amsa masa, 361 "Bakin naki za a kai?" "Eh su za a kai, kai dai labari ne mai tsaho zan sanar da kai sai mun shiga mota. Mota Kirar Intergra ce keyi mana jagaba. Ta ja ta tsaya daidai lokacin da muka isa gindin wani katafaren gida. Bayan fitowarmu daga motocinmu Hafiz ya kwankwasawa mai gadi kofa. Ya dauki tsahon wani lokaci kafin ya bude Kofar. Bayan Hafiz yayi masa sallama sai ya nemi yayi masa sallama da mai gidan. "Wane mai gidan kuma?" Mai gadi ya tambaya yana mai shakka. "Wannan dai mai gidan mana A.M. Sadiku." Hafiz ya sanar da shi. "Ahaf, ka ce ba ka san ya kwanta cuta ba?" Sai da dukkaninmu muka dubi juna a yayin da muka ji wannan magana. "Allah sarki yaushe kenan." Hajiya Mai-Duka ta tambaya. "Haba yau kusan shekara biyar da wasu 'yan watanni." Ya fada yana sosa keya. "Amma ku shigo in kai ku Bangaren matarsa. Bayan fitowar matar A.M. Sadiku daga cikin uwar dakinta sai muka gaggaisa. Tabbas duk hankalinta yana kan Nafisat ne a yayin da ita ma sai tayi kuri tana kallonta. Hajiyar a zahiri kyakkyawa ce ainun, domin kuwa zaka ga duk da tsufanta ba ta da siffar Allah ya isa. Can daga baya sai Hajiya Mai-Duka ta nisa ta ce "Hajiya baki gane ni ba ko?" Hajiya Yaha ta kalli H. Mai-Duka a tsanake, daga bisani bakinta ya dan fadada zuwa murmushi take kuma ta fara darıya tana fadin "La!! Mai-Duka ke ce kuwa a duniyar 62 nan?" Tana fadin haka ta mike ta nufi H. Mai-Duka ta rungume ta. Duk wannan abu da suke yi babu wanda ya ce kanzil daga cikinmu. Su kuwa banda murna babu abin da suke yi. Bebi Maryam kuwa tunda muka baro gida ba ta farka daga barcin da take yi ba sai yanzun. 10 RANAR FARIN CIKI Bacin mun nutsu H. Yaha tasa mai aikinta ta kawo mana Five Alive mai matukar sanyi, kowannenmu ya kurkurba. Daga bisani H. Mai-Duka ta nisa ta ce "To Hajiya Allah ya kawo mu ranar farin ciki, ranar da ya cancanci in nemi gafararki. Ina rokonki da Allah ki yafe mini akan abinda nayi miki wanda ba ki san da shi ba. Ina san ki ba ni aron hankalinki, sannan ki kai zuciyarki nesa. Idan ba ki manta ba shekaru ashirin da doriya da suka shude kin haifi 'yarki mace kyakkyawa wacce a rashinta Alhaji ya kamu da ciwon hawan jini kuma kuka fita daga kamanninku gaba daya. Abun da ya faru ne..... Takę ta fara ba ta labari kamar yadda ta sanar da mu tana ba ta labari ita kuwa Nafisat sai kallon mahaifiyarta take tana zubda hawayen farin ciki. Gamawar H. Mai-Duka ke da wuya ta nuna Nafisat ta ce "Yanzun dai ga Nafisat Allah ya raya miki ita, da fatan zaki yafe mini." 63 Тарн даma fadin haka Hafiz ya durkusa уa се "Hajiya dan Allah ni ma ki yafe mini kuruciya ce ta sa ni nikata hakan." "Haba babu komai ai hakan ma da kuka aikata kun nikata alheri tunda baku dauki ran yarinyar ba, sannan kuma rashi ne ya saku aikata hakan," Hajiya Yaha ta fada tana sharar hawaye. T'sam! Nafisat ta mike ta nufi mahaifiyarta, da zuwanta ta fada kanta tana kukan farin ciki. Lokacin da suka nutsu ne mahaifiyarta tayi mana godiya Kwarai, sannan tayi ma Hajiya Maryam addu'a ta gari da kuma yayana. Da gamawarta ta amshi bebi Maryam tayi matn addu'a a kunnenta, sannan ta ci gaba da yi mata waки. Jmmwa kadan da yin hakan ta nemi da mu je Bangaren mabaitin Natisat. Da zuwanmu dakin muka tarar da wasu maza su hudu n zazzaune suna bira. Shi ma dattijon da ke zaune akan gondo yana sahün hirar tasu, Hannun dattijon da ya dan motse Endan a yayın da sauran jikinsa bai yi kama da na mai jinya ba. Bayan mun gaisa dattijon ya kalle mu daya bayan daya, yanp żuwa kan 11, Mai-Duka ya shaida ta "Kar dai a ce MaiDoka dillaliya ce wannan." Ta fan yi murmushi yayin da take amsa tambayara Athap or ye оanа." Yayı murmushi shi ma ya ce "A'a ashe rai kan ga rai Mm Duka? Yn fashe da dariya. "IHakn abun yake Alhaji, wallahi ba na zama a garin me osgt shн уn sа." Та fada tana kallonsa, A'a wannan ba hujja ba ee Mai-Duka." Lo Alhaji nayi laifi a gafarce ni, ya kuma aka jí da bakmi Mat yri snu ma'niki." Ya amsa ta'aziyyar, 64 Hajiya Yaha ta kalli mijinta tare da sauran samarin da ke dakin, sannan tayi ajiyar zuciya,"Alhaji yau fa zaka ji abun da zaka yi mamaki Rwarai da kuma farin ciki." Ya daga kai ya kalle ta "Kamar me fa?" Ya tambaya. "Ga 'yarka mace tilo da kake da ita Allah ya dawo maka da ita." Ta nuna Nafisat. Gaba daya ya sukurkuce yana mai tambayar "Ban gane manufarki ba." "Zaka ji komai yanzun a bakin Mai-Duka, dan an ce waka a bakin mai ita tafi dadi." Ba tare da 6ata lokaci ba H. Mai-Duka ta kwashe duk abinda ya faru a baya ta sanar da shi, sannan ta hada da neman gafara. Mahaifin Nafisat tare da yayyenta musamman ma wadanda suke uwarsu daya wato Isma'il da Ahmed sun yi farin ciki matuka hade da mamakin faruwar hakan. Shi ma Haruna yayi murna kwarai wato kanin Kabir. Alhaji ya nisa ya ce "Amma kuma abinda mamaki yake ainun. Na gode kwarai dillaliya kuma na yafe muku har ita Hajiya Ubaidan Allah kuna ya jikanta." Sannan muma yayi mana godiya tare da yiwa yayana da matarsa addu'ar samun aljannatul-Firdausi. Daga bisani Hajiya Mai-Duka tayi mana sallama da zummar zata tafi. Take Alhaji ya sa Haruna da yake shi ne babba a cikin samarin da suke zaune ya dauko masa takardar cak a daki. Take ya sa ya rubuta zunzurutun kudi na dubu dari uku ya baiwa Hajiya Mai-Duka da danta. Tayi godiya marar misaltuwa sannan suka fita, mahaifiyar Nafisat na biye da su. A daidai lokacin da suka bar dakin ne Nafisat ta dube ni ta ce da ni "Yaya dubi wuyansu yaya Haruna ka gani." Ina kallon wuyan su kuwa idona ya ci karo da tsagun dake wuyansu. Tabbas sai yanzun na tabbata gadon gidansu 65 kenan. Hajiya mahaifiyarda ke thigia dakin fuskaz cike da fara a. Nafisat ta tura Hn takana ta ciro ata 'yar karamar sarka mai kýélrkai tana daya d22 cikin alamomin da Hajiya Marym tsaka a čikin bakar ledar da muka dauko a cikin dirowarta. Sannan ta senar da mu a wasikarta cewa da ita aka tsinci Nafitata sakamakon sa mata shi a hannu da aka yi, lezle anu1 "Momi kin t ta huna wa mahaifiyarta. Ta amsa tana nazarmtaWanhan ai kamar sarkar da ka siyo daga umara Alhaji." Hajrya ta fada tana mai mika masa -Shakka babu ita ce, Kih gaa ba ia styanta nayi ba wani balarabe ne da muka yi haji taleya ba ni ita wai in kaiwa "yata, kin san kuwa baki haife'ta ba a lokacin." Ya fada yana jujjuya sarkar Muna isa gida muka tarar an yi manyan haki Dr. Aimana ne zaune akan motarsa kirar HALA fare de abokinsa. Mun yi farin cikin ganin juna hatuka ba tare da mamakin ganinsa ba, domin kuwa ya yi manz alkawarin ziyartarmu. Da yake Magariba ja kawo kai ba mu tsava bata lokaci ba na bude kofar gida Bayar mun yr fakin đĩn motocinmu a cikin garejin gidan, sai muka nufi cikin gidan. Sai bayan da kowannenmu ya nutsu sannan muka fara hirar yaushe gamo, sai bayan da su Kafisat suka yi wanka sannan suka shiga kicin domii girka mana mana dina. Da gama girka mana abincin suka kai dining suka shirya. Duk wannan kai komo da suke yi idon Dr. Ailfiana na kan Moda. RED Sai da muka zazzauna akan dining din. sannan ygaba daya muka ji Nafisat da wannan bako suh haga baki wajen cewa "La!!" 66 Sannan Nafisat ta hada da cewa "Dama kai ne ban gane ka ba tuntuni?" Shi ma bakon ya amsa da "Ni ma wallahi ban ganc ki ba ko kadan sai yanzun. Nafisat tayi dariya ta ce "Ashe rai kan ga rai dan Fulani ya ga furar gero. Dukkansu suka kwashe da dariya. Mu dai mun yi saroro muna kallonsu. Bakon ya kalli Dr. Aimana ya cé "Gogan ga fa madam din da nake fada maka nan." Dr. Aimana yayi dariya shi ma ya ce "Au Nafisat da ma ke kika kusan sa aminin nawa gangarawa?" Nafisat tayi murmushi kunya ta kama ta. Bayan wani lokaci ne ta sanar da ni cewa shi ne mutumin da ya rage mata hanya a lokacin da motarta ta mace a tsakiyar daji "Ka san lokacin ina yawon neman Uzaifat." "Ba shakka an yi haka, da ma shi ne?" "Eh" Ta amsa. Sannan muka ci gaba da cin abincin. Bayan mun gama cin abinci ne Dr. ya tashi ya nufi kofar fita "Engincer ina zuwa" ya ce da amininsa. "Ba laifi" Ya amsa daga nan aka fara kallon soyayya tsakaninsa da Nafisat. Dr. ya shigo falon hannuwansa rike da ledoji wadanda ban taba ganin irinsu ba. Bayan ya zauna sai ya miko mini daya ya ce "Sirikina ga taka tsarabar Holland din." Ban yi mamakin jin hakan ba, domin kuwa ko yaro ne yake tare da mu zai fahimci cewa akwai so da kauna tsakaninsa da Moda. Ya sake mikawa Uzaifat tata ledar, sannan ya mikawa Engineer leda daya, da mika masa ya kalli Nafisat ya ce "To Honey ga taki tsarabar." Kunya ta hana ta karba har sai da ya mike ya je daf da ita ya mika mata sannan ta amsa. Shi ma Dr. da kansa ya 67 matsa kusa da Moda yayi murmushi hade da cewa "Have it my soul, wannan ita ce tsarabar da nayi miki, domin na nuna miki kaunata a gareki a fili I Love U." Moda ta sa hannu ta karba "Thanks alot." Ta ce da shi. "Don't mention." Ya fada yana kallonta a daidai lokacin muka kalli juna ni da Uzaifat muka yi murmushi mai karfafa zuciyoyin masana'love. Sai da suka kwana sannan suka yi haramar

Chapter 4 of 6