Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 5
fitsari ta cewa Salama "Wallahi Salama fitsari nake ji, ya matseni matuka kamar ya zubo kuma naje bandaki na tadda layi yanzu ya zanyi?" Wani irin kallo ta yi mata shekekek sannan ta ce mata "To ya kikeso na yi miki? Ko bakina kike so na bude ne ki yi fitsarin a ciki? Suma da kike gani a layin ai a matse suke amma kuma dole suka hakura, don haka ke ma hakurin zaki yi har azo kanki shiyasa ake so a gasa maka cibiya sabida ka dinga rike fitsari." 114 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Wani takaici ne ya turnuke ta, kallonta kawai ta yi ta girgiza kai sannan ta fice daga dakin da kyar take takawa domin ko yaya ta taka sai ta ji kamar fitsari zai zubo gaba daya. Tana isa gurin layin ta tadda na ciki ya fito wani kasurgumin kato, ganinsa ya tsorata ta, amma sai kawai ta matsa kusa da masu bin layin ta karyar da murya ta ce musu. "Don Allah ku taimakeni ku barni na shiga wallahi na matsu kar fitsarin ya zubo. Gaba daya suka harareta cike da mamakin raina musu hankalin da take neman yi. Delu ce ta kalleta ta yatsina fuska sannan ta ce, "yau nake jin karfin hali barawo da sallama, mu da muke bin layin an gaya miki ba a matse muke ba?" 115 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Kande ta amshe tana rike da kugu cike da takaici ta ce "To matsuwa kuma ta nawa?" Ta nuna wata dake durkushe ta ci gaba da cewa "Wannan da kike gani gudawa takeyi tun dazu take murkususu amma dole ne sai ta bi layi domin haka tsarin gidan yake, mu bamu iya kashin dankali ba, na sama ya danne na kasa, don haka yi azama ki bi layi kar wata ta zo ta shige gabanki." Wani irin takaici ne ya turnike Mero bata iya cewa komi ba illa komawa da ta yi jikin bango ta rakube tana zubda hawaye mai zafi na takaici. A nan a tsaye ta ji fitsarin na jikinta, babu yanda zata iya domin bata isa ta maidashi ba, sai da ta gama fitsarin sannan ta bi jikinta da ruwa ta wanke ta bar gurin ta nufi daki tana jin mutanen gidan suna mitar anyi musu fitsari a tsakar gida amma 116 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE2 ta yi biris bata ko tanka musu ba domin abin yayi mata yawa matuka. Bakin kofar dakin kawai ta je ta zauna tana ci gaba da zubda hawayen dana sani. **** Can gudansu Mero kuwa hankalin Baba Kande ne kan diyarta,kullum damuwa ta rashin sanin inda diyar tata take, tana so ta yiwa Baba Idi magana amma tana gudun taşhin hankalinsa. Izuwa yanzu dai kam damuwar tata takai makura don haka ta yi karfin halin tinkararsa da maganar. A zaune suke bisa tabarma suna hira jefi jefi da karfin hali ta yunkura ta ce masa "Mai gida yanzu yarinyar nan ba za a bincika a ji inda take ba, da kanka fa kace kaje gurin mijinta ka bashi hakuri 117 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE- 2 yace maka bata dawo gidansa ba, anya kuwa ma zuba idanu?" A fusace ya dubeta sannan yace mata "To ai sai ki tafi neman nata tunda ke kin damu da ita, yarinyar da muka koreta amma sabida bamu isa ba memakon ta koma dakinta ashe tanada inda yafi gidan Ubanta dana mijinta." To ni ba tsohon banza ba ne, idan da ya gujeni ba zan tafi nemansa ba domin shine ke neman albarka a gurina amma ba ni ke neman albarka a gurin sa ba, don haka ga hanya nan daga nan har bayan duniya ki tafi neman diyarki amma ba da yawuna ba." Hukuncin da ya yanke ya yi mata tsauri amma babu wani abu da zata iya yi domin tana matukar shayin mijin nata, sannan tana girmama aurenta na shekaru masu yawa tun bata san kanta ba. 118 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Don haka ta rangwadar da kanta kawai ta ce "Shi kenan Allah ya bayyanata a duk inda take." Amma cikin ranta ta kudire cewar zata dage da addu'a kuma zata sanya a tayata da addu'ar Allah ya bayyana mata inda diyar tata take." Cikin halin halin ko in kula yace mata "Kuma dai, ai ni ba hanaki zuwa nemanta na yi ba, amma dai nace ba da yawuna ba." Bata sake ce masa komi ba illa mikewa da ta yi tana fadin "Allah ya kyauta." Ta nufi dakin girki domin fara aikace aikacen ta na gida, cikin ranta tana addu'a Allah ya kawo mata karshen wannan al'amari ya bayyana mata diyarta." Ita kuwa Mero tana can gidansu Salama tana faman shan wahala, yau kuma 119 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 da ciwon ciki ta ta shi, don haka take ta murkususu tana fama shafa cikin nata ita kadai tasan wahalar da take sha. Salama ta kalleta shekeke cikin daga murya ta ce mata "Wai ke Mero me ke damunki ne kike ta faman murkususu? Ko cikin naki ne ke miki ciwo? Ai gashi nan kinga abin da ya sameki ai ba irin gargadin da ban miki ba akan kar ki yarda da mutumin nan baki yarda ba, gashinan kina fama da dirkeken ciki shi kuwa yana can zai bare sabuwa dal a leda ko tunawa da ke bayayi." Wata kwallar takaici ce ta fito mata cikin shesshekar kuka ta ce mata "Yunwa ce ke damuna Salama tun farau farau din da na sha dazu shikenan a cikina, kuma kin san ba ni kaďai bace." Kwabe baki ta yi ta yatsina fuska ta ce. "Mero kenan to ke da wai kina nufin nice zan dinga ci da ke? Tabdijan nima sun 120 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CЕ-2 Inna da za su tafi ba su barni da komi ba illa rai da lafiya, ni ke fita na yi 'yan shige da ficena na ci da kaina, kin sani kuma ba sana'ar komi nake yi ba, in zaki saida kadara ki samu abinçi to, in kuma zaki zauna ki bushe ke da dan cikin naki duk dai ke ya ragewa." Wani irin daci ta ji kan harshenta sabida bakin ciki da takaici, ba zata iya magana ba, illa ci gaba da shafa cikinta da ta yi wanda ke azalzalarta, tamkar dam cikin zai fito. Cikin ranta take fadin "Lallai maza basu da tausayi, duk da dai tasan ta yi laifi amma ai bata cancanci wannan hukuncin ba ko don cikin dake jikinta, wai yau ita ce abincin da zata ci ya gagareta, hawayen dai ke sake biyo idanuwan nata, ta sanya hannunta ta share tausayin kanta da na dan cikin nata ya mamayeta. 121 AWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CЕ- 2 Ita kuwa Salama tsaki kawai ta yi ta wuce ta barta a nan tana fadin "Yau na ji karfin hali dana baki gurin da zaki zauna ma ai nayi ca nake iyayenki ne suka koroki ni na rufa miki asiri na karbeki shine kuma zaki zauna ki saki baki na baki abin da za kicin? Lallai Mero baki da lissafi sam.' Shi kuwa Alhaji Sadik kamar kullum yana gaban gimbiyar tasa ya sanyata a gaba tamkar zai lasheta, ita kuwa sai wata ran gwada take yi tana yin abubuwab da tasan yana tafiya da imaninsa. Cike da kulawa ya kalleta daga sama har kasa ya saki murmushi cikin tausasa murya yace mata "Dafatan dai duk abin da bai yi maki ba ki fada sai a sauyashi." Wani fari ta yi masa sannan ta zari idanuwa ta ce masa "Haba ranka ya dade ai wallahi komi ka yi hidima kwarai, Allah ya saka da alkairi ya bamu zaman lafiya." AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE 2 Maganganun nata sun ratsa shi sosai wani dadi ya ji ya mamaye ko ina nasa domin ba abin da yake kauna a duniya irin ya faranta mata don haka cike da jin dadi ya amsa mata da "Ameen, ko dama godiyar da kike ta yi mini a waya kenan?" Ta rangwadar da kai abin da ke kara daukar hankalinsa sannan ta ce "Eh mana kai da baka gane ba? Ai Inna ma ta ce na yi maka godiya sosai, kana jin yanda aurenmu ya zama abin yadawa a gari?" Dariya ce ta subuce masa, ya amsa da cewar "Ai haka ake so dama, domin kyakkyawa kamarki abin da ya dace ayi mata kenan." Gaba dayansu suka yi dariya Sadiya ta sake rangwadar da kai ta yi masa wani irin fari da ya aikata shi sannan ta ce masa "Amma godewar da kike min kamar ta yi yawa, ai ban kaiyadda kake fada ba." 123 AWITYA WADA ISA- YAR ALJANNA CE Maganar tata ta ratsa ruhinsa cikin kasalalliyar murya ya ce mata "Sadiya kenan ai komi naki ya yi, ba kya kallon kan ki ne a madubi shiyasa inajin baki san kanki aba, amma mu da muke kallonki ko yaushe ai mun san bamu ce komi ba a yabawa halittarki da iya tsara kwalliyarki, shi yasa nake jin kamar gC ACI na janyo kwana biyun nan da suka rage na ganki a dakina." iseoe gvibog sAsπ Wani irin dadi ta ji ya mamaye ta domin ba abin da take kauna a ranta illa ta ji cewar ta tafi da imanin Alhaji don haka ta zaro idanuwanta da suke dauke hankalin Sadik sannan ta yi dariya ta sunkuyar da kai kasa kana ta ce, "Uhum Alhaji kenan, gaskiya kana da zumudi dad yawa. cikin mutuwar jiki Alhajin yace mata "ke kinsan kanki kuwa?sb aswabog smmA" Ai dole nayi zumudi akan ki, ke ni ko ma na shiga gurin Inna ne yanzu nace a 124 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE- 2 fasa yin taron bikin kawai ki sanya mayafinki yanzu na tafi dake." Da sauri ta zaro idanuwa ta bude baki, sannan ta juya ta nufi gidansu tana fadin "Tabdijan bari kaga tafiyata tun kafin mafarkina ya tabbata." Ya bita da kallo tana matukar jan hankalinsa tamkar wani magana disu take tare da shi, cikin kasalar murya yace mata "Ko sallama ba zaki tsaya muyi ba Sadiya?" Tana zuwa dai dai kofar shiga cikin gidan nasu ne ta bashi amsa da cewa وو" Mayi a waya. Tana gama fadin haka ta shige cikin gidansu. Tsayin lokaci yana tsaye yana kallon kofar gidan nasu sannan daga bisani ya hakura dolensa ya shiga motarsa jikinsa a sanyaye yana jin tamkar ya bita cikin gidan nasu. 125 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 **** Ita kuwa Mero duk ta yi baki. ta rame, idanuwanta duk sun fada sunyi zuru zuru, sai ciki a gabanta tororo. Suna zaune ita da Salama a cikin dakinsu wata jaka ta fado daga kan tsirin kayan da ke kan dakin, wani yariin gwal ne ya fado daga cikin jakar dukkansu idanuwansu suka hadu a kan kallon yarin. Mamaki ya cika Mero, don haka da sauri ta kalli Salama ta ce mata "Salama wannan yarin da ke kusa dake naki ne?" Wani irin kallo ta yi mata a wulakance sannan ta masą mata da cewa "Nawa ne mana ji wata irin tambaya, tunda kika ganshi a kayana ai kinsan nawa ne. Da sauri ta dauko yarin tana kallonsa a hannunta tana dubawa san a ta ce mata 126 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE2 "Ashe kina da irin yarina da ya bata amma ban taba ganinki da shi ba sai yau?" A fusace Salama ta ce mata "Ban gane me kike nufi ba, kina nufin yarinki ne daya bata ni kuma na sace kenan ko? 3 Tunda dama ke kadai aka Kerawa irinsa ko? Kuma ni talauci ba zai barni na 2 mallaki yarin gwal ba sai ke matar Alhaji.' A sanyaye Mero ta ce mata "A'a wallahi ni ba haka nake nufi ba, da ga nace irin nawa?"d iv i emsta2 n Tamkar wacce aka tsaikara sai kawai ta mike ta tsaya akan Mero a fusace tana fadin "Haka kike nufi mana Mero, wallahi haka kike nufi, yau na ji masifahaka kawai na jajibo ki har gidanmu zaki zo ki kala min sata kiri-kiri ina ji ina gani." anoy Mero ta mike jikinta na kyarma ta ce "Haba Salama menene na yi mini gori akan 'yar wannan maganar?" 127 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE- 2 Cikin daga murya ta ce, "Ke ce kika dauketa 'yar magana ni babba ce a gurina domin sharrin sata bashi da dadi, don haka ni kam ba zan iya zama da ke ba kina yi mini sharri bayan ci dake da nake yi da baki makwanci." Wani irin tashin hankali ta ji cikin ranta, da kyar ta iiya mikewa jikinta ba kwarin jiki na daukarta ta janyo mayafinta ta yafa ta janyo akwatinta sannan ta ce. "Shi kenan Salama ki yi hakuri insha Allah yanzu zan bar miki gidanki." Daga nan bata sake cewa komi ba illa janyo akwatinta da ta yi tsakar gida. Ita kuwa Salama tuni idonta ya gama rufewa da masifa don haka cikin daga murya take fadin. "Ey aje Allah ya raka taki gona Umma ta gaida Assha, ba zan lamunci sharrin sata ba ko kadan, abi wani sarkin kuma." 128 AWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE 2 gidan mijinta, Allah ya rufa mata asiri bata 99 gane ba, gashi nan ta tonawa kanta. Delu ta amshe da cewa To ai jiki magayi, mu din nan da muke cikin talauci da wahala ma bamu yi wasa da aurenmu ba, ballantana wanda ke cikin daula irin ta Mero. Ita kuwa Mero jan akwatinta ta yi ta nufi kofar fita, tana zuwa daidai kofar ta juyo ta dubi Salama kamar tana wani tunani sannan ta gyada kai kawai ta juya ta fita, ita kuwa Salama fadi take. iAje dai Allah raka taki gona haka kawai zan daukowa kaina ruwan dahuwar kaina, ina zaune cikin rufin asirina, ba zata sabu ba bindiga a cikin ruwa." Da kyar take daga kafafuwanta tana jan Trolly din nata hawaye na bin idonta ita kanta bata san ina ta dosa ba. Nima na dakata anan. mu hadu a littafi kashi na üku insha Allah. y dallA 130 S AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 ALAWIYYA WADA ISA (maman twins) 08033472866 DAGA TASKAR SARAUTA 08034255307 TALLA! TALLA!! TALLÁ!! "Abban Ilham yau ina zuwa ne da sanyin safiya haka.?" Ya dubi Agogon Bangon dake dakin tara da 'yan mintuna. "Me ki ka ga ni.?" Shi ma ya tambaye ta. 131 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE- 2 "Na ga ne ka ci ado kamar wadda za ka fita wani taro na musamman." "An ce ba kullum ake kwana a gado ba, kuma haka ne wadannan masana fadin magana sun fadi gaskiya, yau kai ne a can gobe kai ne a nan." Ta bishi da kallon mamaki domin amsar tasa bata fuskanci ainihin abin da take son ji ba." "Uhm sai an karya min harshe kuma, ni dai tambaya na yi amsa nake bukata kawai ina zuwa yau da safe.?" "Neman aiki.?" Ta jima ta na kallon sa da mutukar mamaki. "Neman Aiki.?' Ta fada da mamakinta.?" 132 AWITTA WADA ISA- YAR ALJANNA CE2A "Zan je neman aiki ne saboda al'amura sun fara yawa, duniya ta na da girma, haka hanyoyin samu na da fadi, babu mamaki idan can ta ki ka koma can, fadi ta shi dai dama bawa bai isa ya ce yafi karfin yi ba, in har ina busar numfashi. Zan je ko Allah zai sa a dace." "Me ne ka rasa.?" rude of sa nennsw, sh iy unn os sy ofcoaр ок eр t ad edog "Me ne na samu.?"sxinub sh nioelol WUYBI Ya dawo mata da tambayar ta kai tsaye. sd Tsyinub Ita kuma ta saka masa ido cikinmutukar mamakin kalamansa. S Ba samu komai 318h smmA samu komai ba, Hafsa dan ki ka auna cewar idan Allah ya ba mu aron rai gobe ba irin yau ba ce jibi ba rin gobe bace haka gata citta, don haka ya zama dole na shiga duniyar neman abin rufin asiri abubuwa sun cunkushewa rayuwa ta, na ga alamar baki san da haka ba." nsW EBW sWtun an ibsi Ta mike daga in da take ta dawo kusa da shi "Mai yasa kake yanke kauna da daukaka ta. 133 E AWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE 2 ( t ( Ya zuba mata ido kafin ya ce komai sannan ya gyara murya ya ce, "Daukaka lokaci ne da ita, ki na nan za ta zo ta turmeshi ki, kuma kada ki manta ba a rayuwa a dakushe." "Kamar yaya.?" "Da ni na ke shuhura, yanzu kuma ke ce, gobe ba fa ba ke bace, to ya za mu yi da wannan rayuwa, lokacin da duniya take yi da kai, lokacin jama'a ke yi da kai. In kin ji an ce duniya. To ba duniyar ba ce jama'ar cikinta ne. Ranar da jama'ar suka koma kan wata, kaka ke nan.?" "Amma dai ka san duk lalacewar dan zaki yafi karfin kadangare, ko da a ce ban da wani abu da zan tabuka mahaifina mai kudi ne, ba kuma zai hanani duk abin da nake bukata ba." Ya dora hannuwansa a kai, daga bisa ni wani murmushi ya kubuce masa "Da a ce zan fadi na mutu. Wannan shi ne abu mafi soyuwa a cikin zuciyar iyayen ki, ni kuwa don me zai sa na 134 시 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE-2 zauna ina barautar abin da za su ba ni, wadanda ko kauna ta a raye ba sa su. Hafsa ki rike daukakar ki, ni ma zan je na nemi abin da zai rufamin asiri, daga rana irin ta yau na rabu da harkar rubutu, har Abada kuma ina mai nadamar kasancewa ta marubuci. Tirkashi, in ba ka yi ba ni guri. Wani kasaitaccen labari, mai sa ka zubar kwalla, mai dauke da wata sha'umar soyayya, wannan labarin ya kasaitu ya samu ingancin aiki, sabon salo a cikin rubuce rubucen zamani, ka da ka saki a baka labarin wannan kasaitaccen littafi mai suna. BA ALJANNA BACE. Matashiyar marubuciyar nan 'yar uwa ga Hadiza Adam shi shitu wato Rabi'atu wacce ta rubuto littafaina kamar haka BAKIN JINI NA. 135 ar a AWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE- 2 TAKAICINA FARIN CIKINA. MURAIDIN RAINA DAN KUKA ALKIBLATA NI CE NA DACE ZANEN DUTSE ТА КARA YUNKURAWA TA KAWO SABON LABARI MAI SUNA ...BA ALJANNA BACE, KI NEMI NAKI А KASUWA DA ZARAR YA FITO. Kada ku manta da sunan BA ALJANNA BACE 136 Littartafan marubucivar: SHARRIN ZUCIYA ...RABIN JIKI GUGUWAR ZAMANI RUWANIDO DUNIYAR MAKARANTA CЕ YAR ALJANNA CE YarAljanna Ce ALAWIYYA WADA ISAH BUGAWA DA YADAWA: Printing & Publishing by: SARAUTA PUBLISHERS 08034255307 Cover Graphics Anka-Graphics fagge 07030319787 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 5 of 5