Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 5
zumudi ya ce mata "zanyi miki kyakkyawan tanadi kuwa, bari na fita don kada na makara." 28 AWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE 2 Cikin yauki ta mike ta bi bayansa, ta raka shi har gurin mota, sai da ta ga tashinsa sannan ta dawo gida ta zauna a falo tana kallon talabijin. Karar kwankwasa kofa ta ji, don haka ta tabbatar tana da bako ta tashi da sauri ta bude, suka yi ido biyu da ita, cike da farin ciki suka rungume juna sannan suka nufi kujera suka zauna. Mero ce ta dubeta cike da murna ta cс, "Yar halak kin ki ambato yan zunnan na gama zancenki cikin raina har ina tunanin buga miki waya, ashe kina tafe.." Salama ta yi murmushi tana sake kallon hadadden lafiyayyen falon ranta na yi mata kuna, amma a zahiri babu alamu ta ce mata "Uhum ina tafe amarya kin san ba yanda za ayi yau ta wuce ban zo ba, na dai bari ne mai gidan ya fita kin san hirarmu ba za ta yi dadi ba idan yana nan." Da dariya Mero ta mike ta nufi firij tana fadin "Gaskiya ne kawata ba sakewa kam." 29 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Salama ta bita da kalloo ranta ya biya matuka da matsayin da ya kai Mero, ta hadiyi yawu mukut mai hade da takaici sannan ta dake. Mero ta dauko lemon kwali da kofi ta kawo ta ajiye bisa teburin da ke gaban kujerun ta bude ta zuba mata sannan ta fuskanceta ta ce mata "Ga lemo nan ki sanyaya makoshinki don na ga kamar yau ana zafi-zafi." Salama ta gyada kai ta ce "Nagode amarya, kinsha kamshi ina angon naki?" ta watso mata tambayar daidai lokacin da take kurbar ruwan lemon. Mero ta yi dariya ta amsa mata "Ango yana nan sumul ya fita gurin aiki, wai ana sauke masa wasu kaya don haka dole ne ya je, ba don haka ba ma ai a gida zaki same shi." Cike da mamaki Salama ta dubeta ta cе mata "A gida kuma? A lallai ciniki ya fada kenan, na ga sai wani rawar kai kike yi wa mijin." 30 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE- 2 Mero ta kwabe baki ta cc mata "Haba dai wanne irin ciniki kuma? Ba sai anga'haja ciniki yake fadawa ba? Idan kuma ba a gani ba fa?" Mero ta yi dariya sannan ta ce mata "To kwana gida daya ai ba kwana daki ba ne, kamar yanda kike kwana a gidanki ni kuma na kwana a nan gidan to haka muka kwana a gida, dayan yana Katsina ina Daura." Dadi ne ya cika zuciyar Salama a rude ta ce mata "Allah da gaske kawata? Ta cc, "Wallahi." Da sauri ta rungumeyta suka yi shewa, tana fadin "Amma kin burgeni kawata haka nake sonki mai daukar shawara, lallai kina so ki yi daraja a gurin miji, ki sa ido ki gani kullum sai ya zamo mai dokinki domin abin da baka samunsa ko yaushc ka fi marmarinsa." Mero ta yi dariya suka sake tafawa, ta ce mata "Ai kuwa baki ga yanda ya rude ba, amma dai yau nayi masa alkawarin zan bashi mamaki." 31 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 Salama ta yi dariya ta ce mata "To ai sai bada himmar bayar da mamakin, ni ai na fi son kullum ki bashi mamakin kinji kawata." Suka sake yin dariya suka tafa suka ci gaba da tattaunawarsu da hira irin ta aminai har yamma sannan Mero ta yi shirin tafiya. Bayan sunyi Sallama Mero ta juyo zuwa gidan ta sake kiranta ta ce mata "Kar fa ki manta ki bada mamakin nan kamar yanda kika yi alkawari. Dariya suka yi gaba dayansu Mero ta cc "Kar ki damu kawata zaki sha labarin yanda ta kasance, cike da jin dadi suka yi sallama suna kewar juna, ta nufii gidansu, ita kuma ta koma cikin gidanta ta kulle. Wata irin hadaddiyar kwalliya taci cikin riga da siket da suka fiddo da surarta sukai mata kyau ga wani kamshi mai daukar hankali na tashi daga cikin jikinta, fuskarta ta yi kyau matuka, ta kama gashin kanta ta matse shi da rubon ta saki sauran a baya. Tana zaune a falo tana kallon Tibi ya shigo ya taddata, da sauri ta mike tana yi 32 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 masa barka da zuwa ta amshi ledójin da ke rike a hannunsa ta nufi kan teburin abinci da su, Kamshinta ya doki hancinsa ya bita da kallo wani dadi ne da farin ciki suka mamayeshi, cike da kulawa ya sake dubanta suka yi dio biyu cikin tausasa murya ya се mata "Amarya kinsha kamshi, irin wannan kwalliya haka mai daukar hankali, ga kamshi na ta shi ta ko ina, gaskiya kin matukar faranta mini zuciyata." Wani dadi ta ji cikin ranta domin yabon da ya yi mata, ta saki murmushin jin dadi ta ce masa "Ai duka nayi ne domin na faranta maka maigidana."" Maganar tata ta matukar bashi mamaki don haka cikin mamakin ya bude baki ya ce mata "Masha Allah ko yanzu na fara ganin kadan daga mamakin da kika yi alkawarin zaki bani." Dariya kawai ta yi ta sunkuyar da kai, shi kuwa gogan idanuwansa na kan ta da alamaun yana raya wani abu cikin ransa. 33 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 Dakinsa ya wuce yana fadin "Bari 'na na je na watsa ruwa na yi sallah sai na zo muci abincin ko?" Bai tsaya ya saurari me zata ce ba kawai ya wuce cikin dakin ya cire kayansa ya nufi bandaki ya fara wanka. Sanda ta shiga fakin tuni har yayi nisa a fara wankansa don haka ta bude durowa ta zabo masa wata sassaukar jallabiya ta dauko turare ta feshe masa ita da shi, nan take dakin dukkansu ya hau wani kamshi mai daukar hankali. Sai da ya kammala sannan ya fito ya taddata zaune bisa bakin gadon tana tsumayin fitowarsa, hakan ba karamin dadi yayi masa ba, don haka cike da fara'a a fuskarsa ya dubeta da kulawa ya ce mata "Allah yayi miki albarka Maryama kina ji dani matuka, irin wannan kulawa haka?" Dariya kawai ta yi sannan ta dauko jallabiyyar ta mika masa, karba kawai yayi ya sanya bai iya cewa komi ba domin ta kai matuka a bashi mamaki, kai tsaye bai tsaya 34 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 6ata lokaci ba ya hau bisa abin sallah ya tada sallah. Tare suka fito daga dakin kowannc a cikinsu fuskarsa cike da walwala da farin ciki, kai tsayc kan teburin abinci suka wucc. Farfesun kayan ciki ne da miyar Kaza da kuma shinkafa da taliya sai hadadden salat da kabeji. Tana budewa kamshi ya doki hancinsa, nan take yawunsa ya tsinke sai da ta gama zuba masa ta mika masa sannan ta zubawa kanta. Loma daya kawai yayi ya hau santi, ita kuwa sai dariya take ta yi masa, sai suka kammala cin abincin sannan ya umarceta da ta bude ledojin nan ta kwashe kayan ciki ta saka firij. Ba tare da musu ba ta bi umarninsa, kayan marmari ne irinsu Apple da Ayaba da Lemo da Abarba da sauransu. A falo ya taddata don haka yace mata "Bari naje waje na siyo katin waya, sabida ba 35 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 kudi a wayata kuma kin san bana son kwana ba kudi a waya saboda dare." Ta yi murmushi ta ce masa "To sai ka dawo, Allah ya tsare." Ya amsa da "Amin." Ya fice. Ita kuwa tunda ya fita maganganun ke dawo mata cikin kwanyarta musamman gargadinta na karshe don haka da sauri ta mike ta nufi cikin dakinta ta kulle kofar ta cire mukullin. Tana jin shigowarsa amma ko da wasa ba ta gwada fitowa ba, ya hau duba ko ina bai ganta ba sai kawai ya samu guri ua zauna abinsa yana jiran ya ga ta inda zata fito. Yana,nan zaune har ya gaji da jira don haka ya tashi ya nufi dakin yana kwala mata kira, ko motsinta bai ji ba don haka ya murda kofar dakin zai shiga ya ga ko me ke faruwa, ga mamakinsa kofar ba zata budu ba, domin an kulleta da mukulli, ya sake murda kofar jaro na biyu amma sam taki buduwa sai kawai ya buga kofar dakin cike da takaici da 36 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 kunar rai amma har yanzu dai shiru babu ko motsi. Wata zuciyar ce ta bashi shawarar ya lcka ta taga, don haka kai tsaye ya nufi tagar yana fadin "Mero! Mero!! Ki bude mini dakin mana na dawo fa, idan wasa kikeyi don Allah ki daina, ki bude mini, ki tuna fa alkawarin da kika yi min na yau ya dace ki zamo mai cika alkawari a matsayinki na cikakkiyar musulma musamman akan mijinki." Cike da kasala ya karasa maganar. Ga mamakinsa sai kawai ta zo ta saki labulen tagar ta zuge glass din tagar ta ciki. Wani irin mamaki ne ya cikashi don haka kawai, ya saki baki yana kallon tagar cike da takaici idanuwansa sun kada sunyi jawur tamkar zai zubda hawaye sabida takaici. Bai iya yin wani cikakken motsi ba illa wuccwa da ya yi cikin dakinsa sam babu sauran kwari a jikinsa tamkar wani dan giya san tangadı yake yi. 37 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE-2 Yana isa kan gado ya fada a kai tamkar bugagge, idanuwansa sunyi jawur kamar garwashi, silin din dakin kawai ya zubawa idanuwa, wata kwallah mai matukar zafi ta fito daga cikin idanuwansa, haka nan ya yi ta juyi bisa gado tamkar wanda ya shekara yana bacci, hakika ba don bacci karfinsa ya kai karfi ba da bai isa ya daukeshi ba amma a hakan ya fi karfinsa ya yi awon gaba dashi. **** Washegari bai ko saurari tashunta ba domin izuwa yanzu baya kaunar ganinta ma domin ganin nata kara yi masa fami yake yi kan bakin cikin da take kunsa masa don haka ya fice da wuri ya bar mata gidan. A restaurant ya tsaya ya karya sannan ya wuce ofishinsa duk da yau akwai saukin aiki amma yafi bukatar ya kasance aofishin nasa don yafi sámun saukin bacin rai fiye da gidansa. TE 38 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Sai yamma sannan ya fito daga ofishin kai tsaye ya saita motarsa zuwa majalisar da sukan zauna da abokansa don yin hira. Suna zaune a majalisar suna karta, ya iso ya same su. A gefe ya ajiye motar sannan ya nufi inda suke aiune ya yi musu sallama, Auwalu na zaune cikinsu suka dakata da kartar suka amsa masa cike da zolaya suna fadin "Ango ka sha kamshi, shi kenan kuma sai ka bace ko gaisuwar babu?" Dariyar yake yayi ya amsa musu da cewa "To so kuke yi na dawo ina zama a cikinku bayan ni Allah ya suturtamin. Zaman majalisa ai sai mai kwanan zaure." Gaba daya suka yi dariya, Auwalu ne yace "Mu ma dai mun kusa yin auren nan a dainyi mana gori. Sadik ne ya katseshi da fadin "Kai cakwaikwaiwa gurinka fa nazo kar ka dameni da surutu, taso muje akwai maganar da zamuyi da kai." Ba tare da ya ce komai ba ya ajiye kartar yana murmushi ya bi bayansa sai da 39 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 suka je har jikin motarsa suka jingina da motar suka fuskanci juna. Auwalu ya dubeshi yace masa "Ya akai ne ango dafatan dai alheri ne ya same mu mai tarin yawa." Fuskarsa ba yabo ba fallasa ya amsa masa "To lafiyar kenan, Auwalu ka san irin yarinyar da ka hadani da ita kuwa? Gabansa ya fadi cike da rudewa ya yi saurin tambayarsa "Kamar yaya Sadik har ka sanya gabana ya fadi, me ya faru Sadik daga yin aure yau kwana biyu?" Cike da damuwa ya bashi amsar "meye ma bai faru ba Auwalu?yarinyar nan ta maidani tamkar wani dan aiken gidanta amfanina a gurinta kawai na fita na nemoo sannan kuma nai mata bauta na kawo mata taci ta sha ta zauna cikin ni'ima, amma ni idan dare ya yi sai ta rufe mini kofa ta barni na kwana a falo? Tamkar wanii baran gida, ina cikin damuwa matuka Auwalu. Innalillahi wa innah ilaihirraji'un ya fara amfata sannan yaci gaba "Alhaji bani da 40 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE2 maasaniya akan wannan halayyar tata, domin wallahi ni na sani iyayenta mutanen ne, kuma sunyi mattarbiyya, ban san kuma a inda ta samo wannan mummunan dabi'ar ba." Sadik ya yi ajiyar zuciya sannan yace "Wannan shine abin da na dinga jin tsoro da yin aure shiyasa na baka wuka da nama don ka samar mini mace ta gari, gashi nan ina neman yin gudun gara zai haikewa zago. Auwalu ya ja dogon numfashi sannan yace"Hakane amma inaso ka kwantar da hankalinka abokina, wannan ba zai taba zama matsala ba Insha Allah matso kaji yanda zaka yi duk ka magance wannan matsalar, in tasan wata ai bata san wata ba." Ya matsa kusa da shi ya yi masa rada a kunne, yana gamawa suka dubi juna suka yi dariya, cike da fara'a Sadik yace masa "Allah abokina haka za ayi. Auwalu yayi dariya yace masa "Wallai kuwa abokina kaje kaa gwada ka gani lokacі daya zaka yi maganin iskancinta da ka sameta 41 1 S t i n in fa AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE lokaci daya kuwa ka gama da ita karyarta ta gama karewa, sai kazo ka bani labari." Alhaji Sadik cikin fara'a yace masa "To kai shiru da bakinka kawai, bari naje na kammala abubuwan da ke gabana don na koma gidan akan kari." Bai saurari amsar sa ba yayi saurin bude motar ya shiga ya tadata, Auwalu na yi masa sallama, shi kuwa daga masa hannu kawai ya yi ya wuce ya barshi a nan tsaye. Kamar yanda ta saba tarbarshi kullum yau din ma hakan ta yi masa sannu da zuwanta kawai ya amsa, sannan kai tsaye ya wuce dakinn barcinsu, sai da ya kammala komi a dakin sannan ya sanya rigar bacci marar nauyi. Sam babu walwala a fuskarsa, bisa bakin gado ya zauna, ya dubi Mero yace mata "Ki zubo min Kaza da kuma Lemo shikenan abin da nake bukata ci yau. Da sauri ta mike tana fadin "An gama ranka ya dade. Ya dubeta yace "Sai kacc 42 AWIYYA WADA ISA- YAR ALJANNA CE gaskc da a gaban wani nc sai yace ai biyayya kike yi mini sau da kafa." Kasa ce mata komi ta yi illa wucewa da ta yi ta nufi falo don cika umarninsa. Sai da ya kammala cin abincin sannan yatashiyacbshiga bandaki don wanke hannunsa da bakinsa. Ita kuwa sai ta kwashe kwanukan ta kaisu kitchen, sannan ta ta dawo dakinta sam babu kuzari a tare da ita. Tana ganinsa ya wuce kofar dakin tamkar fita zai yi, sai kawai taga ya janyo kofar dakin ya kulleta da mukulli, ya juyo da mukullin a hannunsa. Gabanta he ya fadimatukar faduwa dama ta kula akwai abin da yake shirya yi mata, shi kuwa ko kallonta bai yi ba, kan wata kujera kawai ya nufa ya zauna. sollel sgnil Ita kuwa can kuryar gado ta nufa ta kwanta jikinta a kankamė ta tákure, kallonta kawai yayi dariya ta subuce masa amma -bai bari ta bayyana ba. a sur A 43 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE- 2 Sai da ya dan dauki lokaci sannan ya taso ya nufi inda take yana fadin "Mero kenan yau dabarar taki ta kare kenan? Bata iya ce masa komi ba illa sakc takurcwa da ta yi ta kankame jikinta, sannan ta janyo bargon da ke kusa da ita ta sake Kudunduncwa ciki, bai san sanda dariya ta subuce masa ba. A bakin gadon ya zauna yana shirin yin magana ta ce, masa "Ka fita ka bani guri Alhaji, wai shin ma me kake nema a gurina ne da har kake mini wannan bibiyar?" Dariyar mugunta ya saki sannan ya matsa inda take yana fadin "Mero kenan, to ke da kina zaton na aureki ne kawai tamkar wata flawa abar ado da zan jerata a gidana na dinga kallonta kawai don ta kawata mini gidan?" A hankali ya fara janye abin da ta rufa da shi, yana sake matsawa kusa da ita, ita kuma tana sake ja da bayaa, da haka dai har ya cimma burinsa a kanta tukunna ya kyalcta, 44 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 P tun tana hawaye har ma ta nemi hawayen ta rasa. A haka Mero ta kwana cikin takaici. Shi kuwa gogan ko ajikinsa domin sautin munsharinsa kawai take ji yana fita daidai da alamun baccin na matukar yi masa dadi, tamkar ta dookeshi haka take ji cikin ranta musamman ita da baccin ya kaurace mata. Washegari Alhaji Sadik ya tashi cikin walwala da jin dadi, kai tsaye bandaki ya wuce ya yi wanka, sannan ya fito. Ita kuwa Mero ta kasa ko da motsi sai faman zubda hawaye take yi. Bai ko kula da kukanta ba illa shiryawa da yaci gaba da yi, sai da ua kammala shirinsa tsaf sannan tukunna ya koma ga Mero, cike da walwala ya dubeta ya ajiye ambulan a gabanta yace mata "Wannan kyautarki се Mero ta kasancewarki kamilalliyar mace, nagode Allah ya bamu zuriya dayyiba." Wani irin takaicii ne ya turnuko mata cikin zuciyarta, da sauri ta wurgo ambulan zin cike da kunar rai, kukanta ya karu tana fadin 45 AWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE 2 "Dauke tsiyarka bana so me zaka gaya mini bayan ka riga ka 6ata mini tsarin rayuwata." Har ya nufi hanyar fita dariyata suбисе masa ya juyo ya kalleta yana fadin "Mero kenan, to ke da wai a gidanku ba a sanar dake menene aurc ba ne? To idan baki sani ba 99 wannan shine aure. Yana gama fadin haka ya juya ya ficc ya barta a nan. Takaicinta ya sake karuwa, ta yi kwafa, sannan cikin muryar takaici t ace, "Ba komai in kasan wata ai baka san wata ba. Shi kuwa Alhaji Habu kai tsaye motarsa ya nufa, daga kallon fuskarsa kasan ya koshi da farin ciki, har wani kuzari yake ji na musamman, ya bude kofar motar ya shiga ya tada ta cike da kuzari ya fice daga gidan. Wayarsa ce ta fara ringin dan haka ya dauko ya duba fuskar wayar murmushi yayi ya danna gurin amsawa ya sanya a kunnensa ya ce "Abokina an tashi lafiya?" uwat riuse ebstisAicus nikic 46 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 "Lafiya kalau abokina, ya nakc jin karar tafiya kamar kana hanya wai kana nufiin har ka fito ne?" Alhaji Sadik yayi dariya yace "Na fito mana abokina, ai kasan lokacin fita ta ya yi, musamman kuma yau wata babbar ran ace a gareni domin ina cikin walwla da nishadi. Auwalu ya yi dariya ya ce masa "To fa! Abokina ko dai an dace ne? Alhaji Sadik ya sake yin dariya yace massa "Tun yaushe ma abokina, ai wannan tarihin ya wuce sai dai wani kuma sabo kai dai kawai sai mun hadu abokina." Dadi ya cika Auwalu yace "To ai ni abokina na fika murna. Allah yasa daga yau damuwa ta kare." Sadik ya amsa da "Amin abokina' sai anjima kasan bana son ina tuki ina waya. Suka yi sallama suka ajiye wayar. Kai tsaye gidansu ya wuce domin gaishe da Hajiyarsa. Zaune ya taddata a falo tana kallo, ya shigo da sallama, cike da fara'a ta amsa masa, 47 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CЕ-2 ya risuna ya gaisheta sannan ya zauna a kujerar da ke fuskar tata. Cike da kulawa ta sake duban dan nata ta cc masa "Dafatan dai kuna lafiya ba wata matsala?" Shima cike da fara'a ya amsa mata "Lafiya kalau muke Hajiya. Cike da gamsuwa ta amsa sannan ta ci gaba da cewa "To dama inaso na gargadeka, ka rike matarka da kyau, kada ka yarda a zigaka akan matarka, mutane yanzu ba so suke Allah ya rufa maka asiri ba, dole kuma sai hada da hakuri, domin yarinya ce, shi 99 kuma dama aure rabinsa hakuri ne. Gyada kansa kawai yayi ya ce mata "Insha Allahu zan kiyaye Hajiya. Hannunsa ya sanya a aljihu ya dauko kudi ya mika mata sannan ya mike ya yi mata sallama. Cike da jin dadi ta amsa tana yi masa fatan alheri da addu'ar Allah ya sake tsareshi yayi masa albarka. 48 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE-2 Ya amsa da amin sannan ya fice ya nufi gurin aikinsa. Ko a can gurin aikin yau kowa ya fahimci Alhaji yana cikin walwala matuka, har rabon kudı ya yiwa kananan ma'aikatansa. A bangaren Mero kuwa said a ta ji ciwon jiki ya ishcta sannan ta tashi ta lallaба ta nufi bandaki, sai da ta samu ruwa mai dumi ta gasa jikinta da shi sosai sannan ta dan ji dama dama, bayan ta idar da sallah ne kuma ta hada shayi mai dumi sannan ta hada da maganin ciwon jiki da paracetamol ta sha, duk wannan abin da take yi kuma cikin ranta tana jin takaicin abin da ya faru da itane, musamman idan ta tuna da hudubar Salama. Wata zuciyar ce ta dinga zigata akan ta duba ambulan din da Alhaji ya bata, don haka ta dauko ta buda dan taga menene a ciki?. Da mamakinta sarka ce ta gwal dankareriya kirar dubai 'yar kwance, wata irin kara ta yi sabida murna da farin ciki, domin a rayuwarta tana matukar kaunar sarkar gwal musamman kirar dubai, don haka 49 AWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE-2 ta yi ta murna tana gwada sarkar, tuni ma ta riga ta manta da wani ciwon jiki ko wani 6acin raid a Aliyun ya haddasa mata. A gajiye tikis ya dawo daga gurin aiki, don haka kawai bisa kujera ya fada sabida tsabar gajiya, tsawon lokaci bai ji ko motsin Mero ba don haka ya hau kwala mata kira. Bata ko amsa ba illa fitowa da ta yi tana faman dacin rai, a gabansa ta tsaya kerere babu ko risinawa. Dubanta kawai ya yi tana faman girgiza tana bata rai ta ce masa "Wai ba kiji shigowata ba ne Mero? Na dawo a gajiye memakon ki zo ki tarbeni sai kuma ki zamanki a daki?" Kwabe baki ta yi tana faman girgiza tana bata rai ta ce masa "Shi kenan dama dalilin da yasa ka kira ni? Ka katse mini hutun da nake cikin daki na? to idan na ji shigowar ta ka sai kuma me? Me zan maka?" 50 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE- 2 Da mamaki ya sake dubanta ransa na yi masa kuna ya ce mata "Bangane sai me ba? A matsayina na mijinki ba zaki zo ki bani hakkina ba, ki bani ruwa da abincin da zanci, sai kawai ki kyaleni, kuma na yi magana kice wai sai me?" Kada kai ta yi ta ce masa "Ruwa da abinci?" Tabdijan, ni wallahi ban girka ba, ai abin sai yai min yawa, ni komi nice zan maka sai kace wata baiwarka? Kuma ai kaine ka zabi abin da ka fi so a tare dani, tunda ka samu ai sai ka nemi mai tarairayarka in ka dawo da kuma dafa maka abinci ko? Ammaba dai ni ba." Tuni zuciyarsa ta ciko da takaici da kunar rai, cikin bacin rai yace mata "Haka kika ce ko Mero?" Juyawa kawai ta yi ta girgiza jiki tana fadin "Zancen kakeso, ni ka ga tafiyata, in zaka nemi mai dafa maka abinci ka nema domin ni abin ya min yawa. Tana kaiwa nan zata shige daki shi kuwa dafe kai yayi kawai cike da takaici ya bi 51 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 ta da kallo, ya ma rasa me zai ce mata, bai sakc bi ta kanta ba illa dauko Kazar da ya shigo da ita da kayan marmari ya sanya su a gaba yana ci tamkar magani sanbida tsabar yunwar da yake ji, ga kuma takaici da ya cunkushc masa zuciya. Washegari haka ya fita babu ko sauraron tsayawa karyawa domin 'yar mulkin tasa bata ma ko tashi ba balle ya saka rai, kuma ko ta tashi ma yasan ba zata damu da bashi abin da zai karya din ba, don haka ya yi wanka kawaiya shirya ya fice. Ita kuwa Mero sai da ta yi baccinta mai isarta sannan ta tashhi ta yi wanka ta shirya tsaf, ta hada lafiyayyen shayinta hade da soyayyen dankali da kwai, da kuma farfesun kayan ciki ta zauna ta cika cikinta tsaf, sannan ta hau bisa kan doguwar kujera ta kwanta tana kallon Tibi. Wayarta ta hau kara alamar kira ya shigo, ta yi sauri dubawa, sunan Salama ne akai don haka da sauri ta dauka cike da fara'a ta ce "Salama kawata ya kike? 52 AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 Salama ta amsa da cewa "Lafiya kalau nake kawata, gani nan zuwa gidanki daga nan zan wuce kasuwa? Da sauri ta amsa mata "To sai kin zo ina sauraronki dama wallahi kewa ta ishcni ta zama ni kadai babu abokin hira." Dariya Salama ta yi ta ce mata "Gani nan zuwa kawata na debe miki kewar, suka yi dariya suka ajiye wayar. Bayan mintina kadan Salama ta bayyana a gidan Mero, kar kaso kaga murnar da ta yi da zuwanta, nan take ta baibayeta da kayan ci da sha iri-iri." Sunyi hira mai dan tsawo, sannan Salama ta ce mata "Dama ina sha'awar zuwa kasuwar nan kawai don nayi kallo idan naga abin saye kuma na siya zama guri daya ya isheni wallahi." Salama ta yi dariya sannan ta ce "To ki zo mu wuce mana Mero menene a ciki? Ni fa da kike ganina wallahi banga abin da zai takura mini ya hanani yin abin da nake so ba." AWIYXA WADA ISA, TAR ALIANNASENа Mero ta zaro idanuwa cike d tsoro ta e mataA Salama ban Sanaida maigidana ba, kinga kuwa banda damar fitaES Salama ta kwaße baki tosaiki yi ta zama ai ki zama daddawar daka mai doyini kam banga namijin da zai tsareni a gida shi yà dinga fita harkokinsa ba haka kawai wai da sunan aure Tabdijan.Podob sn siswsl swuS SN Mero ta gyada kai taceWallahi Salama aure yana da takurawa, yanzu da dane mayafina kawai zan dauka mu zaga duk inda muke so ba fargaba balle tunani, amma yanzu wai idan zaka fita ma sai ka nemi izinin wani wannan abu yana kona mini rai ivnu2 Salama ta yi Isaki ta . Ni dadina dake rashin ganewanewakitaso kiedauko mayafinki, mu wuce kila ma har ma dawo k ma huta a gidanki bai san kin fita ba, in kuma kinga kina jin tsoro ne to sai kiyi ta zama ki rube a cikin gida ni kinga lafiyata.orw um os Mero na ganin haka sai ta mike tana fadin "Bari na dauko mayafina sai mu tafi. Da sauri ta nufi cikin dakinta."р ог эрн 54- AWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CЕ 2 Nan fa Salama ta faki ido ta hau dagedagen matasan kujera a zatonta ko zata yi arba da kudi, ai kuwa sai ta yi ido hudu da yarin gwal, da sauri ta dauke ta jefa a jaka ta hau gyaran matasan kujerar. A daidai wannan lokacin ne Mero ta fito daga dakinta da mayafi bisa kanta ta sakale jaka a kafadarta, da sauri ta hau daga matasan kujerar tana neman yarinta na gwal wanda ta cire da zata kwanta a kan kujerar don kar ya dameta, yanzu kuwa za ta saka ta fita. Salama ta yi kamar bata san me take nema ba, ta ce mata "Mu tafi ko Mero kinsan fa baki da isasshen lokaci." Mero tana ci gaba da duba ta ce, mata "Yarina na gwal na cire na sanya karkashin kujerar nan shi nake nemma na sanya sai mu tafi. Salama ta bude baki da mamaki ta ce, mata "Yari kuma? Kema banda abinki ai nan ba wajen ajiye yari ba ne, yanzu haka

Chapter 2 of 5