Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
abin da yake mai dadi. Ya rasa da wane fuska zai kalli Murja, ya ji dadi? Yana cikin wannan hali ne Murja ta shigo da murnanta, ta fara kawo ma shi shagwaba. "Ka tafi, ka barni ni daya. Wallahi in har aka kuma zuwa, za a tafi da kai ba zan yarda ba, sai dai na bi ka mu je tare." Murja ta fuskanci yadda Magaji ke lallashinta da akwai abinda yake damun shi. Da hanzari tace "Oч sorry! Nawan, ka yi hakuri, ban kyauta ba. Don ban tambayeka dalilin da yasa aka zo aka tafi da kai gida ba ko? Allah sa dai alheri ne? Yanzun menene dalili.? Da Murja ta san amsar da Magaji zai bata da bata tambaya ba. Magaji yayi ajiyar zuciya yace "Dalili shine, an zo an daukeni ne in je in ga matar da iyaye na suka auran min ita." Murja ta daki kirjinta. Ta ja dogon numfashi tace "Mat.... Bata karasa ba, numfashin da ta ja, bai dawo ba. Ta yanke jiki ta fadi. Murja bata tashi farkawa ba. Sai cikin dare, ta ga iyayenta da Magaji suna tsaye bisa kanta. Tayi ajiyar zuciya, ta sauke numfashinta a hankali, tace "Mommy! Daddy! Kun ji cin amanan da nawan yayi min ko? Mommy ya zan yi, in hakura? Ba zan iya rabuwa da nawan ba. Na shiga uku." Ta kuma rushe musu da MAMAN FADILA 76 kuka. Shi ma Magaji hawaye ne ke zubowa daga idansa. Mahaifin Murja ke ba shi hakuri. Murja kuma mahaifiyar ta ke bata hakuri, abinda yasa mahaifin Murja ke lallashin Magaji, saboda Magaji bai munafunci iyayen Murja ba, duk ya sanar da su gaskiyar abin da ya faru da shi da sanadiyar shigan Murja wannan hali. Dan haka basu ga laifin shi ba. Da lallashi mahaifin Murja ya dauki Magaji ya maida shi makaranta, sannan ya wuce gida, suka bar Murja da Mommy ta. Murja tace "Mommy ina son nawan, son da ba zan iya yarda wata ta yi kusa da shi ba. Ba zan iya zama da kishiya ba, ba kuma zan iya fasa auren shi ba. Mommy ya zamu yi da wannan yarinyar mai tsautsayi da ta auri mijin da ba nata ba. Meye abin yi a kanta? Bana son na shiga cikin gidan nawan, na ga wata 'Ya mace da sunan mijinmu guda. Mommy ki san abin yi, in ba haka ba, komi na iya faruwa. Kada ranan da kuka kaini, in banka ma dakinta wuta, ta kone. Daga ita har kayanta. Don hankalina ya kwanta." Jin wannan kalamai da Murja ke furucinsu, suka sa na tsaya da biro. Na cak! Ina mamaki, ya za ayi ace ki na budurwa yarinya da ke, ace kin san zafin kishi irin haka? Dole ne mu da muke zaune da mazajenmu lafiya, mu dunga gudun kishiya. Dole su wance da zaran anyi mata maganan kishiya, ta kan yi kamar ta zare. To ban ga lafinki ba, dole ki tsorata, dan Allah kanninmu ku yi mana adalci. DA SANNU... 77 In kun tashi auren mazajenmu, ku dunga zuwa da zuciyarku guda. Ban da mugun nufi a rai. Da ace ke kika yi cuta. Gara ace ke aka cuta. Mommy da take sauraran 'Yarta, tana wannan mugayen kalaman. Ita sam ko a jikinta, sai ma bata fuska da tayi, tace "Murja dole hakuri za ki yi, kamar yadda na fada miki, na gaya miki Malamaina basu da wani abu da zasu iya yin miki a halin yanzun. Dole sai kina cikin gidan Abdullahi. Sannan za mu cimma duk wani buri namu. Ki yi hakuri. Saura kwana nawa ne? Murja tace "Mommy ina mutukar bakin ciki mu karasa nawan, ya koma ya zauna da wannan yarinya. An cuceni Mommy. Wai ma 'yar gidan uban waye ne? Mommy tace "Za ta wuce 'yar cikin masarautarsu ne? Murja tace "Za ko ta ci jakar ubanta, ko ma 'yar waye, kuma Mommy zan riga nawan gama karatu da kwanaki. Ina gamawa kawai za ku aika maganan aurenmu. Ni ma in shiga gidan. Ya zo ya sameni, in ba haka ba, bani da kwanciyar hankali." Allah Sarki Gaje! Baiwar Allah. Ita a wannan dare da Magaji ya koma. Dare ne da yayi mata tsawo, saboda tunaninta, shine yadda za ayi Magaji ya hakura da ita a mazaunin matar shi. Gaje ta riga ta yankewa kanta zata ci gaba da zama da Magaji, duk irin zaman daya bukaci su yi, ba za tayi ma rayuwar Magaji shisshigi ba, yadda yayi haka zata bi komi da sannu. Shi kuwa Magaji a wannan dare. Ya kasa barci, daga ya juya filo nan, sal ya juya shi can. Sai kuma ya MAMAN FADILA. 78 mike ya zauna. A haka gari ya waye ma shi. Karfe shida yana kofar Asibitin, ya samu Murja bata tashi barci ba. Nan ya zauna yasa ta gaba, yana kallonta, har ta tashi. Ta bude ido ta gan shi, sai kawai ta juya ma shi baya. Yayi ta magana. Amma bata tanka ma shi ba, bata kuma juyo ba. Sai kawai Magaji ya ja bakin shi yayi shiru. Bai kuma tanka mata ba, balle yayi mata wani furuci. Bayan wani dagon lokaci. Murja ta waigo idonta fal! Da hawaye tace "Nawan, yanzun kai ne da bakinka da idonka, ka dubeni, ka ce min kana da wata mata, bayan ni? Kana ko so-na kuwa? Magaji yace "Ya-Salam! Amma dai ce miki kawai na yi matar da aka aura min. To mai zai sa ki damu kanki, har ki shiga cikin wani hali? Aure ne dai sun riga sun daura min. Na kuma karbeta, na ajiyeta, kuma zan ci gaba da aje ta. Ki na ina? Kin riga fa kin dade da sanin ni fa naki ne ke daya, kuma ba ni da wata mata da ta wuceki. Bari in fada miki gaskiya, bacin biyayya, habu yadda za ayi ace in taka waje in wuce. Ita ma yarinyar nan ta taka. Ke duk abin da zan fada miki, ba za ki yarda ba. Har sai kin zo kin ganta, za ki jinjina min biyayyar da na yi. Har na karbi wannan yarinya, na aje ta. Ni yanzun bani da saura kwancíyar hankali, sai na budi ido na ganki a cikin gidana, kin zama matata." Kalaman Magaji sun yi wa Murja dadi sosai. Dalilin haka. Murja bata san lokacin da ta rungume Magaji ba, DA SANNU.... 79 tana fadin "Nawan, yanzun ka aje ta, babu ruwanka da ita, ba wani abu da ya shiga tsakaninka da ita? Magaji yace "A'uzubillahi. Kada ki yi sabo mana, kin kuwa ga yarinyar, ko 'yar aiki ba za ki iya daukanta ba. Ko mutuwa zan yi, ance miki zan iya hada jikina da wannan kwailar yarinyar nan ne? Ke dai biyayya dadi gare ta kawai. Ballantana mu da muka fito gidan sarauta, shi ya sa na aje ta. Amma in ba haka ba. Duka zan yi mata, na sallameta, ta koma inda ta fito. Dan ban ma san inda Baba Hakimi ya samo yarinyar ba. Ni yanzun zan koma gida, na samu Baba Hakimi, na sanar da shi ya turo gidanku a gama komi na auranmи." Duniya kenan! Ta'adanci da shedanci bai da amfani ga Dan-Adam, kamar yadda ake tunani, ko ta zata. Yankewa Lamido hukuncin kisa. To hakan ta kasance. Kotu ta yanke masa hakunci kisa, ta hanyar rataya. Kauyen 'Yan Warin Daji, sun yi farin ciki a boye. Sun kuma yi bakin ciki а baiyane. To ina ranan haka? Sauran duk anyi musu hukunci daurin rai da rai. Dan Allah samari maza, ku daina ta'addanci da shedanci, ku kama sana'a, ku guji rudin shedan da gatan duniya. Allah kuma ya shiryi masu irin wannan halayyan. Rayuwa mai canji. Yanzun Gaje ta zama 'Yar gidan sarauta, ta saki jikinta sosai, ta saba, bata da MAMAN FADILA 80 wata matsala, sai safgarta kawai take. 'Yan aikin gida duk suna kaunarta, sabo da iri halaiyarta. Lanti kuwa ta zame mata tamkar Uwar. Ita Hajiya Safiya kuwa, ita daman kowa ma nata ne a gidan, ballantana kuma matar Magajinta. To kamar yadda yace zai yi maganan kan aurensu. То hakan ko yayi. Ranan da ya dawo ya samu Hakimi, suka gama magana. Ranan ya koma makaranta. Ya shiga sasan shi, har yayi barcin mintocі. Tunda Gaje ta shiga, tayi masa sannu da zuwa, babu maganar da ta kuma hadasu. Koda zai koma ma, bai yi mata sallama ba. Dama jikin Gaje bai bata Magaji zai kwana ba, tunda bata ji ya kira Lanti ya bata umarnin din ta girka masa kalan abinci da yake so ba. Dan haka da Hajiya Safiya ta tambayeta, ko Magaji yana nan. Take tace mata ya koma, dama ta san a komawar nasa. Ta dai tambaya ne. Dan ta san ya zaman nasu yake. Hakimi ya ji dadin maganan auren nan, na Magaji saboda irin korafin auren Gaje da wasu daga cikin dangi suka dunga yi. Dan haka yanzun ya nemi duk wanda ta dace. Sun kuma je har can birni, gidan iyayen Murja. An kuma gama komi. Da zaran ta gama Diflomanta za a daura musu aure, ta tare a gidan mijinta. Hakimi yana zaune. Gaje na durkushe gaban shi. Hakimi yace "Diyata, mijin ki zai kuma kara mata, ina fata hakan ba zai canza miki halayyanki na kwarai da na sani ba tun farkon haduwarmu da ke? nikta DA SANNU... 81 Ina son halavan na kawai su fi na da. Ki zama mai juriya haj. kikas ce mai kawaici da kau d kai, ga abin bahafe ba. Komi kika gani, ki bi shi da saliliu, Adua ki ce za ki vi garajen cin masa. Bi she dai da sannuhankali, sai ki cimma nasara. Dan ha ki kwantar da hankalinki. Allah ya hada kawunanku ke da ahokiyar zamanki, mijinki kuma ki ci gaba da hiyayya a gare shi Tashi ki tafi. Allah yayi miki albarka." Komai Lomai yana da lokacinsa. Murja ta gama Difloma. Shirye-shiryen biki kawai ake yi. Abin sai ka ce babu mafadi. Ango na fama da jarabawa, yana fama da hidiman biki. Wannan fa shine sa kai, wanda ya fi bauta ciwo. Ita kuwa Gaje sai ka ce ba ita za a yiwa kishiya ba. Ni abin nata bani mamaki yake, yadda na ga mata suna jigatuwa in aka kawo musu kishiya, duk su fita haiyacinsu. Sai na ga ita Gaje sam ba haka bane. Kamar na tambayeta. To amma kuma babu dama. Tunanina ni dai ya bani ko dan dai Gaje bata san soyayya bane, shi yasa ita bata damu ba? Dangi na nesa da kusa sun halarci daurin auren Abdullahi da Maurjanatu. Haka kuma gidan Hakimi yа cika, tamkarbabu masa saka tsinke. Taro yayi taro, har da dangin Gaje da kawayenta. Hakimi sai da ya kuma gyarawa Gaje dakinta. Duk dangin Gaje da suka zo bikin, suna shiga cikin MAMAN FADILA 82 dakin Gaje. Sai su rungumeta suna mata murnan.yadda dakinta ya zama. Gaba daya su kishiya bata gabansu. Kyawun dakin Gaje shine a gaban su. To dada ni ma kaina dakin Gaje na ke, gaba daya ma sai na shiga tausayawa dakin, saboda ina ganin kamar Gaje bata san yadda zata sarrafa dakin ba. Da kyar na iya fita, na nufi dakin amaryar. Ina lekawa, na ga kayan sanabe kala-kala na dukiya, an zubasu a cikin dakin Murja. To amma kuma sai bai burgeni ba sosai. Dan wani karyan. Da kyale-kyalen in har yayi yawa, sai ya baci. Ko kusan ince almubazarranci. Dan ba a san ciwon kudin ba. An rasa yadda za ayi da su, an samesu a sama da gumin wasu. Da sauri na koma dakin uwargida sarautar mata. Ina komawa, na samu kanwar Hajiya Asabe mahaifiyar Magaji tana zazzagawa. Gaje kwandon bala'i. "Ni Wallahi ban ga amfaninki ba, tunda na zo gidan nan, babu abinda kike sai lodawa danginki abinci kike suna lodawa a cikinsu. Suna washe baki. An zo gidan akwai. An hadu da abinda ba a saba ci ba, kai tir da irin ku." Karaf! Sai a kunnen Hajiya Safiya ta zo ta kawo wasu baki da za su ga Gaje. Hajiya Safiya tace "Subahanallahi. Hajiya keda waye haka? Ba dai Gaje kike fada mata irin wadannan maganganun ba. To gaskiya kin tafka kuskure, in har da ita kike. Ki bi a hankali, kada ki gamu da bacin ranki. Yanzun muddin Hakimi ya samu wannan labari. Wallahi DA SANNU... 83 ba za ki ji da dadi ba. Ahir dinki, ki rufawa kanki asiri. Gaje taso mu je can sasana." Da guntun hawayenta Gaje ta mike. Hajiya Safiya ta kama mata hannu suka tafi. Suka bar Hajiya Jami nan sansarai, gwiwarta babu kwari. Hajiya Jami kanwar mahaifiyar Magaji, ba wani abu yasa ta ki jinin Gaje ba, sai saboda tilon da 'Yar ta Saratu da take mutuwar so, ta hada su aure da Magaji. Dan haka take takurawa Gaje, ta ki jininta. Take kuma son ta ga Gaje ta bar gidan. Dan kyar ta shigo, sai ka ce an fada mata Gajе ce zata hana ta zuwa. Ganin da Hajiya Jami tayi Magaji ya kara aure, sai take ganin Gaje ce ta jawo hakan. An gama shagulgulan biki. Kowa ya watse, babu kowa sai su. Ango kuma yana can wajen zana jarabawan shi ta karshe. Murja tayi mamakin ganin Gaje a matsayin wai kishiyarta. Ta kuma jinjinawa Magaji daya iya karbanta. A tunaninta dole Magaji yayi kokarin ya ganta ta zama matar shi. dan abin kunya ne. Ace yana da mata. A shigo a ga Gaje, dan haka kishin da Murja ta zo da shi. Sai kawai ta watsar da shi, dan bata ga shiriritan da zai sa ta bata lokaci tana kishi da Gaje ba. Mai zata yiwa kishi? Ga ta da iliminta, na boko, ga ta da kyawu, ga shi ubanta mai kudi ne. Allah Sarki! Tunanin Murja kenan! In kika mallaki wannan, kin fi karfin kishiyarki. To Wallahi ba Haka bane, ba kuma anan take ba. Kishi, koda mahaukaciya da bata da hankali, wanda MAMAN FADILA 84 bata san ciwon kanta ba aka hada ku. To kishi ne, babu zance kin fi karfinta. Ke dai ki iya takunki, kuma babu ruwan kishi da 'yar talaka, ko 'yar mai mulki, ko 'yar mai sarauta. Duk kishi guda daya ne. Kowa dai ya san abinda yake yi kawai. Magaji duk ya kosa ya kare (Exam). Ya dawo gida wajen amaryan shi. To Allah ya taimake shi. Ya gama. Ya kuma dawo gida cikin farin ciki. Hakimi ya tarasu gaba dayansu a gaban shi. Ya fara "Magajin Hakimi kamar yadda muke addu'a ka zama kamar mahaifinmu Hakimi. Allah ya yafe masa kura-kuran shi, ga dukkan alamu ka fara kwatanta zama irin shi. Yayi mata biyu. Kai ma ga shi yanzu kana da mata biyu. To Allah ya ba ka ikon yin adalci, ka rike kowa bisa amana. Dan yin adalcinka, shine zaman lafiyan gidanka, rashin adalcinka, shine rugujewar gidanka, dan haka ka kula sosai. Ku kuma ke diyata, ke cсе uwargida. Dole ki kasance mai hakuri da kauda kanki ga wasu lamuran. Kada ki zama mai sa ido. Juriya ta ki cе. Allah ne ya dora miki wannan sarautan. Duk da dai na yarda da ke, na san ba ki da matsala. Amma dai ki kula. Ke kuma Murja ke ce amarya. Dole ki yi biyayya, ki yi koyi da yadda abokiyar zamanki take yi. Kada ki zama tsagera, mai raini da tijara. Ki bi da sannu. Allah yayi muku albarka, ya hada kawunanku. Ya baku 'Ya'ya masu albarka. DA SANNU... 85 Ke Hajiya Safiya, me za ki ce musu? Hajiya Safiya tace "Ai duk abinda zan fadi, ka fada. Saboda haka abin da zan kara maimaita muku, shine ku yi hakuri da junanku, shine cin ribanku. Allah ya albarkaci zamanku tare. amin." Wata sabuwa! Mace shedaniya ce, in taso shedanci, wato koda suka dunguma suka koma sasansu. Sai Murja ta shige dakinta tana kuka da rawan jiki. Magaji ya sameta yana fadin "Murja lafiya kike kuka? Ranán farin cikinmu. Ranan da muka kosa Allah ya nuna mana ita." Ya kamota ya rungume yana lallashinta, "Fada min Beby na, me ya sameki kike kuka? Dadin kiranta da bebi da Magaji yayi, shi yasa Murja dada kwakume Magaji. Kaman zata shige cikin fatan jikin shi. Shedanci da yaudara irin tamu ta mata, shi yasa Murja dogon ajiyar zuciya, tace. "Nawan, dole in yi kuka. A gabanka Danuwanka da matar shi, suka nuna basa kauna ta, har suna fadin wancan Yarinya ita ce suka san halinta masu kyau. Suna nufin ni bani da tarbiya kenan? Magajiyace "No, ba suna nufin haka bane. Bana son ki yiwa zancen wani zargi. Ki yi hakuri, tashi mu je mu yo alwala, mu gode ma Ubangijinmu, mu roke shi, yasa mana albarka a cikin aurenmu." Koda suka gama nafilarsu raka'a biyu. Abinka da sun kosa, ba su tsaya wani surutu ba. Tambayoyin da yayi mata. Ta amsa mai. Wasu kuma ya ci gyaranta, dan zakuwa ko ma rigar barcin basu nema sun MAMAN FADILA 86 sa ma jikinsu ba. Da dai suka cire kaya, sai gado. Suka ja bargo suka kashe wutan lantarkin dakin. Ni kuma saboda gudun shiga haramcin ganin sirrin ma'aurata. Sai na yo ribas, na fito da gudu. Na nufi dakin Gaje. Da shigata na samu Gaje tana ta faman shirga barcinta. Nai murmushi, wato ita Allah bai sa ta kasa barci ba, irin nasu. Wa ke kuka har da su majina. Saboda yau Maigida yana shimfidan wata? Da abin ya ban mamaki, sai na koma gefe na kurawa Gaje ido, har ni ma barcin ya saceni. Da safe Gaje ta tashi, duk tayi abinda ya dace. Amma ango da amarya basu fito ba, har rana ta baiyana. Gaje ta kosa ta shiga cikin gidan Hakimi kamar yadda ta saba. Babu dama. Tunda bata gaisa da Maigida ba. Da amarya. Bai kamata su tashi ba su ganta ba. Gaje ta gaji da jira, sai kawai ta nufi dakin amarya, tayi sallama, tana tsaye bakin kofa da kyar Magaji ya amsa sallamar. Ta gaida shi, ba tare data shiga ba. Ya amsa mata yana cikin bargo. Ta kuma bude baki, tace 'Amarya kin tashi lafiya? Ta ji shiru, babu amsa. Magaji yace "Je ki, bata tashi ba." Gaje ko a jikinta, ta koma ta nufi inda tafi auki, tana shiga Hajiya Safiya tace "Kun ga uwargida sai yanzu muke ganinki. Lale, sannu fa." Gaje dariya take, tace "Hajiya kun tashi lafiya? Hajiya Safiya tace "Kalau. Ina fatan dai ke ma kalau kuke? Kuma babu dai wata matsala ko? Gaje tace DA SANNU... 87 "Hajiya babu." Ta ci gaba da harkokinta. "Hajiya ni fa yau kalallaba nake so na yi. Ki na da fulawa, in hada, na yi." Mafi yawanci Gaje in ta shigo sasan Hajiya Safiya, ita ce yin dan wake, gauda, dambu, fate ci ma dai irin tamu ta gargajiya. Shi Gaje take yi, dan ta ci, bata damu da ta ci girkin da aka girka a cikin gidan ba. Wani lokacin Hakimi in yana nan. Ci man Gaje yake ci, ya koshi, dan ta iya sosai. Gaje na tsaka da yi tuyar kalallabarta. Magaji suka shigo tare da Murja. rako ar Haia Safiya da fara'arta, tace 'Da kanka ka n? Gaje bata jira ta zo da ita ba." Suka gaisauji ya fita. Murja ta zauna. Gaje ta miko mata kai, tace bata ci. Sai ma ta mike tace wa Hajiya Safiya "Ni zan koma ciki. Ina da aiki." Bata jira jin wani magana ba, tayi gaba abin ta. Gaje sai yamma ta koma, ta samu Magaji baya gida. Sai Murja tana kallon (Nigeria film). Mai suna (Agumba). Tana ta dariyar tau'raron fim din mai suna Nkem Owoh. Yau shine ya gamu da Dan iskan Yaya da yake lallaba shi. Mai yi a banza. Yau ga shi shi ma ta same shi. Shigowar Gaje ta gintse dariyar da take. Gaje har zata shige daki. Murja tace "Ke zo nan." Gaje ta dawo tace "Ga ni." Murja tace "Ki ji ni da kyau, ki kuma san abin da kike, dan irinku ne 'yan kauyen nan, in mutum yayi sake, sai ku kwace mishi miji, ku bar mutum nan. Daga yau kada ki kuma zuwa MAMAN FADILA 88 min daki gaidamu, ki bari in mun fito in da halin gaisuwar, sai mu gaisa. Dan bai zama lalle ba." Tayi shiru kenan. Gaje ko daki bata shiga ba. Magaji yayi sallama ya shigo. Da gudu Murja ta rungumo shi, tana fadin "Nawan, ayoyo. Well come back to me! Tunda ka fita, ko abinci na kasa ci. Because you think! Magaji yace "Ki yi hakuri Bebi-na, wai na ga kin gaji ne jiya, kada na dawo na kuma matsa miki. Gaje da ta ga basu da niyyar sakin juna, abin nasu ba na kare bane. Sai kawai ta kama gabanta. Zata shiga daki. Ashe duk abin da suke. Magaji yana lura da Gaje, ba tare da ya waigo ya kalleta ba, yace 'Ina za ki? Ki tsaya ina da magana da ku." Sannan ya ci gaba da maganan da turanci, yana fadawa Murja wanda haka ya nunawa Gaje alama. Koda ba ta jin turanci cewa da akwai abin da Magaji yake son ya matsawa Murja akai. To haka ne. Domin bayanin da Magaji yake mata, ita tana ganin wannan ba (Reason) bane, wai yace dole ya hadasu yayi magana da su. Ita fa bata dauki Gaje kishiya ba. Sun yi ta musayan turanci tsakaninsu, sannan Murja ta zauna. Magaji ya zauna kusa da ita. Ya dubi Gaje yace "Ke ma samu waje ki zauna." Gaje ta samu kan tuntun dake can gefenta, ta zauna. Magaji ya fara magana kamar haka "Jiya mun gaji, bamu yi miki maganan kwanakin girki ba. A yau mun gama kwana bakwanmu, na amarci. DA SANNU... 89 Zan ci gaba da yin kwana biyu, ko wane daki." Murja tace 'Gaskiya kwana biyu yayi min yawa, sai dai kwana daidai, to wai ke ma ba ki da adalci ne irin na wasu mata. Da suke yi wa amarya. In anyi masu, su kara musu wasu watanni. Dan su fahimci junansu." Gaje bata san dawan garin ba, tace "To kamar wata nawa zan kara maku? Murja tace "Wasu na ga su kan kara masu kamar wata shida. Marasa mutunci, ba sa wuce wata uku. Amma in har akwai mutunci, har shekara daya ake badawa. Ke ma sai ki zabi wanda kika ga dama." Kamar in cewa Gaje ko minti daya ba za ki kara ba. Karya take. Gaje tace "To ni ma na kara muku shekara guda Amarya. Allah shi ma Magaji bai sani ba ko da gaske ne, abinda Murja ta fadi, haka na faruwa. To ni dai ba zan ce hakan baya faruwa ba, dan wasu matan su kan karawa amaryan kwanaki da basu wuce bakwai ba, saboda Allah har cikin zuciyarsu. Wasu kuma sun kara ma miji kwanaki ko ma wata, saboda tsananin kishi, ba dan Allah ba. Sai dan a nunawa miji ko in kula. Amma ita dai Gaje rashin sani kan yadda abin yake, yasa ta bada nata kwanakin, tayi musu kari. Magaji yayi shiru. Gaje ta mike zata koma daki, yace "Ke dawo." Ta dawo yace "Ina fatan dai kin san yawan kwanakin da kika kara mana? In har ba ki sani ba, bari na sanar dake, kin kara mana kwanaki 365. Kin amince? Gaje tace daga kai, alaman ta yarda. Sannan yace "Shi kenan, je ki abinki. Allah zai MAMAN FADILA 90 gyara." "Wai kai mai ke damunka ne? Yarinyar nan fa ko ta kara mana kwanaki, babu abin da zai shiga tsakaninka da ita. To ina laifin dana bata hakkinta, ba mu yi mata fin karfin ba." Magaji yace "Ni na san babu abin da zai shiga tsakanina da wannan yarinyar. To amma ya kamata ranan hakkinta, in kwana ko da a falo ne, dan ya kasance na haifi shege. Dan a hakkin wata ake haihuwar shege. To amma tunda yanzu ita tace da bakinta ta amince da haka din, shi kenan, babu wata matsala. Wannan abun yayi daidai." Kwanci tashi, sun samu wata guda da wasu kwanaki, suna haka. Babu kuma abin da yake damun Gaje, dan ba wai tana yawan zaman sasan nasu bane, balle ta ga bakin ciki. Ita kuma Lanti mai masu aiki, in ta dan zargi wani abu a cikin zuciyarta. Sai tayi sauri ta watsar, dan tana gudun hada husuma. To ita ma Hajiya Safiya tunani ya dan fara damunta. Anya kuwa babu abin da ke faruwa a zaman gidan Magaji, ba a cutawa Gaje kuwa? Kullum tunaninta kenan. Ita ba abni tayi wa Hakimi magana ba. Ya zama tashin hankali, dan ta san yadda Hakimi ke tausayin Gaje. Saboda hakurinta da biyayyarta, kuma koyaushe tace wa Gaje ba kya cikin takura dai ko? Amsar da ta ke bata, babu, suna zaune lafiya. Cikin DA SANNU... 91 wannan hali ne su Naziyatu da Nusaiba suka dawo hutu, cikin murna Nusaiba ta rungume Gaje. Ita kuma Naziyatu ta fada jikin Hajiya Safiya ta dubi Gaje da kyau, tayi dariya tace "Lale, gidanku da rowa. An waye ke ce da wannan kwalliya haka? Sai ka ce 'yar jami'a. Lalle kina tsoron kada Baba Magaji ya auro miki 'yar jami'a kenan. Ba ki san halin Baba Magaji ba. Wannan kwalliyar ta ki, bata isa ta hana shi ya kara auro 'yar jami'a ba. Ki lallabani in koya miki (Dressing) irin ta matan jami'a. Ke ma ki faso." Nusaiba tace "Tunda ke 'yar jami'ra ce, ai dole ki koya mata mana." Naziyatu tace "Ko dai ban je jami'a ba. Amma na fi wata. Kuma ni babu wata kwalliya ta 'yar jami'a da sanabe irin tasu da zai gagareni. Sai dai ban so yi ba." Hajiya Safiya da take zaune ta bude baki tana kallon wannan tsagalewa ta Naziyatu, tace “Ko ki so, ko kada ki so, ki rike (Make up) Da (Dressing) dinki 'yar jami'a ce Magaji Hakimi ya riga ya aurota, tana can sasansu." Nusaiba tace "Hajiya kuka kyale Baba Magaji ya auro 'yar jami'a. Salon su cutawa Gaje. Gaskiya ba ayi wa Gaje adalci ba." Naziyatu tace "To ke kin ga laifinsu? Shi ma adalci aka yi masa? Hajiya Safiya tace "Au, ko zaku ci ubanku. Na ga abin naku ya fara dawowa kanmu. Bari na mike yanzun na yi maganinku. Ai kun MAMAN FADILA 92 dawo kenan." Da gudu suka fita dakin. Kafin Hajiya Safiya ta mike. Suna fadin "Mun tafi wajen amarya, mu ganta, mu kuma ci abincin amarya, mu yini dakinta." Gaje bin su tayi da ido, tana masu dariya, tace "Hajiya watau in ki na neman mai sa ido, kika samu Naziyatu, to an gama. Kin ga dai da dawowarsu ta soma." Murja na kwance da (Novel) na turanci a hannunta. Wai shi (Behind the cloud). Ga dukkan alamu, ta ji dadin kwanciyar da karatun da take yi. Karan kwankwasa kofar yasa ta tashi cikin yin tsaki da bala'i, ta nufi kofar, ta bude tana fadin "Wai su waye zasu matsa min, kamar dole. Sai na bude? Naziyatu tace "Mu ne 'Ya'yan Baba Magaji. Dole ne ki bude mu ganki mana." Suka shige suka zauna. Murja ta kare

Chapter 5 of 7