Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 8
bayan sarki Lazwar ya ɗora magajin gari Yasiran a bisa sarautar shi ya shiga izuwa duniya. Haƙiƙa masu iya magana sunyi gaskiya da suka ce, sannu-sannu bata hana zuwa sai dai a daɗe ba'a je ba, sai ga shi an shafe tsawon kwanaki arba'in da huɗu ana tafiya RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 53 tsakanin sarki Lazwar, gimbiya Mashlira, yarinya Shuraiba, sarkin yaƙi ,bawa Shamsal aljani Za'aratun-layal tare da yaro Imran. A iya tsawon wannan tafiya shaƙuwa mai karfi ta ƙullu tsakanin yarinya Shuraiba da yaro Imran, kuma Imran ya bayyana abubuwan mamaki gami da ƙarfin ikon Ubangiji. Domin sau talatin da bakwai yana ceto rayuwar su sarki Lazwar bisa taimakon Ubangijin musulunci. Bisa wannan dalili ne ya sanya Mashlira da Shuraiba suka fara kwaɗayin shiga addinin. A ranar da kwana hamsin suka cika ne aljani Za'aratun-layal ya sauka a bisa wani daji dake kusa da birnin Istanbul, nan fa farin ciki ya kama kowa shima aljani Hadimul-khair ya sauke Imran da yarinya Shuraiba Bayan kowa ya sauko sai aka shiga tattaunawa akan hanyar da kowa zai bi wajen shiga birnin Istanbul, inda Shuraiba ta dubi kowa sannan ta yi gyaran murya ta ce "akwai shawarwari da zan bamu waɗanda matsawar muka kiyaye su zamu shiga cikin birnin Istanbul lafiya kuma mu fito lafiya sumul. Da farko dole ne kowannen mu ya ƙaurace sanya tufafi masu tsadar gaske, ko wada ke nuna wata alama ta mulki . Na biyu gujewa ƙarya da ha'inci, sannan yin biyayya ga dukkan abin da ya shafi masarauta. Waɗannan sune shawararin da idan muka kiyaye su zamu cimma nasara. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 54 Koda Shuraiba ta zo dai-dai nan azancen ta sai ta juya da dubi Gimbiya Mashlira ta ce "ya ke Mashlira ya zama wajibi idan zaki shiga cikin wannan birni na Istanbul ke rufe fuskarki da rawani, har zuwa lokacin da zamu kammala samun abin da muka shiga nema, domin tsananin kyawun surarki zai jawo miki matsala. Koda yarinya Shuraiba ta zo nan a jawabin ta sai tayi bankwana da damisarta suna masu zubar da hawayen rabuwa da juna, har sai damisar ta ƙule izuwa cikin daji ta daina hangen ta. Ko da jin wannan batu daga bakin Shuraiba sai kowa ya gyaɗa kai cikin farin ciki, kawai sai sarki Lazwar ya karanto waɗansu dalasiman tsafi ya nuna aljani Za'aratun-layal da ɗan yatsan shi na hagu, take Za'aratun-layal ya riƙiɗa izuwa wani garjejen sadauki mai kwarjini daban tsoro, sannan ya sake karanto waɗansu dalasiman tsafin take tufafin dake jikin su ya canja launi zuwa makasƙanta, babu wanda zai ga sarki Lazwar da gimbiya Mashlira a wannan hali face ya cika da mamaki bisa ganin yadda suka koma tamkar almajirai saboda tufafin dake sanye a jikkunansu. kaico! Haƙiƙa masu iya magana sun yi gaskiya da suka biyan buƙata ya fi dogon buri. kuma ranar biyan buƙata rai da dukiya ba a bakin komai suke ba. Kawai sai aka ɗunguma aka durfafi ƙofar birnin Istanbul gadan-gadan, shi kuwa yaro Imran sai ya matsa kusa Shuraiba ya yi mata raɗa a kunne, sannan ya dawo da duban shi ga hadimin shi ya ce dash ''ya kai Hadimul-khair ina ganin ya kamata ka kasance a ɓoye, koda ka bayyana har sai lokacin da na buƙaci hakan" koda jin hakan sai Hadimulkhair ya risina ya ce ''an gama ya shugabana, kawai sai ya RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 55 ambaci sunan Allah gami da yiwa Annabi salati take ya bace bat, tamkar bai taba wanzu wa ba. Wannan shi ne abin da ya faru da su sarki Lazwar lokacin da suka iso izuwa birnin Istanbul. BABI NA TAKWAS BIRNIN ZAWATUL-IFDAR Al'amarin wannan budurwa da magajin gari yasiran ya yi umarni a kai mashi ita izuwa turakar shi kuwa, ba wata ba ce face wata sabuwar amarya, kuma an ɗauko ta ne domin ya keta mata haddi. Lokacin da wannan badakaren ya isa da ita turakar sai ya tarar da kuyangi na ƙawata turakar da kayan ƙawa da alatun jin daɗin rayuwar duniya, wani irin daddaɗan kamshi na tashi a ko ina. A harabar turakar da bakin ƙofa kuwa dakaru ne birjik shirye cikin gagarumar shigar yaƙi hannayensu ɗauke da miyagun makamai. Ya yin da amaryar ta tsinci kanta a ciki turakar sai ta sake fashewa matsanancin kuka mai tsuma zuciya, tsawon sa'o'i tana cikin fargaba da tsoron abin da zai faru gare ta, kuma tana tuna halin da angon ta ya ke ciki. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 56 Haka ta kasance a cikin wannan hali har duhun dare ya fara nisa, a cikin wannan hali ne ta ji motsin shigowar magajin gari Yasiran ba, nan fa tsoro ya kara kamata ainu. Tana cikin wannan hali ne kwatsam! Bazato babu tsammani sai kawai ta ga wani kyakkyawan tsuntsu yana fitar da wani sautin kuka mai daɗin saurare, yana shawagi a harabar turakar. Cike da matuƙar kwadaituwa da son ganin tsuntsun, ta matsa izuwa tagar dake turakar ta leƙa ai kuwa sai ta ga anyi wani rubutu a jikin fuka-fukan tsuntsun da harshen Larabci kawai sai ta furta a bakinta, faruwar hakan keda wuya, ai sai ta ji dukkan baƙin ciki gami da tsoron dake zuciyarta ya tafi, tamkar babu wani mugun abu dake shirin faruwa a gare ta. Cikin farin ciki mara musaltuwa ta cigaba da karanta kalmomin a cikin ranta A dai-dai wannan lokacin ta ji an turo kofar shigowa turakar, tana buɗe wa sai ga Yasiran ya bayyana, yana sanye da wani mayafi na alhariri da ya rufe daga cibiyarshi izuwa gwiwarshi. Sa'adda amaryar ta yi arba da shi saboda matuƙar tsoro ba ta san sa'adda ta faɗi ƙasa ba, jikinta na ƙyarma tamkar mazari, shi kuwa magajin gari sai ya nufi inda take yana mai bushewa da dariyar mugunta har da ƙyaƙyatawa, Lokacin da ya matso daf da ita sai ya kawai ya miƙa hannunshi da niyyar ya cakume ta.amma sai ya ji wani irin tiririn zafi ya tunkaro shi tamkar an yana kusa tanderun wuta. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 57 Al'amarin da ya yi matuƙar ba shi mamaki kenan kuma ya fusata ainun, kawai sai ya buɗe baki da nufin ya karanta waɗansu dalasiman tsafi. Kaico! haƙiƙa rashin sani yafi dare duhu, in da ace Yasiran ya san abin da zai faru da bai yi gangancin karanta dalasiman tsafin ba, domin kuwa yana cikin hakan ne wata irin gagarumar wuta ta kama a jikinshi tana ci. Nan fa magajin gari ya shiga kurma wawan ihu yana mai kai komo a cikin turakar domin ganin ya kashe wutar, amma duk sa'adda ya zuba ruwa sai wutar da ƙara ruruwa. Ita kuwa amarya munirat koda ta ga wuta ta kama a jikinshi, sai ta ci gaba da karanta waɗannan kalmomi na larabci da taga ni a jikin fuka-fukan tsuntsun nan a cikin zuciyarta, kuma ta miƙe tsaye zumbur ta rugawa izuwa ƙofar fita daga turakar. Bisa mamaki duk ƙofar da ta tunkara sai ta ga ta buɗe da kanta, wani abu da ya bata mamaki kuma ya ɗaure mata kai shi ne, gashi dai ƙiri-ƙiri dakaru suna kallon ta ta tsakiyar su take ratsawa, amma babu mai ɗaga mata yatsa ballantana ya ce mata uffan. Haka dai amarya Munirat ta cigaba da tafiya a cikin gidan sarautar, zuciyarta cike da matuƙar farin ciki maral musaltuwa gami da imani da ma'abocin waɗannan kalmomi da ta karanta suka ce ci rayuwar ta. A dai-dai wannan lokaci ne dakarun dake gidan sarautar suka dunga tuttɗowa suna zare makaman su suna rugawa izuwa ɓangaren sarki, bisa jin ihu gami da kururuwar magajin gari Yasiran da suka yi. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 58 kafin ƙiftawar idanun gidan sarautar ya hargitse da gujegujen jama'a gami da ifice-ifice tamkar an busa ƙahon BUSAR MUTUWA. BABI NA TARA A can birnin muridai kuwa, sarki Zammar mahaifin gimbiya Mashlira ya ga dukkanin abin da ya wakana tsakanin yaro Imran da aljani Durusul-fannar. A cikin halarar tsafin shi a lokacin da yake zaune a fadar tare da 'yan majalisar shi. Ko da ganin hakan sai ya cika da matuƙar baƙin ciki maral-musaltuwa. Wata rana sarki Zammar na kwance a cikin turakarshi da ta ƙawatu da kayan alatun more rayuwr duniya, sai ya yi mafarki da yarshi Mashlira tana cikin ƙoshin lafiya. Kuma har ta gaya mashi cewa bata guje mashi domin ta ci amanar shi ba, sai domin ta shiga duniya ta samo masu maganin lalurar da ta addabe, su tun daga wannan rana Sarki Zammar ya kasance cikin matuƙar farin ciki, ya yiwa 'yarshi fatan alheri da samun nasara. Wannan shi ne abin da yafaru acan birnin muridai. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 59 Babi na tara Tafiyar daƙiƙa latalin kacal aka yi aka iso ƙofar shigowa birnin Istanbul, sa'adda aka yi arba da yadda ƙofar birnin takasance sai kowa ya cika da matuƙar mamaki, katangun birnin sun kasance masu matuƙar tsawo, a sama da ƙasan ƙofar birnin miyagun dakaru ne na mutum da aljan ga su nan birjik shirye cikin gagarumar shigar yaƙi hannayen ɗauke da waɗansu irin masifaffun makamai Kai koda tsuntsu ne ya zo giftawa ta wannan waje waɗannan dakaru ba zasu bar shi a raye ba, tsananin kwarjini mayaƙan ya isa ya ɗimauta duk wata halitta mai numfashi. Idan har ƙofar birnin Istanbul takasance haka, to ya tsaron gidan sarautar birnin zai kasance kuwa? Sarki Lazwar ne ya yi wa kanshi wannan tambaya a cikin ranshi ba tare da ya furta wani ya ji ba. Wani narkeken sadauki mai matuƙar muni da kwarjini ya matso daf da inda su sarki Lazwar su ke ya kare masu kallo da yan mini-minin idanuwanshi jajaye tamkar garwashin wuta, cikin wata irin kakkausar murya mai kama da kukan jaki ya ce "ya ku waɗannan baƙi shin daga ina kuke, kuma mene ne ke tafe da ku izuwa birnin nafi daraja a duniya?. Ko da jin wannan tambaya sai zuciyar sarki Lazwar ta kama tafarfasa tamkar zata ƙone. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 60 Bakomai ne ya sanya hakan ba, sai bisa jin badakaren ya ambaci birnin Istanbul da suna mafi daraja a duniya. Amma koda ya tuna cewa shi fa a halin yanzu sunan shi bawa ba BASARAKE ba, sai ya danne zuciyarshi, ya dubi badakaren ya ce "ya kai wannan badakare ka yi sani cewa ba komai ne ke tafe damu izuwa wannan birnin na ku ba face sai domin mu gudanar da kasuwanci, kuma a halin yanzu mun fito ne daga nahiyar ƙasashe larabawan gabas. Ko da jin amsar wannan tambaya sai badakaren ya bushe da dariya sannan daga bisani ya murtuke fuska ya ce "Za mu ba ku izinin shiga wannan birnin saboda muhimmancin abin da ke tafe da ku. Sai dai wani hanzari ba gudu ba idan muka samu ɗayan ku ya karya dokokin wannan birnin namu, to zamu ƙwace dukiyarku gami da tusa ƙeyarku izuwa gidan kaso. Ko da jin wannan batu sai hantar cikin kowa ta kaɗa da karfi tsoro ya kama shi. Kawai sai badakaren ya yiwa waɗansu dakaru inkiya ta wutsiyar idanu take dakarun suka shiga wangame kofar birnin, ƙofar na kammala buɗewa su sarki suka kunna kai izuwa cikin birnin zukatansu cike da matuƙar farin ciki. Lokacin da su Sarki lazwar suka tsinci kansu a cikin birnin Istanbul sai suka kama kalle-kalle da dube-dube tamkar ɗan ƙauye ya shigo birni, kuma suka cika da matuƙar mamaki gami da al'ajabi, bisa ganin yadda birnin ya kasance mai matuƙar kyawun gine-gine tamkar aljannar duniya. Kai tsaye yarinya Shuraiba ta durfafi hanyar kasuwar birnin, amma sai sarki Lazwar ya yi caraf! ya dubi yarinya RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 61 Shuraiba ya ce "ya ke Shuraiba shin mene ne dalilin da ya sanya za ki kai mu kasuwa? Bayan cewa ba kasuwanci ne ya kawo mu wannan birni ba? Ko da jin waɗannan tambayoyi sai Shuraiba ta bushe da dariya ta ce "ai bakomai ne yasanya na kawo mu kasuwa ba sai domin kar ka manta cewa ka faɗawa dakaru masu tsaron kofar birnin Istanbul cewa kasuwanci ne ya kawo mu, tabbas dola ne a kowa ne lokaci dakarun sarki su kawo ziyarar bazato, domin binciken gaskiyar maganar abin da ka faɗa masu, Abu na biyu kuwa shi ne a lokacin da muka shigo wannan birni 'yan fashi da makami gami da 'yan damfara sun shaida shigowar mu, a koda yaushe za su iya kawo mana farmaki domin a tsammanin su za su samu dukiya mai tarin yawa a wajen mu. Waɗannan dalilai ne suka sanya na kawo mu kasuwa domin babu wani waje mai ɗauke da cikekken tsaro fiye da kasuwa". Ko da jin amsar waɗannan tambayoyi daga bakin Shuraiba sai kowa ya gyaɗa kai alamar gamsuwa gami da samun nutsuwa. Lokacin da aka shiga kasuwar sai aka tarad da takasance maƙiyaya mai faɗin gaske, tana ɗauke da gine gine cikin tsari, rumfunan masu siyan da tufafi dabam, kayan masarufi, komai dai an yi bisa tsari mai ƙayatarwa. Kai tsaye aka durfafi rumfar wani dattijo, da ta ƙawatu da kayan alatu na hatimin sarauta, da alama shine shugaba kasuwar. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 62 Tun daga nesa Shuraiba taga ya ƙura mata idanu ko kiftawa ba ya yi. koda shugaban kasuwar ya yi arba da su sai ya miƙe tsaye zumbu! Ya tarbe su cikin matuƙar farin ciki yana yi masu lale marhaban da zuwa, tamkar ya sadu waɗansu yan uwanshi na jini da ya jima bai sadu da su ba. Bayan shugaban kasuwar mai suna Sha'aran ya sauke su a bakin ƙofar rumfar, sai ya yi umarni aka kawo musu abincin kalaci aka jera a bisa wani dogon teburi, nan fa su sarki Lazwar suka shiga kimtsa cikinsu, har suna hannu baka hannu ƙwarya, domin rabon su da cin irin abincin yau wata huɗu kenan cif. Kuma suna mamakin irin karamci da shugaban kasuwar ya nuna masu. Shi kuwa yaro Imran da aka fara cin abincin sai ya yi bisimillah, loma bakwai ya yi sannan ya zare hannunshi ya kurɓi ruwa maƙwarwa huɗu sannan ya koma koma gefe gudal. Al'amarin daya bawa sarkin kasuwa Sha'aran mamaki kenan, ya ƙurawa yaro Imran idanu yana so ya tuna irin mutanen da ya taɓa gani suna irin wannan dabi'a wajen cin abincin su, Shi kuwa aljani ZA'ARATUN-LAYAL, da a halin yanzu sarki Lazwar ya canja mashi siffarshu dagaaljan ya koma bil'adama, cin abincin ya yi yana santi kamar tsohon mahaukaci. Bayan kowa ya kimtsa cikinshi ya dawo hayyacinshi, sai sarki Lazwar ya zira hannunshi a aljihun rigarshi domin ya ɗauko dinare domin ya biya kuɗin bincin da suka ci, da kuma kuɗin hayar gidan da za'a ba su. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 63 Amma sai kawai ya ga shugaban ya dube sa fuskar sa cike da annuri ya ce "ya ku waɗannan baƙi masu daraja ku yi sani cewa, ganin ku da nayi ya sanya jikina ya ba ni cewa ku mutanen ƙwarai ne. Yanzu ina buƙatar ku gabatar min da sunayen ku. Koda jin wannan batu sai mamaki ya kama kowa, sarki Lazwar ya shiga gabatar da sunayen su ɗaya-bayan-ɗaya, Amma koda yazo kan yarinya Shuraiba sai sarkin kasuwar ya dakatar dashi ya ce "ba sai ka gabatar mini da ita ba. Al'amarin da ya bawa kowa mamaki kenan, har Shuraiba ta ce a cikin ranta shin me shugaban kasuwar ya sani game da ni. Kuma me ya sanya yake ƙura min idanu tun da muka shigo kasuwar? Ina dalilin rashin karɓar haƙƙin aikin shi daga gare mu. Amsar tambayoyin da yarinya Shuraiba ta kasa bawa kanta kenan. Shugaba sha'aran na gama faɗin hakan sai ya ƙwallawa wata budurwa kira. Budurwar ta bayyana a gare shi sanye da tufafi masu yalwa, tun daga ƙasa har sama, kuma fuskarta rufe da rawani mai ɗauke da wani hatimin sarauta idanuwanta kaɗai ake gani, ta zube ƙasa ta kwashi gaisuwa cikin girmamawa, sannan ta buɗi baki cikin wata irin lallausar murya mai daɗi tamkar sarewa ta ce ''ga ni ya shugabana me ake da buƙata? Shugaba Sha'aran ya dube ta ya ce "ya ke khadijat ki yi sani cewa bakomai nake buƙata a gare ki ba, sai domin ki yiwa RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 64 waɗannan baƙi jagora izuwa unguwar Madinatul-dinar, masaukin manyan baƙi, ina so ki ba su dukkan abin da suke bukata na kulawa". Koda jin wannan umarni sai B Budurwa khadijat ta mayar da duban ta ga su sarki Lazwar tana ƙare masu kallo ɗaya-bayan-ɗaya. Ya yin da ta haɗa idanu da yaro Imran sai taji zuciyar ta buga ƙarfi kuma tsikar jikin ta ta tashi, kamar yadda ya faru gare ta shi ma haka yaro Imran ya ji wannan yanayi a tare da shi, amma saboda kada wani ya fahimci abin da ke faruwa sai khadijat ta kawar da idanuwanta a kan shi, a ɓangaren bawa Shamsal kuwa, tun sa'adda da ya kalli idanuwan budurwa khadijat sai ya ji hantar cikinshi ta kaɗa da ƙarfi, sannan wani abu ya ɗar su a zuciyarshi da ya kasa gane ko mene ne. Ita kuwa gimbiya Mashlira cikin idanun khadijat kawai ta kalla taji kishi ya kama ta, domin koda cewar fuskar khadijat a rufe take da rawani idanuwanta kaɗai ake gani, ta tabbatar cewa ta shafe ta a kyawun sura ne sa ba kusa ba. Tabbas idan masoyin ta sarki Lazwar ya yi arba da ita zahiri zai iya karkata zuciyarshi izuwa gare ta. Khadijat ta miƙe tsaye ta shige gaba, tana mai yafito su sarki da hannunta, tana mai yi masu nuni da su biyo bayan ta. Ba tare da gardamar komai ba, suka mara mata baya har suka ƙule a cikin kasuwar, duk inda suka gifta sai jama'a su bi su da kallo, haka suka wanzu suna ratsa saƙo da lungu na unguwanni, har suka iso wani ƙasaitaccen gida. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 65 Kai tsaye khadijat ta durfafi kofar gidan ta na isa dakarun dake gadi suka wangame makekiyar kofar shiga gidan suna masu risinawa a gare ta cikin girmamawa. Khadijah ta kunna kai izuwa cikin gidan, su sarki lazwar na biye da ita cike da matuƙar mamakin yadda masaukin ya kasance. Kowanne su ɗaki aka ba shi daban mai ɗauke da gado, kushin da kewayen wanka da sauran kayan more rayuwa. Kuma khadijat ta shaida masu cewa duk mai buƙatar wani abu ya sanar da ita har izuwa lokacin da zasu tafi. kasancewar a wannan lokaci duhun dare ya fara kawo kai, sai khadijat ta yi umarni aka kunna dukkanin fitulun dake gidan. A lokacin da dare ya tsala sai sarki Lazwar ya shiga izuwa masaukin kowanne ya bayyana masa cewa, dole ne su kasance cikin shiri, domin a kowannnen lokaci za a iya kawo masu harin bazato, kuma ba su da tabbacin cewa sarki kasuwa Sha'aran ba shi da wata mummunar manufa akan su, kuma a gobe da duku-dukun safiya za su shiga cikin garin domin gudanar da abin da ke tafe da su. A can masaukin yaro Imran kuwa bayan gabatar da kalacen dare, sai ya shiga izuwa kewayen ya ɗaura alwala ya dawo izuwa turakarshi ya shiga gabatar da Sallah isha'i yana cikin hakanne ya ji an turo kofar shigowa, sai da ya idar ya yi addu'a sannan ya juya domin ya ga kowane ne ya shigo ɗin. Koda ya yi arba da wanda ya shigo ɗin sai ya yi turus!, Ba wani ya gani ba face khadijat hadima ga Sarkin kasuwa Sha'aran, tana durƙushe a gefan shi na hagu ta yi zama irin na sallah. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 66 Cikin matuƙar mamaki Imran ya du be ta cikin girmamawa ya ce "ya ke hidima Khadijat shin ina dalilin shigowarki wannan masauki nawa a dai-dai wannan lokaci bakya tsoron sauran abokan tafiya za su zargi wani abu? Sannan jikina ya bani cewa kina kwaikwayon yadda nake gudanar da ibadar Ubangiji na. Shin baka tunanin hakan zai jefa rayuwarki da tawa a cikin haɗari ba? Ko da jin waɗannan tambayoyi sai khadijat ta yi murmushi mai taushi, sannan ta dubi Imran cikin murya mai daɗin saurare ta ce "ya kai wannan yaro ka yi sani cewa tun sa'adda nayi arba da kai a lokacin da ku ka sauka a rumfar mai gidana, naji ka burgeni sosai a zuciyata tamkar ina tare ɗan uwa na jini, kuma lokacin da ku ke cin abincin na lura cewa duk dabi'un cin abincin naka ya bambanta da nasu, wato naka irin na ma'abota addinin Musulunci ne, tun daga lokacin na ji cewa na samu ɗan uwa. Bisa wannan dalili ne ya sanya na biyo ka izuwa masaukin ka domin na bika sallah. Fiye da shekaru goma sha biyu kenan tun sa'adda an fito neman ɗan uwa na, wanda shi ne kaɗai ya rage mini da a duniya rabon da a ce na samu jam'in sallah sai a yau, Tabbas ina cikin matuƙar farin cikin da ba zai musaltu ba. Haƙiƙa da zaka zauna a tare da ni da ka ɗebe mani kewar mahaifina da na rasa. Tsawon shekarun da na shafe ina aiki tare da Sarkin kasuwa Sha'aran ban taɓa bayyana addini na a gare shi, saboda RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 67 gudun matsala, domin duk wanda aka samu yana gudanar da wani addini saɓanin na birnin Istanbul hukuncin kisa ne a ƙanshin shi. Bisa wannan dalili ne ya sanya kai ma nake baka shawara da ka guji bayyana hakan, har ku kammala abin da ke tafe daku zuwa wannan birni"; Koda jin amsar waɗannan tambayoyi sai yaro Imran ya cika da matuƙar farin ciki yaji ya yi matuƙar shaƙuwa da hadima khadijat, kuma mamaki ya kama shi bisa jin cewa ta fito neman ɗan uwanta ne. Shin khadijat ita ce 'yar uwar shi da ya fito nema ? Amma ta ya zai iya gasgata hakan bayan cewa koda yaushe fuskarta a rufe take da rawani. Amsar tambayoyin da Imran ya kasa bawa kanshi kenan. Khadijat ta katse shirun da wanzu a tsakaninsu ta hanyar buɗar baki ta ce "ya kai ɗan uwa na idan ba za ka damu ba, ina neman alfarma a gare ka da ka amince min kullum na dunga zuwa wajen ka muna yin fira gami da ɗebe kewa Koda jin wannan batu sai Imran ya ce "na yi maki wannan alfarma ya ke yar uwanta". Wannan shi ne abin da ya faru a masaukin yaro Imran ma'abocin addinin Musulunci. A can masaukin sarki Lazwar kuwa, fira ce ta kare tsakanin Lazwar da gimbiya Mashlira, a inda Mashlira ta ci RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 68 gaba da ba shi labarin abin da ya faru tsakanin matsafi Sahibul-ukub da mutanen birnin akan dalilin da ya sanya halittar su ta koma ta maridai inda ta ci gaba da cewa. Lokacin da rundunar matsafi Sahibul-ukub suka afkawa birnin Madinatul-Adfal sai aka ruguntsume da azababban yaƙi mai matukar muni ban tsoro da ban al'ajabi. Nan fa su ma mayaƙan birnin suka dinga tuttuɗowa daga kowacce kusurwa ana yin KARON BATTA. Nan fa sassan jikkunan bil'adama ya dinga shawagi a sama suna zubo ƙas, hankakan mutuwa ya yi dirar mikiya a wajen ya wanzu yana kai komo wajen ɗaukar rayuka. JINI DA ƘASA suka haɗu waje guda, ihun da kururuwar mazaje gami da haniniyar dawakai ta cika dodon kunne. A wannan lokaci mahaifina sarki Zammar ya shiga izuwa cikin gidan sarautar yana shirin yaƙi, jim kaɗan sai ga shi ya fito izuwa filin daga kawai sai ya afka cikin abokan gaba ya hau su da sara da suka. Yazamana cewa duk inda ya sanya a gaba sai dai ka ga dakarun matsafi Sahibul-ukub na zubewa ƙasa matattu tamkar yana sassabe a gonar auduga. Sa'adda matsafi sahibul-ukub ya ga irin muguwar ɓarnar da mahaifina ke yi mashi, sai ya ruga izuwa inda ya ke ya tare shi suka kacame da azababban yaƙi mai matukar muni daban tsoro. Ana fara wannan arbu ne mahaifina ya fara gane cewa tabbas shayi ruwa ne ba abinci mai nauyi ba, domin kuwa duk sa'adda matsafi Sahibul-ukub ya kai mashi hari da takobinshi RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 69 idan ya kare harin, sai kaga ƙarfin saran ya cilla mahaifina sama ya yi ƙundumbala ya kife a ƙasa, amma saboda juriya da mafi irin ta GWARAZAN JIYA sai ya miƙe tsaye zumbur, ya ci-gaba da mayar da martani A wasu lokutan kuwa idan ya kai mashi harin ya kauce, sai ka ga duk abin da takobin Sahibul-ukub ta sauka a kanshi ya kama da wuta, kafin cikar rabin sa'a Sahibul-ukub ya galabaitar da mahaifina ya faɗi ƙasa magashiyan ya na amai na jini ta baki da hanci. Wannan shi ne abin da ya faru a masaukin gimmbiya Mashlira 'yar sarkin maridai da Sarki lazwar. Kamar yadda ya wakana a masaukin gimbiya Mashlira da sarki Lazwar haka al'amarin yakasance a masaukin yarinya Shuraiba da aljani ZA'ARATUN-LAYAL A inda Za'aratun-layal ya ci gaba da bawa yarinya Shuraiba hikayar sarauniya Abidat ta birnin Sin. BABI NA GOMA Lokacin da wannan zakanya ta ruga izuwa inda suhaimat da jaririyar ta ke kwance, koda taga halin da take ciki sai ta ruga izuwa bakin wata ƙorama ta guntso ruwa a baki ta dawo izuwa inda take ta fesa mata ruwan a fuska. Faruwar hakan keda wuya sai suhaimat ta ja dogon numfashi gami da sauke nannauyar ajiyar zuciya, idanuwanta RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 70 suka buɗe tarwai ta wartsake daga suman da tayi kawai sai ta miƙe zaune. Ya yin da tayi arba da zakanyar sai ta razana ainun ta ja da baya tana mai ɗaukar jaririyar ta ta ƙanƙame ta a ƙirji. Koda ganin halin da suhaimat ta shiga sai zakanyar ta juya ta ruga izuwa cikin wannan kogon dutse dake dajin. Cikin matukar farin ciki suhaimat ta mike tsaye taje bakin wannan ƙorama ta yi wa jaririyarta wanka, ita ma ta tsafta ce kazantar da ke jikin ta, sannan ta dawo izuwa ƙarƙashin wata bishiya ta zauna ta shiga sharar da jaririyar tana mai shafa gashin kanta, zuciyar ta cike da matuƙar farin ciki maral misaltawa. Kuma ta shiga tambayar kanta a cikin ranta tana cewa, dhin wane ne ya kashe waɗannan dabaru? Ko kuwa wannan zakanya ce? Amsar tambayar da ta kasa bawa kanta kenen,tana cikin wannan hali ne zakanyar ta dawo gare ta bakin ta rike da waɗansu tarin ganyayyaki ta a jiye a gaban ta, Bisa mamaki a wannan karon sai Suhaimat taji ko kaɗan ba ta tsora ta da ganin zakanyar ba, bata re da fargabar komai ba ta ta duba abin da ta kawo ɗin. Ai kuwa sai taga a she nau'ikan kayan marmari ne dangin su ayaba da inibi, kawai sai ta shiga kimtsa cikinta har sai da ta ci ta ƙoshi, sannan ta fasa kwakwa ta shanye ruwan cikinta. Zakanyar na tsaye na tsaye a gefe guda tamkar mai jiran umarni, a sannanne Suhaimat ta lura cewa jikin zakanyar RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 71 akwai jini, take ta fahimci cewa ita ce

Chapter 4 of 8