Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 6
ni zo gidan nan ba." Inna ta yi dariya ta ce, "Na yarda da laifina ayi hakuri, ku shigo ciki. Hajiya ta ce, "A'a, ciki zafī, kawo mana tabarma tsakar gida mu sha iska." Naja'atu ta shiga cikin daki da sauri ta dauko tabarma sabuwa ta shimfida Hajiya ta zauna, sannan itama Inna ta zauna kusa da ita, yayin da Malam Abdu yake zaune bakin kofar dakinshi bisa shimfidarshi. To itama Naja'atu sai ta nemi kujera ta zauna gefe daya tana sauraren yarda za'ayi, da yinin da ta yi tarc da Hajiya ta ji tana kaunar matar, tana da dadin zama, zama da ita kanshi wata makaranta ce ko ba komi zaka fahimci wasu abubuwa na rayuwa, wadanda idan ba wajen irin su ba, da wuya mutum ya same su. Badiya da Fatima suka zo suka gaida Hajiya suka koma cikin daki in da suke linke kaya, sannan suka shiga gaisawa ita da Hajiya korafi take yi ma Inna kan cewa ba ta son zumunci, to ita Inna abin da take dubawa shi ne, yau da gobe sai Allah, sannan haye ma masu kudi, yana da wuya, idan mutum bai yi a sannu ba, sai ya wulakanta, ita kau abin da take gudu kenan wulakanci. Sai da suka natsu sannan Hajiya ta juya wurin Malam Abdu, ta ce "Zuwa na yi a bani aron Naja'atu ta zauna hannuna kwana biyu, tun da dai ta kare karatu." Malam Abdu ya yi dariya ya ce, "To ai ba wani abu ne 18 ba anima dai ga mahaifiyarta nan ku sasanta." lapv tta dubi Iuna ta oc, "To kin ji don baka ya ya ki ka cc. Itama Innar ta yi murmushi ta cc, "To ai shi kenan, har kwana mawa.?" Hajiya ta cc "Eh to, ina ganin zuwa Asabar in Allah ya kamu zani wucc Abuja, kuma tare zamu taf don haka dai sai kin ganmu." Naja'atu n zauna gefe daya, tana jin maganar da suke yi, mamaki take yi wai ita zata Abuja abin da ba ta taba tumani ba." Sai đai taddi kuma ta yi murna da tafiyar, sai dai wani abktike dubawa shi ne. Inna zata dan takura msammsa yake ta saba tana dan dauke mata wasu ayyukan cikin gida, yanzu idan ta tafi ita zata rinka yinm komi sai idan su Badiya sun dawo daga makaranta. To sai dai Iunar ta ce babu komi ta shirya su tafi, ina laifin wanda ya nuna sha'awar zama da naka, a ganinta wani ci gaba ne ga ita kanta Naja'atun, zama da mata irin su Hajrya Halima alkairi nc, ko ba komi zata koyi abubuwa da dama na rayuwa, kuma ma dai babu dach yarda ta taso takanas ta tambaya ace ta hana wasu masu kudin ma gudun 'yan'uwansu suke yi Naja'atu ta shiga cikin daki ta fidda 'yan sababbin kayanta masu haske, kala bakwai ta diba ta fita zuwa dakin Mas'udu, ta ci sa'a ya shigo ta ce ya bata jikkarshi farama ta zuba kaya, ta sanya kayanta, ya cc, "Ina za ki kuma. Ta yi murmushi ta ce, "Ba ka ga mota ba a waje, tare da Hajiya Halima mu ka z0, tafiya zata vì dani gidan ta, daga can zamu wuce Abuja." Mas'ujdu ya jinjina kai ya cc. "To ni na ga mota, amma ban yi 19 tsammanin baki muka vi ba, na dauka dai ko wani ne ya ajc ta ya shiga wancan lungun, sai ki cc ke lafiya lau." Naja'atu ta yi dariya kawai, ya fidda kayanshi daga cikin jikkar ya ba ta suka fito tare zuwa cikin gida, ya zauna gefe daya yana gaida Hajiya, yayimn da ita kuma Naja'atu, ta shiga cikin daki ta zubá kayanta da 'yan abubuwan da zata bukata, ta zage ta ta aje gefe guda, sannan ta fito. Hajiya ta dube ta ta cc, "Kin gama ko? Mu tati dare nayi." Ta koma cikin daki ta fiddo jikkar Mas'udu ya taso ya karba, yayin da ita kuma ta zuwa wurin Babansu ta dan tsugunna gabanshi tana yi mashi sallama, ya cc, "Sai ki kula ki bi a sannu, ba ni son karambani, kuma ban da gardama, kinga dai arziki ne ya sanya ta nuna sha'awar tafiya dake, to don Allah ki iya kanki ki tsaya matsayinki, kada ki kuskura in ji wani abu na rashin kyautawa ta taso daga gare ki, Allah ya kiyaye hanya." Ta jinjina kai, sannan ta taso ta yì ma Inna sallama, har suka fito Inna na gargadinta akan tabi a sannu, ban da karambani, yayin da ita kuma Hajiya ta cika su da iyayen kudi, kowa da nashi, haka suka rabu cikin dadin rai, Malam Abdu ya rinka nanata mata kalmar ta yi hakuri zama da yaro sai an kai zuciya nesa. Lokacin da suka isa gida karfe goma saura, Daddy ne kadai kwance bisa kujcra, yana kallon wasan kwallon kafa. Hajiya ta nuna mata dakin dake kusa da na ta ta ce ta shiga da kayanta ciki, nan zata zauna, ta wuce da jikkarta cikin dakin ta ajc, dakin yana da 20 girma talkeken gado ne na ba kin Karfe cikin dakin sai madubi da kujera daya itama ta bakin karfen, akwai ba yi a ciki ta bude dirowar bango ta saka kayan gefe daya saboda akwai manyan jikkuna ciki ga alama nan ma kayan sanyawa nc. Da ta ajc ba ta fito ba, sai da ta yi sallar Isha'i, sannan ta cire hijabin ta linke ta aje gefe daya, sannan ta fito cikin falon in da Hajiya take zaune ita da Daddy, ko kallonta bai yi ba, haka itama ba ta damu da shi ba, shi kadai ne take ganin zaya zame mata matsala a gidan, to shi din ma ba damuwa ta yi da shi ba, ai sai dai ta shiga harkarshi ne zaya yi mata. Kafin ta zauna Hajiya ta ce ta shiga kicin ta fiddo masu abinci, sai lokacin ta tuna-ba su ci abincin dare ba, rayuwar gidan dabance, kalaci sai sha biyun rana, haka na rana sai wajen la'asar. Suka ci shi, yanzu kuma na dare sai karfe goma. Kan tabur ta shirya kayan abincin, sannan ta koma kicin dauko ruwa, da ta dawo daga Hajiya har Daddyn sun hau tebur din suna zubawa, ta aje farantin itama ta zauna sai da suka gama diba sannan itama ta zuba kadan Hajiya ta rinka yi mata fada, kan ta saki jiki ta ci abinci nan gida ne ba ta son zama da yunwa musamman ta dare. Naja'atu ta ce, "Allah kuwa Hajiya wannan ya ishe ni." Ta ce, "Shi kenan." Ta rufe sauran suka ci gaba da cin abincin, tana lura da Daddy ya daure fuska sosai, ba ya magana sai ita da Hajiya ke hira jefi-jefi. Zuwa can wayarshi ta yi kira, ya dauka ya duba sai ya yi murmushi ya dauka yana magana a hankali 21 cikin kwantar da hankali ya cc "Kada ki damu, insha Allahu ina nan tafe gobe, nima Katsinar ta ishe ni." Ya dan yi shiru, sai kuma ya yi dariya yana shafar kai, а hankali ya yi satar kallon Hajiya ba ta damu da harkarshi ba, ya ce "Ke ki ke ganin haka, kiyi hakuri idan na iso zamu tattauna komi, baye bye ok good night." Ya rufe wayar yana murmushi ya ce da Hajiya, "Mummy Farida ce ta ce a gaida ki." Hajiya ta skai fuska tana murmushi ta ce, "Ina amsawa, nasan dama saboda ita ne kake ta wannan rawar jikin tafiyar ka tafi ka barni ni daya." Ta dubi Naja'atu tana dariya, ta ce, "To ai nima ga tawa diyar nan na dauko, sai ka tafi Allah ya kiyaye hanya." Bai sake cewa komi ba har suka kare cin abincin, Naja'atu ta kwashe kwanonin ta maida kicin, sannan ta dan zauna falon kadan amma barci ya taho don haka ta yi ma Hajiya sai da safe, ta raba ta gefen kujerar da Daddy yake zaune ya bita da ido kawai, ta bude daki ta shiga abinta. Sai ya cije lebe yana kada kai mamakin daukar da yarinyar ta yi mashi ya ke yi ta raina shi da yawa, duk sarda ya kalle ta sai ta yi mashi, kallon banza, to baya son ta raina shi ne don haka baya biye mata. Washe gari tunda safe ta tashi, bata saba da irin wannan barcin ba, mutum yai ta kwanciya har rana cikin daki ta tsiri goge-goge ta wanke kewayen dakin wai duk don ta rage lokaci, har karfe tara ta fito bata ji motsin kowa ba, Hajiya ba ta tashi ba, to ita kam ta gaji 22 don haka ta fan zauna cikin falon shiru, to sai kuma ta shi ta isa wajen da kayan kallo suke, ta rinka binciken kasasuwansu, ta ci sa'a ta samu DVD, na kira'a sai ta hada wuta ta kunna kira'ar tana fita a hankali, muryar Shcik Ahmed Sulaiman cc, ta koma ta kwanta tana bi. Karatun yana yi ma ta dadi, ta shagala sosai, lokacin shima ya fito daga cikin dakinshi, har yazo ya zauna ba ta sani ba, sai dai ta ji muryarshi yana magana kan waya, a hankali ta sauke hannuntà da ta rufe fuska tana kallonshi, shima ita yake kallo, sai ta tabe baki ta maida idanuwanta ta rufe. Har ya kare wayar yana kallonta, yanzu ya daina mamakinta dariya take neman sanya shi ya rasa dalilin wannan fushin da take yi mashi, ta cika riko abu baya wucewa wajenta koda yake wasu abubuwan da take yi harda yarinta, amma shi bai ga laifinshi ba, a nan, ya rufe wayar ya saka cikin aljihu, yana kallonta ya ce, "Ke." Ta. sauke hannunta tana kallonshi ya ce, "Wai ke ba ki iya gaisuwa ba ne.?" Ta zuba mashi ido kawai, ba ta ce komi ba, ta yunkura ta mike tana shirin tafiya, da saurinshi yasha gabanta har ta ji tsoro ta tsaya tana kokarin maida lumfashi, ya tsare ta da idanuwanshi babu wasa ya ce, "Ina yi maki magana, shi ne za ki tashi." Ta sarda kai ba ta ce komi ba, ya ce, "Wai me kika taka ne? Da za ki rinka hararata, ni fa ba abokin ki ba ne kin sani." Тa сe, "Тo in kasan haka tunda ban shiga harkar ba, kaima sai ka fita tawa ka yi harkarka, ko ko nace 23 dole sar ka tanka mani?" Ya girgiza kat yа ссe, "Вa ki ce ba, amma tunda gashi Allah ya hada mu zama wuri daya dole ne in yi maki magana don ni ban iya gaba ba, sai dai kuma dole ne ki shiga hankalinki, tunda gaba na ke da ke." Ta yi shiru ba ta ce komi ba, ya tsaya kawai yana kallonta, mamakin yarinyar yake yi, tana cin sa'arshi ya ce, "Yanzu shiga ki fadi ma Hajiya na ce na fito." Ta tsaya shiru kamar ba za ta je ba shima bai sake magana b a ya koma ya zauna yana kallonta to itama da ta duba sai taga abin da take yi bai dace ba, ko ba komi gabanta yake, haka nan yanzu a karkashinsu take zaunc, dole ne ta rinka daratta shi, in dai tana son ta zauna lafiya, sai dai zancen shiri tsakaninshi da ita babu shi har abada, ra'ayinsu bai zo daya ba. Ta sanya kai ta dan kwankwasa kofar dakin Hajiya ta shiga har yanzu kwance take a hankali ta bude ido tana kallon Naja'atu, yayin da ita kuma ta dan rusuna tana gaida ta, ta ce, "Naja'atu lafiya dai ko.?" Та cc, "Lafiya lau, Daddy ne ya ce a fadi maki ya fito." Hajiya ta yi murmushi ta ce, "Ni wallahi har na manta da tafiyar shi, shi kenan ki ce mashi ya dan jira ni, bari in yi wanka gani nan fitowa, sai ki shiga kicin ki sama mashi abin da zaya ci, ba ni son ya hau hanya da vunwa." Ta amsa "To." Ta fito, yana nan zaune in da ta bar shi, sai ta dan dafa kujera tana kallonshi, ta ce, "Та ce ka jira tana fitowa yanzu." Bai ce komi ba. Abin da tafi tsana kenan rainin wayau, yarda ya nuna kamar ba da shi take magana ba, alhalin shi ne ya aike ta, don 24 haka ne ta ke yi mashi haka, don in ta ce zata rinka binshi tana kwantar da kai yarda yake so to wahalarshi zata sha. Da wannan tunanin ta shiga kicin ta yi tsaye tana kalle-kalle ba ta san ta ina zatga fara ba, sai ta hango files din ruwan zafi ta duba, cike yake da ruwan zafi ta aje gefe daya, ta hada kayan tea da bread, ta dauko tazo ta ajc mashi, kallonta yakc yi kawai ta koma ta dauko filas ta aje mashi tana shirin tafiya, ya ce "Ni ki ka kawo ma wa:?" Ta daga kai, sai ya yi murmushi karo na farko kenan da ya dan sakar mata fuska, ya ce "To amma sai ki kawo kaya ki aje mani kamar kin kawo ma kurma, ba bayani." Ta kara faure fuska tana kallon wani sashin, bai sake magana ba, don haka itama ta yi tafiyarta cikin daki tga kwanta, tana jin shi da Hajiya suna sallama, har ya tafi bata sake fitowa ba, sai ta ji gidan ya yi mata dadi, dama shi ne matsalarta, ta saki jiki sosai yayin da Hajiya ta rinka nuna mata gata tana janta jikinta, a kalla sai da ta yi mata sabbin dinkuna kala biyar masu tsada, sannan ta kara mata wasu cikin diyarta Ummi da ke karatu A.B.U ai don da nan Naja'atu ta kara zanzarewa, ta fito sosai kamar ba ita ba, hutu ya samu Hajiya ba ta so taga tana aiki cikin gidan fada take yi, ta ce "Meye amfanin 'yan aikin da suka aje, ba ta dauko ta ba ne don ta yi mata wahala." Ita kau Naja'atu ba ta saba da zaman ba ne, to tun zaman na isarta har ta kai ta fara sabawa, itama ko ta tashi ba ta fitowa sai rana ta yi, 25 amma duk da haka takan yi wasu 'yan aiyukan da basu taka kara suka karya ba, kullum rana ita ke gyaran dakin Hajiya da kewayenta, to da yake ba yara gare ta ba, ko ina fes yake, sai dan abin da ba'a rasa ba. Kwananta takwas gidan Hajiya ta ce, "Ta yi shiri washe gari zasu tafi Abuja, da daddare ta sanya direba ya kai ta gidansu ta yi sallama da iyayenta, daga Inna. har Babansu suka taru suna yi mata nasiha tare da gargadinta, akan ta aje rayuwarta matsayinta kada ta dauki girman kai rawanin tsiya ne." Ta yi masu alkawari, suka yi mata fatan alkairi, gaba ki daya suka yo mata rakiya, ta shiga dankareriyar motar gidan su Hajiya, suka taho tana daga masu hannu. Washe gari kuma sai karfe sha biyu suka bar Katsina zuwa Abuja, ita ke zaune gaba kusa da direba, yayin da ita kuma Hajiya take kwance baya, sanyin A.C na ratsa su, yayin da direban ke ta aikinshi, sai zuba gudu yake yi, amma tafiyar a natse. Karfe biyu suka tsaya Zaria, makaranta wajen Ummi, sai dai ba su bata lokaci ba suka dauki hanya, gaskiya Naja'atu ta yaba da halayyar yarinyar, ta karbe ta hannu bibbiyu bata da girman kai irin na Daddy, tana da son mutane yun kafin Hajiya ta yi mata bayaninta ta fara tambayarta, sunanta. Hajiya ta fadi mata ai shi kenan ta rinka janta da hira, har tana rokonta akan kada ta tafi sai tazo hutu. Hajiya ta yi dariya ta ce, "Kwantar da hankalinki Naja'atu ta dawo hannuna kenan sai aure zaya raba mu." Tana kallonta tana dariya, to itama dariyar kawia tayi, bata san irin 26 daukar da matar ta yi mata ba, tana nuna mata kulawa sosai, don haka itama har cikin ranta kaunar matar take yi. An gama sallar Isha'i suka shiga garin Abuja, gaskiya birnin ya kayatar da Naja'atu, ta rinka mamakin tsarin garin, lallai kam an ci gaba sosai a Nigeria, ba ta yi tsammanin haka ba, ta saki ido sosai ta na kallekallenta ba ta san in da akc zuwa ba, sai dai ta ji an tsaya bakin wani gida ana yi hon. Maigadi ya bude get yana yi masu sannu da zuwa, yayin da motar ta shiga ciki, bakin kofar shiga gidan ta isaya lokacin Daddy ya fito daga cikin gidan shi ya bude ma Hajiya kofa ta fito yana yi mata sannu. Naja'atu ta kalle shi kawai, ba ta cсе komi ba, ya kamo hannun Hajiya suka shiga ciki, yayin da ita kuma ta tsaya ta dauki jikkar Hajiya ta hannu da 'yan tarkacen da ke kusa da ita, sannan ta bi bayansu zuwa cikin falon, shima ya kayatu sosai ba sai an yi bayani ba. Hajiya ta nuna mata wata kofa ta ce, "Shigar mani da jikkar ciki, sai ki ciro mani wayata daga cikin jikkar ki taho mani da ita." Ta amsa "To." Ta shiga dakin, shima ya tsaru wani dunkulallen gado ne dan Italiya, ya yi kyau komi ya tsaru babu tarkace, kai lallai masu kudi na jin dadi. Ta aje jikkar ta fiddo waya ta dawo falon lokacin direban yake shigowa da kayansu, don haka ta kwashi na Hajiya ta kaisu cikin dakinta da ta fito Hajiya ta nuna mata wata kofar ta ce, ta kai nata ciki, fakin Ummi ne, ta shiga shima fakin ya tsaru gadon iri 27 daya ne da na dakin Hajiya, ta shirya kayan ba ta fito ba sai da ta watsa ruwa, ta dauro alwala ta yi sallolin dake kanta, to sai ta sanya jallabiya marar nauyi, sannan ta fito falon Hajiya ta cc, "Da kyau Naja'atu, har kin yi wankanki ko? Ta yi murmushi kawai ta dubi Daddy kallonta kawai yake yi ba ta ce mashi komi ba, Hajiya ta ce, "Bari nima in shiga in dan watsa ruwan in fito mu ci abinci. Ta tashi ta shige cikin faki, don haka suka zauna su kadai cikin dakin. babu wanda ya yi ma wani magana tana nan zaune Hajiya ta kwalla mata kira, ta shiga dakin da sauri ta ce, "Kice ma Daddy yaje ya dauko Ibrahim yanzu." Ta-fito ta same shi yana kallon Kwallon kafa, ta ce, "Hajiya ta ce kaje ka dauko Ibrahim." Ya yi shiru kamar bai san tana magana ba, ta dan tsaya tana kallonshi, tasan dai ya ji abin da ta fada, to sai ta rabu da shi ta yi zamanta, shiruj-shiru bai tashi ba ta sake yi mashi magana, ta ce, "An ce fa ka je ka dauko Ibrahim." Ya juyo yana kallonta, muryarshi a hankali ya ce, "Wai don Allah me ki ka dauke ni, tunda ki ka zo gidan nan baki yi mani magana ba sai yanzu." Ya yi shiru, sai kuma taga kamar bata kyauta ba, ta cе, "To amma Daddy daure mani fuska kake yi yaya kake so in yi da kai.?" Ya cc,"Ba wani daure fuska, ki dai ce kin raina ni ne kawai." Ta yi murmushi ta ce, "wallahi har abada babu raini tsakaninmu, ban ga fuska ba ne, idan na kalle ka naga ka daure fuska, sai raina ya baci, don 28 haka kaga ina yin shiru." Ya girgiza kai ya cc, "To gaskiya ba ni jin dadin abin da ki ke yi mani ki daina." Ta jinjina kai, ya ce "Yanzu muje ki raka ni a dauko shi, gidna wani kanin babanmu ne yake can Maitama." Ta yi murmushi ta ce, "Don Allah kayi hakuri, na gaji da yawa." Ya zuba mata ido, sai kuma ya jinjina kai ya aje remote fin dake hannunshi kan kujera, ya dauki makulli ya fice yana ce mata "Sai na dawo." Ta zauna shiru tana mamakin halayyar Daddy, miskili kafi mahaukaci ban haushi, yau kuma 'yan kirkin yake ji. Hajiya ta fito ta sanya ta fiddo kayan abinci daga kicin kukun gidan ne ya girka, abinci lafiyayye tuwon shinkafa miyar agushi, yasha naman kaji da na sa tsoka zalla ga kuma kifi, naman har ya fi karfin miyar, ta rinka mamaki a ranta sai ka ce abincin Yarabawa, suke irin wannan hadin. Suna tsakar cin abinci su Daddy suka dawo tare da Ibrahim ya kama Hajiya ya rike gam yana murnar dawowarta itama ta rinka shafa kanshi cike da kulawa tana lallashin dan auta, da banne ga alama ana ji dashi. To ranar hirar ta dan yi ma Naja'atu dadi, saboda Daddy ya saki jiki sosai ana hira da shi, duk da cewa ba ta cika sanya masu baki ba, idan ya yi magana yana kan sako ta, haka nan idan an yi abun dariya tana taya su. Hajiya ta ji dadi sosai da taga tana sakin jikinta sai da dare ya yi sosai, sannan suka kwanta, sai lokacin ta gane abin da ke sanyawa suna yin barciu da safe, ashe basu kwantawa da wuri. Ga mamakinta itama da kyar ta 29 tashi ta yi Sallah da asuba, ta koma ta kwanta ga gajiyar tafiya don haka barcin ta yi sosai sai sha daya ta tashi. Mamakin barcin da ta yi ta yi, da kyar ta shiga kewaye ta yi wanka, sannan ta shirya ta fito. Hajiya na zaune cikin falon da wata yarinya ta ida rufe kofar ta iso in da suke, tana gaida Hajiya, Hajiya ta yi murmushi ta ce, "Naja'atu duk gajiyar ce yau ta kwantar dake, ke da ba ki barcin safe." Ta yi murmushi tana kallon yarinyar, kyakkyawa da ita fara sai dai da gani idanuwanta a bude suke, haka nan sai taji jinintga bai hadu da ita ba, amma ta daure ta gaida ta, itama kallon Naja'atun take yi, Hajiya ta ce mata "Farida ga Naja'atu diyata ce daga Katsina na taho da-ita." Ta juya kan Naja'atu ta ce "Wannan ita ce Farida, in Allah ya yarda ita ce matar Yayanki Daddy." Naja'atu ta kara kallon yarinyar a karo na biyu, sai ta dan yi murmushi ta cе mata "sannu." Itama dai babu wani sakin fuska ta amsa. Sai ga Daddyn ya fito daga cikin daki, ta gaida shi, Hajiya ta ce, "kije ki yi kalaci, mun yi tun dazu." To sai ta nufi teburin cin abinci ta zauna tana kalacinta, yayin da shi kuma Daddy ya zauna don haka Hajiya ta tashi ta koma cikin daki, ta bar su suna hirarsu. Naja'atu ta ci gaba da kalacinta tana satar kallon su Daddy, sam ita dai yarinyar ba ta yi mata ba, wayewar ta ta yi yawa tun akan suturar dake jikinta, ta raina mata, a ganinta ko tana sanyawa tunda zata zo gidan surukai ya dace ta sanya kayan kirki, wani material ne bula a jikinta, daga einkin siket din har na rigar sun matse mata jiki kamar 30 zata kare a ciki, gashi dinkin an bi an yayyaga shi sai kacc tsumma, kuma babu mayafin kirki ga gashin kanti a kanta, kamar kwancen hauka. Da ta kare mata kallo tsab,m sai taga hatta farin nata ta kara shi da man kanti, tana jin maganarta daga in da take babu wani kamun kai, sar kace fiyar yare." Ta taße baki ta ci gaba da cin abinenta abin da babu ruwanka ciki, babu ruwanka har abada ita dai 'yar kallo ce. A hankali ta sauke kwayar idonta akan Daddy, yana kallonta da wani irin yanayi, sai ta ji gabanta yana faduwa, ta sauke kai amma duk sai taji ta takura da kyar ta kare cin abincin ta tashi ta koma cikin daki. To har aka yi sallar azahur Farida na gidan, suna hira da Daddy cikin falo, Naja'atu ta rinka mamakin wannan wace irin rayuwa ce? Mai da kai bayan har ya yi yawa, ba zata bari yaje gidansu ba, sai ita ce zata zo? Kuma ko kunya babu ta yi zaune, koda yake ta lura shima yana sonta, don haka duk abin da zata yi ba zaya ga laifinta ba. Bayan ta gama Sallah, cikin daki ta dan murza ma hannuwanta mai ta gyara fuskarta ta fito ta raba su, ta shiga kicin in da kukunsu Mick yake aikin abinci, nan ta zauna tana kallon tsarin girkinshi, suna hira a hankali idan taga abin da bata gane ba, sai ta yi mashi tambaya shi kuma ya bata amsa cikin dan lokaci suka shaku ta shiga cikin harkar girkin tana taimaka mashi. Yana da kirki da sakin fuska, don haka ba ta samu matsala ba, ta kwantar da hankalinta tana daukar darasin girki, itama wata makarantar ce. 31 Da aka kammala, ta rinka jidowa tana shiryawa bisa tabur, har yanzu suna nan zaune, Daddy na kwancc bisa kujera, yayin da ita kuma take zaune bisa kujera karama, bata da alamar tafiya. Idan ya kalli Naja'atu sai ta dauke kanta kamar ba ta ganshi ba, sai da komi ya kammala sannan taje ta dan kwankwasa kofar dakin Hajiya, ta bata iznin shiga, ta shiga ta sanar da ita abinci ya kammala, Hajiya ta ce, "Ina Daddy yakc.?" Ta yi murmushi ta ce, "Suna nan zaune cikin falo." Hajiya ta dan tabe baki, ta ce, "Wai Faridar bata tafi ba har yanzu.?" Та се, "Тa na nan." Hajiya ta jinjina kai ta cc, "To Allah ya kyauta, wannan bayar da kai har ina? Ji ki zuba mani abincin, ki kawo mani kema ki zauna ki ci kada ki biye masu." Ta dawo falon ta shirya mata abincin akan faranti, ta dauka ta kai mata, sannan ta fito, to kuma sai taga kamar bata kyauta ba idan ta zauna tana ci ba tare da.ta yi masu magana ba, don haka ta isa in da suke, Daddy ya zuba mata ido, ta ce, "Ga abinci idan kun tashi cі." Ba ta jira amsa ba, ta tafi ta zauna tana zuba abincin." Sai gasu sun taso, da ta gama zuba nata, ta aje masu, Daddy ya ce, "Ba ki zuba mani ba." Ta yi murmushi ta ce, "Ba aikina ba ne." Ta dubi Farida tana murmushi amma sai taga ta daure fuska, yayin da shi kuma Daddy ya sanya hannu ya dauki wanda ta zuba ma kanta, bai yi magana ba ya fara ci, ta bishi da ido kawai, ya share ta sai ta girgiza kai ta dauki wani filed din ta zuba ta nuna ma Farida abincin ta ce, "Bissimillah." Amma sai 32 ta girgiza kai ta ce, "Alhamdulillahi." Daga ita har Daddy suka zuba mata ido yanayinta ya canza-sosai, ya yarda duk wanda ya dubc ta zaya gane. Daddy ya ce, "Lafiya zaki ce kin koshi, alhalin ba ki ci komi ba." Naja'atu ta ce, "Laifinka ne, ita ce bakuwa ita ya kamata ka fara ba, amma ka janye nawa kana ci, kanka kadai ka sani ba dole ta

Chapter 2 of 6