Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 8
ta kashe waɗannan dakaru domin ta ceci rayuwar ta da jaririyar ta. Lokacin da aljani ZA'ARATUN-LAYAL ya zo dai-dai nan a hikiyar sarauniya Abidat ta birnin Sin da yake bawa yarinya Shuraiba sai ya tsuke bakinshi ya yi shiru. Al'amarin da ya sanya yarinya Shuraiba ta dube shi cikin alamun tsananin damuwa ta ce "ya kai masanin HIKAYAR DUNIYA shin mene ne yasanya zaka katse min wannan daddaɗan labari? Tabbas ina so naji wace irin rayuwa Suhaimat da jaririyar ta za su yi a nan gaba, kuma menene dalilin da ya baro da ita daga birnin su? Shin ma mene ne ya sanya dakarun ke farautar Suhaimat? Koda jin waɗannan tambayoyi sai aljani ZA'ARATUN-LAYAL ya bushe da dariya ya dubi yarinya Shuraiba ya ce "ya ke Shuraiba shin baki gani ba ne har alfijir ya keto safiya ta yi". Koda jin wannan batu daga bakin Za'aratun-layal sai Shuraiba ta cika da mamaki, ai kuwa sai ta miƙe tsaye ta domin ta fara shiri kamar yadda sarki Lazwar ya yi masu bayani. Wannan shi ne abin da ya faru a masaukin yarinya Shuraiba. Kamar yadda ya wakana a masaukin Shuraiba haka al'amarin ya kasance a masaukin darki Lazwar da gimbiya mashlira. A inda Mashlira ta katse labarin bawa sarki Lazwar na matsafi Sahibul-ukub da mahaifin ta sarki Zammar. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 72 Saboda ganin ketowar alfijir a sararin samaniya. A ɓangaren masaukin yaro Imran kuwa, ya yin da ya ga alfijir ya gabato sai ya ɗaura alwala ya shiga gabatar da nafita, bayan nan kuma sai gudanar da sallar asuba, q lokacin da hadima khadijat ta bisa a baya a matsayin mamu. Lokacin da rana da fito ne ta yi haske sai khadijat ta yi umarni aka kaiwa kowannnen su bahon ruwan wanka, bayan kowa ya tsaftace jikinshi ya yi kalaci, sai aka ɗunguma izuwa cikin gari domin gudanar da abin da aka zo nema. Wannan shi ne abin da ya faru da su sarki Lazwar a lokacin da aka kai su izuwa masauki. Babi na sha ɗaya Lokacin da amarya Munirat ta ci gaba da tafiya a cikin gidan sarautar birnin Darul-usur bayan ta kuɓuta daga sharrin magajin gari Yasiran. Sai ta cigaba da tafiya a cikin gidan sarautar tana ratsa ƙofofi da dakaru iri daban-daban, zuciyarta cike da matuƙar farin ciki maral musaltuwa. Ta na cikin wannan hali sai wannan tsuntsu ya sake bayyana a gare ta a sama cikin iska Tsuntsun ya riƙiɗa izuwa wani kyakkyawan aljani mai kyawun sura, aljanin ya na ɗauke da sura irin ta bil'adama, sai dai yana ɗauke da fuka-fukai. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 73 Aljanin ya dubi Munirat ya ce "ya ke Munirat ki yi sani cewa da farko dai suna na Lailatul-azhar kuma ni hidimi ne ga sarkin musulmin aljanun duniya baƙaƙen fata. Ubangiji ya bayyana wa sarkin mu halin da ki ke ciki dama sauran mutanen birnin ku na irin baƙin zaluncin da magajin gari Yasiran ke yi maku, sannan kuma ya turo ni ne domin na kawo ƙarshen mulkin zaluncin shi baƙi ɗaya. Ki yi sani cewa kalaman da ki ka karanta a jikin fuka-fukaina har kika tsira daga sharrin magajin gari, ba wasu kalmomin ba face KALMAR SHAHADA wacce duk wanda ya furtata ta da tabbatar wa a zuciyarshi to ya yi imani da Ubangijin gaskiya da ya halicci komai da komai. Idan har kin bayar da gaskiya da Ubangijin ɗaya daya baki nasara akan magajin gari to tabbas zamu samu nasarar ganin bayanshi. Koda jin wannan batu daga bakin aljani Lailatul-azhar sai amarya Munirat ta cika da matukar farin ciki maras musaltuwa, ta dube shi ta ce "ina so yanzu ka shigar da ni addinin ka". Ba tare da wani ɓata Lailatul-azhar ya karanta mata KALMAR SHAHADA. Nan fa ya zamana cewa kafin mako guda fiye da mutanen birnin sun karɓi addinin musulunci a hannun amarya Munirat. Magajin gari Yasiran kuwa sai ya kamu da wata irin rashin lafiya, sakamakon wannan wuta da ta ƙona jikinshi, Nan fa aka rasa wanda zai gaje shi a kan karagar mulkin shi. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 74 'Yan Majalisar suna ganin cewa tabbas yanzu hawa karagar mulkin Yasiran ana iya kiran shi da SARAUTAR MUTUWA. Domin su ganin a ko da yaushe magajin gari zai iya samun lafiya, ko kuma sarki Lazwar ya dawo daga tafiyar da ya yi. Saboda ba zai yiwu a zauna haka babu shugabanci bisa dole jama'ar gari suka ɗora amarya Munirat a matsayin sarauniyar su. Nan fa jama'a suka fara samun yanci, farin ciki gami da walwala sakamakon hasken musulmi da bayyana a gare su, Al'amarin Shuraiba kuwa Lokacin da ta cigaba da tafiya a cikin birnin Istanbul domin nemo mahaifiyarta sai ta wanzu tana tafiya babu sassauci, tana cikin wannan hali ne sai ta hango wajen waɗansu almajirai ke zaune suna bara a kasuwar, kawai sai ta matsa izuwa daf da inda suke ta shiga yin nazarin su. Abu na farko da ya faɗo mata a rai shine shin yanzu ina kike da tabbacin mahaifiyarki take, ki na ganin cewa mahaifiyarki zata kasance daga cikin waɗannan almajirai dake yin bara? An ya kuwa sarki Ladiyas bai mayar da mahaifiyar ki matar shi ba? Amsar tambayoyin da ta kasa bawa kanta kenen. kawai sai ta ɗauki mayafi ta ɗaure fuskarta da rawani, kana ta ɗauki wani ƙoƙo ta ajiye a gaban ta, sannan ta shiga izuwa cikin su ta saje da su tamkar ba ita ba. Zaman ta ke da wuya sai wata dattijuwar almijira dake kusa da ita ta du be ta ta ce "ya ke wannan yarinya shin ke kuwa me kika rasa a rayuwar ki da za ki fito bara, baƙya duba wa ki ga cewa ke yarinya mai karancin shekaru". RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 75 Koda jin wannan batu daga bakin dattijuwar sai Shuraiba ta cika da matuƙar mamaki ta dube ta ta ce "ya ke wannan dattijuwa ki yi sani cewa bakomai ba ne ya sanya ni aikata wannan bara ba sai domin na samu abin da zanyi kalaci. Mahaifina ya mutu tun ina da shekara bakwai a duniya, mahaifiyata ce take a raye ina neman ta ruwa a jallo, domin ita ce kaɗai ta rage min a duniya. Koda jin amsar wannan tambaya sai dattijuwar ta bushe da yar karamar dariya ta dube ta ta ce "tabbas yaro yaro ne kuma duk wanda ya riga ka kwana dole ya riga ka tashi, na san cewa akwai muhimmin al'amari daya sanya ki zuwa wannan waje domin, ban taɓa ganin ki ba tun da nake fitowa wannan bara tawa". Koda jin wannan batu daga bakin dattijuwar sai Shuraiba ta yi dariya ta ce "tabbas da akwai buƙatar hakan da na nema a wajen wani tun kafin na iso wannan waje, amma tambayar da zan yi maki wace matsalar dake tattare da wannan waje? Dattijuwar ta yi dariya ta ce ''ya ke wannan yarinya ki yi sani cewa bakomai yawan dinaren da mutum zai samu na sadakar da za a bashi, sai dakarun sarki Ladiyas sun zo sun karɓi haraji, da ƙyar za ka samu ka tsira da kaso ɗaya cikin goma. Idan kuwa aka yi rashin sa'a baka samu sadaka ba, to fa sai sarki ya sanya an kai mutum aikin horo a gidan sarauta domin ka yi aiki adadin wannan dinare da baka biya harajin ba"; Da jin wannan batu daga bakin almajirar sai yarinya Shuraiba ta ji ta ƙara tsanar sarki Ladiyas fiye da komai a rayuwar ta. Sannan ta dubi almajirar cikin alamun matuƙar tausayin ta ce "tabbas sarki Ladiyas ya cika azzalumi kuma maras tausayi, yanzu a ce almajirai ma sai sun biya haraji, RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 76 Koda jin wannan batu sai mamaki almajirar har ta buɗi baki da nufin ta ce wani abu sai a ka hango dakarun sarki Ladiyas sun shigo kasuwar a bisa dawakai su kamanin ɗari biyu shirye cikin gagarumar shigar yaƙi hannayensu ɗauke da waɗansu murtuka-murtukan kulake. Nan fa kasuwar ta hargitse jama'a suka dunga kwashe kayayyakin su suna buɗa wa dakarun hanya, domin idan har suka iso mutum bai kwashe ba take za su bi ta kan kayan da dawakan su su tattake. Lokacin da dakarun suka iso wajen da su Shuraiba su ke sai suka shiga karɓar harajin a wajen dukkan almajiran dake wajen, suna cikin karɓar ne suka iso kan wannan dattijuwar almajira dake zaune kusa Shuraiba. Jikinta na ƙyarma ta zira hannunta cikin ƙoƙon barar ta lissafo dinare ta miƙa wa wani badakare, bakinta na karkarwa ta ce "ga shi ya shugabana har da harajin wannan yarinyar da ke zaune a kusa da ni, Kafin hannun badakaren ya kai inda dinaren yake yarinya Shuraiba ta shammace shi ta gabza mashi wawan naushi a maƙogaronshi. Saboda matuƙar ƙarfin dukan sai badakaren ya yi karanta wa sau biyu a sama, sannan ya faɗi ƙasa matacce ko shurawa bai yi ba, al'amarin da ya firgitarwa jama'a dake kasuwar kenan kuma ya harzuƙa zukatan sauran dakarun. Wannan shi ne abin da ya faru da yarinya shuraiba a lokacin da shiga cikin gari domin neman mahaifiyarta. Al'amarin sarki Lazwar kuwa lokacin da fice da ga masaukin su ya kutsa cikin birnin Istanbul domin nemo hanyar da zai RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 77 sadu da baiwa Sharifa, sai ya wanzu yana ratsa layu ka da unguwanni babu sassauci. Yana cikin tafiyar ne ya hango waɗansu cincirindon al'ummar a gefen kasuwar, cikin hanzari ya matsa daf da wajen domin ya ga wata irin waina ake toyawa. Sa'adda da ya matsa daf da wajen sai ya ga ashe waɗansu ƙarfafan samari ne guda biyu ke baiwa hammata iska jama'a sun kewaye su suna kallo. Idan ɗayan ya gabzawa ɗan uwanshi naushi sai ka ga ya faɗi kasa tim q matuƙar galabaice, amma saboda naci da juriya sai kaga ya miƙe tsaye zumbur ya mayar da martani. A gefe guda kuwa wani badakare ne mai ƙirar samudawan farko ma'abocin kwarjini da haiba, kallo ɗaya zaka yi mashi ka fahimci cewa ya kasance GWARZON DUNIYA mai ƙarfi na Allah ya isa, yana zaune bisa wata ƙasaitacciyar kujera ta alfarma, ya zuba idanu yana kallo yadda artabun ke wakana da alama shine mai kula da gasar da ake aiwatar wa. Sarki Lazwar ya matsa daf da wani mutum ya dube shi ya ce " Wai shin mene ne amfanin abin da waɗannan samari ke yi na yaƙar junan su? Koda jin wannan tambaya sai mutumin ya dubi sarki Lazwar ya bushe da dariyar mugunta ya ce "da alama kai baƙo ne a wannan birni ko? Sarki Lazwar ya gyaɗa kai alamar haka ne, Mutumin ya ce "ya kai wannan baƙo ka yi sani cewa waɗannan da ka gani bayi ne da aka farauto daga can wata nahiya daban, duk bayan mako ɗaya mai girma Ladiyas yana sanya a fitar mashi da RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 78 GWARAZAN JARUMI a cikin su da zai kasance ɗaya cikin masu tsaron lafiyar sarauniya. Bisa wannan dalili ne ya sanya aka tara su a wannan waje domin fitar da zakara. Koda jin wannan batu daga bakin mutumin sai Lazwar ya cika da matuƙar farin ciki, domin kuwa dama ta samu wacce zata zamto sanadin kasancewar shi bawa a masarautar Istanbul. Domin dai ya cika burin shi na saduwa da baiwa Sharifa da za ta taimaka mashi wajen mallakar abubuwan da zai karya sihirin tsafin da abokin gabar shi sarki Darwazu ya yi mashi. A ɓangaren jarumai biyun kuwa tuni labari yasha banbam domin kuwa ɗaya cikin jaruman ya samu nasara akan ɗayan Inda ya yi masa jina-jina har layi na ɗibarshi yana faɗuwa ƙasa. Nan fa wannan badakare dake kula da gasar ya shiga ƙyalƙyala dariya bisa ganin yadda ɗayan jarumin ke yin nasara akan ɗayan, al'amarin da ya fusata sarki Lazwar kenan yaji ya kamu da matuƙar tausayin jarumin, kawai sai ya dako wawan tsalle daga inda yake tsaye ya daki ƙirjin jarumin dake samun nasarar da dukkan ƙarfin shi. Saboda ƙarfin dukan sai da jarumin ya yi sama yana mai tsandara ihu sannan ya faɗo ƙasa a matuƙar galabai ce, hannayen biyu suka karye ji kake ruƙus! Ƙas. Cikin matuƙar al'ajabi jama'a suka duba domin su ga ko wane ne, ai kuwa koda suka yi arba da sarki lazwayr sai suka cika da matuƙar mamaki, domin sun san cewa tabbas koma wane ne shi baƙo ne kuma ya jifa kanshi a cikin bala'i, domin ba ka RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 79 yi laifin komai ba ma sarkin yaƙi Darusu ya zalunce ma ballantana ka shiga gonar shi. Sarki Lazwar ya matsa izuwa inda ɗayan jarumin ke kwance ya tashe shi zaune ya karkaɗe mashi ƙurar dake jikin shi. Al'amarin da ya yi matuƙar fusata sarkin yaƙi Darusu kenan zuciyarshi ta kama tafarfasa tamkar zata kone, kawai sai ya dakawa dakarun shi tsawa suka zare makaman su suka yi ɗauki kan Lazwar. Lokacin da aka haɗu sai aka ruguntsume da azababban yaƙi nan fa artabun ya zamto abin tsoro da kuma ban al'ajabi, domin ga shi dai sarki Lazwar ba ya riƙe da makami amma sai ya zamtowa dakarun alaƙaƙai kuma GUGUWAR AJALI suka rasa yadda zasu yi da shi. Duk wanda ya gabzawa naushi a wata gaɓa a jikin shi sai ka ji ta ƙarye ta yi ƙara ruƙus! Ƙas. Kuma ya wanzu yana zillewa hare-haren dakarun cikin matuƙar zafin nama JUTIYA DA BAJINTA irin ta ZARATAN MAYAKA, Nan fa ihu da kururuwar dakarun gami da ƙarar karafniyar karafa ta cika dodon kunne, nan fa ya zamana cewa waɗansu dakarun na daban ya rugawa izuwa kan sarki Lazwar cikin matuƙar fushi, bisa ganin yadda yake ragargazar 'yan uwan su. Kafin cikar daƙiƙa arba'in sarki Lazwar ya bazar da dakaru fiye da saba'in, dukkanin su sun zube a ƙasa magashiyan suna nishin wahala. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 80 Nan fa zuciyar sarkin yaƙi Darusu dake tsaye a gefe guda ta kama tafarfasa tamkar zata fasa ƙirjinshi ta fito waje, amma kuma wani abu da ya faɗo mashi arai shi ne. Tabbas wannan baƙon jarumi ya cika GWARZON DUNIYA yadda ake bukata, kuma tabbas idan na kai shi ga mai girma Ladiyas zan samu ƙarin daraja da girmama wa, shin me zai hana ka kama shi a matsayin bawa ga tafi da shi ga mai girma Ladiyas? Koda gama yanke wannan shawara sai sarkin yaƙi Darusu ya shammaci sarki Lazwar ya lallaɓo ta bayan shi ya dunƙule hannunshi ɗaya ya kirɓa mashi wawan naushi a fuska a gadon bayan shi. Saboda ƙarfin dukan sai da ƙashin bayan Lazwar ya yi ƙara ya faɗi ƙasa sumamme. Cikin matuƙar farin ciki sarkin yaƙi ya yi umarci waɗansu dakaru suka ɗaure hannayen Lazwar da wata sarƙa suka ɗora shi a kan doki. Nan take Darusu ya kama dokinshi ya haye ya sakar mashi linzami ya durfafi hanyar da zata sada shi da gidan sarauta dakarunshi suka rufa mashi baya Waɗansu kuma suka shiga ɗaukar dakarun suka samu raunuka domin ba su taimakon gaggawa. Wannan shi ne abin da ya faru da sarki Lazwar a lokacin da ya shiga cikin gari domin saduwa da baiwa Sharifa. Al'amarin yaro Imran kuwa, lokacin da fice daga masaukin su bayan ya kammala kalaci sai ya wanzu yana ratsa saƙo da lungu na birnin Istanbul. Domin cigiyar 'yar uwarshi, hakan ya sanya duk wajen da hango taron jama'a sai ya je ya tsaya, domin ya ga me ake gudanar wa. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 81 Yana cikin hakan ne ya iso wani waje mai cike da tarin al'umma, wani dattijo yana tsaye yana yi masu wani jawabi, kallo ɗaya za ka yiwa mutumin ka fahimci cewa ya kasance jagoran wani addini. Kawai sai yaro Imran ya ja ya tsaya yana sauraren jawabin sa. Malamin na cikin jawabin shi sai yaro Imran ya ɗaga hannunshi ya ce "ya shugabana ina da wata tambaya idan ba za ka damu ba. Koda jin wannan tambaya daga bakin Imran sai gaba ɗaya jama'ar dake wajen suka cika da matuƙar mamaki. Domin ba a taɓa jin wanda ya yiwa matsafi Shamrul wata tambaya ba akan abin da yake bayani game da bautar gunki. Cike da matuƙar mamaki matsafi Shamrul ya dubi yaro Imran da fuskarshi ke rufe da rawani idanuwan kaɗai ake gani ya ce da shi ''ya kai wannan yaro faɗi tambayar ka ina sauraren ka". Yaro Imran ya yi gyaran murya sannan ya ce "ya kai wannan malami tambaya ta a gare ka ita ce, shin waɗanne mutane ne suka fara bautar gumaka a duniya kuma mene dalilin su na yin hakan? Tambaya ta biyu mene ne ya sanya gaba ɗaya gumakan da ake bauta mu ne muke sassaƙa su da hannayen mu, to ya ya abin da mune muka samar da su daga babu a ce kuma su ne allolin mu? Koda jin waɗannan tambayoyi daga bakin yaro Imran sai fuskar matsafi Shamrul sai ta sauya daga walwala izuwa fushi, kuma ya ji zuciyarshi ta buga da ƙarfi tsoro ya kama shi ainun. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 82 Amma saboda kar jama'ar dake wajen su fahimci hakan sai kya basar. Abin da matsafi Shamrul bai sani ba shi ne haƙiƙa maganganu Imran sun yi tasiri a zukatansu baki ɗaya al'ummar dake wajen. Tabbas waɗannan tambayoyi da wannan yaro mai hikima ya yi sune abubuwan da ya kamata kowannen su ya sani kafin ya kasance cikin wannan addini na bautar gumaka, Nanfa mutanen dake wajen suka dunga cewa a amsa masu waɗannan tambayoyi haƙiƙa muna so mu ji ya tabban malami. Sautin muryoyin jama'ar ya sake ruɗa matsafi Shamrul, kuma suna amsa kuwwa izuwa cikin birnin, tare janyo hankulan sauran mutanen gari suka dunga tuttɗowa izuwa wajen, sa'adda da matsafi Shamrul ya ga cewa adadin mutanen da ke wajen yana cigaba da hauhawa, kuma ya tabbatar da cewa idan ya amsa tambayoyin abin kunya zai faru. Sai kawai ya yi wuf! Ya shafi wani gurun tsafi a damtsenshi na hagu, nan take cikin daƙiƙa biyu kacal hadari ya taso gadangadan sama ta yi duhu, a ka fara tsawa, walƙiya gami da iska mai ƙarfi, nan fa waje ya hargitse jama'a suka fara darewa suna rugawa izuwa unguwannin su domi kar ruwa ya yi masu ɓarna. A bangaren yaro Imran kuwa yana ɗaga kanshi sama ya kalli hadarin sai ya fahimci cewa, an samar da shi ne ta sihirin tsafi domin matsafi Shamrul ya kawar da hankulan al'umma daga amsar tambayoyin da ya yi nashi. Kawai sai ya yi dariya ya juya ya nufi hanyar koma gida, domin ya tabbatar RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 83 da cewa idan har matsafi Shamrul ya kasa amsa wa mutane tambayoyin za su juya mashi baya su daina karɓar fatawar addini daga gare shi, sai da yaro Imran ya bar wajen, sannan matsafi Shamrul ya daina waigen shi ya na satar kallon shi Wannan shi ne abin da ya faru da yaro Imran BABU NA SHA ƊAYA Al'amarin Gimbiya Mashlira kuwa dukkan abin da wakana da masoyin ta sarki Lazwar a kasuwa tun daga lokacin da ya fafata artabu da waɗannan dakaru har izuwa lokacin da sarkin yaƙi ya yi umarni aka ɗauke shi aka nufi gidan sarautar, tana tsaye a gefe guda tana kallo. Koda ganin hakan sai hankalin ta ya dugunzuma ainun, bisa ganin cewa babu tabbacin za su bar shi a raye, bisa mummunan laifin da ya aikata. To kenan idan har hakan ta faru za bai samu damar cika burin shi na saduwa da baiwa Sharifa ba, harya bayyana mata bukatar shi, wai shin ma ta ya ya zan iya barci a daren yau matsawar ba na jin motsin masoyina Lazwar a kusa da ni, bayan cewa zuciyata ta kamu da matuƙar kaunar shi. Tabbas zan kasance a tare dashi duk TSANANI DA UKUBA koda kuwa bazai taɓa gane cewa ni ba ce RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 84 Sa'adda gimbiya Mashlira tazo dai-dai nan a tunaninta, sai kawai ta dunga bin sahun su sarkin yaƙi Darusu a baya ba tare da wani ya gan ta ba , lokacin da ta ga cewa an kusa isa gidan sarauta sai kawai tayi ruf ta rafke ɗaya daga cikin dakarun, a cikin wani lungu ta maye gurbin tufafin dake jikinta da na shi, sannan ta kama dokinshi ta haye ta shiga cikin dakarun ta saje da su ba tare da wani ya gane ta ba. Wannan shi ne abin da ya faru da gimbiya Mashlira 'yar sarkin maridai Zammar, bayan ta fice daga masaukin su dake tsakiyar birnin Istanbul. BABI NA SHA BIYU Al amarin yarinya shuraiba kuwa lokacin da ta gabza wa ɗaya cikin dakarun dake karɓar haraji naushi a magoranshi ya faɗi ƙasa matacce, sai sauran suka zare kulaken su cikin matuƙar fushi suka yi ɗauki kan ta. Ko da ganin hakan sai almijiran dake wajen suka ruga suka bar wajen domin su tsira da rayukansu. Ita kuwa Shuraiba sai ta gyara tsayuwar ta tana jiran isowar dakarun a lokacin da jama'a suka buɗe masu fili mai faɗi sosai. Lokacin da suka iso sai aka yi KARON MAZA suka afkawa Shuraiba da azababban yaƙi, suka wanzu suna kai mata duka da kulaken cikin zafin nama domin su yi mata kisan farat ɗaya. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 85 Ana fara wannan artabu ne wani abin mamaki ya fara gudana, domin kuwa Shuraiba ta zamo tamkar shaidaniya a tsakanin dakarun, ta wanzu tana zillewa tare da hare-haren dakarun cikin matuƙar zafin nama. Nan fa ta dunga haɗa karo tsakanin dakarun, suna zubewa kasa magashiyan. Amma sai su yunƙurawa su sake afka mata da yaƙi. Lokacin da aka shafe tsawon rabin sa'a ana wannan karon batta sai ya zamana cewa Shuraiba da dakarun sun fara galabaitar da juna Ana cikin wannan yaƙi Shuraiba tayi wuf ta ƙwaci wani kulki a hannun ɗaya daga cikin dakarun, ta shiga gabza masu duka a ƙafafuwansu, kafin lokacin mai tsawo, ƙafafuwan dakarun sun sage, sun yi tsami gaba ɗayansu su sun zube a ƙasa suna nishin wahala Nan fa jama'a suka dunga shewa suna yiwa Shuraiba jinjina gami da kirari cikin matuƙar farin ciki bisa ganin cewa ta karya alƙadarin dakarun Kwatsam! Bazato babu tsammani sai akaga jiyo haniniyar dawakai gami da bugun tambura daga can nesa kaɗan, alamun dake nuni da cewa wani ma'abocin sarauta yana gab da bayyana. Koda jama'a suka waiga baya sai suka hango ashe tawagar gimbiya Lamrat ce. Cikin matuƙar firgici suka sunƙuiya ƙasa bisa gwiwoyin su, domin girmamawa a gare ta, sannu a hankali har suka iso izuwa wajen. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 86 Kawai sai aka ga keken dokin dake ɗauke da gimbiya Lamrat ya tsaya dai-dai inda yarinya shuraiba take tsaye Take Waɗansu dakaru mutum biyar suka ruga izuwa inda Kofar keken take suna masu durƙusawa ƙasa bisa gwiwoyin tare shimfiɗa gadon bayansu, sannu a hankali ƙofar keken dokin ta buɗe, sai ga gimbiya Lamrat ta fito ta taka gadon bayan dakarun ta sauko ƙasa. Sanye take cikin kariyar alƙyabba da aka yi mata cin baki da zaren lu'u lu'u da zubar daju, sanye a kanta akwai wani kambu na sarauta na zinare fuskarta rufe take da wani mayafi idanuwanta ma'abota kwarjini kaɗai ake gani. Kai tsaye gimbiya Lamrat ta taka da ƙafafuwanta ta durfafi inda yarinya Shuraiba ke tsaye wacce ita ce kaɗai bata faɗi ƙasa domin girmama a gare ta ba. Lokacin da ya rage saura taku uku a tsakanin su sai gimbiya ta ja ta tsay, ta kai duba izuwa kan dakarun da Shuraiba ta a raunata, sannan ta dubi Shuraiba tana mai ƙura mata idanu ko kiftawa ba ta yi. Nan take su duka biyun suka ji zukatansu na buga wa da ƙarfi wani abu ya ɗar su a cikin ta. Al'amarin da ya yi matuƙar bawa gimbiya Lamrat mamaki kenan, ta tambayi kanta a cikin ranta tana mai cewa. Shin mene ne ya sanya zuciyata ta buga lokacin da na yi arba da wannan yarinya? Shin ko kuwa hakan na nufin har yanzu 'yata ƙwaya ɗaya tilo tana raye? Amsar tambayoyin da ta kasa bawa kanta kenan, kawai sai ta cigaba da ƙurawa mata idanu. RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 87 Daga can sai ta buɗi baki cikin zazzakar murya mai ɗaɗin sauraro ta ce "ya ke wannan yarinya shin wace ce ke kuma mene ne dalilin da ya sanya kika zaɓi ki yi bara ki ƙyale sana'a, wacce za ta ba ki damar ci da sha. Ko da jin wannan tambaya sai yarinya Shuraiba ta dubi gimbiya cikin ladabi da girmama wa ta ce "ya shugabata ki yi sani cewa ni baƙuwa ce a wannan birni, bani da kowa na shigo wannan birni domin neman mahaifiyata da aka rabu Ni da ita tun ina yarinya ƙarama". Da jin amsar wannan tambaya sai gimbiya ta sake jin zuciyarta ta buga da ƙarfi a karo na biyu Koda ta sake ƙurawa Shuraiba idanu sai ta taga tana ɗauke da kamanni iri ɗaya sak da na masoyin ta kuma uban 'ya'yanta sadauki Murrasu. Nan take abubuwan da suka faru da masoyinta da sarki Ladiyas ya fara dawo mata a cikin ƙwaƙwalwarta, cikin ƙanƙanin lokaci zuciyarta shiga tafarfasa tamkar zata ƙone. Tsananin ƙiyayyar sarki Ladiyas ta ci gaba da ruruwa a cikin ranta. Haƙiƙa babu makawa wannan yarinya ba wata bace face 'yata Shuraiba, wata zuciyar kuma ta ce da ita, amma a halin yanzu bai dace ki wani yasan da hakan ba, dole ki yi jinkiri ki sake nazari akai sosai. Koda gama tunanin hakan sai ta dubi Shuraiba ta ce "ya ke wannan yarinya idan ba za ki damu ba ina so ki zauna tare da ni, har izuwa lokacin da zan sa a nemo maki mahaifiyarki". RANAR MUTUWA MUKHTAR KWALISA 88 Da jin wannan batu sai farin ciki ya kama yarinya Shuraiba ta ce a cikin ranta, tabbas wannan wata dama ce da zan ɗauki fansa a kan sarki Ladiyas da kuma gano inda mahaifiya ta ke. Shuraiba ta ce "na amince da wannan alfarma da kika yi min, amma nima ina roƙon alfarma a wajen ki da a daina karɓar haraji a wajen waɗannan almajirai har abada". Koda jin wannan batu daga bakin Shuraiba sai gimbiya Lamrat ta cika da matuƙar farin ciki ta dubi wani badakare a dake tsaye a gefenta ta ce da shi ''daga yau na haramta karɓar haraji a hannun dukkan wani almajiri dake wannan waje. Badakaren ya risina ya ce ''an gama ranki shi daɗe''. kawai sai ta kama hannun Shuraiba ta durfafi inda keken dokinta yake suka shiga izuwa ciki suka zauna a tare, sannan badakaren dake kula da keken ya zaburi dawakan kenan ya ci gaba da tafiya. Nan fa jama'a suka cika da matuƙar mamaki, almajiran dake wajen kuma sai sai farin ciki ya turnuƙe zukatansu, suka shiga yin shewa, kiɗa da rawa bisa

Chapter 5 of 8