Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
na kurba na sake kurba sannan na ce "To bisimillah sai ki fara ba ni labari" ga mamakina sai na ga ko tanka mini bata yi ba, don haka sąi na sake maimaitawa, sai ta ce "Ka yi hakuri domin sai na fara jin naka labarin” ina jin haka sai nima na share kawai na bar zancen. Bayan na kwana biyu a asibiti Uzaifat ta yi mini dawainiyar nemo yayana ranar asabar da misalin karfe goma saura ya zo tare da matarsa Hajiya Maryam. Bayan sun yi mini sannu sai muka kama hirar yadda abu ya kasance, dana kammala fada musu Hajiya har hawaye sai da ta yi don tausaya mini. Yayana kuma cewa ya yi duk inda suke sai ya sa an nemo su. Hajiya ta ce wai su wadannan mutane ba za su rabu da kai ba ne? yanzu kusan shekara biyu kenan suna binka? Ko so suke yi su raba ka da duniya ne?" na ce "Haba Hajiya ai ba su isa su kashe ni ba domin sai kwanana ya kare zan mutu sai dai kuma idan ranar karshe ta zo mini, kin san hausawa sun ce "Wuya bata kisa". "Haka dai muka ci gaba da hirar mu har Uzaifat ta shigo. Bayan sun gaisa da su Hajiya sai yayana Alhaji Yusuf ya kara yi mata godiya kan irin taimakawar da takc yi mini, daga nan suka yi mana sallama suka tafi. * * Satina biyu na samu sauki na koma garau kamar ban taba yin ciwo ba sai Uzaifat ta fara shawarar sallamata domin duk ciwukan jikina sun warke. Bayan ta dada tabbatarwa na warke sai ta rubuta mini takardar sallama, na yi farin ciki kwarai da gaske. Na yi mamaki da naga Uzaifat bata bukaci ko mai da sunan kudin magani ko 7 a kudin gado ba. Don haka nima sai na sakc yi mata godiya ta musamman amma sai ta ce "Not to bother" Bayan na kammala harhada kayana sai Uzaifat ta ce da ni in tsaya ita zata kaini gida, don haka sai na nemi guri na zauna. Ina zaune Uzaifat ta shigo ta ce da ni "Uzaif ka saurareni zuwa minti ashirin domin an kawo wata haihuwa kuma haihuwar na son kawo gardama shi ya sa I have to make it my self" na ce da ita "Ba komai" sannan ta fita. Bayan fitarta da kamar minti talatin sai ta shigo hannunta rike da hankici tana share gumin fuskarta. Ta umarce ni da in tashi mu tafi, har na dauki jakata sai Uzaifat ta karba nayi-nayi da ita a kan ta bari in dauka amma taki. Mun shiga motar Uzaifat kirar ACURa Intgra muka nufi hanyar gida. Muna tafiya muna hira a nan Uzaifat take fada mini irin kirkin Ilajiya Maryam har nima na ce da ita "Ai abin da take yi mini ko 'yarta Nafisa bata yi wa" muna cikin sharar gudu sai Uzaifat ta kalli madubin mota ta ce da ni "Uzaif kaga motar da ke bayanmu kamar mu take bi" cikin sauri na kalli madub kana na yi ajiyar zuciya na kalli Uzaifat na ce "Yanzu idan mu suke bi yaya zamu yi? ta bani amsa ba tare da ta kalle ni ba "To sai me idan mu suke bi? Ta fada a sanyayc sai dai fa kai har ka ji tsoro ko? Amma bari na tababtar naga idan mu suke bi din" saboda haka sai Uzaifat ta kara giyar mota ta manna da gudu. Ga mamakina sai na ga wannan motar kirar HONDA ita ma ta sharo da gudu tana binmu. Daga nan sai hantar cikina ta kada hade da juyawa. Nan take na fara tunani "Lallai wadannan su T.J. ne ba wasu ba yau ina zan sa kaina? Da fitowata daga asibiti kuma zasu nemi komar da ni?". Gaskiyar Hausawa da suka ce rikicin duniya da mai rai ake yi. T.J.!!! yanzu ba zai bar bina ba sai ya ga ya hallaka ni? Lallai yau ake yinta wai ansa mage a lalle.... Maganar Uzaifat ce ta katseni "Uzaif mu fa suke bi" na ce "Yanzu ya kenan? Ta ce "Ya ke nan kuwa ai sai mu zuba hausawa dai sun ce inda ba kasa..." Ni dai na yi kasake 8 ina jin ta domin duk a tsorace nake. Ta sha kwana a daidaj lokacin da ta bude wani dan guri a jikin murfin kofar wajenta, ta fauko karamar bindigarta sannan ta kara gudu ba ji ba gaı kamar wata barauniya "Kada ka damu ka saki ranka insha Allah zamu tsira da yaddar Ubangji". Kana ta yi wani fan murmushi. Ni dai gabana sai faduwa yake yi duk da yake bayau na taba hoduwa da T.J. ba yau dai naa tsorata da shi macen bon ba haduwa da ita ba haduwarmu ta farko ita ce ta kainı ga kwanciya a asibiti to shi yasa nake tsoron ha fuwarmu ta biyu kada ta kaini ga kwanciya a kabari. Ba wani abu ke bani tsoro da macen ba illa kawai wannan arnen takalmin da take sawa mai tsinin tsiya. Hankalina ya dawo ne a daidai lokacin da na ji harbin bindiga. Ba kowa ya yi harbin ba illa su T.J. sun yi ne domin su sace mana tayar mota ganin bamu da niyyar Isayawa. Nan da nan Uzaifat ta gyara tata bindigar ta leka ta taga ta sakar musu harsashi amma bata yi sa'a ba domin kuwa babu harsashi a cikin bindigar. Cikin sauri ta kalle ni "Uzaif ka iya tukin mota? Cikin tsoro da razana na kallcta" na-iya- amma a gaskiya yanzu ba zan iya ba don kuwa sai na fada rami domin na gama tsorata. Ta kalle ni fuskarta babu alamar fara'a "To dinga juya mini sitiyarin ni zan yi sauri na zuba harsashi a bindigar "Na karbi sitiyarin mota na fara juyawa cikin faragaba. Bayan ta gama zuba wa sai ta karbi sitiyarin ta ci gaba da juyawa. Kai lallai idan mutum ya ga bala'i sauyawa yake yi. Na yarda da haka ne ganin yadda fuskar Uzaifat ta sauya babu ko alamar imani. Aka dada yin harbin ita ma Uzaifat ta harba tata bindigar, ai fa daga nan aka fara bude wuta har abın ya fara ba ni tsoro. Da Uzaifat taga basu da niyyar barin harbi sai ta waiwayoni da sauri "Uzaif koma kujerar baya ka kwanta". Cikin firgita na ce da ita "Haba hauka nake yi? zaki taimake ni sannan na koma bayan mota na kwanta? "Uzaif" ta ce da ni cike da damuwa. "na'am" ta ci gaba 9 "Na san da haka amma zamanka a nan hatsari ne domin za su iya harbi ya sameka" na ce "Kece idan suka yi bazai sameki ba.... Ban karasa ba ta yimini magana cikin ihu "Uzaif sunkuyar da kanka za su yi harbi.... Ita ma bata Karasa ba harsashi ya bi ta saman kanta ya fasa mudubin gaban motar, Allah ya yi bai same ni ba. Cikin fushi ta ce "ai ga irin ta nan, ka koma baya na ce" "Wallahi ba zan koma ba sai dai in rasa raina". Na fada a gaggauce. Da ta ga ihu ba zai yi mata ba sai ta koma lallashina tana ba ni hakuri. Duk da haka naki komawa da ta ga ba ni da niyyar komawa sai ta ce da ni "To tunda kaki sai ka sunkuyar da kanka kasa har sai ka ji na ce ka dago" nan ma sai da muka fafata da kyar na yarda na sunkuyar da kaina, duk abin da muke yi motar mu tana sharar gudu haka suma masu bin mu gudu suke don neman cim mana. Duk da sunkuyar da kaina da na yi ina satar kallon Uzaifat wacce duk ta bi ta dibirbirce. Uzaifat ta karya kwana sannan ta rage gudun da ta ke yi. suma su T.J. sun rage gudu na lura da haka ne a sakamakon fakar idon Uzaifat dana yi na leka tagar motar. Uzaifat ta cire mayafin dake kanta ta goge gumin dake tsattsa owa daga fuskarta, Tasa hannu ta danna na'urar sanyaya n ta bayan haka ta sake mannawa da gudu. Wata sabuw ta dada aukuwa domin su T.J. suma sai suka kara giyar motarsa suka yi wo kan motarmu da gudu, irin gudun da su T.J. suke yi na san suna nufin ayi ta takare ne domin saura kadan su cimmana. Ashe Uzaifat tarko ta dana musu sai da ta bari duk sun saki karfin motarsu sun zo kusa da ita sai kawai ta taka birki suka wucemu da gudu. Kalin ta yi ribas tuni sun sake yiwo baya sun tarar da mu suna zuwa daf da mu sai Uzaifat ta daga bindigarta ta sakar wa T.J. harsashi amma sai ya sunkuya don haka sai ta zarce la samu abokiyar harkarsa a kafada. Ta yi wata irin kara wadda ta firgitar da T.J. har ya so ya saki sitiyarin. Duk na lura da haka ne a sakamakon daga kaina da na yi ina mai kallon komai ita da kanta Uzaifat ba ta lura ba. Bayan Uzaifat ta harbi mcen sai ta manna da gudu ta bar motar su a wajen a tsaye shi kuma T.J. yana jinyar kafardar 'yar'uwarsa. Tun da muka bar gurin babu wanda yace kala balle mu kai ga yin hira, sai da muka isa gida. Bayan mun fita daga cikin mota sai muka shiga cikin gida, muna shiga gida Hajiya ta taso ta taryemu cike da farin ciki. Muka nemi wuri muka zauna. Bamu dade da zuwa ba iga yayana ya fito daga cikin daki, muka gaisa shi ma mi guri ya zauna. Bayan kowa ya nutsu sai na fara bawa su Hajiya labarin gamuwarmu da su T.J. da suka ji labarin nan fa suka dinga yi wa Uzaifat godiya har yayana ya bata kudi mai dimbi yawa ya ce tasai gilashin mota, amma taki karba. Yayi-yayi da ita taki, nima na sa baki amma duk banza. Hajiya ta yi mata addu'ar Allah ya biya mata da gidan aljanna ta amsa da amin. a Bayan ta yi sallama da su Hajiya sai na yi mata rakiya zuwa bakin motarta. Ta jingina da murfin mota ta kalle ni ta ce "UUzaif yaushe zaka samu dama mu zauna mu saukewa kanmu nauyi? Na daga kaina sama wanda hakan ya nuna cewa ina tunani "Me zai hana jibi, don gobe ina son in huta" ta ce "Yauwa, ya kuwa yi daidai da abin da nake tunani domin nima gobe zamu je mintin (meeting)" la ci gaba "A ina zamu hadu domin bana bukatar tawowa nan na yi murmushi karo na farko ke nan tunda muka baro asibiti "Ina kika ga ya dace mu hadu? amma bana son guri mai nisa kin san cewa inna cikin hatsari" tayi mini kallon kai matsoraci ne sannan ta ce "Na san da haka to mai zai hana ka je gidanmu? Na nisa kańa na cc da ita "Ai ba hawan ba saukar" ta ce "Ban gane ba hawan ba saukar" na ce "Ba zuwa gidan naku ba vadda zan je din" ta yi mini wannan murmushin nata ma Kosar da mayunwaci “Kai dai matsoraci ne, in be matsorav .... na tari numfashinta "Haba Uzaifat wane mahaluki ne ba zai yi dari-dari da ransa ba? Na tambayeta ta ce "I know, but yours is too much" na ce da ita "Thank you amma duk da haka ni dai ba zan je gidanku ni kadai ba" "To naji zanzo in dauke ka da kaina, ya yi hakan? Na ce "wannan babu laifi" muka yi sallama da ita ta shiga mota ta yi gaba ni kuma na juya na shiga gida. Ranar da muka yi da Uzaifat ta zo tunda misalin karfe goma sha daya saura minti goma ta zo. Bayan sun gaisa a Hajiya sai muka fito muka rankaya cikin mota. Data tashi mota ba mu tsaya a ko'ina ba sai a DAULA ta ja burki ta tsaya a kofar wani katafaren gida mai fenti shudi da fari. Muka bude kofa muka fita ta yi mini jagora har cikin gidan. Lallai gidan ya kawatu matuka domin harabar gidan nasu ma abin kallo ne. Gidan akwai shi da yawan lunguna da lankwashc-lankwashe domin mun lankwasa ya fi sau hudu. Lankwasawar karshe da muka yi shi ya kai mu ga bakin bene. Na kalli Uzaifat na ce "Wannan gida naku na rufin asiri ne" ta ce "Uzaif wanc gida ne bana rufin asiri ba?" na ce da ita a daidai lokacin da muka hau benen "Ba hakа nake nufi ba wato ina nufin cewa ya cika lunguna, kafin barawo ya shigo ko ya fita tuni an kama shi tunda ba gane hanya zai yi ba" "Haka ne amma sai dai kawai mu ce Allah ya kare mu domin hausawa sun ce maso abinka.. na karashe mata "Ya fika dabara" "Ka gani ko? Sai dai kawai mu ce Allah ya kare mu" na ce "Amin". Muka shiga wani makeken falo kawatacce mai kyaun gani, kujeru sun zagaye shi sannan ga wani tebiri round a tsakiyar falon muna shiga na'urar sanyaya faki ta yi mini maraba. Uzaifat ta yi mini umarni da na zauna, na nemi kujera na bi lafiyarta. Sannan itama ta zauna. Bayan mun nutse cikin kujera sai Uzaifat ta kalle ni ta ce "Uzaif Allah ya kawo mu dama an ce rana bata karya sai dai uwar diya 12 יי ta ji kunya saboda haka sai ka bani labari amma before that ina zuwa bari n'a je na dawo" ta mike ta nufi wata kofa ta bude ta shiga. Bayan kamar minti bakwai da tafiyarta sai ta dawo ta ce da ni ""Uzaif Momy dina ta ce kaje ku gaisa" nan take mamaki da kunya suka rufe ni. Na mike na bita ina tafiya kamar kazar da kwai ya fashe wa a ciki. Ta bude kofar data shiga dazu. Ashe bene ne ba daki ba, koda yake dama gidan hawa biyu ne saboda haka ban yi wani mamaki ba. Bayan mun hau bene sai gamu wata 'yar hanya siririya sai muka bita wannan hanya muka fada wani makeken falo wanda ya yi wanda muka fara shiga uku. A can gefe mahaifiyar Uzaifat ce a zaune tana sanye da alkebba baka mai ado a gaba. Tana kallon wani kaset na America NO WIIERE TO RUN, na durkusa gwuiwa biyu-biyu na gaishe da ita, ta amsa cikın murna da lallausar murya. Da ganin Hajiya mahaifiyar Uzaifat kasan barewa ba zata yi gudu 'yarta tà yi rarrafe ba, domin kuwa sun yi matukar kama. Bayan mun dan yi hirar da bata wuce minti goma sha uku ba sai na yi wa Hajiya mahaifiyar Uzaifat sallama, daga nan muka koma falon farko. 13 2 a bude baki kenan zan fara baiwa Uzaifat labari, N sai wata irin kara mai razanarwa da ban tausayi ta bayyana kunnuwanmu. Gabadayanmu muka mike da dai naga Uzaifat ta yi hanyar kofar bene sai nima na bita da sauri muka rankaya izuwa falon mahaifiyarta. Abin da idon mu ya gani mun so mu karyata shi, wato yankan rago aka yi wa mahaifiyar Uzaifat, wuyanta sai shatatar da jini yake yi. Uzaifat ta nufi wajenta a guje ta jata a jiki tana kuka mai ban tausayi. Ni kuwa sunkuyar da kaina kasa na yi domin al'ajabin yadda abin ya faru bamu sani ba. Shin yaya aka shigo aka yi wannan aika-aikar? Ko dama an a binmu a baya ne? ko su T.J. ne suka yi wannan aikin ganin cewa Uzaifat na taimaka mini? Amma babu amsa duk wadannan tambayoyi. Don haka sai na daga kaina don na tambayi Uzaifat ko akwai wata hanya banda wacce muka biyo. Amma sai na raina idona, domin kuwa babu Uzaifat babu alamarta amma mahaifiyarta na nan a kwance cikin maliyar jini. Na tashi da sauri ina kiran sunanta Uzaifat! Uzaifat!! Amma babu amsa. Dana tabbata Uzaifat bata cikin gidan na fa na fara tunanin shin idan ba a ga Uzaifat ba wa za'a ce ya yi kisa? Dole idan aka tarar da ni a cikin gidan a ce ni na yi domin babu Uzaifat babu wanda ya yi kisa. Lallai idan ban san inda dare ya yi mini ba saina shiga tarko babba. Gabana ya yanke ya fadi, hantar cikina ta kada hade da juyawa miyan bakina ya kasa hadiyuwa a daidai lokacin dana ji jiniyar motar 'yansanda. Shike nan ta faru ta kare an yiwa mai dami daya sata. "Shin wa ya sanar da 'yansanda? Babu amsa. "Ko dai tarko aka dana mini ne? na sake tambayar kaina. Don tsananin tsoro da razana sai na kasa tabuka komai, in gudu na kasa in tsaya waje daya na kasa sai safa da marwa nake yi a tsakiyar wannan katon falo. Na yi hanzari na koma na boye a bayan wata kwana 14 kusa da wani daki, dana ji gudun mutane a kan matattakala. A inda nake a boye zai yi wuya mutum ya gane ina wajen amma ni duk abin da ake yi ina gani. Wani mutum dogo baki sanye da kananan kaya riga da wando na Jeans ya shigo hannunsa rike da waya mai amfani da iska wato salula. Ya shigo ya tsaya a kan gawar mahaifiyar Uzaifat, ya kalleta ya girgiza kai cikin takaici. Wadansu mutane su shida suna bayansa sanye da kayan 'yan sanda wanda hakan ya dada rikitar da ni" In fito ne ko in ari kafar kare? Na tambayi kaina. Sannan na bada amsa -gwanda na yi tsayiwata domin na shiga ban dauka ba bata fitar da barawo. Bare kisan mutum" maganar wannan mutun ce ta katse ni. "Ku shiga ku dudduba dakunan ko za'a yi dace a samu imformation "Suka kame sannan suka amsa "yes sir" kana kowa ya kama diretion dinsa. Ni dai banda tunanin yadda zan tsira babu abin danake yi. Bayan 'yan mintina ‘yansandan nan suka fito suka shaida cewa babu wani imformation a cikin gidan. Wannan mutum dana fahimci Ogansu ne sai ya ce "Kun tabbata kun duba ko ina? Suka amsa bayan sun kame "Mun tabbata" ya tsaya yana kallon kasa yana bubbuga salular hannunsa a baki wanda hakan ya nuna cewar tunani yake yi, ya ce "kwa iya tafiya nima ina zuwa within three minute". Wani irin dadi ya shiga zuciyata ya ketata, don murna sai da na yi murmushi. Har 'yansandan nan sun juya za su sauka sai ya ce da su "au kun duba wancan 6angaren? daya daga cikinsu ya amsa "No sir" ya ce "To ai sai ku duba don mutabbatar wa da kanmu babu komai a cikin gidan" hudu suka juyo suka nufo inda nake. Ai nan da nan murna ta koma ciki na fara tafiya da baya, sai dana dan yi nisa da tafiya sannan na juya domin na san inda na nufa 'banyi taku shida ba na ji an gargade ni "tsaya inda kake in ba haka ba kuma ranka yana bakin wannan bindiga "cikina yabada wani irin kara 15 kululu !!! sai kawai naja na tsaya domin in ceci raina, mutumin da ya umarceni da na tsaya dayaga na tsaya sai ya taho a hankali yarikemini kugu tabaya zatonsa ina da makami. Ya hura husir sau uku kafin kace me! Tuni 'yansanda sun zagaye ni. Duk da haka dansandan bai yarda ba sai da ya ce a cajeni tukunna. Wani guntu fari da fuska kamar alkubus ya caccaje ni da ya ga bani da komai sai yave da su "He has nothing" nan na fahimci yarensa. Aka buga mini ankwa a hannu sannan aka tunkuda keyata zuwa waje inda motarsu take. Muna sauka da dai sauran 'yansanda suka ga an fito da ni har da ankwa sai dukkansu suka gyara bindigar hanaunsu, suka daidaitoni da ita. Mototcin da suka kawo ya iaban shida, sanan su da kansu sun kai goma sha hudu. Kai! Allah ka rabamu da sharrin "Ba mu ji ba ba mu gani ba", Ogan 'yansandan nan ya turani cikin mota, 'yansanda uku suka shigo biyu na hannun haguna daya kuma yana hannun dama. Mutanc kuwa sun cika sai kallona suke yi suna nunani. Abin da ya fado mini ina zaune a kan kujerar cikin mota shi ne shin ina Uzaifat ta yi? wa ya shaidawa 'yansanda? Yanzu idan ba'a ga Uzaifat ba na kade har ganyena domin za'a iya cewa ni nayi wannan aika-aika. Innalillahi wa inna ilaihirraji'un... na fada a daidai lokacin da na ji yawun bakina ya kafc. Naga tashin hankali domin irin marin da kwamishina ya yi mini saida naga taurari bakwai sun wuce. "Kaidan iska ba zaka fadi inda sauranku suke ba ko? Wato kun kama mai gidan duk da haka bai yi muku ba sai da kuka ga kun kashc matarsa ko? Zaka dandana kudarka" wannan ma gana ta kwamishi na ta girgizani kwarai, kuma ga shi yaki bari na nayi magana sai dukana yake yi batare da laifin tsayc ba balle na zaunc. Da na ga idan ban yi da gaske ba kashe ni za su yi saj na fara magana da ihu "na fada muku ban san da komai ba domin wannan shi ne karo na na farko da naje gidan kuma tare da 'yar mai gidan muke... ban karasa ba kwamishina ya dakatar dani da hannunsa, "Isa" ya kira wani dansanda. Ya sara "Yes Sir" "Kwance shi tukunna" Isa ya nufo ni yaа kunce ni domin daure ni suka yi a kan wani benci sai jigba ta suke yi kamar Allah ya aikosu. Kwamishina na zaune a kan kujera ya yi mini umarni da na zauna a kasa. Bayan na zauna sai ya ce da ni "Ка се baka san da komai ba?" na amsa "Wallahi ban san da komai ba" ya kalle ni ya yi murmushi mai cike da alamun bai yarda da abin da na ce ba. "Kai nan ba gurin rantsuwa ba ne". ya gargade ni. "Baka san da komai ba me ya kaika gidan? Kuma aka sameka a dakin da aka yi kisan sannan ita wacce kace tare kuke me yasa ita bata nan sai kai aka taras? Na ja gwauron numashi sannan na ce "Yallabai muna tare amma sai na nemeta na rasa" Ya kalle ni cike da mamaki ya ce "ka nemeta ka rasa? Na amsa "Haka ne yallabai" ya ce "Kana nufin ka ce ta yi layar zana ke nan? Na amsa "Bang e ba yallabai ni da kaina ma I can't just understand yo ci gaba "Kana nufin wannan magana taka mai hankalı zui yarda da ita? Ya za'ai kana tare da mutum ka ce ka neme su ka rasa? Gwanda ka sake tunani domin nan da sati za'a gurfanar da kai a gaban kotu tun da an kamaka da hujja kwakkwara guda biyu, na farko dakin da aka yi kisa you was there.domin kuwa ba'a ga komai ba, kuma an kamaka ne a lokacin da kake kokarin guduwa" Na yarda da duk abin da yace dmin babu karya a ciki amma duk da haka sai na ce "Yallabai abin da nake son ka lura a nan shi ne babu yadda za a yi ka dauki ran mahaifin wanda kai ya ceto naka ran daga halaka. Saboda haka Uzaifat ita ce shaidata ta fili Ubangiji kuma shi ne na boye domin bani na yi.... na kasa karasawa don tsananin 17 bakin ciki da takaici na kai hannu na goge hawayc daga fuskata. Shi da kansa Kwamishina jikinsa ya yi la'asar, don haka sai na sake marairacewa inna mai tbbabatar masa da gaskiyar al'amarina. Kwamishina ya ja numfashi sannan ya ajiye "Shike nan na ji tun da ka ce tare kuke da Uzaifat ni zan maka kokari daya insa a yi investigation a nemota as possible as I can, kafin a gurfanar da kai a kotu" Maganar Kwamishina ta da dada mini rai matuka, amma abin lura anan shi ne ina za'a samu Uzaifat? Kwana biyu a gidan yari sannan yayana Alhaji Yusuf ya zo shi da matarsa Hajiya Maryam. Da ya zo ne yakc shaida mini cewa ya yi tafiya ne zuwa Abuja shi yasa bai san an kama ni ba sai da ya dawo Hajiya ta ce. "ai ni a ranar da kuka bar gida da Uzaifat Alhaji ya bugo waya zai je Abuja to sai na ji tsoron fada mas gudun kada ya tsurc. Jiya sai da muka yi ta bilinbituwar neman police station din da aka kawo ka amma bamu yi sa'a ba sai da magariba tukunna aka ce kana nan, to da muka zo sai me tsaron ya ce ba zamu samu haduwa da kai ba sai dai mu dawo yau" yayana ya yi kasake yana jin mu bai ce komai ba. Bayan mun yi 'yar hira sai suka yi mini sallama suka tafi ni kuma na koma gadirum dina na fada cikin tunani, ina cikin tunani na ji an bude kofa, na maida kallona izuwa inda kofar take, kurtun dansanda mai lura da ni ya shigo hannunsa rike da jar roba. Bayan ya ajiye mini sai ya fita abinsa, na kalli abin da ya kawo mini naga garin kwaki ne fal a robar don haka sai na janyo robar gabana na tsoma hannu na cikin garin na debo, ina kaiwa bakina na fito da shi don tsananin gishirin da ya kame mini baki. Na zubar da yau yafi sau biyar don tsananin kame bakina da gishirin ya yi. Daga nan na fara nadamar rashin fadawa su Hajiya a dinga kawo mini abinci, koda yake ban san irin wannan mugun abinci za su dinga bani ba. Domin jiya ma wake suka kawo mini. Ina cikin wannan hali sai na ji an bude kofa wannan kurtun dansandan ya karа 18 shigowa ya ce "Ka yi bakuwa" ko tsayawa bai yi ba ya yi ficewarsa. Na fara tunanin inda na san wata har da zata kawo mini ziyara a jarum ba'a gida ba. Da naga tunani ba zai kai mini ba sai na mike tsaye na yi mika sannan na nufi kofa. Ta yi mini murmushi a daidai lokacin da muka hada ido da ita. Nima na yi mata yake don bana ce murmushi ba. Koda yakt ban yi mamakin ganinta ba tunda nasan ta tafi kasar waje karo ilimi a kan cause dinta. Tana sanye da riga da wando na fakistan kanta yafe da wani dan mayafi shara-shara na fakistan din ta kalle ni "Yaya sannu" na ce "Yauwa Nafisa" "Yaushe kika dawo? Ta ce "wallahi yau na dawo" ta sunkuyar da kai "Yaya wallahi ban ji dadin labarin da na tarar ba domin ya yi matukar razana ni”"

Chapter 2 of 7