Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 6
masa riga malam masallaci." Muka yi dariya ni da Nafisa. "Allah dai ya sauwakc." Nafisa ta fada. Bayan na sanya kasct din ne na koma na zauna tare da daukar littafina domin in ci gaba da karatun. Muryar da karet din ya amayar ne ya sanya mu daga kai gaba dayanmu lokaci guda muka kalli juna, muryar yayana ne yana baiwa su T.j. kashedi akan kar su kuskura su saurara mini, wato dai kaset fin da na baiwa baba Musa ne ya daukar mini a ranar da su T.j. suka ziyarci gidanmu. Na tashi nayi hanzarin cire kaset din zuciyata cike da al'ajabin yadda hakan ya faru. Sai a 17 lokacin na lura domin tabbas ba shi ne kaset din Celine Dion din ba, dan shi fari ne wannan da nakc rike da shi kuwa baki ne, lallai ido gululu ne hankali ne ke gani ba shi ba, dan kuwa shi ma yana kan redio a ajiye gefe guda hade da 'yan makullaye guda biyu su ma ajiye. Na so in manta in da na taba ganinsu, sai dai cikin ikon Allah na tuno cewa na safe din yayana ne da ke dakinsa na sama. Su Uzaifat su ma sun riske ni suna masu farin ciki marar misaltuwa. "Ubangiji yana bayan mai gaskiya yaya. ba ga shi ya sanya shi mantawa da keset din ba anan, ina kyautata zaton garin sauri ne ya manta su." In ji Uzaifat "Har da makullin safe dinsa ga shi." Na fada ina nuna masu. Take muka nufi dakinsa. mun sha gwagwarmaya sannan muka bude dakin. Safe din dam yake da kudi rafa-rafa na dari bibbiyu. * ** * Har yanzu tunanina bai wuce yadda aka yi yayana ya manta da kaset din da ya karba a hannuna tare da dan mukullin safe din sa ba, duk da na san babu yadda ubangiji ba ya ikonsa, to maganganun Uzaifat ma sun sake sanyawa na sadudu domin a yadda ta fada ta nuna cewa ubangiji yana bayan mai gaskiya, kuma ba zai taba fora mai karfi akan raggo ba, hakazalika ba ko zai taba dora azzalumi akan na-gari ba, in ko har yayi hakan to tabbas hakan ya so domin kuwa wata shari'ar sai lahira. "Kamata yayi muyi saurin faukar mataki. in kuwa ba-haka ba duk sanda ya farga bai ga kaset din 18 nan da dan mukullinsa ba, to wallahi zai farma na tunda a tabbata yanzun tuni labari ya isar masa cewa kun dawo gida." Nafisa ce ta katse mini tunanina. Na ja numfashi na ce "Tabbas hakan zaa yi. amma before that ina son muyi hanzarin zuwa Abuja wajen Hajiya tun kafin ya dawo kamar yadda ta fada. Suka nuna amincewarsu hade da murna. Ko ni ina farin cikin sake hada ido da Hajiya Maryam wacсе na rika tamkar mahaifiyata tun bayan rasuwar iyaycna. Cooker Gas na janye daga mazauninsa na sanya dan mukullin hade da kaset din a bayansa, sannan na mayar da shi mazauninsa ya zauna tsaf kamar ba'a taba wajen ba. Nayi hamdala ga ubangiji sannan nayi dakina. * ** * Washegari bayan mun karya muna zaune akan dining kowannenmu na saka nasa zaren a zuciyarsa na daga abinda yake tunani. Na katse musu tunaninsu da cewa "Na yanke shawara wacce nake ganin ita ce mafi dacewa a tare da mu." Na ja na tsaya tare da lura da fuskokinsu, ganin sun ba ni hankalinsu ainun yasa na samu kwarin gwiwar ci gaba "A ganina bai kamata muyi gaban kanımu mu ce zamu tafi gidan yaya ba tare da sanin hukuma ba, domin kuwa sanin kanku ne cewa babu yadda za'a yi ya zauna ya sakankance ba tare da kasancewa cikin shiri ba alhalin ya san yana cikin hatsari, dan haka zan nemi taimakon Inspector Kabir saboda ba na son mu fauki law into our hand." Shakka babu su kansu sun san cewa wannan shawara tawa ingantacciya cc, danhaka suka ba ni goyon baya, sannan wani matashin murmushi ya biyo 19 baya, wannan kuwa sako ne daga SAHIBATA. Na dauki kan waya na danna lambobi. Ba tare da 6ata lokaci ba ta fara ringing, zuwa dan wani lokaci aka dauka, na amsa da cewa "Ina son inyi magána da Inspector Kabir." Sagent ya sanar da ni ya fita amma in sake bugowa nan da awa daya. Garin yayi lub-lub kamar furkar angon da ke sauraren zuwan amaryarsa, da ma tunda Asuba aka tashi da sanyi mai ratsa jiki, domin kuwa saboda sanyin yayi yawa ma har sai da hazo yayi kaka-gida inda har ya hana jirage tashi, kamar yadda aka sanar a labarani, bakwai na safe. Danhaka mun rufe kowacce kafa da muke tsammanin sanyin ka iya shigowa, sannan na mike na danna Heater inda falon ya fara amsar/bakon dumi. Award din India muke kallo wanda SHARUKHAN ya lashe. Su Uzaifat, sai faman zabga musu suke yi, ni kuwa dariya kawai nake yi, musu. In suka jeho mini tambaya akan waya fi gaskiya cikinsu, sai ince Uzaifat ce. Kai har Nafisat dai ta hakura da musun tana fadin "Ni ma Allah ya kawo mini nawas masoyin da ba zai taba ganin laifina da karyata ba, domin kuwa wallahi yaya ka nuna mini son kai." Na tuntsire da dariya na mike na nufi Telephone domin sake neman Inspector Kabir. Nayi sa'a kuwa ya dawo, bayan na sanar da shi bukatarmu ne ya yaba da hankalina tare da ba ni goyon baya akan shi da kansa ma zai bi mu, hade da cewa zai zo gidan, namu ma yanzun. Nayi masa godiya, sannan na ajiye kan wayar. Ina cikin sanar da su Nafisa yadda muka yi ne aka yi 20 wani irin buga Kofa wanda ya gigitamu. Cikin hanzari na tambaya "Waye ne haka?" Amma shiru ne ya biyo baya, sai ma wani bugun da aka sake yi. Mamaki ya kama ni, ni dai na ga cewa akwai Bell da ake dannawa a bakin kofar, mai zai hana mai shiga ya danna cikin mutunci? Take zuciyata ta tabbatar mini cewa ai kuwa tunda ake irin wannan bugu tofa rashin mutunci ne ya kawo sa. Su Nafisa duk sun yi tsuru-tsuru yayin da aka ci gaba da buga kofar. Cikin sanyin murya Nafisa ta ce "To wai shin ina baba Musa yake ake irin wannan bugu?" Na amsa mata da "Ai tunda kika ga haka sai dai Allah ya kiyaye shi kawai zamu ce." Gaba faya aka ci gaba da girgiza kofar. "Wallahi kowaye sai dai ya balle kofar ba za a bude ba." Uzaifat ta fada ranta a басе. Muna tsaye kikam muna kallon sarautar ubangiji kofa na barazanar 6allewa, take na nufi Telephone domin na sanar da Inspector Kabir halin da muke ciki don yayi saurin kawo mana agaji, amma sai me? Ai tuni an tsinke layin ban da shuuu! babu abin da kan wayar ke yi. Ajiye kan wayar da nayi yaya daidai da fadowarsu falon kowannensu na muzurai. Sanye yake da bakar shirt mai gajeren hannu da koren wand hannunsa rike da karamar Pistol. Mutuniynta ko wannan karon shigar da tayi sai ka rantse da Allah idan a kasa sa ta a masallaci za tayi limanci, bakar abaya ce a jikinta hade da mayafinta, wannan karon arnan takalmin nata ba baki ba ne shudi ne, Sussy kenan wanda Gulawa mutum ciki da takalmin nan nata ba 21 wata tsiya ba ce, hannunta nke vake ita ma da Pistol. Shi. ma cikon na ukum masu wani katon gaske ne fuskarsa sai naso take tana maiko kamar kosai ya ji man gyada, wanda a zahirı nayi tsammanin cewa уa dade da shekawa barzahu an jela gawarsa a teku kifaye sun cinye, abokin harkar T.j kenan wanda ya keta rigar mutuncin mahaifiyar Uzaifat wanda take nemansa ruwa a jallo da gidauniyar mutuwarta wato Chiko kenan. Fuskarsu sam babu utunci, suka ci gaba da tsayawa a yayin da mu kuma suka yi mana umarni da mu zauna, duk mun žauna face-izaifat da ta ki zama ta ci gaba da kallon Chiko bå ko kakkautawa. "Ke ba da ku ake magana ba ne, ko kin fi sauran ne da suka bi umarni?" Sussy ta daka mata tsawa. T.j. ya kalli Sussy ya ce "Take it casy baby aí ba sai kin daga murya ba, in san cewa ba fada ko ta'addanci ne ya kawo mu ba amma duk da haka ba zamu yarda da taurin kai ba." Yayi shiru sannan ya ci gaba da "dan gyara mata-tsayuwar kuncinta may be she will obey." Kafin ya rufe baki Karar saukar mari ya dira a dakin, wanda saboda tsananin Karfinsa sai da Uzaifat ta kife kasa. Nayi yunkuri domn kai mata agaji amma ina! Takalmin Sussy ne ya maida ni baya, na rike cikina ina salati. Nafisa ko také ta saka ihu tana kuka "Wayyo Allah mun shiga uku." Ta fada.cikin murya mai cike da ban tsoro. "Cool down." Chikova fada. 22 "Samari da yan mata ku kuka jawo hakan ta faru, mu abinda ya kawo mu daban in har kun ba mu shikenan you are very free." T.j. ya fada muryarsa cike da gargadi. Uzaifat na kwance tana nishi amma dan taurin kai irin nata sai da tayi nagana "Wallahi koma mene ne ba zamu baku shi ba, sai dai ku yi duk wacce zaku yi. Ta fada muryarta na rawa. "Fine" T.j. ya ce yana murmushi. "Duk da haka gara dai mu tambaye ku, kuna gwamma dai ku ba mu kafin mu nemi oga a waya ya ba mu izinin saba muku kamanni." Yayi shiru "Kaset din da ya manta shi a falo hade da dan makullin safe dinsa, sannan sai Film din da ke cikin Camera da ka fau hotonmu wato Nagetive kenan, su zaku ba mu mu juya muyi tafiyarmu cikin mutunci mu barku cikin aminci." Na ja numfashi na ce "Mu ba mu ga komai ba domin shikaran jiya muka dawo sai dai in wani ne ya shigo ya dauka, camera kuwa tun a ranar da ya riske ni a daki rabona da ganinta." "Kai kar ka kawo mana rainin hankali mana ka ji? Ku fito mana da shi tun kafin ran kowa ya baci." Chiko ya fada yana muzurai. Ni dai banda addu'a babu abin da nake yi, na ubangiji ya kawo mana wanda zai agaza mana. "Wai kai gwari ne?"" Uizaifat ta fada tana kallon Chiko, sannan ta ci gaba "in ba gwari ba ai maka Hausa ka kasa fahimtar me ake fada' Mun ce ba mu ga komai ba sai ku fice ku bamu waje. 23 Chiko yayi kanta, a yayin da T.j. ya dakatar da shi "Rabu da su dama ce suka samu, amma duk za su gane kuskurensu yanzun nan, jeka mayar da wayar nan mu yi kiran Oga mu sanar da shi don ni wannan raini ya ishe ni." Take Chiko ya fice. Tj. ya nufi gindin "Telephone din ya kara a kunne, zuwa can waní lokaci sannan ya danna lambobi "Hello Oga mu ne...ch nuna nan din amma sun Ki ba mu hadin kai Oga..., Haba mun yi iya kokarinmu Og To sbikenan dama umarninka mu ke jira mu ji, yanzun nan zamu cika aiki." Ya ajiye kan wayar yana murmushin keta "Baby Ogu ya ba mu izini ko ta halin Kaka mu karßar masa sakonsa Even if it takes a lifo." Cabana ya yanke ya fadi da jin kalamansa, dan na san yayana sarai zai iya fadin hakan. Lokacin da Sussy ta auni Rafata da Pistol dinta, to a lokacin ne wata siririyar murya ta ratso fafon "Hold on! Kutsaya a position dinku ba tare da motsi ba in kuwa ba haku ba ranku yana bakin wanan bindigar tawa. Shirun da muryar tayi ne yayi daidai da harbin da ya dira akan fanka, wanda hakan ya sanya su T.j zubewa a Rasu tare da fatali da bindigoginsu. Kwanciyar da suka yi a Rasa ne ya baamu damar ganin wannan mai magana. Fara ce kynkkyuwa mai matsakaicin tsaho, hannunta rike da Pistol, tayi murmusbi hade da fadin "Ku tashi ku kwashe bindigoginи," Muna Kokarin mikewa zuciyarmu cike da farm ciki, a lokaci guda murnarmu ta koma ciki, Chiko ne ya 24 kara mata bindiga a kunnenta yana fadin "Ajiye bindigar ki ko in fasa miki kwanya." Cikin nutsuwa tayi wurgi da bindigar. Jin muryar Chiko ya sa su T.j. mikewa kowannensu ya dauki bindigarsa, sannan Chiko ya ingizo wannan kyakkyawar budurwa ciki yana dariya. Ganin haka ya sanya ni yanke hukuncin ba su dukkan abinda suka bukata, tunda sun ce babu abinda za su yi mana, in ya so ubangiji shi ya san yadda zai yi da su kawai kar taurin kanmu ya sanya su kashemu a banza. Tunanina ya tsaya cak! A lokacin da su Inspector Kabir suka shigo kusan su bakwai, kowanne da zungurazunguran bindiga. "Your hands up." Inspector Kabir ya fada. Gaba dayansu suka daga hannayensu, 'yan sandan suka karbi bindigoginsu sannan suka sanya masu Handcuff, lokaci guda Inspector Kabir ya ba su umarnin suyi cikin mota da su yana zuwa. Bayan mun gaisa nai masa godiya ne yake sanar da ni cewa "Ai makotanku zaku yiwa godiya, domin su suka yi mana waya cewa gidan nan babu lafiya, dama ai mun yi da ku zan zo, har na fito Sajen ya biyo ni ya sanar da ni sakon wayar da ya aiko, to ganin haka ya sanya na bugo maku waya, sam! layin ya ki shiga alamar an yanke wayar, to ganin haka ya sanya na dada tabbatar da gaskiyar lamarin." Muka sake yi masa godiya, sannan yayi mana sallama ya tafi hade da sanar da mu cewa yana jiran mu a can Police Station din. Bayan tafiyarsu ne kowannenmu ya nemi guri ya zauna, zuciyarmu cike da 25 godiya gurin ubangiji hade da hamdala da fatan cowa InshaAllahu karshensu T.j. ya zo, saura ogan nasu. Sallama muka ji daga can harabar gidan, na shaida mai muryar makocinmu ne Alhaji Mudi mai zarc wanda Inspector Kabir ya ce gidansa akai musu waya. Bayan na fita mun gaisa nayi masa godiya, shi kuma yayi mini jaje. "Ai a bandaki nake ina wanka kamar an ce in juya in ga, kawai sai na hango su uku kowanne da Pistol a hannunsa suna kokarin shiga dakin Musa mai gadinku, to shi ne na tabbatar cewa babu lafiya domin kuwa Barayi yanzun sun tayar mana ba sa sati ba su shigo layin nan ba. To ko wankan ban gama ba na fito daga bandakin na sauka falon kasa, shi ne na sanar da 'yan sanda." Sai yanzun na tuna da Baba Musa, duk a tunanina ko ya fita ne a lokacin da abin yake faruwa, to amma yanzun kuma da Alhaji Mudi yayi maganar cewa ya gan su suna kokarin shiga dakin sai zuciyata ta fara bugawa a hankali hade da razana. Na nufi dakin a hankali kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki, nan na bar Alhaji Mudi a tsaye yana bi na da kallo. Bayan na tura kofa ne na saki uban salati hade da fadawa dakin baba Musa. Sai bayan da na kwance masa daurin da suka yi wa bakinsa hade da hancinsa, sannan Alhaji Mudi shi ma ya shigo ya taya ni kwance masa daurin hannunsa, jikina na rawa na fada bandakinsa na debo ruwa a cikin karamin bokiti na fito. Alhaji Mudi ya amsa a hannuna yana salati yana yayyafa masa. Ai tunda na ga jini yana gangarowa daga kofar hancinsa, zuciyata ta sallama domin sun yi masa dauri ne ba na 26 wasa ba. Alhaji Mudi ya ajiye bokiti hade da taba Jijiyar wuyan baba Musa, ya sake yin salati cikin murya mai cike da ban tausayi ya ce "Uzaif sai dai mu dau hakurin Musulunci domin kuwa Musa rai yayi halinsa, Allah ya jikansa da rahama." Ai ban san sanda nà daka tsalle nayo waje a guje ina ihu ina kuka kamar wani dan yaro, wanda dalilin yin hakan ya sa su Uzaifat bazamowa waje. Suna taradda abinda ya faru su ma suka soma kuka da kyar Alhaji Mudi ya lallashe mu hade da sanar da mu illar yi wa mamaci kuka, haka dai muka hakura ba dan zuciya ta so ba. Take na shiga na bugawa Inspector Kabir waya na sanar da shi rasuwar baba Musa, yayi mani ta'aziyya hade da sanar da ni cewa shi ma yana nan tafe. Muna tsaye a harabar gidan Inspector Kabir ya iso tare ua 'yan sanda biyu, bayan sun shiga dakin baba Musa sun yi 'yan dube-dubensu ne suka fito, ya sake yi mini ta'aziyya sannan yayi wa su Nafisa. Lokaci guda ya ci gaba da kallon wuyan Nafisan take kuma ya shafa nasa, komene ne dalilin yin hakan ba zance ba. Kallon kurillan da yake yi wa Nafisan kamar sai a lokacin ya taba ganinta ne ya sanya ta sunkuyar da kai hade da kunce dan kwalin da ta daura a kanta ta yafa a kanta hade da wuyanta, kasancewar jikinta ba hijabi kamar yadda ta saba sawa a dalilin rudanin da muka shiga. Can kuma kallonsa ya koma ga bakuwarmu wacce har yanzun ba mu san ta ba ballantana dalilin zuwanta, sai dai tabbas ina yi mata kallon sani, yayi mata murmushi fuskarsa cike da mamakin ganinta. 27 "Yallabai na iya suturta mamacin yanzun ko?" Alhaji Mudi ya tambaya. Inspector Kabir ya dago kai ya ce "Tabbas! Sai ku hanzarta domin yamma tayi kar a bari lokaci ya Kure. Zan koma Station na rubuta Statement, ba zan samu damar halartar jana'izar ba domin daga nan zan wuce gida in kai mahaifina asibiti." "Assha bai ji dadi ba ne?" Na tambaya. "Eh ba shi da lafiya ne." Muka yi masa sannu hade da fatan Allah ya ba sa lafiya. "In mun gama karbar ta'aziyya ka kai mu mu gaida shi." Na rufe da ina mai nuna damuwata domin kuwa Inspector Kabir ya taimakawa rayuwarmu saboda haka ya cancanci yabo. 7 An yi jana'izar baba Musa mai gadi da fatan Allah ya ba sa Aljannatil Firdausi, amin. Bayan sallar Magarib ne muna zaune a falo, na kalli bakuwarmu na sake yi mata sannu da zuwa hade da tambayar ta ko ita wace ce. Ta yi murmushi hade da fadin "Da farko dai Moda nake kamar yadda mutane ke kirana, amma ainihin sunana Nafisat Abdulmalik, wanda na san kana da labarin rasuwar mahaifina daga bakin Hajiya, a takaice dai ni ce 'yar Hajiya da ke Zariya." 28 Haba! Hajiya Maryam ce kamar da na gani a jikin bakuwar, tabbas da ita tayi kama. Lallai Hajiya ta sanar da ni rasuwar mahaifin Moda bayan an haifeta da wata uku. Nafisa tayi tsalle ta fada kanta tana murna, ni ma na ji dadin zuwanta kwarai da gaske. Na tambayc ta vadda aka yi ta san nan gidan. "Kakata ce ta ba ni address, wato mahaifiyar abana. Ta tambaye mu labarin labarinsu T.j. Bayan un ba ta labari tun daga farko har karshe, ta sanar da nu cewa ita C.I.D. ce. "Yanzun ma yadda zamu sadu da Hajiyar a Abuja müke shiryawa." Bayan sallar Isha'i muka kai Moda gidan Hajiya Tsohuwa mahaifiyar Hajiya. Mun tarad da ita tana kadin auduga a fakinta, daga yin sallamarmu ta dau murya "A'a ku shigo, sannunku da zuwa sai yàu a gari?" Nayi dariya na ce "Haba Hajiya wallahi harkoki ne su kai yawa shi ya sa." Tayi murmushi "To ai shikenan, ya gida? Ya su Hajiya?" Nayi saurin amsa mata, gudun kar wata daga cikinsu ta sanar da ita abinda ake ciki "Suna nan lafiya, ai tana Abuja tafiyar ce ta zo cikin gaggawa shi ya sanya ba ta samu zuwa ba, amma duk sanda ta yi waya tana aiko da sakon gaisuwa, muma gobe muke son mu je Abujan shi ya sa na ce gara mu zo mu yi miki sallama. Wannan ma Moda ce wato Nafisa 'yarta da take Zariya yau ta zo." 29 Hajiya tsohuwa ta kalli Moda tayr mormashi hade da jin dadin ganinta. "Y'anzun nan daga zowata ko dan kwana biyu ba zata yi mini ba. zata wuce Ta fada tana kallona. "Haba ai kwana daya za můyi ko biyu. zata dawo mana tayi miki ko da sati daya ne. Tayi dariya "To Allah ya sa. Bayan wani lokaci muka vi sallama muka fito. Moda kuwa ranta duk a bace ba ta so ta rabu da kakarta ba, domin kuwa wannan shi ne karo na farko da suka sadu tun bayan da kakarta ta wajen uba ta zo ta dauke ta, lokacin Hajiya na shirin auren yayana dan ba ta ti shekara daya da 'yan watanni ba a lókacin. "A ce mutum yana da yan'uwa da dangi anuņa ganinsu ya gagara? Tunda nayi wayo nake son in hadu da sauran 'yan'uwana na wajen uwa, amma Gambo lu hana, tana ganin in na taho ba za a bar ni na koma ba, wallahi wannan zuwan ma sai da muka kai ruwa rana sannan da 6acin rai ta ba ni address na taho." Moda ta fada tana matse hawayc. Hakuri muká ba ta ta ci gaba da fada mana halayen kakarta na rashin son ta rabi dangin uwarta. Washegari bayan mun karya sai na fuskanci Uzaifat na cikin damuwa, don haka nayi kiranta muka kebe na tambaye ta meke damunta? Ta so ta boye mini, amma sai na ce da ita "Haba Uzaifat yanzun har akwai abinda zaki boye mini? Tun dazun fa na lura cewa you are not yourself why?" Idonta ya kawo hawaye lokaci guda ta sa hannu ta goge "Am really sorry Uzaif, wallahi ba haka ba ne 30 tunanin alhalin da mahaifina yake cike kawai nake yi. wallahi na matsu in gansa, gaskiya ain feeling bad." Na tausar da muryata na ce "Ki yi hakuri ai dole ne mu san inda yake tunda su Chiko din sun zo hannu. bayan haka ni ma abin ai yana damu na ko tsammaninki ke kadai ce 'yar abban?" Tayi murmushin jin dadin lafazina. "Ki bari zan bugawa Inspector Kabir waya ya tuhumar mana su, in ya so Abujan mu bari sai gobe. Zuwa an jima sai mu je Station fin mu ji yadda zata kasance." * ** * Na sanar da su Nafisa sakon Inspector da ya ce ba sai mun zo ba, mu bari sai gobe da safe kamar karfe tara mu zo gaba faya a wuce Abujan. Sannan ya sanar da mu mutuwar Sussy wanda ban so hakan ba, na so а ce ta er bakar wähala sannan ta gangara. Sannan a fadarsa su 1j-da Chiko sun nuna taurin kai matuka. don har electric aka sa musu a jikinsu kan su fadi inda mahaifin Uzaifat yake. amma sun ki fada. "Kar ka samu damuwa Uzaif am ready to help you, ba su gagare ni ba. ka bari sai mun dawo daga Abuja za su gane kuskurensu." Ya ce da ni. Yayin da ya ajiye kan wayar. Nafisa ta nuna farin cikinta sosai da jin tafiyarmu Abuja da su Inspector, domin a ganinta abin zai zo da sauki. Kwamishinan da aka canja sam bai yi mini ba, domin na fuskanci yana da girman kai tare da wulakanci, idan ka lura da irin kallon biyu ahun da yake yi mana: Mun riske su da Inspector Kabir a 31 harabar Station din suna zantawa, bayan mun gaisa ne Inspector ya gabatar dà mu gare shi, sannan ya kara da cewa "Shi ya sa nake son na bi su can tare da yara kamar uku ko biyar domin taho da Alhaji Yusuf din, don yana da dukkan proof da ake bukata kuma tun jiya na karbi warrant din arresting nasa. Kwamishinan ya bata rai hade da fadin "To ai ba komai sai in ce a dawo lafiya." Ganin wannan shan Kanshi da yake yi ne ya sanya Uzaifat fidda 1.D. Card dinta ta nuna masa hade da fadin "Ni sunana Uzaifat as you can see am a professional doctor." Ita ma Nafisat nuna masa nata 1.D. Card din, ganin haka ya sanya Moda tura hannu cikin jakar da take rataye a kafadarta ta fidda nata Card din ta ce "Nafisat Abdulmalik C.I.D." Ai da ganin haka fuskar mutuminka ta sauko ya dan yi murmushi ya ce "Commissionar Faruk Salami you are highly welcome." Ya juya suka yi magana da Inspector Kabir wanda ba nace ga abin da suke fada ba. Bayan sun kammala yayi mana sallama ya shige cikin Station din, na kalli su Uzajfat nayi dariya. Nafisa ta ce "Yaya dariyar me kake yi haka?" Tùn kan nayi magana Uzaifat ta amsa "Ba dole yayi dariya ba, ya ga mun fito da kimar mu kar a raina mana hankali mana wani shankanshi haka kamar а kansa aka saba kai wani matsayin mukami." Duk suka kwashe da dariya. Inspector Kabir ya ce "A'a kar a yagewa Ogana fa a gabana, kar in sa ayi cikin cell da ku yanzun nan: 32 Gaba daya muka dada kwashewa da dariya. Motarmu na gaba ta su Inspector Kabir na baya hat muka isa kofar gıdan yayana. Ni kadai na fito daga cikin motar na waiwaya na kalli motarsu Inspector nayi masa alamar'su dakata daga nan baya kar su karaso. domin ban manta ba Hajiya ta sanar da'ni a wasikarta cewa ya zuba masu gadi a gidan, to in har kuwa haka ne ba za a shiga gidan ta dadin ba, sai dai da dabara. Na nuff-Rofar Gate din na kwankwasa na ji shiru, na sake kwankwasawa a karo na biyu, sai a garo na uku ne na ga an bude wata yar kafa da ke jikin Gate din. Puskarsa na da kauri idan ka yi la'akari da kumatuna zaka yarda da hakan. 2eAssalamu alaikum." Nayi masa sallama. geb Bai amsa ba, dan haka sai nayi tunanin ko arńe ne Ko kưwở ma ba bahaushe ba ne. Shiru yayi yana kallona. kuma yana kallon motarmu, amma ban yi amnlanin ya hango motarsu Inspector Kabir ba, dan ltaka-sar navi masa nuni da motarmu na ce shi "Dan Allah-imu bakíne mun zo gun Hajiya ne" Ed Ya kailf Kwayar idona a fusace ya ce "Wa ya ba kü izimin Anwa?" ub Awaka cé dan iska da kana jin Hausar? Na fada a zuciyata. Da ya ga nayi fan shiru ban ce komai ba ya sake magana a fusace Kai mallam ku bacebmana da gain saboda Strangers are not welcomo herelit sZarmañda abün ya rufé nayi saurin tsayar da shia Hajiya Maryam dm ce tarce mu zo, ta san da zuvanmu ka tambayo ta ka ji: 33 "Ko ma Hajiya wace ce babu halin ganinta." Ya fada muryarsa na tabbatar mini da maganar da ya fada har zuciyarsa haka yake nufi, Ganin zai Bata mana lokacı ya sa na ce da shi "To yallabai in ba zaka damu ba zan baka sako ka kai mata. Yayi jim kamar bai amince ba, can sai ya ce in kawo. Zuctyata, küwa saka tunanin yadda zan bullo masa kawa ta ke yi. Na Karasa gindin motarmuna sanar da su Uzaifat yadda muka yi da shi. Nafisa ta ce "To ar-ina

Chapter 2 of 6