Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
ma ya fada tsakanin kujeru, kinga kuma in hakane 55 AWIYYA WADA ISA- YAR ALJANNA CE2 ba za ki ganshi ba sai sanda aka balle kujerun don haka ki bar neman nan kawai ki zo mu wuce ni wallahi ke nake ji ba ni kaina ba, ni ko kwana zanyi a tafe ba ruwan wani da ni ke kuma fa?" Mero ta ce "To ai ni abin ne ya yake daure mini kai, domin ba yanda za ayi yarin nan ya fada cikin kujera don na sha ajiye shi a nan kuma na dauki abina inda na ajiye. Salama ta dubeta shekeke ta ce mata "Af! To yanzu wa ya daukeshi? Ko kuma ni kike zargi? "Ta fada cikin bata fuska. Mero ta kalleta ta ce, mata "A a ni wallahi ni ba haka nake nufi ba, muje kawai dan na dawo na dubashi cikin tsanaki." Salama ta juya ta nufi kofar fita tana fadin "Ato da dai ya fi miki." Itama Mcron ta bi bayanta suka fice zuwa kasuwa. 56 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE 2 Tafe yake a kan hanyarsa ta zuwa gida daga office, wata zuciyar ce ta raya masa ccwar ya kamata yaje gurin Auwalu don haka ya juya kan motarsa zuwa majalisarsu domin yasan a wannan lokacin a nan ne kawai zai iya samun Auwalu. Kansu na kasa sun dukufa suna faman karta, har ya tsaya da motarsa ya fito sannan suka kula da zuwansa, ya yi musu sallama sula amsa sannan ya tambayi Auwalu. Babu wani gamsasshen bayani na ina yake don haka ya yi musu sallama ya juya zuwa motarsa. A daidai kan hanya suka ci karo da Lado daya daga 'yan majalisar tasu, da zolaya yace masa "Ango ka sha kamshi, shima yayi dariya ya amsa masa da cewa "Lado kartagi uban 'yan karta, an taho sana'ar ne? Suka sake yin dariya, Lado yace masa "Saddiku baka da dama ina amarrya?" Sadik ya ce "Amarya tana can gida abinta." 57 AWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE 2 Lado yace "Ko da yake dazu 'na shiga kasuwa na gansu ita da wata kawarta sunyi siyayya ko da yake dai basu ganni ba amma ni na gansu, ai abokina ka iya kiwo yarinya ta yi kyau ta yi 6ulbul da ita haka. Alhaji Sadik ya katseshi cike da mamaki yace masa "Kasuwa kuma Lado ko dai wata ka gani ba ita ba?" Lado ya yi murmushi yace masa "Haba Saddiku ai Mero ba zata bace mini ba, yarinyar da ta taso a gabanmu? Ai a sanin Mcro daga Auwalu sai ni ke rufa masa baya." murmushin Alhaji Sadik ya kakaro yake da niyyar rufawa kansa da iyalansa asiri yace masa "Hakane Lado ka sanni da mantuwa, na tuna ta sanar dani zata je siyo abubuwan da suka kare a gidan. Lado ya yi dariya yacc masa "Ai kai Saddiku tsufanka da kallo, nan da na sai kacе ka manta abu, kuma har ma abin da ya shafi aurenka? Allah ya yaye maka, ni dai na san Mero na gani yarinya ta yi kyau abinta amma dai duk da haka ban kasa ganeta ba." 58 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 Alhaji Sadik bai ce komi ba domin tuni ya kure da takaici da kunar rai musamman yanda Lado ke bayyana matarsa, don haka motarsa kawai ya nufa yana fadin "Gaskiya bari na koma sai anjima." "To sai anjima Allah ya kiyaye, Lado ya amsa masa sannan ya nufi gurin 'yan uwansa 'yan karta, shi kuwa Alhaji Sadik tashin motarsa ya yi da sauri ya dagawa sauran abokansa hannu ya wuce zuciyarsa na yi masa kuna tana azalzalarsa. Kai tsaye gida ya wuce, cike da bacin rai ya dire a falo yana kwalawa Mero kira, cike da yauki ta fito daga cikin dakinta tana yatsina tana bata rao, ganin halin da take ciki ne ya sanyata mamaki ta zo ta tsaya kawai a gabansa. A fusace yace mata "Wai ke don Allah wacce iri ce? Ke wai bakya son zaman lafiya ne a rayuwarki? Na auroki don na huta amma banda takaici da bacin rai da bakin ciki ba kya haddasa mini komi? 59 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE 2 Da mamaki ta dubeshi ta ce masa "Me kuma na yi kake mini wannan tashin hankalin daga shigowarka ko zama baka yi ba?" Ya sake hasala ya dubeta da bacin rai yace mata "Kinji irin rashin da'ar taki ko? Waye ya baki izinin fita daga gidannan ki ka je kasuwa ba tare da sanina ba?" Kwabe baki ta yi ta yatsina fuska ta cе, "Af wannan 'yar karamar fitar da nayi har munafukai sun je sun sanar da kai? To da sunyi hakuri ma ai da zan sanar da kai cewar na dan fita."" Nan take ya hau huci tamkar wani Zaki sabida Kara masa bacin rai da ta yi, cikin karaji yace mata "Ok wato kina ma tabbatar mini da kin je kenan inyaso duk abin da zanyi na yi ko? Wai ke wacce irin tarbiyya aka yi maki a gidanku ne?" Kuka kawai ta saki, cikin kukan take fadin "Af abin har ya kai ga zagin Iyayena? Daga na dan fita kuma nace dma zan gaya maka, me Iyayena suka yi mak 60 AWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE 2 Cike da takaici yace "Mata to biyayya cc basu yi maki yanda ta dace ba, ko kuma basu sanyaki a Islamiyya ba domin da kinsan ilimin Addininki da dole zaki san cewa matar aure sai da izinin mijinta take fita ko ina nc. Kara ci gaba ta yi da kukan, ta juya kawai ta nufi cikin dakinta tana fadin "Wallahi ba zan yarda ka dinga zagar mini lyayena ba domin alheri suka yi maka da suka haifeni har ka samu ka aura. Tana kaiwa nan ta shige cikin dakin, shi kuma kawai binta yayi da kallo cike da takaici da bacin rai ya dafe kansa idanuwansa sunyi jawur sabida takaici. Ji yayi ba zai iya zama agidan ba domin zuciyarsa tafarfasa kawai takeyi don haka ya mike ya dauki mukullinsa ya nufi motarsa ya tasheta ya fita, yana tafe kan titi amma bai san ina ya nufa ba, haka ya dinga tafiya a kan titi ba shi da gurin zuwa har sai da dare ya soma yi masa sannan ya juyo ya dawo gida. 61 AWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNА СЕ- 2 Haka nan 'dukkansu suka kwana kowa ransa babu dadi, washegari har ya nufi ofis ko motsin Mero bai ji ba, balle ya saka ran fitowarta. Sanda ya taso daga ofis sai ya ji yana bukatar ganin Hajiyarsa don haka sai kawai ya nufi gidannasu kai tsaye. Da sallama ya shiga ya taddata zaune tana hutawa a falo, sai da suka gaisa sannan ta fara yi masa da cewa "Kamar kasan ina so na ganka sai gashii Allah ya kawo mini kai, ka bani mamaki matuka, har yaushe aka yi auren naka da har matarka zata fara kawo mini karar ka? Kuma abin takaici da 6acin rai wai Iyayenta kake zagi, abin da ban sanka da shi ba, na ji ciwon wannan abu sosai, domin ya nuna baka daukar hudubar da nake yi maka a kullum akan matarka. Maganganun Hajiyar tasa sun daure masa kai, mamaki ya cikashi. 62 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Da sauri ya yace mata "Hajiya wallahi ba haka bane, ni nafi so ki saurareni na gayа miki yanda komi ya kasan..... Da sauri cikin fada ta katseshi da cewa "Rufe mini baki, bana so na ji komi daga bakinnka, wannan yarinyar 'yar albarka mai ganin girma da mutuncin mutane, ba za ta taba shirya abin da bai faru ba ta zo ta fadi, yarinyar da babu sawa ba fitarwar me zata yi wa mutum na 6acin rai." Dagowa kawai ya yi ya kalleta cike da 6acin rai ya girgiza kai kawai. Cikin fada Hajiyar ta ce, Ai dama sai dai ka kalleni din amma baka da ta cewa, wato ka fara biyewa zigar abokai ko? Sunga Allah ya rufa maka asiri shine suke so su shirya maka gadar zare, su kai ka su baro, to wallahi ba zan lamunta ba, sam kar ka bari na sake jin wani abu makamancin wannan ya sake faruwa. Cike da karfin hali ya girgiza kai kawai ya ce mata "Shi kenan Hajiya Allah bayyana gaskiya komi daďewa. 63 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE- 2 "Yo ga gaskiya nan ta tabbata ni dai na gaya maka ka kiyaye." Kansa na kasa ya ya amsa da cewa "Shu kenan Hajiya Allah ya kiyaye gaba." Da "Amin ta amsa, shi kuma yayi mata sallama ya fito ransa na yi masa Kuna. Yana tafe bisa hanya ne wayarsa ta hau kara, Auwalu ne don haka ya saka handsfree suka fara magana. Bayan sun gaisa ne Auwalu yace masa "Dama na kiraka ne na isar da sako, su Ahmad ne suke so za su zo gidanka su ga amarya, shine suka ce na sanar da kai, to ni kuma zata iya kasancewa su zo bana nan don zan danyi tafiya, shine nace bari na gaya maka ta waya don kar na manta." Duk da gabansa ya fadi domin ya san yanayin da gidansa yake ciki amma hakan bai hanashi amsawa ba. 64 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 Cikin karfi hali yace masa "To shikenan Allah ya kaimu, zamu shirya zuwan nasu insha Allah, akwai maganganu da yawa da nake so muyi amma sai mun hadu sai mu tattauna. Auwalu ya amsa da "To ba komi, ni yanzu na saita hanyar tafiya, amma Insha Allah idan na dawo zan lalubeka sai mu tattauna din." Alhaji Sadik ya ce "To shi kenan Allh ya tsare, suka yi sallama suka ajiye wayar. Jikinsa babu kwari ya shiga cikin gidansa. A zaune ya taddata a falo tana kallo, ya nemi guri ya zauna ko kallonta bai yi ba. Sannu da zuwa ta yi masa gami da zuwa kusa da shi ta zauna, ko kallonta bai yi ba illa sake dauke kansa da yayi ya sauya tashar da yake son ya kalla. 65 AWIYYA WADA ISAYAR ALJANNA CE2 Yana ajiye remote din ne ta sa hannu ta dauka ta sauya tashar sannan ta sake maida kallonta gareshi. Juyowa ya yi ya harareta sannan ya dauke kansa, kamar ba zaice mata komi ba sabida zafinta da yake ji, amma sai ya daure yace mata "Yanzu ke abin da ki ka yi ya dace kenan? Da sauri ta yi dariya ta ce masa "Mе kenan na yi? Canja tashar da na yi ne ban kyauta ba?" A fusace ya fizge remote din da ke hannunta yace mata "Yanzu ke tsakaniinki da Allah ni ban kai ki kara ba sai kece zaki je ki shirya mini sharri kice wai na zagi iyayenki? Anya kuwa kina tsoron Allah kuwa?" Kanta na sunkuye tana wasa da yatsunta ta amsa masa da cewar "Ai sako Iyayen da ka yi ne ya bani haushi, amma 66 AWIGYAWADAISA YAR ALJANNAICRA tunda Hajiya da bani hakuri komi ya wuce nia gurina har ma na manta anyi Kansa kawainya girgiza yácet Allah sya kyautanyanzu abin da nake so na sanar imiki shinewgobe insha Allah abokaińa ża su zorsu tayamu murna sabida basa nan akaniyin bikinmu don haka ina neman alfarma da hadin kanki, ki yi musu.duk rabin da ya dace wanda zamu fita kunya." isl si Gike da gamsuwa tace masaBa kominAllah yakaimu za ayi komisinsha ilahys iss sbu nice Test Star 6 вгnollsAmsar tata ta sanyashi farin cikirdon haka yayi murmushi yace "Shi kerian Allah yayi miki albarka, Allah yásáłki dore a haka ki igane gaskiya." A E2707ETINTE пнсо Миmushi kawai ta yistarmikeita nufi kan tebur domin hada masa abincin da zai cin shilkansa abin mamaki yake bashi, Gikin mransa yake fadin "Anya ukuwa yarinyar nan bata da iskoki?( g 67 AWIYTA WADA ISA- ‘YAR ALJANNÀ CH Yau birkice gobe ta koma daidai. Haka nan ta yi ta tarairayarsa tana kula da shi, har lokacin baccinsu. Yau kam har bisa shimfidarsu, ta bashi mamaki domin abubuwan da ta yi masa bata tabayi masa ba irinsu ba, wannan ya sanya ya kwana cikin farin ciki marar misaltuwa." Washegari da safe hatta ruwan wankansa itace ta hada masa, sai da ta kai masa wajen shiryawa sannan ta nufi tebur ta hada masa abincin da zai karya. Shi kansa tamkar a mafarki yake kallonsa abin." Haka ta yi ta kula da shi da tarairayarsa har sai da ya tafi izuwa gun aiki sannan ta dawo gida ta shiga kokarin gyaran gidan da sauran ayyukan gida. Da yamma ya shigo gidan cike da zumudi, dadi ya sake kamashi domin tun daga waje wani kamshi ya daki hancinsa a 68 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE2 cikin gidan kuwa tamkar komi na gidan sabo aka sake don kyau, domin ta goge komi ta kuma gyare komi sai daukar ido yake yi. Tana jin motsinsa ta fito da sauri tana yi masa barka da zuwa, ita kanta ta yi kyau tamkar wata 'yar tsana, sai daukar ido take yi, dadi ya sake cikashi, bai san sanda murmushi ya subuce masa ba yace mata "Ko ke fa Mero, yanzu don Allah da haka kikeyi yaushe zamu dinga fada dake? Lallai yanda kika gyara gidannan tsaf, ki ka yi komi yanda na umarce ki, gaskiya yau kin fiddani kunya, Allah ya yi miki albarka, bari kawai na juya na shigo da bakin domin tun dazu sun min waya suna jirana." Bai saurari amsarta ba kawai ya juya ya fice, ita kuwa binsa kawai ta yi da kallo tana murmushi. 69 AWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE2 Bayan 'yan mintuna ne suka shigo tare da abokan nasa, su uku dukkansu cikin fara'a suka yi sallama suka shigo. Mero ta amsa musu gami da yi musu barka da zuwa, cike da zolaya Umar yace mata "Amarya kinsha Kamshi." Ahmad ya amshe da sauri yace mata "Amarya kuma? Ai yanzu ta zama uwargida, ka sani ma ko har an samo kyautar daki?" Shehu ne ya amshe da cewar "Nima dai abin da nake so nace kenan ka rigani, ka san yanzu tamkar tuntube ake dashi a bakin kofar daki." Gaba daya suka yi dariya, Alhaji Sadik ya dubeta ya ce mata " kina ji suna yi maki tsiya amma kinyi shiru? Baki da amsar da zaki basu?" Da sauri ta mike ta nufi hanyar daki tana fadin "To me zance?" 70 AWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE-2 Alhaji sadik ya bita da kallo yana fadin "Ya kike tafiya daki ne baki sauki bakin ba? Juyowa kawai ta yi tana nuna wajen da tebur yake ta ce masa "Ai ni na gama saukar baki, komi yana bisa tebur. "Tana gama fadin haka ta shige cikin daki." Bai ce komi ba illa mikewa da ya yi ya nufi kan teburin yana fadin "Ku taso mana kuci irin girkin amarya." Kai tsaye suka mike suka nufi kan teburin suka zauna suna sauraron a basu abin da za su ci din." Alhaji ne ya hau bude kwanikan da ka jera don ya taimaka musu wajen zuba abincin. "Sai me? Ga mamakinsa kowanne kwano ya bude sai ya ga danyen abinci ba dafaffe ba, na farkon danyar shinkafa ce a ciki, na 71 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE 2 biyun kuma kayan miya ne danyu aka jera a ciki, hakan dai duka sauran kwanukan suka Kunsa. Nan take hankalin Aliyu ya tashi, idanuwansaaa suka rune suka yi jawur, su kuwa abokan nasa ta sjii kawai suka yi daya bayan daya suka yi masa sallama cike da mamakin abin da Mero ta aikata, suka fice. Ko sallamar ta su bai iya amsaea ba, illa kwalawa Mero kira da ya yi cikin 6acin rai da tsananin bacin rai, kai tsaye dakin nata ya nufa domin ba zai iya jira ta fitoo ba sabida tsabar 6acin rai da takaici. Zaune bisa gado ya taddata idonsa a rufe ya hau fadin "Wai ke Mero wacce irin dakikiya ce ne? ki rasa sanda zaki tozarta ni sai a gaban abokanaina? Yan zu ni ban isa ki dafa mini abin da zanci a gidana ba? Sannan idan na kawo baki suma haka? Ban isa ki fiddani kunya ba? Sannan 72 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ» 2 karin takaici da bakin ciki da tozarci wai sai ki zuba danyen abinci cikin kwanuka, ni kam wallahi na gaji da wannan auren naki, na yi dana sanin auren domin ba komi a cikinsa sai 6acin rai da tozarci." Muryarsaa rike ya karasa maganar. Ita kuwa yatsina fuska kawai ta yi ta ce masa "Haba Alhaji menene na wannan ta da jijiyar wuya haka. Na sha gaya maka wallahi ba zan iya girki ba, na ji ma da larurar da take jikina, ko kamshin abinci na ji amai nake yi, kuma kaine ka jawo, don haka ni wallahi ba zan iya ba." Kansa ya dafe kawai sabida takaici, ya koma falo ya zauna cike da tashin hankali, kansa na sunkuye yana zubda zazzafan hawaye, cikin ransa yana fadin "Wacce irin masifa na daukowa kaina har cikin gidana? 73 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Kuma na kashe kudina da kaina na dauko abin da zai aur Hawayen nasa ne suka karu, nan yaci gaba da tunane-tunane barkatai har ya nemi hawayen ya rasa. Don haka ya tashi ya nufi dakinsa yana ambaton Innalillahi wa inna ilaihirraji'un, da haka bacci ya dauke shi. **** Washegari da sassafe ya fice kai tsaye gidansu ya wuce, yaci sa'a ya sameshi a kofar gidansu bisa dakali yana zaune.61 zeDa sauri ya taso ya tareshi kan dakalin suka koma suka zauna, bayan sun gaisa ne Alhaji Sadik ya fara dacewa "Nasan za ka yi mamakin ganina yan zu? Auwalu ya ce "Babu mamaki nasan halin rayuwa ai, wani abin zai iya taso 74 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 mutum ba tare da shiri ba, kuma bahaushe ya ce labarin zuciya a tambayi fuska, tunda na ganka fuskarka ta bani labarin halin da kake ciki." Alhaji Sadik ya yi gyaran murya sannan ya ce, "Wato Auwalu na rasa ta inda zan bullowa lamarin yarinyar nan domin wulakancin da ta yi mini da tozarcin da ta yi mini a jiya a gaban abokaina gaskiya ba zan iya dauka ba Auwalu, ina ganin gara na hakura da ita kawai, na kaddara kawai ban dace da aure ba, don haka zan saketa kawai..." Da sauri Auwalu ya katseshi da fadin "Haba abokina kar ka yarda zuciya ta yaudareka ka aikata abin da ba shikenan ba. Jiya da na dawo da daddare Ahamad ya gaya min duk yanda aka yi to amma abin da yasa banyi maka magana ba sabida nasan kana cikin 6acin rai, sai na kyaleka sai ka huce tukunna. 75 AWIYYA WADA ISA-"YAR ALJANNА СЕ 2 Ka yi hakuri abokina wallahi na fika tashin hankali da 6acin rai domin nine na kawo Mero. Yanzu abin da nake so da kai ka daure ka janye maganar saki domin yanzu mutane na jin ka saketa ba kowa ya san matsalarku ba sai ace kudi yasa kake so ka fara auri saki, ko kuma dama so kake ka yi auren dandano kawai, ni kuma bana so a sanyaka a baki domin baki bashi da dadi." Cike da damuwa Alhaji Sadik ya ce "To ya kake so nayi Auwalu? Tunda na auri yarinyar nan ban huta ba, sai na zauna 99 neman kudi bai bani matsala sai mace. Auwalu ya gyada kai ya се, "Hakane, amma nafi so ka sauya matakin da ka ka shirin dauka, amma ba wannan ba." Alhaji Sadik cikin sanyin jiki yace "To ina sauraronka bani shawarar matakin da zan dauka? 76 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 Auwalu ya nisa sannan ya ce, "Ai shawara bata wuce ka kara aure ba domin ina tabbatar maka duk tsiyar da take ji ko take takama da ita, daga zarar ta ji zaka auro wata to daga sannan zata shiga taita ".yinta وو Alhaji Sadik cikin rashin gamsuwa da shawarar Auwalu ya ce, "Haba Auwalu wannan kuma wacce irin shawara ce? Na yi auren ban huta ba, kuma sannan na karowa kaina wata? So kake su sanya mini hawan jinin da ban shirya ba. Auwalu ya dan yi murmushin yake yace "Ba haka bane abokina, ai duk wanda ya san lagon mata, da zarar ya ga matarsa zata bashi matsala to sai kawai ya laluba ya samoo wacce ta fita hankali ya uaro, shi kenan sai kaji shiru ta shiga taita yinta ta koma gasar yanda za ta zama tauraruwa a tsakanin su biyun." 77 AWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE 2 Alhaji Sadik ya gyada kai sannan yace. "Ka gwada mana ka gani abokina, musamman da mahaifiyarka ke goyon bayan Mero bata son laifinta kuma yanzu ka je kace zaka saketa, ko ka saketa, kai kanka kasan akwai rikici ba karami ba, amma idan kace aure zaka yi ba wanda zai hanaka domin Allah ma ya baka damar ka yi." Da alamun maganganun Auwalun sun fara ratsashi don haka ya danyi murmushi sannan yace "Ka zo da shawara mai kyau fa abokina, amma kuma sai na duba ta sosai sanan zan yanke hukunci, in har na ga zata bulle mini to Insha Allah zanbita domin wallahi sai na rama takaicin da Mero ta hadani da shi." Auwalu ya yi faffadan murmushi sannan ya сe, "Kо kai fa abokina, kuma ina tabbatar maka wallahisromon da ke 78 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE- 2 cikin hada mata biyu sai ka yi sannan zaka bani labari da kanka." Mikewa ya yi yana dariya yana fadın "Allah ko abokina." Shima Auwalun mikewa ya yi yana fadin "Allah kuwa abokina kaje dai ka yi tunani, ni nasan insha Allah za a dace. Da haka suka yi sallama da juna, Alhaji Sadik ya tafi gun aikinsa cike da tunani akan shawarar da Auwalu ya ba shi. Zaune take a falo bisa kujera cikinta ya fara girma, yana daga cikin daki ya jiyo wayarsa na kara, da sauri ya fito ya nufi kan teburin da ke gaban kujera, a daidai lokacin da Mero ke shirin sanya hannu ta dauka ne ya ture hannunta da sauri ya dauke wayarsa, yana ganin sunan da ke 79 a AWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA СЕ- 2 jikin wayar ne ya danna ya hau amsa wayar. Cike da zumudi yake fadin "Hello ai ina nan tafe insha Allah yanzu nake shirin fitowa daga gida Insha Allah." Kashe wayar ya yi ya nufi cikin daki ya sanyo wata hadaddiyar shadda sai kyalli take yi da daukar ido, takalminsa da hularsa har agogonsa kalar zaren da aka dinka shaddar ne, sai tashin kamshi yake yi. Tana nan zaune ya zo ya wuce, ta taho da sauri zata sha gabansa tana fadin. Malam ni fa bangane ba wai ina kake shirin zuwa ne haka? N a kula yanzu ka tsiri wani sabon salo na yin kwalliya ka fita da daddare sai sanda kaga dama sannan ka dawo." Bai san sanda dariya ta subuce masa ba ya ce "To sai me don kin gane hakan? 1 80 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE-2 Zamanki nake yi da zan zauna ba zan fita ba sai sanda kika bani izini? Kema da kike zamana ni ne na ajiye ki ba kya tambaya ta neman izini na idan zaki fita, ballantana ni da babu wanda ya. ajiyeni?" Wani irin takaici ne ya turnike ta don haka da sauri ta nufi bakin kofar ta babbake tana fadin "To wallahi nima ba zan zauna ni kadai ba, haka kawai 'yar jira ka maida ni.?" Dariya ya sake yi yace mata "Ai kuwa zaki yi jiran nan domin dama da shi aka sanki, banda abinki Mero ai mace ta zaman gida ce dama." Bai jira amsarta ba ya sanya hannu ya janyeta daga jikin kofar ya hadeta da jikinsa ya sumbaçe ta cikin kunnenta ya ce mata "Sai na dawo kinji ki kula da kanki." Ya bude kofar ya fice sannan ya rufe mata kofar. 81 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СE 2 Ita kuwa durkusawa kawai ta yi anan tana faman zubda hawaye domin da alamun harsashenta na nemman tabbatuwa ya zama gaskiya. A kofar gidansu ya yi parking ya kirawota a waya bayan 'yan mintuna ta fito cike da yauki take takawa kamar ba zata taka kasa ba, tana matukar burgeshi da daukar hankalinsa domin ta iya kwalliya matuka, kuma kwalliyar na daukar jikinta komi na ta das-das tamkar a jikin nata aka kirkireshi. Da zazzakar muryarta ta yi masa barka da zuwa, tuni ta tafi da tunaninsa, firgigit ya yi ya amsa mata sannan ya bude motar ya fito. Idanuwansa kyar bisa kanta ya се mata "Komi naki birgeni yake Halima kullum kara kyau kike yi tamkar wata 'yar fulawa." AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Maganganunsa sun birgeta don haka ta yi dariya sannan ta ce, masa "Kai kuma fa gaka nan ka yi kyau kamar wani basarake amma baka ganin naka kyan sai na wani?" Gaba dayansu suka yi dariya, Alhaji Sadik ya nisa sannan yace mata "Kinga hukuncin Allah ko Sadiya? Karamar magana na neman zama babba." Sadiya ta yi dariya ta ce, masa "Wacce karamar maganar ce ke nema ta zama babba Alhaji?" Alhaji ya yi murmushi yace mata "Tamu mana ni da ke Sadiya, kamar yau muka haďu ga shi soyayya mai karfi na Kara kulluwa a tsakaninmu. Cike da yauki ta dago idanuwa ta dubeshi sannan ta ce, "Muka hadu kuma? Ai ni kawai ganinka na yi kazo zance gidan mu, mma ban san a ina ka sanni ba koma ka ganni." 83 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Dariya kawai yayi sannan yace "kin tuna wata ranar asabar da karfe biyar na la'asar kika je wani super market kika yi siyayya?" Jim ta yi alamar tana tunano lokacin, sannan daga baya tayyi dariya ta ce, "Haka ne na tuna, kana kufin anan ka taba ganina?" Alhaji Sadik ya gyada kai yace "Kwarai da gaske anan nayi tozali da wannan kyakkyawar fuskar sai kawai na ji kin tafi dukkan tunanina da hankalina, don haka sai kawai na saita motata na biyo adaidaita sahun da kika hau, har gidanku, sai da kika shiga cikin gidanku sannan na juya. Tun daga wannan rana na fara shirya ranar zuwa zance, gashi kuma cikin yardar Allah na samu karbuwa." Kanta na kasa ta yi dariya amma ba ta ce komi ba. AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Wata tambayar ya sake watso mata "Kin san wani abu kuwa Sadiya? Ta gyada kai ta ce, "A'a sai ka fadi." Murmushi ya yi sannan yace "Ni fa kinsan ana gani na a kofar gidansu yarinya to aure ne ya kawo ni, don haka tun yanzu ki fara shirin zama amarya, kuma ki fara sanarwa a gidanku. Cike da mamaki ta zaro idanuwa, amma bata iya cewa komi ba, shi kuwa gogan girgiza kai yayi alamar jaddada abin da ya fadı sannan yace mata "I da gaske nake, don ba zan bari ai min sakiyar da ba ruwa ba, kuma kinsan na sanar da ke ina da mata ko? Ko dai ba kya son mai mata ne ya yi miki tsufa?" Da sauri ta gyada kai ta ce, masa "A'a wallahi ai tun sanda ka gaya mini ma ni bani da wata damuwa a kai kowa ai da habarsa zai yi tagumi, ko Innata ma da na 85 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE-2 gaya mata cewa ta yi ita tafison hakan domin mai mata yafi rikon aure. Dariyar farin ciki ce ta subuce masa ya ce "Alhamdulillah haka nake sonki Sadiya, shi yasa nake jin kaunarki ta yi yawa cikin raina domin ina da yakinim zaki kawo mini farin ciki a rayuwata, wannan dalilin kuma ya sanya na ji ina Kaunar Innarki dari bisa dari." Dariya kawai ta yi ta sunkuyar da kai tana wasa da yatsunta, shi kuwa gogan bandir din kudi ya dauko har biyu ya mika mata yana fadin "Gashi ki kaiwa Inna daya, daya kuma na kine ki kara siyen kayan kwalliya don na dinga ganinta kullum kala kala a jikinki. Ta risina ta amsa tana godiya ya katseta da fadin

Chapter 3 of 5