Reading ALHINI by Zee Mmn khadye Chapter 5 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta6a ganewa, ai a cewar oga duk macen data kai kanta ga
naminiji batada wani fa'ida yafison wacce za'a d'auko Mashi ya mata fyad'e, yafi
jin dad'in hakan dan duk wacce aka kawo tana tirjewa yasan ba 'yar iska bace, ko ka
manta lokacin damuka kawo mashi wata yarinya tanata ihu tana zillewa, ta d'auka
yankata za'ayi koda tagane ba yankata za'ayiba, tagane manufarsa kawai sai tace
"dakasan wannan ne da baka sa nayi wahalar hawayena ba, kawai mallam bissmillah,
yana ganin haka yace afita da ita, wallahi beyi amfani da itaba, dan ya lura
sana'arta ce.

Zasu tafi kenan wayar fatima tashiga ruri lokacin, kiran jidda ya shigo, cikin
tsananin tsoro da kad'uwa ta sa hannu ta danne wayar, harta tsinke bata d'aukaba
sai kuma aka 'kara kira karo na biyu, tayi ko'karin takashe wayar baki d'aya amma
sai ta kasa saboda tsananin rud'ewa.

Da sauri wad'annan mazan suka shigo cikin kangon gida suna dubawa dan jin waya nata
ringing, lokacin kuwa Fatima tagama sadaukar da rayuwarta, cikin sa'a kuwa suka
ganta basuyi wata-wata ba suka sungumeta, guda ya d'orata kan kafad'arsa tanata ihu
tana dukansa tana yagunsa, hadama cizo amma ko a jikinsa, ganin zata tona masu
asiri yasa gudan ya fiddo wani salatif ya toshe mata baki.

Tafiya marar nisa ta sadasu da inda suka ajiye motarsu wata bakar Hummer jeef mai
ba'kin glass suka jefata ciki, sannan sukaja motar, tafiya mai nisa sukayi wacce
fatimar batasan inda sukeba, bata iya ganin kome, saboda duhun dare ga kuma ba'kin
glass d'in motar.
Bakin wani 'katon gida wanda zamu iya kira aljannar duniya saboda 'kyawunsa, sukayi
horn me gadi ya bud'e masu get suka shiga, wani had'adden bedroom suka jefata kan
gado sannna suka kware salatif d'inda ke bakinta, saboda tsananin azaba saida
tafasa 'kara.

Haka suka fita suka barta sukaja 'kofar, itakuma banda kuka ba abinda takeyi.

'Karar bud'e d'akin yasa ta d'ago kanta wani 'katon mutum tagani, dogo ne fari me
dogon hanci da manyan idanuwa, ga bakinshi ma barakallahu babbane, ga 'kiba dake
gareshi kamar basamude.

Tsayawa yayi ya 'karema Fatima kallo, sannan ya matso yana lasar baki kamar tsohon
maye, yace "kai amma yau nayi dace tunda ake kawomin 'yan mata ba'a ta6a kawomin
'kya'kyawa kamarkiba, yasa hannu ya cire hijabin dake jikinta, ganin surar jikinta
yasashi 'kara rikicewa dan rigar datasa tad'an kameta, ga kanta ba d'an kwali, yayi
dariya yace amma kinada ala'ka da india ko? Wannan 'kya'kyawan gashi haka, yakai
hannu yana shafa kanta, itakuma kuka kawai take takasa ta6uka kome, a zuciyarta sai
addu'a take Allah kada yaba wannan mutumin ikon aikata abinda yake nufi akanta.

Haka yacigaba da shafata yana latsata, inbanda kuka ba abinda take, nan yashiga
'kokarin rabata da 'kayan jikinta, tasa hannu ta rirri'ke koda yaga zata kawo mashi
gardama sai ya nunamata 'karfi lokaci guda ya rabata da rigarta, jikinta yarage
daga ita sai bes, sai wando lagis data Sanya lokacin dazata fito, ganinta haka da
bayyanar 'kya'ky'kawar surarta ya'kara rikitashi, ya fita hayyacinshi gaba d'aya ya
rungomota jikinshi....




_*Ina barar addu'arku masoyana a duk inda kuke, shekaran jiya anyima babana theatre
Emergency, amma yaji sauki, kutayani addu'a Allah 'kara Mashi lafiya da duk musulmi
baki d'aya*_ 👏🏻😭




🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] www.gidannovels.blogspot.com [03/09 4:10 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇


®```NWA```


_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘


4⃣3⃣4⃣4⃣
4⃣3⃣to4⃣4⃣
4⃣3⃣4⃣4⃣

🖊 kuka Fatima tashiga yi ganin yana neman keta mata haddi, tana cewa "dan Allah
kayi ha'kuri kada ka cuceni kada ka 6ata min rayuwa, tana fad'ar haka tana wani
irin kuka me tsuma zuciyar me sauraro, amma mutuminnan ko ajikinsa, dan ko kad'an
bata bashi tausayiba illah 'kara kwad'aituwa dayayi da ita.

'Ko'karin rabata da sauran kayan dasuka rage jikinta yakeyi, itakuma banda addu'a
ba abinda takeyi, dan batada wani sauran kuzari tattare da ita.
A 6angaren Mukhtar kuwa yasha yawo har kusan 'karfe biyar na asuba amma bega Alamar
zega laraba ba, be 'kara shiga tsananin tashin hankaliba saida yafara jiyo kiraye-
kirayen sallar asuba,
haka yakoma gida zuciyarshi cike da takaici da ba'kin cikin rabuwa da
masoyiyarshi.

Yana shiga gidan a falo ya iske Hajiya da jidda sun buga uban tagumi, suna tunanin
ko yaga fatimar,.....
Ganin shigowarshi shi d'aya batare da laraba ba yasa jidda saurin tashi cikin
muryar kuka tace "yaya baka gantaba? Innalillahi munshiga ukku, ta fashe da wani
sabon kuka.

Jiki sanyaye mukhatar yasamu guri ya zauna.
Sai lokacin Hajiya ta kalleshi jiki a sanyaye tace "Mukhtar Yaya ba'a gantaba ko?
Wata nannauyar ajiyar zuciya yayi sannan ya d'ago da idanunshi wad'anda suka kad'a
sukayi ja saboda tsabar damuwa, yace "Hajiya Fatima ta su6ucemin shikenan Hajiya
narasa Fatima, lokacin wasu zafafan hawaye suka zubo daga idanunshi, yace "Hajiya
me mukayima Fatima ta gujemu? Me tanema a gidannan tarasa?.

Lokacin wani irin tausayin Mukhtar tashige hajiya, a zuciyarta tace tabbas mukhtar
yana cikin halin damuwa, dan na lura da yanda ya gama dam'ka duk illahirin
soyayyarshi ga Fatima, a Zahiri kuwa cewa tayi "inshaAllah duk inda Fatima take
zata dawo garemu, kudai kucigaba da Addu'a Allah tsareta a duk inda take,
Lokacin jidda ta fashe da wani sabon kuka tana cewa "ya Allah ka bayyanamin
'yar'uwata a duk inda take, Allah kareta da duk wani mugun abu.

Sai da sukaji an kabbara sallah a masallacin kusa dasu sannan kowanensu yatashi
yanufi sashensa dan gabatar da sallah, mukhtar kuwa koda yayi Alwala masallaci ya
wuce zuciyarshi cunkushe da ba'kin ciki da takaicin halin daze tsinci kanshi inhar
yarasa Fatima.

A 6angaren laraba kuwa haka mutumin yari'ka jagulata amma har yanzu Allah be bashi
ikon cimma burinshiba na keta mata haddi,

Amma duk illahirin jikinta yagama jagulata, hannu yakai yana kokarin ida rabata da
bes d'in jikinta wacce ita kad'ai tarage sai lagis d'inda tasa hannu ta rirri'ke
lokacin dataji yana Neman rabata dashi,

Wani irin 'karfi yazo mata a lokacin hannuwanta tasa duka biyun ta d'ora kan
'kirjin mutumin Wanda gaba d'aya yayimata rumfa dashi, ta turashi iya 'karfinta.

Jiyayi kamar wasu 'katti goma sun angizashi, yayi baya,yafad'i 'kasa, lokacin kuma
Fatima ta taso mashi hai'kan kamar wata tsohuwar damisa, lokaci guda duk wani haske
na fuskarta ya dishe, idanunta suka canja launi zuwa ja, tayo kan mutumin hai'kan,
a tsorace yatashi yafara ja da baya, dan ya masifar tsorata dan yanda take
tunkaroshi.



Saida ya dangane da bangon d'akin lokacin yashiga laluben 'kofa dan tsira da
rayuwarshi, amma kafin yayi yun'kurin bud'e dakin yafita ta kaimashi wani wawan
bugu da hannunta d'aya, wani irin duhu yaga ya gifta mashi, kanshi ya bugu da
bangon d'akin, take yafashe jini yafara ambaliya, yana wanke mashi jiki, a tsorace
yafasa wata uwar 'kara yana Neman taimako,

da gudu yaranshi suka nufo d'akin dan jin ogansu yana neman taimako, suka shiga
tura 'kofar amma ko kad'an ta'ki bud'ewa, da sauri guda yanufi wani d'aki ya d'auko
wani makullin ya bud'e, da sauri suka nufi inda ogan nasu yake kwance yana maida
numfashi sama-sama ga jini duk ya gama wanke mashi jikinshi, suka d'agoshi suna
fad'in "oga lafiya meke faruwa? cikin dusashshiyar murya ya nuna Laraba, yace
"ita....itac...itace... Nan kafin yagama fad'a masu yafad'i sumamme.

A harzuke suka nufi Fatima wacce hankalinta yayi masifar tashi da ganin halin da
mutumin dayayi niyyar yimata fyad'e yake ciki, dan ita bata San meya faru da
itaba, tun lokacin da mutumin yanemi ida rabata da kayan jikinta.

Amma me kafin su 'karaso gareta sai ji sukayi an d'aukesu da wasu mahaukatan
marurruka, kowanensu ya dafe kunci yana duba d'an uwansa, kafin suyi wata magana
aka rufesu da duka ta ko'ina, nan suka shiga ihu suna neman taimako, amma ba wanda
ke jinsu, dan dama haka gidan yake ihunka banza ne, dan da haka ogansu ke samun
damar keta haddin 'ya'yan mutane batare da anji koda ihunsuba.

Saida suka daku sukayi li'kis sannan aka 'kyalesu,
Fatima kuwa banda kuka ba abinda takeyi, dan ita kanta abin ya tsoratata yabata
mamaki dan ganin yanda mutanen keshan jibga batare da su duka sunga me dukan nasu
ba,

Lokacin jikinta yashiga 'kyarma takama kuka tana 'yarfa hannuwa tana kiran
innalillahi,
Hanyar guduwa tashiga nema dan tsira da rayuwarta, lokacin idonta yakai kan 'kofa
dake bud'e tun lokacinda yaran oga suka shigo dasukaji yana neman taimako.

Bata tsaya d'aukar kayan taba tanufi 'kofar tashiga falon d'akin tari'ka shiga
'kofofi na gidan, tashiga nan tafita nan amma har yanzu Allah besa taga 'kofar da
zata sadata da wajen gidan ba, 'karshe ma idan tashiga wata 'kofar sai taga ta
'kara maidota cikin gidan.

Haka tayita zagayen gidan, har 'karfe bakwai da kimanin minti sha shidda na safe,
lokacinne kuma oga ya farfad'o daga doguwar sumar dayayi, yayi saurin kai dubanshi
gurin da laraba take amma be gantaba, cikin tsananin rud'ewa ya kai dubanshi ga
yaranshi dake kwance suma basu san inda kansu yakeba, lokacin ya ta'kar'kara
yatashi yakai masu duka, "kutashi kai dan uwarku ku tashi ina yarinyar nan take, a
firgice suka kai dubansu ga ko'ina na d'akin basu gantaba.

Cikin d'aga murya oga yake magana, kuyi sauri ku nemomin ita, kada ku kuskura tabar
gidannan, da sauri suka tashi suka shiga zagaya gidan suna nemanta, dan sun tambayi
me gadi yakuma tabbatar masu da bata fitaba, aiko suna cikin dubawa sukayi kici6is
da ita a cikin wani korido, wata 'kara ta fasa tayi baya, kafin tayi wani yun'kuri
har sun cafkota.

Cikin gidan suka koma da ita, wannan karon wani d'akin suka kaita ba wanda suka
fara ajiyeta da farko ba.

Wata igiya suka sa suka d'ad'd'aureta, sannan sukaja 'kofar d'akin sukasa key suka
kulle.

Banda kuka ba abinda Fatima keyi, wannan karon tariga ta gama sadau'kar da
rayuwarta,

Bayan kamar awa d'aya da d'auretane, taji ana murd'a kofar, takai dubanta ga 'kofar
dan ganin me shigowa.

Oga ne yashigo cikin shigar ba'ka'ken jacket da wando sai wani ba'kin 'katon glass
dake fuskarshi me suna no respect 😎.

sai yaranshi guda biyu suma cikin 'kananan kaya suna take mashi baya.
Bakin 'kofa yaran suka tsaya, kowane gefe guda yayinda sukasa 'kofar tsakiya,
Shikum oga ya ida shigowa d'akin inda fatima take d'aure yanufa yashiga zagayata
yana tafa hannuwa, itakuma sai binshi take da ido duk illahirin jikinta 'kyarma
yake,
Wani shu'umin murmushi yayi yace.......




4⃣5⃣to4⃣6⃣ Very 4⃣5⃣4⃣6⃣
4⃣5⃣4⃣6⃣




🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] www.gidannovels.blogspot.com [04/09 3:57 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇


®```NWA```


_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘


4⃣7⃣4⃣8⃣
4⃣7⃣to4⃣8⃣
4⃣7⃣4⃣8⃣


🖊 Cigaba yayi da kallonta, sannan yace "A gaskiya na kwad'aitu da kyakkyawar surar
da Allah yayimaki, kuma iya tsawon rayuwata ban ta6a d'ora idona kan wata mace ba
tabani sha'awa in kyaleta batare dana biya bu'katataba, amma ke sai gashi na kasa
aiwatar da kome a kanki.

"Ianso zan miki wasu 'yan tamaboyoyi yanzu, ki tabbatar da kin bani amsarsu iyakar
gaskiyarki, hakan zesa in fiddaki daga gidannan da kaina batare da wani abu yafaru
dakeba.

Binshi kawai takeyi da ido, dan ita ahalin yanzu tariga ta sadaukar da rayuwarta,
kuma yanzu take danasanin gudowa datayi daga hannun mutanen dasukayi mata halacci,
yanzu batasan halin da guduwarta ya jefasu cikiba, tabbas ko ba'a fad'aba tasan
idan hankalinsu yayi dubu yatashi, ba kamar masoyinta Mukhtar Wanda ya d'auki son
duniya ya d'ora mata, a zuciyarta tace _(ya Allah ka fitar dani daga hannun wannan
mugun mutumin, Allah ka maidani gurin masoyina abin 'kaunata Mukhtar)_.

Wata uwar tsawa ya daka mata, wacce tayi saurin maidota daga duniyar tunanin data
afka, yace "miye sunanki?
Jiki na 'kyarma ta kalleshi idanunta na zubar da hawayen nadama tace
"Sunana Fatima...
Murmushi yayi sannan ya maiamaita sunan fatima koh? Ya'kara tambayarta, ta d'aga
Mashi kai alamar eh.

Yayi shuru na kimanin mintuna biyu sannan ya'kara jeho mata wata tambayar,
"Fatima ke mutum ce ko Aljan?
Tace "ni mutum ce.
"Amma ke matsafiyace,
Jiki na 'kyarma ta girgiza kai tace
"Ni ba matsafiya bace ban ta6a tsafiba.

Shuru yayi na wani d'an lokaci sannan yace "to fatima abinda yafaru jiya miye
kikayi idan kince keba Aljana bace, cikin muryar kuka tace "minayi,? Wallahi banyi
kome ba.

Cikin takaici ya kalleta yatuno da irin 'karfin data nuna mashi jiya lokacin dayake
'ko'karin yimata fyade, da ciwon data jimashi, yashafa kanshi inda ta dokeshi gurin
ya fashe, take wani irin mugun tsoronta ya dirar mashi a zuciya, ya maida kallonshi
gareta yace "yanzu zaki iya gane gida?
Kai kawai ta d'aga mashi alamar "eh badan tasa ran ze maidata gidan ba.

Hannu yasa ya kwanceta daga d'aurin da sukayimata, sannan yace "zaki iya shiga
toilet ki watsa ruwa ki canja kaya ni zan maidaki gidanku da kaina, dan barin
irinki suna zuwa hannun masu irin halinmu babban had'arine.

Be jira abunda zata fad'aba yafita daga d'akin yaranshi suka take mashi baya.

Tana ganin yafita jiki na 'kyarma taje ta kulle d'akin hada sa key da sakata,
sannan tafad'a toilet tahad'a ruwan d'umi tayi wanka, tad'an gasa jikinta dan duk
illahirin jikin ciwo yake mata, sannan ta d'auro Alwala tafito tasa kayanta sannan
ta d'ora hijab ta kabbara sallah, dan bata manta da batayi sallar asuba ba.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Zaune suke jugum-jugum kowanensu yabuga uban tagumi bakajin kome sai sheshekar
kukan jidda, dan tunda aka tabbatar da 6atan fatima jidda ke kuka, idanunta sun
kumbura ga matsanancin ciwon kai dake damunta sakamakon kukan datake ba
'ka'k'kautawa.

Mukhtar ma kukan yake kamar mace, kokuma 'karamin yaro, sun tasa hajiya gaba, wacce
itama duk illahirin jikinta mace yake, dan ta d'auki fatima kamar 'yar data Haifa
da cikinta saboda haka dole taji 6atanta har cikin ranta, amma ganin yanda yaranta
suka d'aga hankalinsu yasata daurewa tari'ka rarrashinsu.

Suna cikin wannan zaman ne megadi yashigo da sallama, bayan Hajiya ta masa sallamar
yace Hajiya sallama ake a waje, cikin damuwa Hajiya ke tambayarshi "wanene me
sallamar, yace "eh to Hajiya gaskiya ban shedashiba amma yace maganace me mahimmaci
ke tafe dashi idan da hali yanaso ayimashi iso yashigo,
Hajiya tace "OK shigo dashi.

Bayan fitar me gadi da kamar minti biyar saigashi yashigo, cikin shigar manyan kaya
shaddace jikinsa, light blue, sai hularsa light blue, sai takalmi ba'ki, kallo
d'aya zakayimashi ka gane mutum ne wanda naira ta zauna mawa...

Bayan yasamu gu ya zauna yafara magana "ni sunana sadiq kuma ni d'an cikin garinnan
ne, idan bazaku damuba inaso insan yara nawane a gidannan, ma'ana 'ya'ya nawa kuke
dasu.....

Wani 'kululun ba'kin ciki ya tsayama mukhtar a wuya, a fusace ya kalli mutumin yace
"wannan wane irin rainin wayone zakazo kana mana tamabayar da bata shafekaba,
Sadiq yabud'e baki zeyi magana kenan sukaji tafiyar mutum ana shigowa gidan, da
sauri suka kai dubansu gurin....

Da gudu jidda ta tashi taje ta rungumeta tana kuka, tana cewa "sister ina kika
shige kika barmu cikin tashin hankali, fatima kasa furta kome tayi sai hawaye
datake zubarwa, cike da murna da fargaba Hajiya tazo takama hannun Laraba tashigo
da ita falon, mukhtar kuwa kasa furta kome yayi, illah bin fatima da yayi da ido.

Maganar Sadiq ce tadawo da hankalinsu gareshi, yayinda yake sanar dasu abinda
yafaru tsakaninshi da Fatima, be 6oye masu kome ba ya sanar dasu gaskiyarshi, dan
yariga ya tuba daga mummunar d'abi'ar dayake ta 6ata yaran mutane.

Wani irin takaici da ba'kin ciki da kishi suka taru suke rufe Mukhtar dan jin
labarin da Sadiq yafad'a saboda haka ido rufe ya tunkareshi kamar wani tsohon
mayunwacin zakin daya kwana beciba.......




4⃣9⃣to5⃣0⃣ Very 4⃣9⃣5⃣0⃣
4⃣9⃣5⃣0⃣




🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] www.gidannovels.blogspot.com [04/09 10:48 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇


®```NWA```


_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘


4⃣9⃣5⃣0⃣
4⃣9⃣to5⃣0⃣
4⃣9⃣5⃣0⃣


🖊 A zuciye mukhtar yakaima Sadiq wani wawan naushi a fuska, take gancinsa yafara
zubar da jini, cikin 'kankanin lokaci jini ya 6ata mashi tsadaddiyar shaddarsa
wacce tasha d'inkin computer, ganin jinin dake zuba daga hancin Sadiq besa Mukhtar
ya saurara mashi daga dukan dayake mashi ba, cigaba yayi da dukanshi ta ko'ina,
sannan yacimashi kwala ya tadashi tsaye ya angizashi, cikin fushi da d'aga murya
yace "kafita daga gidannan tun kafin inzama ajalinka, mugu azzalumi barin irinka
cikin Al'umma had'arine.

Duk abinnan da Mukhtar yayima Sadiq beyi 'ko'karin hanashiba, kuma be kare kanshi
daga dukan dayayi mashiba, badan beda 'karfin daze ramaba, dan a girme sadiq yakai
d'aya da rabin mukhtar, dan acewarshi duk abinda Mukhtar yayimashi ya can-canci
hakan.

Jidda ce taga abin na yayanta yayi yawa dan dukan sad'iq yake kamar baze barshi da
rai ba, ta kalli Hajiya tace "dan Allah kihanashi kada ya kasheshi,
Bata jira hajiyaba tanufi gurin tari'ke hannun mukhtar tana cewa "dan Allah yaya
kayi ha'kuri ka 'kyaleshi tunda Allah be bashi ikon aiwatar da kome kan Fatimar ba.

Ganin beda niyyar sauronta yasa ta kama hannunshi tari'ke tana bashi ha'kuri a
zuciye ya hankad'ar da ita tafad'i zaune tafashe da wani irin kuka.
Ganin abin na Mukhtar bana hankali bane yasa Hajiya tazo ta kamashi, tace "kai
mukhatar ka daina dukanshi nace, be saurari hajiyaba sai 'ko'karin tura Sadiq waje
yake, yana cewa "kafita kabar gidannan ban 'kaunar ganinka, wallahi idan ina
ganinka zan iya illataka dan ban had'a fatimana da kowaba.

A fusace Hajiya ta fincikoshi, cikin fushi take magana "wai kai Mukhtar wane irin
mutum ne, yaushe kafara rainani da inama magana baka saurarena.

Wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonshi, baya yayi yasamu guri ya zauna kan
d'aya daga kujerun falon yana cika yana batsewa, jiyake dama Hajiya tabarshi da sai
yakusa halaka sadiq.

Fatima kuwa tunda suka shigo gidan taga halin data iskesu hankalinta yatashi, bata
'kara shiga wani tashin hankalinba saida taga yanda Mukhtar ke dukan Sadiq gashi
harya fitar mai da jini amma be daina dukansaba.

*_Innalillahi'wa,inna'ilaihirraji'un_* tashiga furtawa, tana kuka kamar zata cire
ranta, jidda ce takamata tace "ki daina kuka fatima ki godema Allah daya tseratar
dake da mutuncin ki,
Cikin dusashshiyar murya Alamar tayi kuka tagaji tace "jidda dole inyi kuka, duk
halin damuwar da kuka shiga nice na jefaku, sannan abinda mukhtar yayi yanzu duk
saboda ni yakeyi, wayyo Allah na ina zani da Alhaki, nazama butulu, na guji mutanen
dasukayimin hallaci a rayuwa, mutanen dasuka sharemin hawayen da 'kanin mahaifina
yakasa sharemin,

Zuwa tayi gaban Hajiya ta dur'kusa gwiwa biyu, tana kuka tace "dan Allah Hajiya Ku
yafemin nasan nashiga rayuwarku na jefaku cikin damuwa.

Cike da damuwa da tausayi Hajiya takama hannun fatima ta zaunar da ita kan kujera
tana gogemata hawayen dake zuba Daga idonta.

.
Hajiya takai dubanta ga Mukhtar Wanda keta cika yana batsewa, tace "ba haka
akeyiba kawai ka kama mutum kayita duka har ka jimasa ciwo, duk da abinda yafad'i
yana aikatawa ai bekai ga aikatashi ga ita fatimar ba,
Kuma tunda kaga yakawota har gida ina tunanin akwai dalilin sayasa yakawota.

Sannan ta maida dubanta ga Sadiq tace ina jinka yaro, cike da nadama Sadiq yafara
magana,cikin muryar tausayi da nadamar abubuwan daya aikata a baya.
_ ```na kasance ni 'kadai iyayena suka haifa, kuma iyayen nawa sun kasance masu
tarin dukiya, tun ina 'karami suke nunamin tsantsar so da 'kauna, hakan yasa
natashi banajin magana ko kad'an kuma duk abinda naga dama shi nakeyi, tun ina
secondary school nake 6ata yaran mutane, ta hanyar yimasu fyade idan sun'ki
amincewa, a lokacin nama fi so inyi fyaden dan nafi jin dad'in hakan, kuma idan aka
ganeni aka kawo 'karata babana sai yakama fad'a yace anjamin sharri dan ana ba'kin
ciki da dukiyar da Allah yayi Mashi, kuma yabani shi amatsayin d'a d'aya tilo haka
yake fatattakar mutane, wasu su fita suna kuka wasu kuma suje suna Allah ya isa,
ana cikin wannan halinne mamana da babana sukayi tafiya, kan hanyarsu ta dawowa
suakayi had'ari suduka suka mutu, nayi kukan rashin iyayena sosai, bayan kome ya
lafa aka raba gado aka bani, kasancewar bani ganin Kowa da gashin arzi'ki yasa ba
wanda yayi gigin cewa ze ri'kemin dukiyata, cikin dangin mamana, kona baba na, haka
nacigaba da bushasha, har basamu yarana wad'anda sune ke d'aukomin 'yan mata ina
keta masu haddi ta 'karfin tsiya```

Wasu hawaye masu zafi suka zubo daga idanunshi, yace amma sanadin zuwan fatima
gareni yasa natuba na daina wannan mummunar d'abi'ar danikeyi, kuma inaso dan Allah
fatima ki yafemin, yafad'a yana kallonta.

Mukhtar be tausayama sadiq ba ko kad'an illah wani irin haushi daya 'kara bashi
yace "dallah Malam kafita kabar gidannan munji duk bayaninka Allah shiryeka, bani
son ganinka cikin gidannan kuma bani bu'katar jin muryar ka.

Cikin fad'a Hajiya ke magana, dan mukhtar yafara 6ata mata rai tace "wai kai wane
irin mutum ne, mutum yazo har gida yaro'ki yafiya amma kakama cimasa mutunci, ay
inajin koda kafirine yazo neman gafara gareka zaka gafarta mashi kodan yasan
musulunci akwai Alfarma acikinsa, barantana d'an uwanka musulmi, Allah yana son
masu yafiya ga junansu, wai Mukhtar ina iliminka yake,?
Kuma kafin wannan ma ay komiye fatima itace babbar mai laifi, da bata fitaba da duk
haka be faruba.

Sadiq yace "ni najin dad'in fitar tata dan tazama sanadin shiriyata, fatana shine
tace ta yafemin, yafad'a yana zubar da hawaye...


Cikin muryar kuka fatima take magana "tabbas kome yafaru nice na jawo, dan daban
fitaba da hakan bata faruba,
Ta kalli sadiq tace nayafema, Allah 'kara shiryaka, kuma naji dad'i dana zama
sanadin shiriyarka.

Tana gama fad'in haka Sadiq yami'ke yace nagode Hajiya sai anjimanku, yafice daga
gidan.

Fatima kuwa durkusawa tayi tsakiyar falon tana kuka, tana ro'kon Hajiya da jidda da
mukhtar su yafemata,
Mukhtar har cikin ranshi yakejin kukanta, baze iya juraba saboda haka barin d'akin
yayi zuciyarshi na tafarfasa.




5⃣1⃣to5⃣2⃣ Very 5⃣1⃣5⃣2⃣
5⃣1⃣5⃣2⃣




*_'kya'k'kyawar gaisuwa ga 'kanwata, NASIBAT ELKASEEM_*
_Love u my sister_😘




🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] www.gidannovels.blogspot.com [06/09 3:22 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇


®```NWA```


_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘


5⃣1⃣5⃣2⃣
5⃣1⃣to5⃣2⃣
5⃣1⃣5⃣2⃣
🖊 washe gari bayan kome ya lafa, da misalin 'karfe tara da rabi na safe,
Zaune suke a general falo, bayan sun kammala kalacin safe, Kowa yayi shiru, amma
akwai abinda yake sa'kawa cikin zuciyarshi, yayinda Fatima takan goge guntayen
hawayen dakan zubo mata daga idanunta akai-akai.

Mukhtar yana lura da halin datake ciki saboda haka hankalinshi duk yana gurinta,
fatanshi Hajiya ta wuce d'akinta ya rarrashi fatimarsa ya kwantar mata da hankali,
dan idan akwai abinda yafi tsana a duniya shine 6acin ran hajiyarsa sannan kuma
yaga fatimarsa cikin damuwa.

Hajiyace ta maido da kowanensu daga duniyar tunanin daya Lula, yayinda ta kalli
Fatima tace "Fatima inaso ki nutsu ki kwantar da hankalinki ki fad'amin gaskiyar
dalilin dayasa kikayi 'ko'karin guduwa daga hannunmu wanda hakan yajefamu cikin
matsanancin tashin hankali.

Shuru tayi na d'an wasu mintoci bakajin kome sai sheshshekar kukanta, sannan tafara
magana cikin sarkewar murya tace "da farko inaso in ro'keku yafiya akan halin
damuwar dana jefaku na 'ko'korin guduwa danayi,
Bawai nayi hakan bane dan kun gaza da ri'kon da kukemaniba, ba kuma dan na raina
hallacin da kukayimani bane, a'a nayi hakane saboda baniso in sakamaku da sharri
akan Alkhairin da kukayimani.

Sannan inaso Ku gafarceni akan 6oye maku wasu abubuwa da dama danayi dangane da
labarina, yau inaso zan sanar daku kome bakin gaskiyata, dan baniso nazama sanadin
rushewar farin cikinku.

*_HAKA LARABA TA KWASHE LABARINTA KAF TA FA'DA MASU BATARE DATA 6OYE MASU KOME BA_*

Bayan tagama basu labarinta ne tacigaba da cewa "muddin na yarda da auren mukhtar
nasan shima 'karshen rayuwarsa yazo, nasan shima ze mutune kamar yanda maza ukku
suka mutu sanadiyyar aurena, a 'kauyenmu' yayinda na hud'unsu yasha ba'kar azaba
har yarabu dani ranar dana tare gidanshi, shima na tabbata kwanasa ne be 'kareba da
yanzu shima sai labari.

Jidda wacce tunda Fatima tafara bada labarinta take kuka tace "Fatima duk wanda
yamutu kwanansa ne suka 'kare kuma inshaAllah yayana ze aureki kuma ze zauna dake
ba abinda ze faru daku.

Hajiyama saida ta goge guntayen hawaye dan tausayin da Fatima ta bata, tace ki
kwantar da hankalinki Fatima ni nayi Al'kawarin zama dake kuma inshaAllah ko miye
ze rabu dake, kuma aurenki da Mukhtar ba fashi muddin kuna son junanku.

Wani sanyi Fatima taji har cikin ranta, dan son mukhtar ya dad'e da d'arsuwa a
zuciyarta.

Shima mukhtar haka yaji,
Cike da farin ciki yace "Hajiya inaga Al'amarin Fatima kamar hada iska cikinsa,
saboda haka inaso zan kaita gurin wani friend d'ina wanda shida babanshi sun 'kware
gurin magance irin wannan matsalar ta hanyar amfani da ayoyin Allah da kuma
magungunan musulunci wanda babu shirka a cikinsa.

Cike da jin dad'in yanda d'anta keson taimako Hajiya tace "to Allah taimaka Allah
sa a dace.
Su duka suka amsa da Ameen.

Sannan jidda takama hannun Fatima suka nufi d'akinsu, kai tsaye toilet suka shiga
suka d'auro alwala suka kabbara sallar nafila da niyyar Allah yayema Fatima lalurar
dake tattare da ita.


°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Washe gari da musalin 'karfe goma na safe sun fito cikin shiri, jidda da faima suna
sanye da riga da wando na fakistan sannan suka d'ora hijabansu, sunyi kyau abinsu,
Mukhtar kuma cikin shigar manyan kaya shadda ash colour sai ba'kin takalmi sai
'kamshin turarensa daya buge ko'ina,

Har mota Hajiya tayi masu rakiya, suka shiga me gadi ya bud'e masu get suka d'au
hanya.

Mintuna talatin suka sadasu da gidan mal bature, shine mutumin daya 'kware gurin
magance matsalar jinnu ko asiri ko sihiri, ta hanyar amfani da ayar Allah batare da
an kauce hanya ba.

Suna Isa Mukhtar yayima abokinshi waya me suna Usman ya sanar dashi isowarsu,

Da far'a ya fito ya tarbesu, sannan yayimasu iso,
Bayan sun shiga sun gaggaisa Mukhtar ya sanar dashi abinda ke tafe dasu, duk da dai
kamar 'karin bayanine yake mashi dan sun riga sun gama maganar kome ta waya, har
Usman d'in ya Sanar da babanshi zuwansu.

Nan ya nunamashi Fatima matsayin wacce za'ayima maganin, Fatima wacce tunda sukazo
kanta ke sadde 'kasa Usman yakira sunanta "Fatima, sai lokacin tad'ago ta kalleshi,
suna had'a ido gabanta yayi mummnar fad'uwa wanda ita kanta batasan dalilin hakan
ba.

Cewa yayi su biyoshi zuwa gurin babnshi, haka suka bishi Fatima jikinta sai 6ari
yake kamar wacce ake girgizawa....




5⃣3⃣to5⃣4⃣ very 5⃣3⃣5⃣4⃣
5⃣3⃣5⃣4⃣




🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] www.gidannovels.blogspot.com [06/09 7:00 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇


®```NWA```


_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘


5⃣3⃣5⃣4⃣
5⃣3⃣to5⃣4⃣
5⃣3⃣5⃣4⃣
🖊 Bakin 'kofar d'akin Fatima ta toge ta'ki shiga, mukhtar ya kalleta yace "muje
mana Fatima ko wani abu kk jira, banza tayi ta 'kyaleshi ta tsaya gurin

Please Login or Register in order to submit comment