Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 6
yi fushi ba." Ya zuba ma Faridar ido, ya cc, "Wai haka ne.?" Ta dan tsuke bakinta, tana yatsuna fuska ta cè "Ban ce ba." Ya ce "To ki zuba abinci ki ci, ai ba bakuwa ba ce, idan kuma laifi nayi kiyi hakuri." Ya zuba mata ido da sigar zolaya, sia ta yi murmushi ta zuba abincin dan kadan ta ci. Naja'atu dai bata sake sanya masu baki ba, har ta gamaci, ta tashi ta basu wuri. ta dawo cikin falo ta ta zauna. Sai ga Ibrahim ya shiga lesson ya tafi tun safe, nan ya zauna suna hira, sai da su Daddy suka gama sannan ya tashi ya nufi cin abincin. To suma ko da suka dawo, basu dade da zama ba, Farida ta ce, "Tafiya zata yi." Ya dubi Naja'atu ya ce, "Shiga ki gaya ma Mummy Farida zata tafi." Ta tsaya kawai tana kallonshi, sai ka ce yarinyarshi, amma ita kanta ta kagara yarinyar ta tafi, sai wani cika take yi tana batsewa, don haka ta shiga cikin dakin Hajiya ta sanar da ita, daga nan ta fito da kwanonin da ta ci abinci, ta nufi kicin. Sai da suka fita sannan ta dawo suka ci gaba da hira ita da Ibrahim. A can kuma suna fita waje, Farida ta daure fuska sosai, Daddy ya zuba mata ido, ya ce, "Wai me yake 33 damunki, tun dazu naga kin canza.?" Ta dan zobari baki, ta ce, "Daddy kasan ina da tsananin kishi a kanka ko? Ya ci gaba da kallontga ya ce, "Uhm." Ta ce, "To gaskiya bani jin dadin yarda naga kana jan yarinyar nan da wasa.?" Ya saukar da ajiyar zuciya ya ce "To me hakan yake nufi.?" Ta ce, "Shi ne ban sani ba, amma ni na san matsawar ku ka ci gaba da tafiya haka, wani abu zaya iya biyo baya." Ya ce, "Kamar me.?" Itama ta zuba mashi ido, ta ce "Wannan kai za'a tambayà." Ya yi murmushi ya ce, "Dadina dake kenan Farida, kin cika zargi da kawo abu a ranki, yarinyar nan 'yar'uwata ce ko." Ta ce "Amma kuma ba cikinku daya ba." Ya jinjina kai-ya ce, "Haka ne.?" Sai dai abin da na ke so ki fahimta shi ne, abin da ke ki ke tunani ba zaya taba faruw ba, zuciyata ke kadai take so, sannan yarinyar nan ina jin duka jiya ne ma muka fara magana da ita, tun a Katsina fada muke yi, sannan ba zaya yiwu ba ace muna zaune gida daya kuma 'yar'uwata ce, amma ace ba mu magana tsakaninmu, Mummy ba zata ji dadi ba, kuma itama yarinyar ba zata sake ba, don haka ki kaga ina shiga harkarta, ba wai don wani abu ba." Ta ce, "Amma kai kanka kasan abin da ka yi dazu ba ka kyauta ba.?" "Da na yi me.?" Ta ce, "Yarda ka rinka janta da wasa a gabana har da daukar abincinta." Ya yi murmushi ya ce, "Har yanzu dai kin kasa fahimta ta, Farida akwai wani abu a tare da Naja'atu da nake so.?" Ta dube shi da sauri, ya ce, "Ba wai ina nufin wani abu daban ba ne, tana da saurin fushi ne don haka 34 ki ka ga ina janta, don kawai ta yi fushin." Ta dan cije lefenta tana jinjina kai, ba ta ce komi ba, ya yi mata rakiya da nisa babu nisa zuwa gidansu cikin unguwar daya ne, duk da haka dai Farida ba ta sa ki fuska ba sosai, ita dai tana zargin wani abu to shima bai sake tada mata maganar ba, suka yi sallama ya yi mata godiya kan zuwan da ta yi yima Hajiya sannu da zuwa. 'Yan kwanaki kadan Naja'atu ta warware cikin Abuja, koda yaushe tana like kicin tare da Mick tana koyon girki kala-kala, tun Hajiya na yi mata fada akan ta rinka zama tana hutawa, har ta gaji ta rabu da ita, to sai ta samu littafi duk girkin da aka yi wanda ya burge ta zata rubuta. Tana jin dadin zaman gida, babu in da Hajiya ta rage ta idon zata fita unguwa takan fita tare da ita taga gari to shi kanshi Daddy yana son ya rinka fita da ita ita ce dai taki amincewa sau daya ta bishi suka je gidan Aisha diyar Hajiya dake aure nan Abuja, daga nan koya nemi su fita ba ta binshi ita kau ba don komi ba sai don ganin yarda yake neman makale mata, duk in da take zaune shima yana nan, yana jifarta da mayataccen kallonshi wanda ita kanta bata san dalilinshi ba, cikin faki ne kadai take shiga ta samu lafiyar shi, idan ma ta shiga dakin Hajiya ta rinka jajenta kenan tana tambayarta abin da ke damunta, ko ta ce babu komi duk da haka sai ta dan damu. Yanzu haka duk wasu hidimominshi ya dauko ya dora mata, ko abinci zaya ci idan ya shigo zaya kwalla mata kira, duk in da take sai ta fito ita zata zuba mashi 35 abincin kuma ya tsare ta sai ta zauna a gabanshi zaya ci abincin.Abun yakan daurc mata kai, idan ta yittunani shi ba fitowa ya yi ya sanar da ita wani abu ba, amma duk ya bi ya daure ta, ita ba abun ta kai karar shi wurin Hajiya ba, to ta ce mata mi? Tunda ba wani labu ya cc mata ba. Lokuta da dama idan suna zaune yakan kira Farida ta waya ko kuma ita ta kira shi gabanta za su yi hira yana fadi mata kalaman soyayayya da matsayinta cikin zuciyarshi, kai ko wajenta yajc ya dawo zaya ba ta labarin hirar da suka yi, don haka nc take ganin kamar yana neman ya maida ta sakarai, to sai ta rinka daure mashi, amma duk da haka a banza, bata smau lafiyarshi ba, sai da ya koma bakin aikinshi, idan ya fita tun safe, shi da gida sai dare, sai kuma ta rinka tausaya mashi baya da hutu sai Asabar da lahadi. Abu guda ne ya ke damunta rashin jin labarin gida ta damu kwarai, rannan ba zato Hajiya ta fita cikin gari da ta dawo sai ga waya sabuwa fil ta kawo mata mai kyau, da gani za ta yi kudi, don murna Naja'atu rasa abin da zata ce ta yi, to itama Hajiyar ta hanata yin godiya, ta shige cikin daki ta barta da Ibrahim suna ta dannar wayar. Cikin jikkarta ta laluba ta fiddo Diary dinta, ta duba lambobin dake gare ta na kawayenta ta loda cikin wayar har da ta kaninta Mas'udu ta rinka neman layin shiru ba ta samu ba, ta damu kwarai amma can da daddare da ta sake kira, sai ta ji wayar ta shiga ta tsaida hankalinta wuri daya tana dokin ta ji ya dauka, kuma cikin sa'a yana kusa ya amsa da sallama. Ta cе, 336 ki ka ga ina janta, don kawai ta yi fushin." Ta dan cije lefenta tana jinjina kai, ba ta ce komi ba, ya yi mata rakiya da nisa babu nisa zuwa gidansu cikin unguwar daya ne, duk da haka dai Farida ba ta sa ki fuska ba sosai, ita dai tana zargin wani abu to shima bai sake tada mata maganar ba, suka yi sallama ya yi mata godiya kan zuwan da ta yi yima Hajiya sannu da zuwa. 'Yan kwanaki kadan Naja'atu ta warware cikin Abuja, koda yaushe tana like kicin tare da Mick tana koyon girki kala-kala, tun Hajiya na yi mata fada akan ta rinka zama tana hutawa, har ta gaji ta rabu da ita, to sai ta samu littafi duk girkin da aka yi wanda ya burge ta zata rubuta. Tana jin dadin zaman gida, babu in da Hajiya ta rage ta idon zata fita unguwa takan fita tare da ita taga gari to shi kanshi Daddy yana son ya rinka fita da ita ita ce dai taki amincewa sau daya ta bishi suka je gidan Aisha diyar Hajiya dake aure nan Abuja, daga nan koya nemi su fita ba ta binshi ita kau ba don komi ba sai don ganin yarda yake neman makale mata, duk in da take zaune shima yana nan, yana jifarta da mayataccen kallonshi wanda ita kanta bata san dalilinshi ba, cikin daki ne kadai take shiga ta samu lafiyar shi, idan ma ta shiga dakin Hajiya ta rinka jajenta kenan tana tambayarta abin da ke damunta, ko ta ce babu komi duk da haka sai ta dan damu. Yanzu haka duk wasu hidimominshi ya dauko ya fora mata, ko abinci zaya ci idan ya shigo zaya kwalla mata kira, duk in da take sai ta fito ita zata zuba mashi 35 abincin kuma ya tsare ta sai ta zauna a gabanshi zaya ci abincin. Abun yakan daure mata kai, idan ta yi tunani shi ba fitowa ya yi ya sanar da ita wani abu ba, amma duk ya bi ya daure ta, ita ba abun ta kai karar shi wurin Hajiya ba, to ta ce mata mi? Tunda ba wani abu ya cc mata ba. Lokuta da dama idan suna zaune yakan kira Farida ta waya ko kuma ita ta kira shi gabanta za su yi hira yana fadi mata kalaman soyayayya da matsayinta cikin zuciyarshi, kai ko wajenta yaje ya dawo zaya ba ta labarin hirar da suka yi, don haka ne take ganin kamar yana neman ya maida ta sakarai, to sai ta rinka daure mashi, amma duk da haka a banza, bata smau lafiyarshi ba, sai da ya koma bakin aikinshi, idan ya fita tun safe, shi da gida sai dare, sai kuma ta rinka tausaya mashi baya da hutu sai Asabar da lahadi. Abu guda ne ya ke damunta rashin jin labarin gida ta damu kwarai, rannan ba zato Hajiya ta fita cikin gari da ta dawo sai ga waya sabuwa fil ta kawo mata mai kyau, da gani za ta yi kudi, don murna Naja'atu rasa abin da zata ce ta yi, to itama Hajiyar ta hanata yin godiya, ta shige cikin daki ta barta da Ibrahim suna ta dannar wayar. Cikin jikkarta ta laluba ta fiddo Diary dinta, ta duba lambobin dake gare ta na kawayenta ta loda cikin wayar har da ta kaninta Mas'udu ta rinka neman layin shiru ba ta samu ba, ta damu kwarai amma can da daddare da ta sake kira, sai ta ji wayar ta shiga ta tsaida hankalinta wuri daya tana dokin ta ji ya dauka, kuma cikin sa'a yana kusa ya amsa da sallama. Ta ce, 36 "Mas'udu ni ce Naja'atu." Shima murna yake yi va ce. "Yaya Naja mun yi missing din ki sosai, kulluna sai mun yi maganarki, ba'a gaisawa ba wani labari yaya Abujar?" Ta rumtsc ido tana jin dadi, ta ce "Alhamdulillahi, komi lafiya. Mas'ud yaya Baba da Inna.?" Ya ce, "Duk suna nan lafiya, gasu nan ma kusa ga Inna ku fara gaisawa." Cike da doki ta gaisa da Inna, Inna ta ce. "Yaya Hajiyar.?" Ta ee "lafiya lau, ita ce ma ta sai mani waya yau, shì ne na ce bari in kira Mas'ud mu gaisa пa yi kewarku Inna." Inna ta ce "To ai komi lafiyha lau dai.?" Ta ee "Wallahi lafiya lau Inna, sai dai godiyar Allah, ba ki ga yarda Hajiya take yi mani ba, ko ita ta haife ni sai haka, yanzu tana cikin daki ne, amma idan ta fito zani kira ku gaisa." Inna ta ec, "Shi kenan Allah ya saka mata da alkairi, ga Malam nan ku gaisa." Shima tikin doki suka gaisa har da su Badiya sai da aka ba su suka gaisa, gaskiya ta ji dadi waya rahama ce, sai ta ji duk wata damuwarta ta warware. A hankali ya murda kofa ya shiga, hannunshi daya rike da kwat dinshi, yayin da dayan hannun ya na rike da allon kwamfuta (laptop) daga ita har Ibrahim suka maida idanuwansu akanshi, suna yi mashì sannu. Akwai alamar gajiya sosai a tare da shi, sai ta ji tsikar jikinta yana tashi a hankali ta sauke kwayar idanuwanta kasa, ta rasa abin da yake damunshi cikin ta wahin han har ba ta so ya shigo gidan, sai đai yanzu da ta lura da yanayin aikinshi tausayi yake bata ba tare da ta kalle 37 shi ba, ta ce "Sannu." Ya saki fuskarshi ya ce, "Yauwa Naja'atu yaya gidan.?" ta ce "lafiya lau." ya ce "Mc ki ka aje mani da zani ci.?" Ta dube shi tar cikin ido, ta се "Kamar me.?" Ya ce "Abinci ko.?" Ta ce "Akwai abinci." Ya jinjina kai ya ce "Shi kenan bari in shiga in dan watsa ruwa sai in fito ki bani." Ya huce zuwa dakinshi, sai ta saukar da ajiyar zuciya a hankali tunanin da take kokarin danne wa, ya dawo mata cikin zuciya cikin 'yan kwanakin nan tana wahala sosai dangane da abin da zuciyarta take neman janyo mata, sai dai duk iya kokarin da take yi wajen ganin ta kawar da abun, ya faskara saboda wanda ake abun dominshi kullum rana kara iza wutar abun yake yi tana ruruwa cikin zuciyarta ko shakka babu ta sani Kaunar Daddy ce ke wahalar da ita, wanda ita kanta tasan cewa bugun iska take yi. Daddy ba nata ba ne, satin da ya shige ta ji Hajiya da mahaifiyar Farida suna maganar sanya lokacin aurensu, kuma shi ma ya amince babu yarda za'ayi ya dawo gare ta, sai ta rinka jin tausayin kanta, yaya aka yi haka ta faru gare ta? A duk iya tsawon rayuwarta bata taba yin soyayya ba, don mi yanzu ta fara da son maso-wani? Tabbas tana cikin wahala. Wasu siraran hawayhe suka sauko bisa fuskarta, bata ankara ba sia dai taji muryar Ibrahim akanta, ta sanya hannu tana share fuskarta ya ce, "Anty Naja lafiya.?" Ta yi murmushi ta ce, "Lafiya lau Ibrahim." Ya ce, "Naga kin yi shiru." Ta ce, "Babu komi wani 38 tunani ne nake yi." Sai ya zauna suka ci gaba da danna waya, yana gwada mata yarda komi yake. Suna nan zaunc Daddy ya fito, ya watsa ruwa yana sanye da jallabiya fara sol, mai gajeren hannu. Naja'atu ta zuba ido ta ce, "kan tabur zaka ci abincin ko a kawo maka nan.?" Ya ce, "Kawo mani nan, na gaji da yawa." Ta tashi a hankali ta zubo ta kawo mashi, sannan ta je ta kawo mashi rujwa ta samu har ya fara cin abincin, don haka tà aje ta zauna, to shi Ibrahim sai ya tashi. Ya tafi dakin karatu yana da Assignment. Naja'atu ta zauna shiru, yawanci ta fi maida hankalinta kan akwatin talabijin, yayin da shi kuma Daddy ya tsare ta da kallo, wanda ita kanta ba ta san dalilinshi ba, yana damunta da yawa. Tun tana daurewa har ta kai ta yunkura ta mike tana shirin tafiya. Ya ce, "Ina za ki kuma.?" Ta ce, "Ina cikin daki." Ya cc, "Zauna hira zamu yi, duka yanzu karfe nawa.?" Bata yi musu ba ta koma ta zauna, ya gyara zama yana kallonta, ya ce, "Wai in tambayc ki, kin gama NCE din ki ko.?" Ta ce, "Eh." Ya ce, "To yanzu sai me kuma za ki yi.?" Ta dube shi tar cikin ido ta ce, "Me fa? Duk abin da Allah ya kawo shi zan yi." Ya ce, "Kamar me.?" Ta yi murmushi ta ce, "Ka cika tambaya Daddy." Ya rinka kyalkyatar dariya, ya ce, "Abin da ka damu dashi Naja'atu shi kake tambaya kanshi, yanzu bani labarin saurayinki." Ta dube shi da sauri, ta ce, "Na ina.?" Ya ce, "Kina nufin ba ki da saurayi.?" ta ce, "kusan haka ne, bance maka bani da samari ba, ina da 39 so sat dai babu wanda nake so, don haka zani iya ce maka bani da shi.""Ya ce, "To wane irin miji kike so.?" Ta ce "Bani da zabi sai abin da Allah ya yi." Ya се, "Kina ganin ba matsala, idan ni na samo maki.?" Ta yi dariya ta cc, "Ce maka na yi ina nema.?" ya cc. "Ba ki ce ba sai dai ni ina ganin ya dace ace kina da shi." Ta kada kai ta ce, "To ban sanya ka ba, saboda ba dole ba ne in so abin da kai kake so." Ya zuba mata ido a hankali ya ce, "Ko.?" Jikinta ya ida mutuwa sai tga sarda kai bata ce komi ba. Shima cin abincinshi yake yi yana kallonta, har ya kare bai sake magana ba. Hajiya ta fito ta zauna, Naja'atu ta zubo mata abinci ta zauna tana ci suna hirarsu gwanin ban sha'awa, akwai fahimta sosai tsakaninsu haka nan Hajiya na kokarin hada kansu a bangare daya kuma wani tunani ta soma yi, yanzu da take zaune da Naja'atu ta yaba da kyawawan dabi'un yarinyar, tana kaunarta har cikin ranta, sai ta rinka sha'awar dama ace ita Daddy yake nema ba wai Farida ba, ta kowane fangare ta auna Naja'atu sai taga ta yi ma Farida fintinkau, kyau ne, asalin kyaun hali, da sanin ciwon kai, sai dai kai ya ce don ita Naja'atu iyayen talakawa ne kuma bata waye ba irin Farfida haka nan ta 6angaren ilimi ita kanta Faridar yar Diploma ce ta kulla, to ita ba ta damu da talaucin iyayen Naja'atu ba idan dai zaya amince da ita duk abin da iyaye zasu yi ma diya ita mai yi mata ce tana son halin dattakun yarinyar. To shi duk duk baiga wannan 40 ba, ya rufc ido baya ganin wata diya mace da mutunci idan ba Farida ba. Cikin 'yan kwanakin han tana nazarin takunshi da Naja'atu cikin gidan, sai take jin dadın yarda suka kara kusantar juna, tana fatan Allah ya karbi addu'arta, idan haka ta faru sai tafi kowa farin ciki, ko ba komi ta yi sarakuwa ta gari kuma ta yi imanin zamansu zaya yi dadi, duk wannan sabanin da suke samu ba ta dauke shi matsala ba, da zaran sun fahimci juna shikenan. To sai dai lura da yanayin da ake ciki yanzu ba a yi ma 'ya'ya dóle, sai ta zuba ido taga iya gudunsu, kullum dai addu'arta guda Allah ya sanya burinta ya cika. Karfe goma daidai, Naja'atu ta mike-zata tafi ta kwanta ta yi ma Hajiya sai da safe sai ta juya tana kallon Daddy wanda shi ma ya zuba mata ido, ya ce "Barcin ne ko.?" Ta yi murmushi kawai ta ce, "Sai da safe." Ta nufi daki ta yi shirin kwanciya ta kashe fitila, ta kwanta tana karanto addu'o'i, tunanin hirar ta da Daddy ya tsaya mata a zuciya, "Wai shi ne zaya nemo mata saurayi? To ko dai ya gane cewa tana sonshi? Don haka yake zolayarta? Ta rinka jinjina magar, cikin zuciyarta. Dole ne ta bi a sannu kada ta bada kanta abun ya kaita ga cin fuska, to amma kuma da ta tuno Farida da matsayinta sai ta tabbatar da bugun iska take yi, me yiwuwa shi ba ya ra'ayin diyar talakawa irin ta, haka nan waycwarta bata kai ta Farida ba, kai nazarin da ta yi mashi ma ya damu da Faridar sosai, ba ya shakkar yin hira da ita ko gaban waye, haka nan da wuya su 41 zauna a waje ba ta ji ya ambace ta ba, tabbas yana Kaunarta, don haka da wuya ya dawo gare ta, sai ta rinka jin tausayin kanta ta fada tarkon son maso wani. Can falo kuma da Naja'atu ta tashi Daddy ya bita da kallo, har ta shiga daki, sai ya yi murmushi yana kada kai, da ya sauke kwayhar idonshi sai yaga Hajiya na kallonshi, to sai ya dan ji nauyin ta, ya yi. Hajiya ta yi murmushi ta ce, "Ya ya ko nan zaka dawo ne.?" Ya shafi kanshi yana dariya, ya ce "Mummy in yi yaya da Farida.?" Та сс, "Кana namiji zaka tsaya tambayar yarda zaka yi da 'yan mata duka biyu, gurbin hudu fa ke gare ka fa". Ya kyalkvace da dariya, ya ce "Haba dai Mummy sai ka ce mutumin karkara? To ai ko kauyen ma yanzu gudun tara matan suke yi, balle ni da nake mijin mace daya". Hajiya ta yi dariya ta ce, "Cika baki dai, kada fa a wayi gari wata rana in ga ka hada hudu cikin gida." Ya ce, "Allah ya kyauta, mu bar maganar nan Mummy, bakin uwa saurin kama da take yi, kada abun fa ya tabbata, da na bani." Hajiya don dariya har tuntsuwa take yi, shima ya tayata ta ce "Muyi maganar sosai Daddy, da gaske fa nake yi idan dai kana ganin zaya yiwu, to ka dawo in baka diyata, yarinyar na da kyaun hali, kuma naga kamar hankalinku ya hadu." Ya zuba mata ido yana nazari, sai kuma ya girgiza kai ya ce, "Kiyi hakuri Mummy ba zaya yiwu ba, ina son Farida kuma kin sani itama tana sona, mun yi ma juna alkawari da dama daga ciki har da na aure, idan na 42 ce yanzu in rabu da ita, na ci amana, ba zata ji dadi ba, kuma maganar gaskiya, ni ita kadai nake so. ba zani iya barinta ba in koma ma wata." Hajiya ta dan cije lebe, sai kuma ta ce, "Ni kau sai nake ganin Naja'atu na da halayc managarta, da duk wani da namijin da ya san ciwon kanshi zaya so ace ya mallake ta matsayin mace a gidanshi wadda zata zamo uwar 'ya'yanshi, ta samu tarbiya mai kyau haka nan idan kyau ne ba za'a nuna mata komai ba, ka dubi takunta tasan abin da take yi, zaka yi alfahari da aurenta." Ya yi murmushi ya ce, "Mummy duk nasan wannan, sai dai abin da za ki duba shi ne, ina son Farida-sosai, mun yi alkawarin aure ysakaninmu, kuma maganar nan ba wai tsakaninmu ta tsaya ba, kin san maganar nan haka iyayenta sun sani, yanzu haka ko jiya da naje gidansu munyi magana da mahaifinta ya ce in turo ayi maganar lokacin auren, maganar da nake son muyi kenan dama, to kuma Mummy sai in zo yanzu in kawo wata maganar, ko kuma suga na janye mata, daukar me zasu yi mani? Ke kanki za ki ji nauyin abun. Kiyi hakuri insha Allahu Naja'atu zata yi miji, wanda ya dace da ita." Hajiya ta jinjina kai, ta ce "Shi kenan." Ya zuba mata ido da sigar lallashi, ya ce "Amma don Allah Mummy kuyi hakuri kada kiyi fushi dani, gaskiyar abin da ke cikin zuciyata ne na fadi maki, idan na ce maki zani iya rabuwa da Farida saboda wata nayi Karya." Hajiya ta yi murmushi ta ce, "Shi kenan Daddy na fahimce ka, yanzu ina magana ta tsaya.?" Ya dube ta 43 yana murmushi ya ce, "To Mummy yarda duk ki ka gani su dai sun yi mani magana he." Ta ce, "Nima şun aiko mani, don haka yanzu ka tsaya kan haka.?" Ya jinjina mata kai, yana murmushi. Ta cc, "Babu damuwa, Allah ya tabbatar mana da alkairi, zani samu lokaci in je gidan Babanku, in ji yarda zamu yi. maganar gidan nan na Arca II, ka ce ka basu Notice din ko.?" Ya oc, "Eh, tun katin in tafi hutu." Ta ee, "To nan zaka zauna, don haka sai ka maida hankali kaga sun bada gidan, yarda za'a yi gyaranshi sosai, ina ganin ya fi sauki akan ace a gina wani, kuma kaga dai gidan yana da kyau." Ya ce, "Ya yi sosai Mummy." Ta watsa hanu ta ce "Shi kenan sauran shiryc-shirye kuma sai yadda muka yi da Babanka, shi kenan hankalinka ya kwanta.?" Ya yi dariya kawai. To amma da ya shiga cikin daki, sai ya rinka juya maganar Hajiya, "Tabbas yana son Naja'atu, akwai wasu abubuwa a tare da ita wadanda yake so, yana son ya kasance tare da ita, ko ba komi takan sanya zuciyarshi nishađi, to sai dai a ganinshi son da yake yi mata bai kai matsayin da zaya ce ya zabe ta matsayin matar da zaya yi rayuwa ta har abada da ita ba, yana da wadansu ra'ayoyi na daban da ya ruga ya gabatar ma Farida dasu, kuma ta karance su, don haka take saurin samun kanshi. So daban ne yaso Farida tun bata kai matsayln mace ba, mahaifinta Banufe ne, sai dai mahaifiyarta Ibra ce, su duka ma'aikatan Gwamnati ne, ita mahaifiyarta Hajiya Hafsatu sun yi aiki ofis daya da 44 mahaifinshi tana karkashi ta haka ne suka san juna ita da Mummy suna mutunci sosai, idan tazo gidansu tare da Farida da Kannensu yama janta wasa, saboda lokacin da tana karama ta yi kyau sosai ga baki tana da yawan surutu don haka take da farin jini wajen mutane, duk wanda ya zauna da ita cikin dan lokaci sai ta shiga ranshi da irin haka ne suka saba da ita cikin dan lokaci sai ta shiga ranshi da irin haka ne suka saba da Daddy, idan suka zo gidan koda yaushe tana wajenshi yana sha'awar abubuwan ta lokuta da dama idan suka zo ba ta tafiya sai ta yi kwana biyu a gidan, Hajiya ma na sonta, yauda gobe da ta yi girma ne ta rage zuwa gidan, amma dole da haka akwai fahimtar juna tsakanin zuri'ar biyu, mahaifinta matukin jirgin sama ne. Lokacin da girma ya farfa zo ma Farida ne ta fara nuna jin kunyar Daddy shi kuma hakan ya dauki hankalinshi ya fara nuna ra'ayinshi akanta, Hajiya na lura da shi da ta tsare shi tana tambayarshi bai ji kunya ba, ya fito fili ya sanar da ita da gaske yana sonta, kuma in Allah ya yarda ita ce matar. Hajiya dariya ta rinka yi, saboda tana ganin abin har da yarinta, amma a hankali yau da gobe sai ga soyayya ta fara kafuwa tsakaninsu, to gaskiya lokacin ta tsorata ganin cewa su duka basu kai wani matsayi ba da za'a ce sun maida kai ga soyayya irin haka don haka ta gargadi Daddy da ya bi a sannu saboda Farida yarinya ce, a kalla su duka akwai karati gabansu, bai dace ace sun tsaya wata soyayya ba, 45 to Daddy ba ya da taurin kai don haka ya bi umarnin mahaitiyarshi ya yi kokarin kauda abun a ranshi. Lokacin da yake shirin fita karatu duka Farida na aji daya na babbar sakandire SS1, don haka basu tsaida wata kwakkwarar magana ba, ya tafi. Duk lokacin da suka yi magana da Hajiya yakan tambayi labarin Farida, Hajiya dauriya take yi ta ce tana nan lafiya lau." Shekararshi biyu da tafiya, Allah ya yi ma mahaifinsu rasuwa, sakamakon wani mummunan hadari da suka yi kan hanyar Katsina zuwa Abuja, to lokacin ne ya samu zuwa gida, ya yi mamaki kwarai da ya ga girman da Farida ta yi, komi

Chapter 3 of 6