Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
"Na barki ki yi nazari sosai, Allah ya kara sauki." Ya juya yana shirin fita ta budc idanuwanta tar tana kallonshi, ta ce "Ba wani nazarin da zani yi ka bar maganar ba ni so." Ya yi murmushi ya dubec ta cikin ido sai ta ji nauyinshi ta sarda kai ya ce "Ban yi maki musu ba, sai dai abu guda ne zaya sanya in iya hakuri dake, idan da kin ce mani kina da aure ko kuma wanda na ganku tare saurayinki ne, to gaskiya sai in yi hakuri, saboda na ga ya damu dake yana nuna kulawarshi sosai, to kin ce yayanki ne, kinga zancen in bar ma wani ke ma bai taso ba, don haka ki kwantar da hankalinki, idan kika fahimce ni za ki nine mijin da ki ke jira, Allah ya bamu alkairi." Bai jira ya ji ta bakinta ba, ya sanya kai ya fita, Naja'atu ta rumtse ido tana mamakin wannan wane irin mutum ne Allah ya hada ta dashi.?" Daga ganin sarkin fawa shi kenan sai miya ta yi zaki.?" 60 To amma wani abun mamaki sai ta samu zuciyarta da karkata wajen sha'awar wasu abubuwa da ta fahimta a tare dashi, kai gaba ki daya ma sai ta ji tana ra'ayinshi, muryarshi mai taushi tsab-tsab da shi. A hankali ta rufe fwayar idonta tana kallonshi yana yì mata murmushi, sai ta saukar da ajiyar zuciya bata san me zata kira wannan al'amarin ba, amma a bangare daya kuma sai kaunar Daddy ta rinka neman fizgarta har tana jin ba zata iya amsa tayin Likitan ba. Daddy ya murda kofar ya shigo, Ibrahim yana biye da shi sai Hajiya, Ga ba ki daya suka shigo suna yi mata sannu Hajiya ta kalli farin ruwan ya yi nisa sosai, don hala suna sanya ran cewa zasu tafi gida a ranar. Nan suka zauna ana ta jinya Ibrahim ya cc ma ta ga wayarta nan ya taho da ita Mas'ud yana ta kira, amma ya sanar da shì tana asibiti." Hajiya ta ce, "Ka kira shì sai ka bata su gaisa, kada hankalinsu ya tashi gashi ta samu sauki. Don haka Ibrahim ya kira sannan ya bata suka gaisa da Masud, ta sanar dashi zazzabi ne kawai, amma ta samu sauki, karin ruwa ne aka yi mata da zaran ya kare kuma zasu tafi gida." Ya cc., "To Allah ya kara sauki, Inna na gaida ki." Ta cc. "Ina amsawa, ka gaida su duka har da Baba." Ta yi sallama ta rufe wayar. Babu laifi ta dan samu sauki, suna magana da Ibrahim, Hajiya na zaune gefe daya shi kuma Daddy wayarshi ta yi kira, don haka ya bude dakin ya fita tasan mutuniyar ce ta yi kira, ya cika damuwa da wannan Faridar, sai ka ee ta asirve whi. Suna nan zaune har ruwan ya Rarc, don haika Doiddy ya fita ya kirawo Nas din tazo ta cire ya сc. "Ta je ta nemo Likita ya sallame su" Amana sai Nas cin ta ce "Likita ya (tafi, Ruma yaoc kada a sallame ta sai da safc." Naja'atu ta kalle ta da sauri, to sai dai ta san manufarshi, don kada ta taftne hai samu abin da yake so ba to ko kwanan tayi ha abin da zaya samu zaya gaji da fwafwarshi ya rabu da ita. Ta maida kanta ta kwantas yayin da su Hajiya ke ta korafin don mi zaya ce sai da safc alhalin gashi ta smau sauki kuma da kanshi ya ce ba zata kwana Hajiya ta kalle ta ta cc. "Yanzu yaya za'ayi kenan?" Daddy ya yi sauri ya ce. "Rabu da shi kawai Hajiya, tafiyarmu zamu yi tunda gashi ta samu sauki." Hajiya ta oc. "Ba'a haka Daddy, idan mun tafi yanzu wani abun ya sake tasowa kana ganin zasu saurare mu?" Ya ce "Ga asibiti da yawa a gari, sai mu camza wani" Naja'atu ta coc. "Babu komi mummy ku tafi zani kwanan da safe sai a dawo a dauke ni Hajiya ta cc, "Yaya za'a barki ke daya a asibiti Ta cc, "Ga Nurses dim su nan, suna kulawa sosai, Allah kuwa babu komi." Hajiya duk tabi ta dmau, ta cc ""Sai dai nì in tsaya mu kwana tarc." Ta cc, "Yaya za'ayi ki kwana nan Mummu? Ke ma fa har yanzu ba ki ida warwarcwa ba, Allah babu wani abu. Hajiya ta jima tana kallonta, sai kuma ta jinjina kzi ta oc, "To tashi kici abinci, gaya nan." Naja'atu ta tashi zaunc, yayin da Hajiyar ta zubo mata abincin ta bata tana ci, su duka suna nuna kulawarsu gare ta. Daddy ya fita ya kira wata Nas da zata kwana ya сс, "Don Allah ta rinka kula da Naja'atun." Ta cc, "Babu damuwa, insha Allahu zata kula." Ita kuma Naja'atun ya rinka bata hakuri, gani yake yi kamar sun yi mata ba daidai ba, to sai dai matsalar maza ba su jinyar mata, da ya tsaya tarc da ita, tunda babu macen da zata zauna da ita, Zainab ce tana makaranta, amma cikin satin suke sanya ran zuwanta. Naja'atu ta yi murmushi, tana kallonshi ta ce, "Allah kuwa babu komi Daddy, awa nawa ne." Shima ya zuba mata ido ya ce, "Kin tabbata.?" Sai ta yi dariya, tana kallon Hajiya, itama Hajiyar murmushi take yi, yanzu hankalinta ya kwanta, tunda taga Naja'atun bata damu ba." Karfe goma suka yi mata sallama suka tafi. Ta kwanta shiru, duk sai ta ji ta dan takura, ta lalubo wayarta, ta bude sai ta kunna kira'a, da ta dauka ta aje wayar gefe daya tana bi a hankali zuciyarta ta samu nutsuwa tana tunanin kamalan Likita da abin da ya yi mata, kome yake nufi.?" Karatun ya tsaya yayin da kira ya shigo, ta lalubo wayar tana kallo, sunan Daddy ne faro-6aro bata yi mamaki ba, kila Ibrahim ne ya sanya mata lambarshi, ta Glo, to amma shi ina ya samu lambar?" Ta danna wayar ta amsa mashi da sallama ta ce, "Har kun isa gida.?" Har ma na yi wanka na kwanta amma sai na kasa barci ina tunanin wane hali kike, baki takura ba ko.?" Ta ce, "Eh." ya ce "ko dai in zo in 63 dauke ki yanzu.?" Ta yi murmushi a hankali, ta ce kada ka samu damu, zani kula sosai, sai da safc." Ya cc, "kora ta kike yi kuma?" Ta ce, "Ba haka ba ne, naga dare ya yi sosai, ya dace ka kwanta saboda tafiya ofis da safc." Daga in da yake ya lumshe ido, muryar nayi mashi dadi, tana cikin abubuwan da yake so a tarc da ita. Ya yi murmushi ya cc, "kin san wani abu.?" Ta yi shiru tana saurarenshi, ya ce "Ni kuma nafi jin dadin wannan hirar da muke yi akan barcin da zani yi, yanzu haka kwance nake amma na kasa yin barcin, tuninki ya hana ni zama lafiya, gani nake kamar kina nan cikin damuwa, da kamar namiji na jinyar mace, wallahi ba zani barki ki kwana ke daya ba cikin asibiti." Naja'atu ita daya cikin daki, mamaki ya cikata, "Me ke damun Daddy yau? Kalamanshi sun fara zarta hankali." A bangaren shi ya yi shiru yana sauraren ya ji abin da zata fada, shiru ba ta ce komi ba, ya yi gyaran murya ya ce, "Naja'atu kina jina kuwa.?" Ta ce, "Ina saurarenka." Ya ce, "To yaya baki ce komi ba.?" Та сс, "To me zani ce maka? Na lura yau hirar ka ke ji, me zaya hana ka kira Farida kuyi." Yana saurarenta ya yi shiru, to sai dai shima da ya yi nazarin kalaman da ya. fada, sai yaga ba shi da hujjar fadi mata haka, to sai dai abin da zuciyarshi ta kudurta kenan, me yiwuwa wani sirri ne na daban a cikin zuciyarshi, yake neman bayyana kanshi." Sai yaga kamar bai kyauta ba, amma kuwa a wani 6angaren bai yi nadamar maganarshi ba, saboda kullum rana kima da martabar Naja'atu karuwa 64 yake yi cikin zuciyarshi, wani lokacin idan yana tunaninta sai yaga matsayinta yana neman kai wani matakin da shi kanshi bai san yarda akai haka take neman faruwa ba. Muryar Naja'atu tadawo dashi, in da ta ce, "Daddy ka aje ne, na ji shiru.?" Ya yi murmushi yana shafa kai, ya ce "Shi kenan bari in barki ki huta, na ji kin fara korata kada ki kai ga rufe wayar." Ta ce, "lah! Ni fa ba korarka nake yi ba, kayi hakuri idan kuma kana ganin mu ci gaba da hirar to bissimillah, ba matsala, ni dai gani nayi doguwar hira ta ma'abota soyayya ce, don haka na cc ka nemi Farida." Ya cc, "kina son ki fadi mani ke ba ki soyayya?" Ta cem "Ban ce ba, sai dai komi lokaci ne, idan yazo zani yi." Daddy ya rinka kyalkyatar dariya ya ce, "Ashe mu zuba ido zam,u ga takun soyayya.?" Ta ce, "Amma fa mai tsabta, ba wai ta rashin hankali ba." Ya ce, "Ashe har soyayya ke akwai ta rashin hankali.?" Та се,"Sosai ma." Ya ce "Kamar wace kenan.?" Ta ce, "Kasan kowa da irin yarda ya dauki soyayya, to ni abin da na dauke ta wani abu ce mai muhimmanci, da ta dace ayi ta da wanda ya cancanta, wai don mutum yazo ya ce yana sonka, ba shi ne so ba, sai ka natsu ka fahimci menene dalilin son da yake yi ma? Wadanne abubuwa ya duba har yazo ya сe yana sonka, haka nan menene manufar son da yake yi maka. A ra'ayina ba zani taba tsayawa in yi soyayya da wani ba, sai wanda ya cancanta kuma naji ina sonshi, na yaba da dabi'unshi da manufarshi a kaina, kuma 65 wanda nasan a Karshen soyayyarmu aure zamu yi mu yi rayuwa ta har abada Kaga wani zaya iya zuwa yа се. yana sona amma ba manufarshi ya aure ni ba, kawai don acc wance budurwarshi ce, ko kuma don ya saka ki cikin lissafin 'yanmatan da ya nema wani ma kai tsayc wani abu ya hango tare dake yazo kaga wannan ba so ba ne, don haka idan na ce maka yanzu ina soyayya nayi karya, saboda har yanzu ban samu wanda ya cancanta in yi ma irin son da kai kake magana ba." "Na Daddy ya saukar da ajiyar zuciya, ya ce, fahimce ki Naja'atu, kuma abubuwan da kika fada sune suka dace akasari ma'aurata su rinka dubawa kafin su yi aure, nima na karu da nasihar ki, idan kin dawo gida zani yi wata shawara dake, na gode, Allah ya bamu alkairi." Ya rufe wayar, ya aje gefe daya sai ya sanya hannu ya tallabe kanshi daga kwance yana kallon silin, tunani barkatai a ranshi. Can itama ta kwanta tana tunanin Daddy da kuma dangantakarshi da Farida, akwai abubuwa da dama da ya kama ta ya duba matsawar dai yana son suyi aure mai dorewa. A hankali tunaninta ya dawo kan Likitanta, "ko me ye sunanshi ma.?" Ta lumshe ido tana sauraren kalamanshi, amma data tuno yaudarar maza sai taji sam ta tsane shi, balle kuma ga jin zafin abin da ya yi mata na rike ta asibiti, sai ta share tunaninshi, a haka barci ya dauke ta. Da safe karfe bakwai da rabi, tana kwance Likitan ya shigo fuskarshi a sake yana murmushi, ya ce, "Good mornin my dear, yaya jikin? Naja'atu ta daure fuska 66 sosai, bai yi fushi ba yana kallon kwayar idonta, ya сс, "Ayya na yi laiti ko? Kiyi hakuri kada kiga laifina, na san idan ba haka na yi ba, idan kika tafi jiyan ba zani ji abin da nake so ba, daga gare ki, don haka na ba da umarnin kada a sallame ki so ki yi hakuri dani." Duk ya marairaicc yana kallonta, sai ta yi murmushi ta ce, "Amma kasan ba ka kyauta ba, jiba yarda ka janyo mani kwana cikin asibiti a takure." ya ce, "Na sani na yi laifi, amma kiyi hakuri yanzu zaki tafi gida, muje in kai ki da kaina don inga in da ki ke." Ta kalle shi da sauri, shima kallonta yake yi da salon yaudararshi, sai ta sauke kwayar idonta tana girgiza kai ta ce, "Gaskiya ba zani bika ko ina ba, za'a zo a tafi-dani yanzu." Daddy ya murda kofar ya shigo, idanuwanshi na kanta, sai kuma ya juya kan Likitan yana tuhumarshi, amma shi Likitan sai ya washe ya mika mashi hannu suka gaisa, ya na bashi hakuri kan rashin sallamar su jiyan. Daddy ya ce, "Ba damuwa, ta wuce gashi har garin ya waye." Ya dubi Naja'atun, yayin da itama take kallonshi da shirinshi na tafiya ofis, akasari dama ya fi sanya fut, to yau ma tsanwaye ne jikinshi sunyi mashi kyau. A hankali ya isa gaban gadon yana tambayarta jiki, ta ce "Ya yi sauki." Insha Allahu gida zata yanzu, ai naga jikin ya yi sauki sai dai za'ayi allura daya." Su duka suka yi dariya. Likitan ya duba ta ya kara rubuta mata wasu maganin da zata ci gaba da sha. Daddy ya karba ya sanya aljihu ya ce, "Zaya taho mata da su, idan ya taso daga ofis. 67 Don haka ta zama cikin shiri, direba na nan zuwa da Mummy zasu dauke ta, ya duba agogo lokaci yaja, gashi akwai tazara zuwa ofis dinsu, don haka ya yi mata sallama ya fita. Ta bishi da ido sai da ya fita, sannan ta sauke kwayar idonta akan Likitan shi kuma ita yake kallo, suka yi murmushi baki daya, ya ce, "Yanzu ina magana ta tsaya.?" Tа сс, "Tо ai ka ji dai za'a zo a dauke ni yanzu." Ya ce, "To ki bani address din ki zani zo." Ta girgiza kai ta ce "Na fadi maka ka yi hakuri ni fa ba zani yi wata soyayya ba." Ya zuba mata ido ya ce, "Saboda me.?" ta ce, "Ba ni da ra'ayinta ne.?" ya dan yi shiru, amma kuma sai ya ce, "Ni kau sai nake lura da man din nan kamar yana nufin wani abu akanki." Naja'atu ta kalle shi da sauri ta ce, "ban fahimce ka ba." Ya watsa hannayenshi, akwai alamar damuwa a fuskarshi, sai dai yana kokarin boyewa, ya dan cije lebenshi yana kallonshi ya ce, "Mu maza muna da wani sirrin kishi a ranmu, wanda idan ba mu ba babu wanda zaya iya fahimtar hakan, bari in tambaye ki wani abu, shin cikin ku daya da shi.?" A hankali Naja'atu ta sauke kwayar idonta tana kada mashi kai, ya yi murmushi ya ce, "Nasan a rina, wai an saci zanin mahaukaciya, to amma tunda ku duka kuna kokarin 6oyewa, shi kenan ni dai ba zani 6oye maki ba, ki saurari zuwana gare ki koda wane lokaci, me yiwuwa rabon nawa ne don haka ya tsaya kauron baki." Naja'atu ta tashi zaune tana kallonshi ta ce, "Kaga ni fa babu wani abu tsakanina da Daddy, yana da yarinyar da 68 zaya aura kowane lokaci za'a ya sanya lokacin aurensu." Ya cc, "Shi kenan, nima sai kiyi mani kokari mu fahimci juna, yarda zata kaimu ga irin wannan matsayin." Naja'atu ta yi shiru tana jin shi bata taba ganin mutumin da ya iya naci irinshi ba, ga baki da wayaun tsiya, duk ta in da ta bullo mashi sai ya san abin da zaya ce mata, ya jima tsayc yana kallonta, bata ce mashi komi ba, sai ya ji muryarshi ya cc, "Shi kcnan bari in barki ki huta, sai kin ganni." Bai jira amsa ba ya bude kofa ya fice, ta bi kofar da kallo, sai ta saukar da ajiyar zuciya, ya ta iya da rayuwarta?. Bai jima da fita ba, sai ga su Hajiya sun iso ta godc ma Allah da ya sanya basu samu Likitan ba, tasan Hajiya zata yi tsammanin wani abu, ko shi Daddyn ta lura dashi bai gamsu da abin da ya gani ba, tana lura dashi yana tuhumarta da ido, to ita kanta ba damuwa ta yi bashi ba bata san dalili ba, sam bai burgeta ba illa dai kawai bata iya fitowa fili ta yi mashi, rashin kunya, to kuma ta wulakanta shi, amma zancenta tsaya ta sauran ra'ayinshi ma bai taso ba jininsu bai hadu ba ba irin mutumin da take so ba nc. Amma da ta natsu tana tunani sai taga idan ba ta so shi ba, ta so wa? Zuciyarta ta rinka raya mata "Dady." To sai dai da kanta tasan Daddy ya fi karfinta, wannan shi ake ce me son maso wani. Suka gaisa da Hajiya tana yi mata sannu yayin da direba ya shigo da kayan kalaci ya ashe, sannan ya yi 69 mata sannu, Hajiya ta ce, "Amma dai yanzu jikin ya yi sauki ko.?" Ta cc, "Sosai ma, tun jiya ban sake jin zazzabin ba." Hajiya ta cc, "Allah ya kara sauki, bari in je in samu Likitan ya sallame ki mu koma gida, zaman asibitin babu dadi." Naja'atu ta cc. "Ya shigo ya sallame ni, Daddy ya tafi da takarda d ata magani ya ce, in jira zaku zo yanazu sai mu tafi gida: yana sauri zaya tafi ofis." Hajiya ta ce, "Au! ya biyo ta na kenan? Naja'atu ta daga mata kai tana kallonia ta ce, "To ai shi kenan, kiyi kalaci sai mu tafi." Naja'atu ta ce, "Mummy idan mun je gida na ji bakina babu dadi ban yi brush ba." Hajiya ta ce, "To shi kenan tashi ki lallaba mu tafi kije ki yi wanka kin fi jin dadin jikin." Ta umarci direban ya dauki kayan da ya shigo da su ya kai cikin motga ya dawo ya dauki sauran sannan suka fito. Daga nesa ta hango direban suna magana da Likitan ta ji haushi sosai, tasan abin-da taki fadi mashi ne yake tambaya, kuma tasan fadi mashi zaya yi, sai ta daure fuska ta kauda kai kamar bata gansu cikin zuciyarta ta ce, "makwakwanci." Da suka isa in da mota take, tana shirin shiga idanuwanta suka kai kanshi, a hankali ya dan daga matga hannu yana murmushi, sai ta sharc shi suka shiga direban yaja suka nufi gida. Da ta shiga bata zauna ba, sai da ta yi wanka da ruwan dumi ta ji dadin jikinta sosai, ta zauna gefen gadon tana shafa mai. Mas'ud ya kirata ta waya, ta dauka suka gaisa ta sanar da shi ta dawo gida, kuma 70 jikinta ya yi sauki. Ya yi mata fatan alkairi. Ta rufc wayar ta ta aje gefe guda, sannan ta ida shiryawa cikin wata shadda mai jinin kare, siket da riga ta sha aiki dinkin ya tsaru, dan madaidaici daidai jikinta, Anty Aisha cc ta yi mata kyautarsu sabbi ne, ta dinka suka yi mata kadan. Ta yi kyau daidai gwargwado ta gyara gashinta ta daura sannan ta tuke shi ta tura ciki, ta maida kallabin kayan ta daura fuskar tasha kwalliya daidai gwargwado, jikinta ma na kamshi mai sanyi zuciyarta fes, kamar ba ita ce ta kwana asibiti ba, babu abin da ke damunta sai dan ciwon da wurin da aka yi mata karin ruwa yake yi, shi kuma tasan a hankali zaya daina. Da ta fito kai tsaye kicin ta nufa, ta hada tea kofi daya ta dauko biredi ta dawo falo ta zauna tana kalaci. Mummy ta fito daga cikin daki, tana kallonta sai ta yi murmushi, har kullum idan Naja'atu ta yi kwalliya burge ta take yi bata gajiya da kallonta, Allah ya yi ma yarinyar kyhaun diri, komin munin kaya idan ta sanya su jikinta zasu karbe ta, insha Allahu ko burinta bai cika ba, watau Daddy bai aure ta ba, tasan a sannu wata rana zata samu miji na gani a fada, in da zata huta ta taimaka wa iyayenta. Ta shigo cikin falon suka dubi juna da Naja'atun, sai suka yi murmushi baki daya, Hajiya ta ce, "Da kyau Naja'atuna, kin yi kyau sosai kamar ba kece kika dawo daga asibiti ba." Naja'atu ta yi murmushi ta ce "Da na yi wanke sai na kara jin karfin jikina sosai." Hajiya ta cc 71 "Ai wanke rahama ne, amma tea zaya rike maki ciki? Ki yi kalaci sosai mana." Ta yi murmushi tana kallon Hajiyar ta ce "Mummy idan na ce zani ci abinci sosai amai zani yi sai a hankali zani warware." Hajiya ta jinjina kai ta cc "Babu damuwa, Allah ya Kara sauki ai kina kokari." Suka ci gaba da hira Hajiya na kara janta jikinta, sai ka yi tsammanin ita ta haife ta. Da aka yi sallar azuhar, Mummy ta shirya ta tafi unguwa don haka itama ta shige cikin daki ta kwanta jiya bata yi barci ba sosai, duk a takure ta kwanta, don haka da ta kwanta ta samu barci sosai, ga shi ta rufe wayarta don haka babu wanda ya tada ta, Ibrahim ne da ya taso daga makarantga ya shigo yaga tana barci bai yi mata magana ba, ya fita to shima Daddyn yau da wuri ya dawo, tun karfe hudu ya shigo gidan shiru shima Ibrahim yana cikin dakinshi, ya yi waya da Mummy ta ce mashi bata gida, don haka yasan itama Naja'atun tana cikin dakinta, don haka bai takura kowa ba, shi kadai ya yi hidimominshi ya dan watsa ruwa sannan ya dauro alwala yayi sallar La'asar ya sanya wando trosser baki da shirt mai dogon hannu ruwan madara ya dawo falo ya dan zauna shiru yana duba jarida, sai kuma ya aje ya nufi taburin cin abinci ya zuba yana ci. Lokacin itama Naja'atun ta fito daga cikin daki, da nufin ta samu dan abin da zata iya ci, saboda har yanzu bakinta babu dadi. Da ta hango Daddy sai ta nufi in da yake tana murmushi ta ce, "Wai ashe ka shigo, ban ji ba." Ya zuba mata ido kawai bai san dalili ba zuciyarshi 72 ta cika damuwa da lamarin yarinyar duk sadda ya kalle ta sai yaga abin da ya burge shi, kwakwarta ta yi mashi kyau, ya aje cokalin yana kallonta ya ce "An ya Naja'atu ciwon da kika yi na gaskiya ne.?" Ta tsaya tana kallonshi da mamaki, ya yi murmushi ya ce "kin yi kyau ne kamar bake ce kika kwana asibiti ba." Ta yi dariya ta isa taja kujera ta zauna ta cе "Mummy ma haka ta ce, ni kuwa ji nake yi duk na rame jikina babu karfi." Ya ce, "Babu wata rama, sai dai ki ce rashin karfin jikin." Ta yi murmushi kawai ta debi abinci kadan tana ci haka nan ba don dadi ba. Da ya gama shi kuma ya tashi ya fita, sai ga shi ya shigo da ledoji, ya zube mata bisa tebur, ya ce "Ga magungunan nan da kuma karin ciwo." Ta dube shi tar cikin ido, shima ya zuba mata nashi, ta ce "Don mi ka dora ma kanka wata wahala haka, ina laifin maganin ma.?" Ya'ci gaba da kallonta ya ce, "Ni bani tare da wahala, kuma nasan ba rokona kike yi ba, nine na sanya kaina, ko ba haka ba?" ta daga mashi kai ya ce "To kiyi mani godiya ko kuma kiyi shiru." Ta yi murmushi ta ce, "To na gode, Allah ya kara arzuki, sai dai naga kamar ranka ya baci, ni kuma gani nayi kudin da yawa." Ya yi murmushi ya ce, "Amma kinsan wanda ya cancanta ake yi ma kyauta ko? Haka nan ban ga laifin ki ba, sai ma burge ni da kike yi idan na yi la'akari da yarda halayyar 'yan matan yanzu ta lalace, ba ke ba su ba 73 ma roko suke yi kamar zasu shiga aljihun mutum, idan ma kyautar ka yi masu babu godi bare na godc, sai ka ce sun ba mutum ajiya, idan ba ki sani ba wani, lokaci godiyar da kike yi mani, ina jin dadi shi yake nake yawan yi maki kyautar, idan naji kina yi mani godiya, burge ni kike yi sosai, wannan shi ne halin dattaku da kawaici." Naja'atu ta jinjina kai, ta ce "To ai godiya ba, saboda Mummy da abin da ta ke yi mani zani iya gode maka ai duk dan halak ya san an yi mashi." Ya ce "Haka ne, yanzu yaya kike jin jikin.?" Ta ce "Jiki Alhamdulillahi, ya yi sauki sosai." Ya ce, "To idan kin gama cin abincin ki fara shan maganin gaya nan." Ta jinjina kai, yayin da shi kuma ya koma cikin falo, ya dauki jaridarshi yana dubawa, itama da ta gama nan ta dawo har da Ibrahim suna hirarsu a mutunce. Yamma ta yi sosai, Mummy ta dawo suka tarbe ta tana tambayar jikinta, ta ce ya yi sauki, ba ta zauna ba kowa ya nufi Sallah, magariba ta gabato. Karfe takwas kowa ya dawo falon suna nan ana ta hira har da Mummy, maigadi ya kwankwasa kofa, Ibrahim ya tashi yaje ya bude ya ce mashi, wani bako ne yake son ganin Naja'atu." Ibrahim ya saki labulen ya dawo ya zauna, ya ce, "Anty Naja wai bako ne kika yi." Wuta ta dauke mata, ido cike da tuhuma, itama Hajiyar kallonta take yi tana murmushi, ta ce, "Waye ke nemanki Naja'atu.?" Ta kalle ta a marairaice, ta ce 74 "Nima ban san shi ba." Hajiya ta dubi Ibrahim ta ce, "Je ka gano waye.?" Ibrahim ya tashi ya fita, ita kau Naja'atu kamar ruwa ya cita, ga Daddy ya hada rai sosai bata san abin da yake nufi ba, koda bata san mai kiran ba, tasan ba ya wuce Likita, idan ba shi ba bata san kowa ba. Ibrahim ya dawo yana dariya ya ce, "Ok, Doctor din nan ne da ya duba ki jiya." Daddy ya dube shi a fusace ya ce, "Je ka kace mashi bata zuwa." Hajiya ta dube shi da sauri ta ce, "Don mi? Wannan ba mutunci ba ne, ina laifin wanda ya taso takanas yazo in da kake, kuma kasan abin da ke tafe dashi?" Daddy ya yi sukuti, Hajiya ta dubi Naja'atu ta ce, "Tashi kije ki ji abin da ke tafe da shi wulakanci babu kyau." Kamar zata nutse don kunya, haka nan ta daure ta tashi, idan bacin kada Hajiyar ta ce "ta watsa mata kasa a ido ita kam da ra'ayin Daddyn ta bi ba za ta fita ba, to sai dai bata son yi ma Hajiya gardama, don haka ta shiga cikin daki ta dauko mayafi tazo ta raba su ta fita. Yana zaune cikin harabar gidan bisa kujerar roba, kananan kaya ne jikinshi, sun fito da sigar kyaunshi kamar koda yaushe fuskarshi dauke da murmushi, sai ta ji zuciyarta ta dan yi sanyi ba zata iya wulakantashi ba, Mummy ta yi gaskiya da ta ce "Babu kyau wulakanci, to ita kam kwarjininshi ma ba zaya bari ta samu kafar fadi mashi komi ba. 75 A hankali take tafiya

Chapter 5 of 6