Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 8
cewa yaron nan da yiwa matsafi Shamrul tambaya akan addininsu za'a yanke wa hukuncin kisa, sai suka yaɗa labarin izuwa cikin gari, nan fa al'ummar gari suka dinga tuttuɗowa suna cincirindo a fadar domin su ganewa idanuwan su. Domin a yau ne zasu tantance shin tsakanin Ubangijin wannan yaro Imran da matsafi Shamrul wane ne na abin bauta na gaskiya. Sarki Ladiyas na kammala wannan batu sai sarki Ladiyas ya koma kan karagar mulkinshi ya hakimce. Kawai sai wani garjejen ƙato ya ɗauki yaro Imran ya ɗora a jikin wani zagayayyan tudu a fadar sannan ya koma gefe guda RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 107 ya ja ya tsaya, sarki Ladiyas ya yi wa sarkin yaƙi Darusu inkiya ta wutsiyar idanu dake nuna bashi umarni. Cikin dakewar zuciya gami da zafin nama sarkin yaƙi ya zare wata sharɓeɓiyar adda a gadon bayanshi ya durfafi inda Imran yake domin ya datse wuyanshi. Sarki Ladiyas, matsafi Shamrul da sauran bokayen suka bushe da dariyar mugunta har da ƙyaƙyatawa. Jama'a kuwa da yawan su sai suka fara zubar da hawayen takaici da baƙin ciki Ya yin da sarkin yaƙi ya isa daf da shi sai ya daga addar ya ɗora akan waya yaro Imran. Kwatsam! Bazato babu tsammani sai aka ga wata kyakkyawar halitta ta keto daga saman fadar ɗauke da waɗansu mutane guda biyu. Ba wani bane wannan halitta da mutanen biyun ba face aljani Hadimul-khairi ɗauke da gimbiya Lamrat matar sarki Ladiyas da 'yarta yarinya Shuraiba. Kafin addar sarkin yaƙi Darusu ta yanka wuyan Imran aljani Hadimul-khairi ya ɗauko wata farar kwalba mai ɗauke da wani koren ruwa ya watsa inda Imran da baiwa Sharifa suke, take sarƙoƙin dake ɗaure a jikkunansu da addar dake wuyan Imran sun narke suka zama ruwa. Cikin matuƙar firgici sarkin yaƙi, sarki Ladiyas da sauran jama'ar fada suka ɗaga kawunansu izuwa sama. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 108 Yaro Imran, hadima Khadijat, sarki Lazwar, sarkin yaƙi, bawa Shamsal, gimbiya Mashlira da aljani Za'aratul-layal, kuwa sai suka cika da matukar farin ciki maral-musaltuwa. Aljani Hadimul-khairi ya a sauka a turba bisa diga-diganshi. Nan fa aka shiga kallon-kallo tsakanin sarki Ladiyas, da uwar gidanshi gimbiya Lamrat, matsafi Shamrul da yaro Imran da hadima Khadijat wato baiwa Sharifat, sarkin yaƙi Darusu da sarki Lazwar. Cikin matukar ɓacin rai mai girma Ladiyas ya dubi uwar gidanshi Lamrat ya ce "ya uwar gidana shin ina dalilin wannan zuwa naki a cikin wannan yanayi? Koda jin wannan tambaya daga bakin Sarki Ladiyas sai gimbiya Lamrat ta tari numfashinshi tana mai daka mashi tsawa, ta dube shi cikin matuƙar fushi ta ce "kai tsohon AZZALUMI kuma la'ananne ka yi sani yanzu kan mage ya waye, a yau ne zan ɗauki fansar jinin mai gidana maƙeri Murrasu daka ni da 'yata Shuraiba, haƙiƙa masu iya magana sun yi magana da suka rana dubu ta ɓarawo, rana ɗaya ta mai kaya, ka yi sani cewa tsawon shekarun da ka shuɗe kana azabtar da jama'ar birnin ISTANBUL kana yiwa mutane BAKIN ZALUNCI, to ranar ƙin dillanci ta zo maka. Shawarar da zan baka ita ce ka yi hanzari ka rubuta wasiyyar da kake son bar wa jama'ar kafin mu zare maka ruhinka daga gangar jikinka. Sannan ina so ka yi sani cewa ni da 'yata Shuraiba tuni mun karɓi addinin yaro Imran. A halin yanzu ni ba uwar gidanka ba ce face abokiyar gabar ka, dama dai-dai da rana ɗaya ban taɓa ƙaunarka kawai ina yi maka biyayya ne bisa dole don tana din gobe na". RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 109 Sa'adda mai girma Ladiyas ya ji wannan batu daga bakin gimbiya Lamrat sai zuciyarshi takama tafarfasa tamkar zata ƙone ya daka mata tsawa a lokacin da idanuwanshi suka kaɗa suka yi jajur cikin kakkausar murya mai ya ce "kaicon ki yake Lamrat haƙiƙa kin tafka babban kuskure da har kika yi gangancin haɗa kai da maƙiya na domin farautar rai na, a yau ne zan yi maki hukunci mafi muni ke da 'yarki Shuraiba". Sa'adda sarki Ladiyas ya zo nan azancen shi sai ya miƙe tsaye zumbur daga kan karagar shi ta mulki ya cire alƙyabbarshi, take wata irin gagarumar shigar yaƙi mai matuƙar firgici da ban tsoro ta bayyana a jikinshi. Kawai sai ya dako wawan tsalle daga inda yake tsaye yana saman ya daga hannunshi sama wata irin sharɓeɓiyar takobin sihiri ta bayyana a gare shi, ya sauka bisa diga-diganshi a daf da inda Lamrat take. Koda ganin hakan sai yarinya Shuraiba tayi wuf ta zare kwari da bakanta ta yi shirin ko ta kwana. Sarki Lazwar kuwa duk da cewar jikinshi ya yi tsami akwai manyan raunuka, amma sai ya yi wuf ya kwaci wata takobi a hannun wani badakare ya falfala da azababban gudu izuwa kan sarkin yaƙi Darusu Baiwa Sharifa da yaro Imran kuwa sai suka yi ɗauki izuwa kan matsafi Shamrul suna masu ƙwala kabbara, bawa Shamsal da sarkin yaƙi kuwa sai suka tari dakarun dake fadar, aljani za'aratul-layal sai ya yi girgiza take surarshi ta canja daga ta bil'adama izuwa ta aljani kawai sai ya rufawa mai gidanshi sarki Lazwar baya, a lokacin ne gimbiya Mashlira sai cire hular ƙarfen dake kanta fuskar ta ta bayyana a fili, nan fa kowa ya cika da mamaki RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 110 ganinta, kawai sai ta yi koyi da aljani Za'aratul-layal ta kaiwa masoyinta sarkin Lazwar ɗauki. Lokaci guda ɓangarorin biyar suka afkawa juna aka garƙame da azababban yaƙi mai matuƙar muni da ban tsoro. Wohoho! kaico haƙiƙa guguwar annoba idan ta taso babu mai maganin ta face Allah, kuma tabbas in da babu ƙasa nan ake gardamar kokowa, domin KARON MAZA sai JARUMAN DUNIYA da suka ciri tuta a GUMURZUN SHEKARA DUBU, waɗanda komai TSANANI DA UKUBA a filin DANDAZON MAYAKA baya sa su gudu. Haƙiƙa komai dakewar zuciyar mutum idan ya ga yadda fadar ta yamutse da gumurzu dole ne ya ɗimauce ya fita daga hayyacin shi domin dola ne artabun ya zamo tashin hankali. Nan fa jama'a suka ɗimauce suka kama guje-guje da ifice-ifice domin tsira da rayukansu Ɓangarorin suka wanzu suna kaiwa juna miyagun hare-hare cikin matuƙar baƙin zafin nama JURIYA DA BAJINTA tamkar jikkunan su basu kasance na bil'adama mai jini tsoka ba. Kaico! Haƙiƙa duk wanda bai fita filin yaƙi ba to bai ga ƙarshen tashin hankali ba, wanda bai san shi ba shi ne yake fatan zuwan shi, ana fara wannan ɗauki ba daɗi ne gimbiya Lamrat, yarinya Shuraiba da Aljani Hadimul- kahiri suka fara gane cewa tabbas shayi ruwa ne ba abinci mai nauyi ba, domin kuwa tsananin zafin naman sarki ladiyas ya nunka nasu sai arba'in, Nanfa ya zamana cewa mutum uku sun kasa galaba akan ɗaya ya zame masu alaƙaƙai, duk sa'adda suka kai mashi hari RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 111 da makaman smmsu idan ya kare da takobinshi, sai kaga makaman sun dakushe kuwa ko gezau bai yi ba. Idan kuwa Ladiyas ya kai masu harin idan suka goce sai ya zamana cewa duk abin da takobin ta saran sai ya yi bindiga ya tarwatse koda kuwa gini ne. Matsafi Shamrul, yaro Imran da hadima Khadijat kuwa tuni labari yasha banbam, domin kuwa sun hana tsafi Shamrul rawar gaban hantsi, har sai ya zamana cewa ya daina amfani da makami ya dawo yaƙar su da ƙarfin sihirin tsafi, domin wani lokacin idan Imran da Khadijah suka sare shi ta takubban su sai su ga raunin ya koma ya haɗe sumul, wasu lokutan ma sai ya rikiɗa ya zama haske. Sarki Lazwar, gimbiya Mashlira da aljani Za'aratul-layal kuwa sun wanzu suna masu kaiwa sarkin yaƙi Darusu harehare cikin gwanintar yaƙi tamkar za su cinye shi ɗanye. Amma bisa mamaki sai ya zame masu ƙadangaren bakin tulu suka kasa samun nasarar koda lakutar jikinshi, duk kuwa da cewar ƙarfin mutum biyu ne da aljani ɗaya akan mutum guda. A ɓangaren bawa Shamsal da sarkin yaƙi ku wa sun wanzu suna ragargazar dakarun dake fadar duk inda suka sanya gaba sai ka ga dakarun na zubewa ƙasa matattu, nan fa ƙarar karafniyar ƙarafa, ihun mazaje hade da hargowar aljanu gami da ifice-ificen jama'a ya cika dodon kunne, ƙura ta turnuƙe fadar baki ɗaya tamkar haɗari zai gangamo a kece da ruwan sama. Lokacin da aka ruguntsume da azababban yaƙi tsakanin manyan sarakuna biyu, aljanu biyu, gami da jarumai RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 112 shida sai yaƙin ya zamto tashin hankali gami da ban tsoro ga yan kallo. Sai da aka shafe tsawon sa'a biyu ana wannan ɗauki ba daɗi tsakanin jaruman ba tare da ɗayan su ya samu nasarar hallaka ɗaya ba. A bangaren sarki Ladiyas kuwa ya zamewa su gimbiya Lamrat ANNOBA ƊARI domin duk da cewar Hadimul-kahiri na amafni da addu'o'i domin su hallaka sarki Ladiyas amma sai hakan ya gagara domin sai sun datse wuyanshi suna tunanin ya mutu sai kawai su ga wani ruhun ya keto daga cikin ƙarƙashin ƙasa ya sake shiga jikinshi. Sai kuma a ɗora wani gumurzun, nan fa ya zamana cewa su Hadimul-kahiri sun kashe fiye ruhika arba'in na sarki Ladiyas. Al'amarin da ya sanya su duka ukun suka samu miyagun raunuka musamman yarinya Shuraiba. Haƙiƙa sarki Ladiyas bakaramin hatsabiba ne domin ya yi nisa a halarar tsafi wanda cimma mashi abu ne mai matuƙar wahala. A dai-dai wannan lokaci ne yaro Imran da hadima Khadijat suka samu nasarar hallaka matsafi Shamrul, ta hanyar amfani da takubbansu suka soka mashi akan ƙawon zuciyarshi, ya yin da suka hango su yarinya Shuraiba kuma suka ga irin mugun halin da suke ciki sai suka kai masu ɗauki. Nan fa ya zamana cewa labari ya sha bamban domin a wannan karon sai ya zamana tasirin sihirin dake tare da sarki Ladiyas ya fara karyewa, domin duk sa'adda hadima Khadijat da yaro Imran suka kai mashi hari da makamansu duk inda suka sara sai su ga sun tsarga jikinshi. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 113 Bisa taimakon Ubangijin halitta daƙyar da siɗin goshi suka samu nasarar hallaka sarki ladiyas, ta hanyar sare mashi hannaye da ƙafafuwanshi suka jefar da gawarshu a ƙas. In da ace mutum ya na wannan waje a lokacin da sarki Ladiyas da matsafi Shamrul suka yi mutuwar wulakanci dole ne ya yi farin ciki maral-musaltuwa. Bisa ganin yadda Allah Ubangijin halitta ya kawo ƙarshen azzalumai. A dai-dai wannan lokaci ne su gimbiya mashlira, Aljani Za'aratul-layal da sarki Lazwar suka samu nasarar hallaka sarkin yaƙi Darusu. Sa'adda al'ummar fadar da su bawa Shamsal suka yi arba da gawar sarki Ladiyas, da ta matsafi Shamrul sai dukkanin su suka durƙusa ƙasa bisa gwiwoyinsu suka yi mubaya'a, suna masu cewa "haƙiƙa mun bayar da gaskiya ga Ubangijin yaro imran Cikin hanzari waɗansu likitoci suka shigo fadar ɗauke da kayan aiki suka shiga duba lafiye yarinya Shuraiba, gimbiya Lamrat,da sarki Lazwar. Sannan yaro Imran ya ruga izuwa inda hadima Khadijat take suka rungume juna cikin matuƙar farin ciki maralmusaltuwa bisa sake saduwa da juna da suka tsawon shekaru. Daga bisani yaro Imran ya janye jikinshi daga na 'yar uwarshi Sharifa. Ya juya ya fuskanci jama'a sannan ya buɗi baki ya ce "ya ku al'ummar wannan birni mai albarka haƙiƙa na tabbatar da cewa a halin yanzu zukatanku sun gamsu cewa babu abin bauta da gaskiya sai Allah mai kowa mai komai. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 114 Saboda haka yanzu ba tare da wani ɓata lokaci ba yaro Imran ya faɗi kalmar shahada, take ɗaruruwan jama'ar dake fadar suka maimaita. Sautin muryoyinsu ya cika fadar kuma ya amsa kuwwa izuwa cikin birnin baki ɗaya. Bisa mamaki sai Imran da hadima Khadijat suka ji sarki Lazwar da sarkin yaƙinshi haɗe da bawa Shamsal tare gimbiya Mashlira sun amsa kalamar shahadar. Nan fa suka cika da al'ajabi, sarki Lazwar ya tako da ƙafafuwanshi izuwa inda imran da Khadijat suke ya dubi Khadijat cikin girmamawa ya ce "ya ke Sharifat Haƙiƙa rashin sani yafi dare duhu, na zo wannan birni neman ki, ashe kina tare da ni ban sani ba, yanzu ga shi na karɓi addinin Musulunci shin ina makomar tafiya ta izuwa nemo abubuwan da za su warkar da ni daga sihirin da abokin gaba ta sarki Durwazu ya yi min, na karɓi Musulunci ne domin yadda a zuciyata, na samu tabbacin ne a lokacin da nake fafata yaƙi da miyagun halittun dake cikin ɗakin duhu, inda dukkan wata dubara ta ƙwace min na nemi taimakon Ubangijin imran". Sa'adda sarki Lazwar ya zo nan azancen shi sai Sharifa, yaro Imran da sauran jama'a suka cika da matuƙar mamaki. Sharifat ta ce ''ya kai wannan sarki mai daraja ka yi sani cewa ai shi addinin Musulunci yana shafe duk abin da ya tuve, saboda haka a halin yanzu sihirin da sarki Durwazu ya yi maka ya karye. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 115 Babu buƙatar sai na taimaka maka wajen mallako abubuwan da za su warkar da kai daga sihirin, domin abubuwan da za'a mallako dukkanin su na tsafi ne. A halin yanzu zaka iya kusantar kowace irin 'ya mace kuma har ka samu haihuwa ka yarda Ubangijin musulunci kawai a koda yaushe"; Koda jin wannan batu daga bakin Sharifa wato sai sarki Lazwar ya cika da matuƙar farin ciki wanda bai taɓa yin kamar shi ba. Daga wannan ne aka ɗunguma izuwa gidan sarauta domin kowa ya huce gajiyar dake tattare da shi. A cikin wannan dare ne hirar soyayya ta ɓarke tsakanin sarki Lazwar da gimbiya Mashlira 'yar shugaban maridai, yaro Imran da yarinya Shuraiba, Sharifat da bawa Shamsal. Kuma a wannan dare ne akayi shelar naɗin sarautar yaro Imran da wazirinshi Shamsal. kafin wayewar gari ciki da wajen birnin Istanbul ya cika ya batse da jama'a baƙin sarakuna daga kowa ce nahiya da 'yan kasuwa. Tun lokacin da alfijir ya keto bayan an gabatar da sallar asuba sai jama'a suka yi tsinke a fadar maza da mata yara da manya. Sarakuna da manyan baƙi an ware masu wajen zaman su daban, haka ma na talakawa, komai dai an yi shi bisa tsari. Sarkin fadar birnin Istanbul wani dattijo ya tashi ya gabatar da jawabin maraba ga mahalar ta taro. Sannan ma'ajin sarautar RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 116 ya gabato da kayan sarauta da suka haɗar da alkyabba, rawani, kwagiri, takalmi da sauaran su. Sarkin fada Huzaifa ya ɗauki kayan ya shiga sanya wa yaro Imran a jikin shi, bayan ya kammala ne sai ya umarci yaro Imran ya je ya zauna bisa karagar mulki ya hakimce, nan fa tsananin kyawun surar Imran ya fito ƙarara yarinya shuraiba kuwa sai ta dunga satar kallon shi tana yi mashi kallo mai nuna alamun tsantsar so da ƙauna. Nan take jama'ar fadar suka yi mubaya'a a gare shi, daga bisani kuma sai aka shiga shagalin ɗaurin aure mutum shida sarki Imran da yarinya Shuraiba baiwa Sharifa da bawa Shamsal, sarki Lazwar da gimbiya Mashlira. A wannan rana anyi gagarumin shagalin da ba'a taɓa yin kamar shi ba tsawon kafuwar birnin Istanbul. Bayan an kammala ciye-ciye da tanɗe-tande, kowa ya cika cikinshi sai sarakunan da suka halararci bikin naɗin sarautar suka dunga zuwa, gaban sarki Imran suna karɓar KALMAR SHAHADA tare da jama'arsu, haƙiƙa farin ciki ya cika zuciyar kowa. Bayan tarewar angwaye uku sarki Imran, shamsal da sarki Lazwar. Sai sarki Imran ya umarci aljani Hadimul-kahiri ya ɗauki sarki Lazwar da amaryarshi gimbiya Mashlira da sarkin yaƙi haɗe da aljani Za'aratul-layal domin ya kai su izuwa birnin ZAWATUL-IFDAR, amma sai da aka fara zuwa ta birnin su gimbiya Mashlira aka musuluntar da sarkin maridai da mutanenshi kuma aka karya sihirin tsafin da aka yi masu suka RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 117 dawo ainahin siffar su irin ta bil'adama suka daina cin naman bil'adama bisa taimakon Ubangijin halitta. An yi shagalin farin cikin dawowar yar sarkin muridai gimbiya mashlira. Sai da aka shafe mako ɗaya sannan aka sake ɗungumawa aka durfafi birnin Zawatul-ifdal, amma sai aka bar sarkin yaƙi imhal domin ya cigaba da bayar da ilimin addini ga jama'ar birnin, kuma sarkin maridai ya naɗashi wazirinshi. Lokacin da aka isa birnin Zawatul-ifdal sai sarki lazwar ya cika da matuƙar farin ciki, bisa jin labarin abin da ya faru da magajin gari Yasiran da amarya Munirat wacce a halin yanzu ita ce ke riƙe da karagar mulkin birnin. Jama'a sunyi farin cikin dawowar sarki lazwar, ba tare da damuwa ba aka sake ɗaura auren amarya Nunirat da sarki Lazwar, sakamakon mutuwar angonta, amma da ƙyar da siɗin goshi sarki Lazwar ya shawo kan gimbiya Mashlira ta amince aka ɗaura auren. Sai aljani Za'aratul-layal da Hadimul-kahiri suka koma izuwa birnin Istanbul. Sannu-sannu bayan mako ashirin sai aka wayi gari matayen sarki Lazwar Munirat da Mashlira suna ɗauke da juna biyu. Farin ciki a wajen sarki Lazwar kuwa kamar ya zautu, ya dinga rabon dukiya da suturu na alfarma. Tun daga wannan rana HASKEN MUSULUNCI ya mamaye duniya baki ɗaya zaman lafiya ya wanzu, zalunci da bautar gumaka suka rushe baki ɗaya. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 118 Ƙarshe Alhamdulillah Daga mai ɗebe maku kewa a kullum da koyaushe. Mansur Usman Sufi Sarkin Marubutan Yaƙi 08137237071 FATAUCIN BAYI Rubuta labari MANSUR USMAN SUFI Lokacin da su jaruma Nabihat suka iso izuwa bakin tanatin, sai Nabihat ta ɗauko hodar banju a cikin aljihun rigarta RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 119 ta busa ta izuwa cikin tantin, jim! Kaɗan sai suka kunna kai ciki suna shiga suka tarar dakaru masu dafa abinci sun kama barci mai nauyi. kawai sai suka cire tufafin dakarun suka maye da na sannan suka rufe fusakunsu da hulunan ƙarfe. Kawai sai suka matsa izuwa inda dakarun suka ɗora sanwa akan wuta suka buɗe murafun tukunyoyin suka zazzaga wannan hodar banju a cikin, sannan suka mayar suka rufe ruf. Bayan shuɗewar daƙiƙa goma sai suka zuzzuba abincin a cikin waɗansu ƙananan akushi, suka ɗora akan farantai na azurfa, sannan juya suka fice daga tantunan suka shiga rarrabawa dakarun dake cikin jirgin ruwan abincin mai dauke da hodar banjun har suka iso izuwa inda wani sadauki yake. Nabihat ta ɗauki akushi ɗaya ta miƙa mashi ya karɓa ya bude ya sanya hannunshi ya yi loma ɗaya, kawai sai ya dubi Nabihat ya ce "ya kai Himairu ya aka yi abincin nan ya yi ɗan karen daɗi haka? Koda jin wannan tambaya sai Nabihat ta yi murmushi gami da gyaɗa kai, kawai sai ta huce gaba ba tare da bawa sadaukin amsar tambayar shi ba. Haka dai suka cigaba da rabawa dakarun abincin, har suka iso inda suka bar saduki Hushaibu. Nabihat ta ɗauki akushin ta miƙa mashi ya karɓa. Har Hushaibu ya buɗe da nufin cin abincin kwai ya ji zuciyarshi ta buga da ƙarfi, kawai sai ya yi jifa da akushin ya durfafi madafa cikin hanzari. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 120 A dai-dai lokacinne su jaruma Nabihat suka kammala raba abincin suka samu wata maɓuya a cikin jirgin suka laɓe. A fusace Hushaibu ya kunna kai izuwa cikin tantin, ai kuwa sai ya yi arba da masu dafa abincin kwance suna sharar barci babu tufafi a tare da su. Cikin matuƙar fushi gami da tashin hankali ya zare takobinshi ya ruga izuwa waje yana mai ƙwallawa sauran dakarun kira. Al'amarin da ya janyo hankalin sadauki Sharkar kenan ya zare takobinshi da nufin dakawa dakarun tsawa. A dai-dai wannan lokaci ne hodar banjun da su Nabihat suka zuba a cikin abincin ta fara bugar da dakarun suna ɓingirewa kasa suna sharar barci. Kafin Sharkar da Hushaibu su farga fiye da rabin dakarun dake cikin jirgin ruwan sun kamu da barci mai nauyin gaske, cikin matuƙar kaɗuwa gami da tashin hankali sadauki Sharkar ya cigaba da falfala azababban gudu, yana mai kurma wawan ihu Nan fa sauran dakarun da ba su kai ga cin abincin ba suka firgice suka ɗauko makaman yaƙin suka dinga fitowa daga kowace kusurwa a jirgin. Kwatsam! Bazato babu tsammani sai aka ga su jaruma Nabihat da sauran 'yan matan fursunonin sun yo fitar burgu daga maɓuyar su suna, suka yi ɗauki izuwa kan dakarun suna ihu da kururuwa mai firgitarwa. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 121 Koda ganin hakan sai dakarun suka yi ɗauki kansu suna ihu da kururuwa mai firgita DANDAZON MAYAƘA a filin daga. Inda ace mutum yana tsaye a wannan waje lokacin da waɗannan zaratan 'yan mata su ashirin kacal! Suka tunkari ɗaruruwan dakarun dole ne ya cika da mamaki kuma ya jinjina masu ya tabbatar da cewa sun cika GWARAZAN JIYA, mata masu kamar maza. Ana haɗuwa aka ruguntsume da azababban yaƙi mai matuƙar muni, ban tsoro daban al'ajabi. Nan fa gaba ɗaya jirgin ruwan ya yamutse da ƙarar haɗuwar makaman yaƙi, gami da ihu da kururuwar mazaje. Nanfa Nabihat da 'yan matan fursunonin suka wanzu suna kaiwa dakarun sara da suka cikin matuƙar zafin nama tamkar jikkunan ba su kasance na jini da tsoka ba. Cikin abin da bai gaza daƙiƙa arba'in ya zamana cewa sun samu nasarar hallaka fiye da mutum hamsin na dakarun sun rauna ta fiye da ɗari biyu. Al'amarin da ya dugunzuma hankalin dakarun kenan kuma ya fusata su ainun, bisa ganin cewa a matsayin su na GWARAZAN MAYAƘA, amma a ce 'yan mata sun zame masu alaƙaƙai kuma GOBARAR ANNOBA. Nan fa dakarun suka ZAGE DAMTSE wajen kaiwa su Nabihat miyagun hare-hare. Ana cikin wannan artabu ne wani garjejen sadauki, ya kaiwa wata daga cikin 'yan matan wani wawan sara, da nufin tsinke mata wuya amma budurwa ta sunkuiya cikin zafin RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 122 nama, takobin sadauki ta sari iska. Kafin ya sake mayar da martani, budurwar ta cire wata siriyar wuƙa a damtsenta s caka mashi a maƙogaranshi, sannan ta sanya ƙafarta ɗaya ta daki ƙirjin shi da dukkan ƙarfin ta. Saboda da matuƙar ƙarfin dukan sai da ya yi sama tamkar an janye shi da ƙugiya ya faɗa cikin tekun yana mai tsandara ihu. Kawai sai budurwar ta sake afkawa cikin dakarun ta ci-gaba da saran su. Ana cikin wannan ɗauki ba daɗi ne SADAUKi Sharkar ya samu nasarar make Nabihat ta faɗi ƙasa, magashiyan nunfashin ta na fita daƙyar, kawai sai ya sanya hannunshi ya damƙo wuyanta ya tattare dukkanin karfinshi da nufin karya wuyan Nabihat. Kwatsam! Bazato babu tsammani sai aka ga Nabihat ta dunƙule hannayen ta biyu ta girɓawa sharkar naushi a fuska. Saboda matuƙar ƙarfin naushin sai da ya yi katantanwa a sama sau uku, sannan ya kife a ƙasa, yana mai tsandara ihu sakamakon zafi da zugin da ya ji, haƙorinshi guda ɗaya ya yi fitar burgu daga cikin bakinshi jini ya yi tsartuwa. Amma saboda karfin zuciya gami da juriya irin ta manyan GWARAZAN JIYA sai miƙe tsaye zumbur yana mai goge jikin dake bakinshi yana mai gyara tsayuwa. A dai-dai lokacin da Nabihat ta mike tsaye zumbur, aka sake sabon kallon kallo, RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 123 Sannan suka sake afkawa junan da yaƙi,ana fara wannan arbu ne Nabihat ta shammaci sharkar ta gabza masa naushi a kirjin sa da kafafun ta biyu, saboda karfin naushin sai da sharkar yayi tafiya a sama ta kamar dakika latalin yana mai kurma ihu Sannan ya faɗa tekun Baharul-sawara, Koda samun wannan nasara sai jaruma Nabihat ta ruga izuwa inda yan uwan ta yan matan suke ta kai musu ɗauki su ka cigaba da ragargazar dakarun. Cikin kankanin lokaci suka hallaka su baki ɗaya. Koda samun wannan nasara sai Nabihat ta umarci yan uwanta fursunonin da su tuka jirgin Ruwan a cigaba da tafiya Cikin matukar kaɗuwa ɗaya daga cikin fursunonin ta dubi Nabihat cikin tashin hankali tace "Yake Nabihat taya ya zamu cigaba da tafiya bayan cewa yarinya lazimat tana cikin wannan Teku,bamu da tabbacin a wane hali take ciki. Koda jin wannan batu daga bakin sharimat sai idanun Nabihat su ka ciko da kwalla, ta dubi shamirat tace cikin matukar RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 124 damuwa"yake shamirat tabbas a yanzu bani tabbacin cewa yarinya lazimat tana raye,shin yanzu zamu tsaya ceto yarinya lazimat ne ? Ko kuwa zamu cigaba da tuka wannan jirgin ruwan domin ceto daruruwan jama'ar mu,yara ƙanana da mata da tsofaffi, Ina so ki kwantar da hankalinki idan har yarinya lazimat na raye zamu sake saduwa da ita, Koda jin wannan batu sai shamirat ta gyaɗa kai cikin alamun damuwa ta matsa kusa da yan uwan ta yan matan suka shiga tuka jirgin ruwan domin koma izuwa birnin su A daidai wannan lokaci shugaba sharkar ya taso daga kasan tekun fuskar sa a murtuke babu annuri,tamakar an watsa masa garwashin wuta akanta, hannun sa ɗaya a cire,gundulmin hannun na zubar da jini, Sa,adda jaruma Nabihat ta cigaba da jagorantar sauran yan uwan ta fursunoni,a bisa kan wannan jirgin ruwa, dake kan tekun Baharul-sawara,domin gudun TSIRA DAGA HAKA. Sai suka shafe tsawon Sa'a biyu suna tafiya babu sassauci. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 125 Lokacin da ya zamana an shafe sa,a uku, sai jaruma Nabihat ta yi umarni aka shiga ɗaki na musamman akasan jirgin ruwan aka ɗaukar gurasar sha'ir gami taceccen ruwan inabi,aka shiga rarrabawa jama,ar su domin kowa ya kimtsa cikin sa. Ana cikin wannan hali ne kwatsam bazato babu tsammani sai aka hango waɗansu tawagar jiragen ruwa kimanin guda ashiri, sun bayyana sun bayyana a saman tekun a kowa ce kusurwa,wato Gabas, yamma,kudu da Arewa, Cikin matukar kaɗuwa gami da tashin hankali Nabihat tayi umarni aka tsayar da tafiya, Kawai gaba sauran yan matan fursunonin suka ruga izuwa Wani bangare a jirgin suka ɗebo makaman yaƙi, sannan suka ruga izuwa tsakiyar birnin suna masu gyara tsayuwar su zuciyoyin su cike da razani, Yayin da yazamana cewa jiragen ruwan suna matso daf dasu sai Nabihat ta sake ɗimauce wa, Su dai jiragen ruwan suna ɗauke ne da waɗansu irin zaratan dakaru masu kirar samudawan farko, suna sanye cikin sulken yaƙi na baƙin ƙarfe, suna da waɗansu miguna MAKAMAN KARE DANGI, RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 126 Tabbas waɗannan dabaru sun kasance ababan tsoro domin babu halitta da zata arba da su face tayi nadamar wanzuwar ta a doran kasa, Nan fa aka fara kallon kallo tsakanin su jaruma Nabihat da tawagar dakarun, Tsawon daƙiƙa arba'in ana cikin wannan hali, a lokacin ne su Nabihat suka hango shugaba Yasiran a ɗaya daga cikin jiragen ruwan, Shirye cikin gagarumar shigar yaƙi hannunsa ɗaya ɗauke da wata sharbebiyar takobi,ɗayan hannun da yayi dungulmi kuwa yana naɗe a cikin wani farin kyalle, fuskarsa a murtuke babu annuri. Al'marin da yayi matukar bawa su Nabihat mamaki kenan, suka tambayi kansu a cikin ransu suna masu cewa, ya akayi Yasiran ya rayu' shi ina yarinya lazimat take tana raye ne ko kuwa ta mutu, Amsar tambayar da suka kasa bawa kansu kenan. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 127 Kawai sai Nabihat su ka hangu dakaru masu yawa sun tsalle daga inda suke suna ihu da kururuwa mai firgitarwa sun tunkaro su,suna shawagi a cikin iska jitamkar sun kasance masu fuka-fukai , Koda ganin hakan sai Nabihat ta daga takobin ta sama cikin karfin hali,gami da ƙarfafawa sauran yan matan gwiwa ta falfala da masifaffan gudu zuwa kan dakarun. Yayin da yan matan suka ga haka sai suka yi koyi da ita, su masu mara mata baya, Tabbas shi ƙarfi a zuciya

Chapter 7 of 8