Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
na kalleta "To yaya za'a yi Nafisa? Kin san abin da Allah ya kaddara" ta karasa mini "sai ya afku". Idonta ya cicciko da hawaye "Yaya ya aka yi wannan abu ya faru?" na ja dogon numfashi sannan na fara bata labari tun haduwarmu da Uzaifat har zuwa ranar da na zo hannun 'yansanda. Ta sa ahannu ta share hawayen da ke kwaranya daga idonta "Babu komai, yanzu abin da nake so da kai shi ne ka kwantar da hankalinka kada ka damu ko kadan ni zan vi kokari in nemo ta insha Allahu. Idan kuma ban ganta ba zan tsaya tsayin daka a kotu in ga na kwato ka. Ka dal se ronka a inuwa kawai”. Ban yi manakro fadin hakan nata ba, domin na san zata iya yin abın da ya fi haka. Ta ci gaba "amma ina son ka tabbatar mini da gaskiya" na kalleta "Haba Nafisa sai ki ce baki san halina ba? Ta ce "Na sani amma ai komai na son gaskiya" na ce Gaskiyata ke nan "To shi ke nan Allah Ya taimaka mana" na ce amin. Bayan mun dan yi hira sai mai tsarona ya ce lokaci ya yi don haka sai muka yi sallama. Har ta fita sai na kwalla mata kira domin sai yanzu na tuno da maganar abinci. Da ta zo sai na shaida mata ta fadawa Hajiya a dinga kawo 19 mini abinci domin ban gane wa na nan ba, ta amsa da "To". Bayan na koma jarun ina zama maganar yayana ta fado mini a rai da ya ce an fara yadawa a labarai a kan kisan da a kayi kuma da sunana a kai amfani. Nan fa na yi ta shabar kuka ina mai cewa a raina lallai idan ba'a ga Uzaifat ba karshena rataya domin hukuncin da aka ajiycwa duk wanda aka kama da laifin kisan kai ke nan. Why? Na tambayi kaina, hawaye ya gangaro mini na sa hannu na goge. Yanzu shike nan duniya ta gama daukar sunana. Uzaifat ta fado mini a rai na ji zuciyata kamar ta fashe don tsananin kunci da takaici. Dana ji takaicin ya yi mini yawa sai na fara karanto wata addu'a da mutum zai iya karantawa idan ya fada cikin bala'i "Allahumma inna na uzu bika min jahadil bala'i wa darkish-shi ka'i wa shima tutul a'a da'i" na shafa da amin. Daga nan na yi addu'a Allah ya sa aga Uzaifat, domin rashin ganinta musiba ne a garc ni. Kwamishina tare da wasu 'yan sanda guda biyu suka shige cikin kurkukun da nake. Yana sanye da kayan 'yansanda a wannan karon, sun shigo sai ga wani saurayi da ba zai fice shekara ashirin da takwas ba ya shigo yana sanye da kananan kaya farare kansa ya dora hular FACIN CAP. Saurayin nan ya nuna ni da danyatsa ya ce "Shi ne wannan? Kwamishina ya amsa "shi ne" Murmushi ya bayyana a fuskar Kwamishina. Ya dan tura hannu a cikin aljihunsa kana'ya ce "Uzaif kamar yadda na yi maka alkawarin neman Uzaifat to na sa an binçika amma ba mu yi sa'a ba" ai nan da nan fuskata ta hade "Ba a ganta ba? Na tambaya cike da damuwa. Ya dan gyara tsayiwarsa "Yanzu dai sai ka zo mu je ofis domn na fi yi maka bayani dalla-dalla yadda zaka gane" ni dai na yi shiru kamar wanda ruwa ya ci, na kasa cewa komai sai da naga sun juya sun fita kana nima na bisu a baya. Ina mai tunanin inda Uzaifat ta shiga, idan ba a ga Uzaifat ba lallai na kade har ganyena.... Ban karasa tunanina ba na ji an yi mini magana "Nan zaka shigo, ina kuma ka nufa? Na waiwayo kana na yi ajiyar zuciya na bi bayan su zuwa cikin ofis din duk jikina a sanyaye. Muna shiga ofis Kwamishina ya nemi guri ya zauna a kan kujcrarsa ta alfarma, shi ma wannan saurayin ya nemi guri ya zauna a kujerar da ke kallon ta Kwamishina. Ya yi mini nuni da hannu wanda hakan ya nuna cewar na zauna, na jawo kujera na zauna na kasa kunne domin na ji labarin rashin ganin Uzaifat. Ya yi gyaran murya kana ya fara "Kamar yadda na fada maka tun farko mun yi kokari a kan mu ga mun samo Uzaifat amma abu ya ci tura. Na sa an yi bincike amma shiru kamar an aika bawa garinsu, to bayan kwana biyu da binciken Uzaifat ba'a samu labarinta ba, kwatsam labari ya zo mana cewa akwai wani gida a dokar wanda a nan ne wadansu 'yan aika-aika sukan yada zangonsu watau suke baza kolinsu. To amma bara dai ka ji daga bakin Inspector Kabir". Ya tsaya kanan ya gyara wata farar takarda dake barazanar fadowa a dalilin fankar dake kadawa ba kakkautawa tamkar iskar bazara. Inspector ya kalle ni kana ya fara nasa labarin "wato da muka samu labarin cewa suna can dokar daji sai muka -shirya muka nufi wajen da motoci hudu, kusan mu ashirin muka je amma mu goma sha daya ne muka dawo dalilin 6arnar da suka yi mana Ya kasance a lokacin da muka je ba mu samu kowa a gidan ba don haka sai muka je can wani gefe da ban muka boye motocin gudun kada suga motocin idan sun dawo su juya. Bayan mun boye su sai muma muka nemi waje muka buya. Ba mu fi minti talatin da buya ba sai ga su sun dawo kusan su goma sha hudu. Suna fitowa daga cikin motarsu kafin su shiga cikin gida tuni mun far musu, ashe suma suna da bindigogi nan fa aka dinga wuta, to dai sai da 21 suka kashe mana mutane tara mu kuma mun kashe kawas. Shida sun zo hannu dauke da munanan raunuka. Bayan mun gama kame su muna shirin tafiya sai ga wata karamar SPORT CAR nan ta danno da ganin mu sai ta juya ta figa da gudu. Muka dinga harbin tayar motar amma a banza domin ba mu same ta ba". Ya dan dakata yana kallon Kwamishina, kana ya mai da kallonsa gare ni. "da muka dawo sai na sa aka ganawa sauran shidan da muka kamo azaba domin su shaida mana inda sauran suke. Tun basa son fada har dai wani da ya ga wuyar ta yi yawa sai ya ce suke nan amma motar ogan su ce ta zo daga baya shi da wata abokiyarsa da kuma wata budurwa. Dana tambayi sunan su sai ya ce T.J. da Sussy amma bai san dayar ba. Na kara tambayarsu ko suna da wani gurin da ya wuce wannan sai ya ce sudai gurin buyar su ke nan amma Ogansu yana da wani gurin wanda suda kansu basu san gurin ba, to kaji yadda abu ya faru". "Da jin cewa Uzaifat na hannunsu T.J. na san ta faru ta kare an yi wa mai dami daya sata. Tun da su T.J. suka ga 'yansandan sun far musu to fa kashe Uzaifat za su yi. Idan suka kashe Uzaifat yaya zan yi da raina? Ban baiwa kaina amsa ba maganar kwamishina ta ratsani "Insha Allahu gobe za'a kaika wajen wadannan 'yan fashi domin mu dada tabbatarwa da kanmu cewa baka cikinsu, kasan fa aikin mu ne we just have to do it, duk da dai mun san kana da kanshin gaskiya. 6 Amma ni har yanzu inan kan bakana na sai na samo maka Uzaifat insha Allahu" Inspector Kabir ya ce "ai da ganinsa ka san ba zai aikata haka ba domin Hausawa sun ce alamar karfi tana ga mai kiba" ni dai na yi shiru ina sauraronsu domin jikina ya yi, sanyi. Na ja wani gwauron numfashi tare da ajiyar zuciya na kalli kwamishina muka hada ido, na dauke kallona daga gare shi izuwa ga Inspector Kabir, wani irin hawaye ya gangaro min na sunkuyar da kaina kasa "Allah ya sa a dace". Na fada a cikin sassanyar murya, suka amsa da "amin". 22 Gari na wayewa Inspector Kabir ya sa aka fito da daga cikin kurkuku. Bayan mun fito waje sai Kabit tsaya tare da kwamishina suna magana wacce bana ce abin da suke cewa ba. Kamar minti biyar da tsayiwarsu s Inpector ya sarawa Kwamishina kana ya juyo ya nufo ni. Yana zuwa muka shiga mota ba mu tsaya ko ina ba sai ofishin 'yansandan da aka kai wadannan 'yan fashi. Dukkanmu muka sauka daga cikin mota muka bi Inspector Kabir a baya har zuwa cikin ofishin 'yansandan. Muna shiga 'yansanda dake wajen duk kansu suka mike tsaye suka kame kana suka sarawa Inspector. "Mu'azu mike ka bude min kofar wajen 'yan iskan nan". Mu'azu ya mike ba tare da bata lokaci ba ya ciro mukullin a jikin bango ya yi gaba mu kuma muka bishi a baya. Muna zuwa ya bude kofar ya ce da su “duk ku fito" jikinsu babu riga duk bayansu ya yi rudu-rudu don duka, fuksarsu kuwa ba'a magana don tsananin kumbura da ta yi. inspector ya kalle su daya bayan daya ya yi tsaki sannan ya ce "Ku kalli wannan mutum da kyau ko kun san shi? Kallon da dukkansu suka yi mini ke da wuya sai abin ya bani mamaki da tausayi, ganin cewa hudu daga cikinsu abokaina ne a lokacin da muke makaranta domin a wannan lokaci babu abin da ke raba mu har bacci. Duk suka sunkuyar da kai don kunya. "Ba mu san shi ba". Za ku ce ba abokin harkarku ba ne" ya ce yana harararsu. Daya daga cikinsu ya yi tsaki ya ce "Yallaba ba mu san shi ba muka ce" inspector ya murtuke fuska ya kalle shi. "Kai ka iya harshenka idan kuma ba haka ba yanzu nasa a kaddamar maka, ni ka ke yiwa magana haka? Gayen ya ce "Haba yallabai ai ban isa in fada maka magana ba”. Ni kuwa dadi ya kashe ni ba su nuna sun sanni ba. Nan na fara tunanin ko na yiwa abokan nan nawa magana? Sai na yi tunanin gwanda na kyale su kada na jawo wata sabuwa a wajen Inspector, su da kansu kunyar ta hana su magana. 23 Daga nan Inspector ya yi umarni da a mayar da su har sai ya bukace su. Mu kuma muka ſito muka shiga mota bamu tsaya a ko ina ba sai a ofishin 'yansandan da nakc tsare. Muna isa inspector ya ce mu zarce ofishin Kwamishina, da muka shiga sai kowa ya nemi wajc ya zauna. Daga nan Inspector ya kwashe duk abin da ya ya faru ya fadawa kwamshina ya yi farin ciki da jin hakan. Kwamishina ya kalli Inspector ya сс "Kа ga kc nan wannan ya tabbatar mana da cewa shi ba dan fashi ba nc kamar yadda muka yi kokwanto, yanzu saura fuskantar alkali domin ya zama dole tunda za'a yi mana yan tambayoyi tunda shi aka samu a dakin da aka samu gawar Hauwa A. Lauya Saleh" Inspector ya ce "Ba shakka". Bayan na tashi zan koma dakin tsarona sai inspector ya shaida mini cewa gobe za'a kai ni kotu. Na ce Allah Ya kaimu goben lafiya. Na zauna na hada kai da gwiwa ina tunanin yayana da kuma dalilin da ya hana shi zuwa yau kusan sati daya da kwana biyu, tun da ya zo sau daya. Shin abin da ya yi kuwa ya kyauta? Kai ina ganin akwai abin da ya faru a gare shi, ga shi kuma gobe za'a kaini kotu a kan laifin da ban aikata ba..... ban karasa ba na ji an bude kofa. Kurtun dansandan nan tsamurarre ya shigo "Ka yi bakuwa" ya juya ya fita, wannan karon ban yi mamakin jin cewa na yi bakuwa ba. Don haka sai na mike na nufi kofa. Ina fita na yi tozali da ita, tana sanye da jallabiya shudiya da mayafinta. "Nafisa lafiya?" na tambayeta domin naga alamar damuwa a fuskarta. "Lafiya kalau" ta ci gaba "Na yi kokari a wajen neman Uzaifat amma na rasata sai kuma na ji cewa gobe za'a gurfanar da kai a kotu shi ne nazo domin na shida maka cewa ka kwantar da hankalinka ni zan tsaya a kotu domin ba zan yarda a aza maka laifin da bana ka ba". Та goge hawayen da ke idanunta. Da na ga hankalinta ya tashi sai na sauya darasi "Su Hajiya kuwa suna nan? Ta 24 amsa "suna nan jiya ma yaya ya shaida mata sakonka m gaisuwa ina jinsu a lokacin inna nazarin wani littafi. Abin da na ji daga bakin Nafisa ya bani mamaki don har kasa magana na yi. dana ji ta ce yayana ya zo har na ba shi sakon gaisuwa. Ta ce da ni "yaya zan koma sai goben domin ina son in je in yi nazari". Na cc ai babu damuwa "Ki gaishe da su Hajiya". Ta ce "saji" ta tafi ni kuma na koma cikin kurkuku. Tunanin duniya duk ya bi ya ishc ni. Na tuno da son da mahaifana suke-yi mini har da yayana da kuma irin mutuwar da su kayi cspecailly irin kisan da aka yi wa mahaifina hawayc ya gangaro mini. Ban san lokacin da na fashe da kuka ba don bakin ciki na yi kwafa kana na hada-kai da gwiwa kai!! Lallai dunya rawar yan mata сс. 25 un isa kotu karfe tara da kwata. 'yansanda kusan M dozin suka take mana baya ni da Inspector Kabir. Suka tura keyata gaba har cikin kotu kamar wani gagarumin danfashi, muna shiga aka bani kujera na zauna idon mutane kuwa duk ya yi kaina. Sabonda kunya da fargaba kasa daga kaina na yi, kotun babba ce kuma cike take da mutane ba iyaka. Daga tsakiya wani katon teburi ne zagaye da kujeru, a kan kujerun kuma lauyoyi ne su hudu. maganar wadansu mutane ce ta dakatar da ni daga tunanin da nake yi. Daya daga cikinsu ya ce "Kai Hadi wannan saurayin daga ganinsa kamili ne kuma gashi shiru shiru ba shi da alamar mugunta" dayan kuma sai ya ce "Kai Ya'u rabu da shiru-shirum mutum ka ji? nan ba gamuwa muka yi da wani kamilin mutum ba? Da muka yarda da shi ba kwace mana fan talatin ya yi ya gudu ba? Yanzu ai shiru-shirun mutum ya fi mugunta kai dai rabu da halin dan'adam" haka dai suka ci gaba da hirarsu. Fitowar Alkali ne yasa kotun ta yi shiru kamar ruwa ya ci ta. Kowa ya mike bayan Alkali ya zauna sai kowa ya nemi guri ya zauna. Wani gwarzon mutum fari dogo mai bille a kumatu lauya ya mike ya karanto shari'a bayan ya gama ya koma ya zauna. Alkali ya yi umarni da na shiga ckin kanta, na shiga ciki na daga kaina duk idanun mutane yana kaina, na yi sauri na sunkuyar da kaina ta faru ta kare na fada a raina. Alkali ya ce da ni "Uzaif ka ji laifin da ake tihumarka da shi na kisan matar Lauya Saleh ko kana da ta cewa? Zan, yi magana sai wani luya baki dogo ya mike ya yi gaisuwa kana ya gabatar da kanshi a matsayin lauyan da dangin mahaifiyar Uzaifat suka dauka shari'a, kana ya matso ni ya ce "Kana da ta cewa?" "Ranka ya dade bani na yi kisa ba". Na fada ina kallon Alkalin Ya ce "Zaka iya nuna shaida ko kuma hujjar hakan?" yana magana ransa a bace. 26 "Ina da shaida amma kuma bata kusa" na ce da shi, "Ko kotu zata iya sanin shaidar taka?" "Why not? Uzaifat Salch shaida ta amma an rasa inda take". "Ban da ita wace alama zaka nuna da zata gamsar da kotu ba kai ka yi kisa ba? Na kara kallon sa cike da mamakin nacewar da na ga ya yi". "Ni bani da wata alama da zata nuna bani na yi kisa ba illa Uzaifat". Ya yi ajiyar zuciya da ya ji ina amsa tambayoyina daidai. "A lokacin da 'yansanda suka je har suka kamaka ka yi niyyar gudu ne ko kuwa?" "Gakiya bana ce ban yi niyyar gudu ba". Nıshare gumi daga fuskata. "Mene ne dalilin yin hakan alhali ka tabbatarwa kanka cewa baka yi laifi ba? "Saboda tsoron kada hukuma ta kamani" na dan yamutse fuska. "Ba kai ka yi kisan ba yaya zaka ji tsoron kada a kama ka?" 'Kai wannan da tambayar tsiya yake'na ce a zuciyata. "Ka san Hausawa sun ce na shiga ban dauka ba bata fitar da barawo shi ya sani na ji tsoron kada a kamani a kan gawar especially ma da banga Uzaifat ba". "Tun da baka da bayyananniyar amsa kotu zata yanke maka hukuncin da ya yi daidai da kai". Kaina ya sara kwakwalwata ta yi wani irin kara kamar an karkada kararrawa. Zan yi masa magana ke nan sai Nafisa ta mike cikin isa da takama da ji da kai. Hankalina ya dan kwanta ganin zan samu mafita ko da dai ba da yawa ba. Та _ gabatar da kanta a matsayin mai kare ni kana ta nufo ni ikin nutsuwa. Bayan ta zo inda nake sai ta dafa jikin _antar dana ke ciki ta kalle ni kana ta maida hankalinta ga Alkali. "Allah ya gafarta malam ina ganin bai dace a ce an nkewa wannan bawan Allah hukunci a kan laifin da bai ba, domin ya kamata ayi bincike dalla-dalla kafin a _vatar da komai gare shi in har shi ya yi laifin". 27 Nan da nan naga hankalin sauran lauyoyin ya yiwo kanta. Ta kalle su ta kauda kai "Dalilin fadin haka shi ne su masu tambayar shi ko kuma ince ma su dora masa laifin ina son su nunawa kotu hujjar da ta nuna ccwar shi ya yi kisa". Wannan lauyan fari ya mikc da sauri ya ccс "Kotu zata iya yarda da shi ya yi kisan musamman idan aka yi la'akari da cewar shi aka samu a dakin da abin ya faru". "Wannan ba shaida ba ce' ta fada tana mai kallon Alkali. Ta ci gaba "Tun da ba'a samu makami a hannunsa ko kuma a inda aka yi kisan ba to kuwa ba za a ce shi ya yi kisa ba". Nan da nan wannan lauyan mara imani ya mike tsaye yana fadin "Karya ne shi ya yi kisan mc yasa zai gudu idan ba shi ya yi kisan ba?Ya daka mata tsawa. Nafisa bata ce masa komai ba amma ta yi masa kallon Baka isa a yi da kai ba wanda ya sa shi ya girgiza matuka. Ta sake maida kallon ta ga Alkali "Allah ya gafarta malam zan so a yi binciken wannan magana tawa da kyau domin bai dace a muzanta mara laifi ba, saboda haka zan so kotu ta bamu dama mu yi binciken wannan yarinya tunda ya nuna cewa ita kadai ce shaidar sa, idan kuma kotu ta yarda da ni a matsayin lauyar da zata iya belin Uzaif" Lauyoyin nan suka mike cikin hanzari suna muzurai dayan fari ya ce da Nafisa yana harararta "Bamu yarda ba, ba za a baku wannan damar ba". Nafisa ta yi murmushi ta ce "Sai ihu kuke bayan hari ku kawo shaidar ku mana wacce ta nuna shi ya yi kisan". Suka koma suka zauna suna haki kamar wadanda suka yi tsere da zomo. Alkali ya yi gyaran murya kana ya ce "Kotu ta baku wata dayar cur ba kari ku nemo shaidarku, an baki belin,Uzaif akan dalili daya kada ki sake ya gudu idan hakan ta faru to kinsan abin da zai biyo baya domin yana cikin littafin doke". Nafisa ta ce "godiya muke ranka ya dade". Ta koma wajenta ta zauna. Murna zan yi ko kuka? Zan so mai karatu ya ba ni wannan amsa domin na rasa abin da zan yi cikin biyun. 28 Bayan Alkali ya mike ya shiga wni daki sa mutane suka dinga sowa suna yin mini fatan Allah ya sa inga Uzaifat ka min wannan lokaci wadannan lauyoyi kuwa banda kallon banza babu abin da suke yi mini. Muka fito bakin titi neman tasi, ko dadewa ba mu yi ba muka samu. Bayan mun fara tafiya sai na tambayi Nafisa dalilin da ya hanata taho da motar gida. Ta shaida mini cewa yayana ne ya fita tun da safe shi ya sa, kuma makullayen duka suna hannunsa. Nan fa na tuno da yayana kome ya hana shi zuwa kotu? Shin yayana yana kaunata kuwa? In har yana kaunata mai zai hana shi zuwa kotu ya ji yadda zamu karke? Tsayiwar mai tasi ce ta dawo da ni daga tafiya dana yi fagen tunani. Bayan mun sauka sai Nafisa ta sallami dan tasi ya yi gaba mu kuma muka shiga gida. Hajiya na ganina ta taso da sauri ta rike mini hannu tana kuka. Ta goge hawayc da leben zaninta "Uzaif lafiya ko?" ta tambaye ni tana hawayc. "Hajiya ai Alhamdu lillahi domin babu abin da ya samu lafiyata". Ta yi ajiyar zuciya "To ai shike nan amma sai Allah Ya saka maka domin duk wanda ya shirya maka wannan tuggun muguntar shi ma yana tare da wahala babba". Na ce "Hajiya ai babu komai Allah ya fisu kuma yana bayan mai gaskiya, ki daina kuka". "Ba dole na yi kuka ba Uzaif?" ai kuka ya zamar mini dole". Muka zauna muka ci gaba da hira. Ashe duk abin da Hajiya ke yi bata lura da Nafisa ba sai da taje ta dauko mini abinci tukunna bayan ta dawo sai Hajiya ta lura da kayan dake jikinta. Duk gidan babu wanda ya san aikin da Nafisa zata yi sai ni. Hatta yayana ma bai san aikin da zata yi ba sai dai karbi kudi wannan ta karbi kudin wancan amma ba zaı taba tambayarta aikin da take karanta ba. Nima da kyar ta barni na san cause dinta". "Nafisa" Hajiya ta kira sunanta; S ta rike baki cike da mamaki sannan ta ce "Wannan kayan kuma fa? Nafisa ta yi dariya ta ce "don Allah ji yadda Hajiya ta rike baki, ai kayan aiki na ne". Hajiya ta ci gaba "Shi ne baki sanar da mu ba? Kwanakin baya da na tambayeki aikin da zaki yi ashe karya kika yi mini na cewa aikin banki zaki yi?" Hajiya na fadi haka ne don kada ku katse mini hanzari ke da yaya shi ya sa na yi muku karya". Yanzu ki rasa aikin da zaki yi sai aikin lauya? Aikin marasa gaskiya ne fa aikin lauya, aikin da karbar cin hanci da rashawa ya yi wa kanta? Lallai baki yi tunanin arziki ba wallahi, gwanda da baki fada ba". Nafisa ta cire hular da ke kanta ta gyara zama ke nan t *afara bawa Hajiya labarin aikin lauya "Hajiya ki kwantar da hankalinki domin ni ba zan kasance mai cin amanar talakawa ba, ina wannan aiki ne domin na karbar musu hakkinsu a dalilin gani da na yi an danne musu. A inda zaki gane aikin lauya sai ansa kai ake karbar cin hanci da rashawa shi ne yanzu idan wani ya kawo mini cin hanci ba sai na ga dama zan karba ba? Idan ban karba ba zai tilasta šini ne? Kinga ai ba zai tilasta mini ba. Kinga aikin lauya yana da amfani musamman yanzu idan wani abu ya faru a dangi ai ba sai an yi wahala ko kuma asarar kudin nemo lauya ba. Ba gashi yanzu na yi kokari na yiwo belin yaya ba? Kina nufin idan wani ya je za'a ba shi? Ai sai lauya dan'uwanmu ko kuma babban dan sanda” haka dai ta ci gaba da baiwa Hajiya haske har itama t gamsu kuma t ayi mata addu'a tare da bata goyon baya. Ni dai ina jinsu sai harraka abinci nake yi a cikina. Da yamma bayan na yi wanka nasa rigata 'Kano State' da wando sầi na nufi falo na tarar da Nafisa tana kallon wani kaset na yaran Amurka LUCKY SEVEN'don haka sai nima na zauna muka ci gaba da kallon. Muna kallon muna hira kama yayana ya dawo daga wajen aiki. Yana gani na ya kame-kame yara fada mini dalilin da ya hana shi zuwa wajena. Da ya gama tsarinsa sai na ce da shi ai babu komai daga nan ya shiga daki mu kuma muka ci gaba da kallo. Na lura da ran Nafisa ya 6aci amma sai na yi kamar ban lura ba, a haka har muka gama kallo kowa ya yi nashi waje. Tun daga ranar da na dawo gida naga yayana ya canja ba kamar da ba, babu wálwala a fuskar shi sannan 'yar hirar da muke yi ma yanzu an daina. Saboda haka sai na yanke shawara in je in tambayi Hajiya ko tana da masaniya. Dana isa dakinta sai na tarar da ita tana sakar rigar sanyin yara da inji. Na zauna a kan kujera dake dakin na tambaye ta amma sai ta ce "Yadda k tsinkayi Alhaji haka nima na. tsinkaye shi" na ce da ita "To Allah ya yi mana magani". Тa се “Amin" daga nan na fita daga dakin na nufi falo. Ina zuwa na tarar da Nafisa zaune ta yi tagumi, tana ganina ta dago kai da sauri kana ta tambaye ni ko na san abin da ke damun yayana. nIma sai na yi ta bakin Hajiya "Yadda kika gan shi haka nima na gan shi". Nan muka fara sakawa muna kwancewa ko zamu gane abin da ke damun sa amm mun rasa. Daga nan Nafisa ta fara bani labarin dawainiyar da take yi mini wajen neman Uzaifat amma abin ya ci tur. "Allah ka taimake mu" na ce da ita ta amsa da "amin". Yanzu na tabbatar Nafisa na son taimakata, domin irin dawainiya da wahalhalun da take yi wajen neman Uzaifat amma shiru kake ji kamar an jefa kwai a ruwa. Wani sa'in idan Nafisa ta fita tun safe sai yamma ko magariba zatı dawo. Na kan yi mata fada a kan ta dinga samun hutu amma ta yi kunnen uwar shegu da ni yau gashi saura kwaga goma sha daya mu koma kotu amma babu duriyar Uzaifat. Na tambayi kaina wai idan ba a ga Uzaifat ba wane irin hukunci za'a yanke mini? Kisa...! Na ji tamkar wani ya bni amsa. Na yi nisa a cikin tunanin da nake yi şai karar tarho ta katseni, na yi firgigit na mike, na duba inda Nafisa take na ga bata gurin a nan na fahimci cewa ta fita ne. ina zuwi nasa hannu na dau wayar "Hello who's talk?'Na tambaya, amma memakon a bani amsa sai nima aka yi mini tambaya "Who are you?"Maganar shi t abani

Chapter 3 of 7