Reading ALHINI by Zee Mmn khadye Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rai mamacine, Allah ji'kan hashim_*

Wata uwar 'kara ta saki tare da fashewa da wani irin kuka, wanda yajawo hankalin
mutane zuwa gareta,

Lokaci guda tanemi numfashinta ta rasa, ta fad'i 'kasa sumammiya, nan fa aka shiga
tsananin tashin hankali, inna tayi saurin tallafota tana kuka, tana kiran sunanta,
da sauri aka d'ebo ruwa aka yayyafa mata sannan numfashinta ya dawo, amma duk da
haka batasan inda kanta yakeba.

A ranar dai anga tashin hankali, mutanen dasuka taru d'aurin Auren Hashim sune
sukayi jana'izarsa,

Bayan an kaishi makwancinsa aka dawo aka cigaba da zaman makoki, mutane kowa na
Al'ajabin yanda mutuwar Hashim ta kasance, dan kuwa ranar saida abokaninsa duka
suka taru, yashiga wanka bayan yafito ya shirya cikin farar shaddarsa, har sun fito
zasu tafi, yace masu kanshi na ciwo zeje chemist ya siyo magani.

Har wani cikin abokanin yace bari yaje ya siyo mashi, amma sai yace ya barshi kawai
zeje da kanshi, haka yatafi yabar abokaninsa suna jiran dawowarsa su wuce gurin
d'aurin auren,

Sun kai kimanin minti arba'in suna jiransa amma shiru,saboda haka suka Yanke
shaawarar binsa.

Innalillahi'wa,inna,ilaihirraji'un suka furta, lokacin da suka hango Hashim kwace
cikin ciyayi, ga jini duk ya 6ata farar shaddar dake jikinsa, amma ba Alamar rauni
jikin sa.

"To ta ina ya samu wannna jinin? Tambayar dasuka rika yima Kansu kenan wacce basuda
amsarta.

Nan suka d'aukeshi suka nufi gida hankali tashe,
Kafin kace miye labari yagama baje gari, abunka da 'karamin gari duk inda kanufa
maganar akeyi, dan wasu har sun fara yima abun wata mummunar fassara,

*_ยฐBayan sati biyu_*ยฐ

6angaren Laraba kuwa tun rasuwar Hashim batasan inda kanta yakeba sai yau tadawo
hayyacinta, abin mamaki batayi maganr mutuwar Hashim ba, kawai tacigaba da
hidimominta,

Wanka tayi ta shirya cikin, sabuwar atamfarta d'aya daga cikin wacce aka kawomata
na lefen aurenta, da aka maida gidansu Hashim suka 'ki kar6a,

Kwalliya tayi sosai, tayi gwanin kyau abunka ga 'kya'kyawa duk yanda tayi kwalliya
yimata kyau take, duk da tana tashin 'kauye, gyale ta dauko ta rataya kafad'arta
tazo gaban inna tace inna zanje gidansu lndo, inna ta d'ago idanunta ta kalleta
cike da damuwa, da mamakin yanda halayyar Laraba ta canja bayan rasuwar Hashim,
tace "haka zaki fita Laraba yakamata ki sanya hijab d'inki, ta turo baki tace ni
gaskiya inna bazansa hijab ba kamar wata me takaba, lnna ta girgiza kai cike da
takaici da kuma mamakin abinda ke damun 'yarta wanda har zatayimata magana tace ba
hakaba, wanda da ba halinta bane.

Koda taga Inna batada niyyar mata magana kawai sai tasa kai tafice, tace "saina
dawo, cike da takaici inna ta matse kwallan dasuka taru idonta tace "Allah maidoki
lafiya.

Tafiya take hankalinta kwance abinta, ga gyalenta rataye a kafad'a gashi ta wani
kashe d'aurin d'an kwali,
Kan hanya kuwa duk wanda yagamu da ita cikin wannan yanayin sai yayi mamaki, kafin
kice me mutane sun fara tsorata da Al'amarinta.

A zaure ta iske indo da saurayita ilu suna zance, Wanda yau yarage saura sati d'aya
bikinsu, dama suna cikin tattaunawa ne akan maganar Larabar ne, inda ilu ke
garagad'in indo a kan ta rabu da laraba indai har tanason su shirya, sai gata
tashigo, ta kalli ilu cikin sakin fuska tace ango kasha 'kamshi,...

Wani irin fad'uwar gaba ilu yaji lokacin daya jad'a ido da Laraba , saboda haka
jiki na kyarma yayima lndo sallama yabar gidan.

Cike da mamaki lndo ta kalli Laraba, tace "kawata yau kece da wannan shigar abinda
ban ta6a gani kinyi ba,
Laraba tayi dariya tace "lndo kenan yo kuma kullum haka zanta yawo da hijabi kamar
me takaba, ay nan gaba ma ko gyalen barin sawa zanyi.

Cike da mamaki indo tace "to Allah ya 'kyauta, sannan suka wuce cikin gidan.

Innar indo na zaune tana shan iska taji shihowarsu,
Laraba ta gaisheta, wani mummunan fad'uwar gaba taji da ganin Laraba, dan taji
rad'e-rad'in da akeyi agari, *aiko dole tasan yanda zatayi taraba 'yarta da Laraba
tun kafin suma ta kashesu.

Indo ce ta lura da yanda mahaifiyarta tashiga dogon tunani tace "inna Laraba na
gaisheki ko bakijiba ne? Firgigit tadawo daga dogon tinanin datake ta washe baki
tana ya'ke tace lafiya lao.




๐Ÿ–ŠZee Elkaseem
Mmn khady๐Ÿ’‹
[10/16, 8:10 PM] www.gidannovels.blogspot.com [21/08 4:53 pm] .: ๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡
๐Ÿ˜ญ *_ALHINI_* ๐Ÿ˜ญ
๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡


ยฎ```NWA```


_written by_
*_Zee Mmn khady_*๐Ÿ˜˜



1โƒฃ3โƒฃ1โƒฃ4โƒฃ
1โƒฃ3โƒฃ1โƒฃ4โƒฃ
1โƒฃ3โƒฃto1โƒฃ4โƒฃ


```Bayan kwana sha ukku```

Yau ake taron 'kawaye na lndo, gobe kuma d'aurin aurenta, 'kawayenta ne cike ma'kil
da gida anata shewa, Kowa kagani cikin farin ciki, hansai ta kalli lndo tace "waini
indo ina Laraba naga tunda nazo ban gantaba, lndo tayi murmushi tace "tun d'azu
muna tare ta koma gidane ta shirya, amma nasan tana gab da dawowa, hansai tace
Allah sarki, sai ta tashi ta goya d'anta tace "to amarya ni zan wuce sai kuma gobe
idan Allah ya kaimu, lndo tace "kai hansai tun yanzu bazaki bari Laraba ta dawo
tabaki biskit d'in ba? Hansai tayi dariya tace a'a ba kome wlh ay zan dawo gobe,
kafin tarufe Baki suka jiyo sallamar Laraba, aiko ko kallon inda take Hansai
batayiba tasa kai tafice daga gidan,
Can sai wasu gun-gun 'kawayensu suka taso suma sun kai su goma suka ce "muma dai
mun wuce, cike da mamaki lndo ta kallesu "tun yanzu baku bari ajima, tare suka
had'a baki suka ce "a'a akwai inda zamu ne, suka sa kai suka fice,

in takaita maku labari shigowar Laraba gidan saida yasa duk mutanen dake gidan
suka tafi.
Indo tasan dalilin tafiyarsu, har ga Allah bataji dad'iba amma ba yanda zatayi, ta
dad'e da sanin mummunan zaton da mutanen 'kauyen keyima Laraba, wasu guntayen
hawaye suka zubo daga idonta tasa hannu ta goge batare da Laraba ta kula da halin
datake ciki ba.

Ranar dai haka suka gama yinin, abin ba dad'i.
Laraba kanta ta fahimci yanda mutanen garin ke gudunta, a zuciyarta tace
_"me nayima mutane suke guduna_ *_Innalillahiwainnailaihirraji'un_*
Tafad'a tare da goge wasu zafafan hawaye.

Washe gari aka d'aura auren lndo da ilu, da dare aka kai amarya,
Ranar Laraba taga tashin hankali, dan 'kiri-'kiri mutane suke nuna tsana da
tsangwama da 'kyama gami da tsoro agareta.

Hakan yasata barin gidan bikin batare da ta shirya ba, lndo ta tausayama 'kawarta,
cike da tausayi take mata addu'a Allah ka yayemata abinda ke faruwa da ita.
ยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐ
Kiyi ha'kuri kinji Laraba, inshaAllah kome ze wuce, kiri'ka addu'a kinji Allah yaye
maki matsalar dake tattare dake, wasu zafafan hawaye suka zubo daga idanunta tasa
hannu ta goge "yanzu shikenan inna babu ni babu maganar Aure duk namijin dayace ze
aureni da lokaci ya gabato sai a wayi gari ya mutu, gashi nazama abin tsoro cikin
mutane duk inda naje sai afara barin gurin, ta'kara fashewa da wani sabon kuka.

Inna har cikin ranata take tausayama d'iyarta, itama hawayen take, tace "kiyi
ha'kuri Laraba ki d'auki wannan matsayin kaddara, inshaAllah wata rana kome ze zama
labari.

Nan lnna tayita rarrashinta tana kwantar mata da hankali,
Harta samu tayi shiru tace "tashi ki d'au tukunya ki d'ebo ruwa kiyi wanka, ba musu
ta tashi ta dauki 'yar 'karamar tukunya tanufi rafi, bako gyale jikinta barantana
hijab wanda har ta manta yanda ake sanyashi, inna tayi fad'an harta gaji ta
'kyaleta

Haruna ta hango zaune cikin gonarshi shida wani abokinshi suna cin gyad'a me 6awo,
suna fira, abokin nashi ne yafara hangota ta doso inda suke, cikin dabara ya tashi
yacema Haruna "ina zuwa bari in d'an zagaya can wlh jiya naci wata tafasa tad'an
6atamin ciki.

Haruna yace "Allah sauwa'ke, ya mi'ka mashi ruwa, ya amsa yawuce, yayi nesa kad'an
ya hango Laraba ta iso inda Haruna yake zaune tanayimashi magana, a fili yace
"Allah nagodema da Laraba bata riskeni gurin can ba, da sauri ya 'kara gaba yayi
cikin gari yana tinanin yanda abokinshi ze rabu da Laraba *Mayya* la'kanin da
mutanen 'kauyen suka fara kiranta dashi kenan dan su acewarsu mayya ce shiyasa duk
wanda yace yana sonta take cinye kurwarshi ya mutu.

Da fara'a take magana "Haruna dama ina nemanka, cike da tsoro ya kalleta, duk
illahirin jikinsa kyarma yake amma bakinsa yakasa furta kome,

Bata kula da halin dayake cikiba tacigaba da magana, "waini Haruna ya maganar
soyayyarmu, tunda Allah besa anyi da Hashim ba mizai hana ka dawo a d'aura mana
aure.
Sai lokacin yasamu yayi magana cike da tsoro bakinsa na 'kyarma yace "Laraba dan
Allah kiyi ha'kuri ni wallahi tuni nafasa yin Aure, bazanyi Aureba kwata-kwata.....

Cike da mamaki Laraba ta 'kara matsowa inda yake tace bazakayi aureba fa kace
Haruna, nice fa Laraba ka manta irin soyayyar da kace kanayi mani, a da,

Yace "a da ba amma yanzu na daina soyayya kiyi ha'kuri, Laraba ta'kara matsowa kusa
dashi yana matsawa "Haruna nice Laraba baka ganeni ba ne?

Cike da tsoro yace "na...na..ganeki mana, haba sai lokacin yasamu ya ranta a na
kare ๐Ÿƒ๐Ÿป
Mamakine tare da takaici da ba'kin ciki suka rufe Laraba ta dur'kusa nan tana kuka.
_Allah sarki laraba na tausaya maki_




๐Ÿ–Š Zee Elkaseem
Mmn khady ๐Ÿ’‹
[10/16, 8:10 PM] www.gidannovels.blogspot.com [22/08 7:26 am] .: ๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡
๐Ÿ˜ญ *_ALHINI_* ๐Ÿ˜ญ
๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡


ยฎ```NWA```


_written by_
*_Zee Mmn khady_*๐Ÿ˜˜



1โƒฃ5โƒฃ1โƒฃ6โƒฃ
1โƒฃ5โƒฃto1โƒฃ6โƒฃ
1โƒฃ5โƒฃ1โƒฃ6โƒฃ




๐Ÿ–ŠZaune suke sun buga uban tagumi, Laraba na zubar da hawaye itama lnna hawayen take
zubarwa dan taji yanda ake maganar Laraba a 'kauyen mutane suna kiranta *mayya*
tasa hannu ta goge hawayen dake idonta, abinda yafaru da ita jiyane yashiga dawo
mata a kwalwa,

shikenan yanzu abin Laraba har inna yake shafa, dan jiya akayi bikin wani d'an
Aminiyarta, wacce a da matar taso ace d'anta Laraba ya aura amma Allah be nufaba,
lnnar Laraba batada aminiya wacce ta wuceta, amma har aka fara biki ba'a
gayyacetaba, saboda haka tace bari taje tayi mata Allah sanya Alkhairi,

Haka ta shirya ta nufi gidan, tana isa zauren gida, magan-ganun dataji anayi
gidanne yasa hantar cikinta juyawa,

Muryar mata taji daban-daban suna magana "wah ay Laraba ta fiddo maitar ta fili,
yanzu fa mutum ukku ta kashe 'kauyennan kinsan kuwa maitarta takai inda takai, can
wata mata ta kar6e zancen "ay ance gado tayi gurin mahaifiyarta, dan ance ita ta
kashe mahaifin Larabar, muryar wata matar taji tana cewa "to mudai uwar biki Allah
sa baki gayyato mamu suba, dan nasan bakida Aminiya kamarta, can sai tajiyo muryar
amiyar tata tana cewa "a da ba, amma banda yanzu dan ban gaji da rayuwaba inaso
inga auren auta ta har inga jikokina, suduka sukasa shewa "heyyyyyy, wata tsagerar
mata takama hanci ta rangad'a guda "ayyuririiii,.........

Innar Laraba najin haka wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonta, zuciyarta
tayimata nauyi, kanta yayi wata irin Sarawa, take ciwon kai me tsanani ya saukar
mata jitake kamar kanta ze rabe, haka ta dafe kanta tanufi gida cike da takaici da
ba'kin cikin magan-ganun data ji, dan gidan bikin da bata shiga ba kenan,

Kan hanya ma duk wanda tayima magana sai taga ya matsa da Alamar tsoro tattare
dashi baze ko amsa maganar ba,
Wasu kau dasun hangota suke rugawa, abin ya matu'kar d'aure mata kai.
ยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐ

Yanzu kai habu larabar kake so, kana ganin yanda mutane ke gudunta, amma kai karasa
wacce zaka za6a sai ita, kuma kariga ka gama sanin *mayya* ce,
habu ya kalli abokinsa cike da takicin kalmar mayya daya furta ga Laraba yace "eh
ni ina sonta koda zata ri'ka yankan naman jikina tana ci d'anye 'karewar maita zan
aureta, abokin nashi yace to "Allah raka taki gona, nidai kaga tafiyata, kuma
muddin kasani idan kana tare da Laraba to abotarmu ta 'Kare, habu yayi wani guntun
murmushi mai d'auke da takaici yace, Allah had'a kowa da rabonsa, rabuwar habu
kenan da abokinsa.

ยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐ

Zaune suke sunyi tagumi duniya tayi masu zafi itada innarta, dan fitama wahala take
masu kullum suna gida basuda aiki sai tinani sai kuka,
Rabon kau da wani mutum yashigo gidansu har sun manta,
Itako Laraba da gidan lndo kad'ai take zuwa taji d'an dad'i-dad'i shima yanzu
yaushe rabon dataje, tun ranar dataje ilu yayimata wula'kanci yace kada ta 'kara
zuwar mashi gida idan kuma bata dainaba hukuma zata rabashi da ita,

Suna cikin wannan yanayin sukaji an bankad'o kyauren gidan kad'an yarage a
karyashi, mal Lawal ne yafara magana cikin bala'i da masifa, watau kin koyama d'iya
maita tana kashe mutanen gari, to wallahi ba maitaba ko uban maita ke gareki dole
Laraba ta fito da miji inyimata aure, dan bazan yarda tana yawo agari ana zagina a
matsayin mahaifinta na gaza aurar da itaba.

Tunda yafara magana basu cemashi 'kala ba, saida yagama bala'i sannan ya kalli
Laraba yace "waye kuma yanzu kike so wanda tsautsayi ke shirin afka mawa,

Cikin kuka da bakin ciki tace "dama Haruna ne tin kafin rasuwar Hashim yake sona,
mal Lawal yace "to bari yanzu inje in samu Haruna idan da gaske yake ya turo
iyayenshi dan bazaki 'kara sati biyu a gidannan ba, sadaki kawai ze kawo a d'aura
aure, haka yafita gidan yanata bal-balin bala'i, inna dai bata cemashi ci kanka ba
illah kuka datakeyi.

Haruna Zaune shida abokinsa suna fira, mal Lawal ya iso gurinsu, suka gaidashi ya
amsa, sannan yace Haruna gurinka nazo kan maganar Laraba, wani irin fad'uwar gaba
Haruna yaji,
jin an ambaci sunan Laraba, mal Lawal be jira abinda Haruna ze fad'aba yaci gaba
da magana, "tace kaine wanda ta tsaida shine nace ka turo magabatanka bamu bukatar
kome daga gareka sadaki kawai zaka kawo nan da sati d'aya a d'aura maku aure.

Haruna Wanda tinda mal Lawal yafara maganar jikinsa ke rawa kamar mazari yace "a'a
ni maganar soyayayya bata ta6a had'ani da Laraba ba, kuma bani sonta, inaji ba dai
ni harunan take nufiba

A fusace mal Lawal yabar gurin da niyyar yaje gida yaci mutuncin Laraba da
mahaifiyarta.

Tinda mal Lawal yabar gurin jikin Haruna ke 'kyarma, ya kalli abokinshi yace kanafa
jin wannan mutumin, abokin nashi yayi dariya yace "watako yarinyar nan tasaka a
zuciyarta tagama kwad'aituwa da kai walh saika tashi tsaye,
Kazo muje gidan kakata 'yar me ganye tana bada maganin mayu, Malam abaka kasha kayi
wanka.

Ba musu Haruna yace mutafi,
Sun isa gidan 'yar me ganye anba Haruna maganin daze ri'ka ji'kawa yana wanka dashi
sannan aka bashi tazargade yari'ka haya'ki, matar tace indai yana amfani da wannan
badai maye ba, ko sarkin mayu sai dai yaganshi ya 'kyale.
๐Ÿ–Š Zee Elkaseem
Mmn khady ๐Ÿ’‹
[10/16, 8:10 PM] www.gidannovels.blogspot.com [22/08 6:41 pm] .: ๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡
๐Ÿ˜ญ *_ALHINI_* ๐Ÿ˜ญ
๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡


ยฎ```NWA```


_written by_
*_Zee Mmn khady_*๐Ÿ˜˜


1โƒฃ7โƒฃ1โƒฃ8โƒฃ
1โƒฃ7โƒฃto1โƒฃ8โƒฃ
1โƒฃ7โƒฃ1โƒฃ8โƒฃ



๐Ÿ–Š "lna 'yar iskar yarinyar nan take, dan ubanki kinsan babu soyayya tsakaninki da
Haruna kika turani gurinshi, naje naji kunya, to bari kiji in gaya maki tunda dai
kinzamar ma mutane bala'i kin zamar masu 'karfen 'kafa to zan aurar dake ga duk
wanda naga dama,sannan ya juya gurin inna wacce tunda yafara fad'anshi ta kauda
kanta gefe tana zubar da hawayen takaici, shin wai dame zasuji da tsana da
tsangwama da tsoro da 'kazafin da 'yan garin kemasu koda masifa da bala'in mal
Lawal.

Yaci gaba da magana, cikin d'aga murya "Kara Ku yanke shawara tun kafin nan da
kwana biyu idan kuma ba hakaba zan yanke duk hukuncin da naga dama, yasa kai yafice
yanata kumfar baki.

Yana Fita Laraba ta taso tafad'a jikin innarta ta fashe da wani irin kuka me ban
tausayi, itama lnnar kuka take amma duk da haka rarrashin 'yar tata takeyi.

*```Bayan kwana Hud'u```*

Inna ce ke rarrashin 'yarta wacce duk yinin yau kuka take, ko ruwa takasa sama
cikinta saboda tsananin damuwa, tariga tagama sanin sunan da ake kiranta dashi a
'kauyen na *Mayya*
"Kiyi ha'kuri Laraba duk tsanani yana tare da sau'ki, in Allah ya yarda duk
masu gudunki sai sun dawo suna binki, kedai kiri'ka addu'a Allah yayi maki maganin
matsakarki.

Suna cikin wannan ne sukaji an bankad'o 'kyauren gidan, suduka suka maida
hankalinsu ga 'kofar ganin 'kyauren sukayi 'kasa ya karye, kasancewar dama na
langa-langa ne bayada wani 'kwari.

Mal Lawal ne yabi ta kan 'kyauren yashigo gidan a sukwane,
Laraba na jikin inna ta 'kan-'kameta duk tsoro yakamata gani take yau baffa Lawal
dukan ta zeyi.

Kudi ya watso jikinta yace "ga sadaki nan na d'aura aurenki da habu, yayan hansai,
idan kin cika ke mayyace yau kada ya kwana da rai, tinda sauran kafin a d'aura kike
kashesu, to wannan karan an d'aura kuma 'kurwarsa kur kuci kanku, *Mayu*.

Wani irin kuka Laraba ta 'kara fashewa dashi, ta 'kara shigewa jikin innarta Wanda
shi kad'aine yanzu take ra6a taji sanyi tace.

"Shikenan inna bamuda Kowa bamuda Wanda zamu ra6a muji dad'i, abin takaici da
ba'kin ciki wai hada baffa Lawal ake kirana *Mayya* to waye ma baze kirani da
*mayya* ba tinda 'kanin mahaifina ma yakirani haka.

Bayan magrib mal Lawal da kansa yazo ya tafi da Laraba tana kuka tana kome ya
kaita gidan miji, basu iske kowa gidan ba amma duk wani Abu na Al'ada na tarbar
amarya an kawo an aje masu,

Haka baffa lawal ya ajeta yabar gidan, tunda Allah ya halicceta bata ta6a ganin
irin wannan auren da akayimata ba, gashi dai ankawota gidan miji amma ba kowa sai
ita kad'ai cikin gida kamar *Mayya* _(sunan da mutanen 'kauyen ke kiranta dashi)_

Ta fad'a kan soson katifar da aka kawota dashi wanda ko zanin kirki bayadashi, ta
fashe da wani irin kuka, baiwar Allah Laraba tana cikin tashin hankali, duk tabi ta
rame, ta kod'e idanun nan nata sunyi zuru-zuru, hancin ya 'kara tsawo sai wani uban
'kashin wuya daya fito yayi mata 'kwaro-'kwaro.

A 6angaren habu kuwa yariga yasan an kawo amarya, yaje gun 'yan uwanshi yaro'kesu
akan suje gidan ayi d'an shagalin bikin da akeyi bayan an kawo Amarya amma sukace
"ina ay basu gaji da rayuwaba tukun, waye ze kai kanshi ga halaka.

Indo kuwa taso zuwa bikin 'kawarta kuma aminiyarta, amma ilu ya bad'e ido toka yace
bazataba, 'karshe data isheshi da magiya sai cewa yayi idan ta'kara maganar zuwa
bikin Laraba to bakin aurenta, hakan yasa ta ha'kura badan ranta yaso ba.

Bayan habu yagama fama da 'yan uwanshi akan suje gidanshi sun'ki sai yatafi gidan
'kanwarsa hansai, da sallama yashiga gidan, ta amsa sannan ta gaisheshi ya amsa,
nan yake tambayarta

"Hansai ya ban ganki gurin bikin ba, lafiya kuwa? Hansai ta yamutsa fuska tace
lafiya lau, kaina ne yake d'an yimani ciwo, cike da tausayi yace eyyah Allah
sauwa'ke tace Ameen.

Yace Amma naga kamar kin d'anji sauki, kozaki daure ki le'ka gidan kai amaryar,
Cikin firgici Hansai ta kalli yayanta tace "wah ni Yaya habu, idan ka ganni lahira
kaini akayi, wallahi bazani gidan *mayya* ba.

Cikin 6acin rai habu ya d'auke hansai da mari yace "idan bazakiba ki zauna, amma
kada ki kuma kiran matata da *Mayya* yasa kai yafice ranshi a 6ace.

Me zai faru yana fita daga gidan Laraba yagani tanayimashi murmushi, ta 'karso
gurinshi tace masoyina nagaji da jira ne gida ni 'kad'ai shine na biyoka...

cike Da mamaki yace "ya akayi kikasan ina nan, murmushi kawai tayi Mashi ta kama
hannunshi suka nufi gida.




๐Ÿ–ŠZee Elkaseem
Mmn Khady ๐Ÿ’‹
[10/16, 8:10 PM] www.gidannovels.blogspot.com [23/08 5:48 pm] .: ๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡
๐Ÿ˜ญ *_ALHINI_* ๐Ÿ˜ญ
๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡


ยฎ```NWA```


_written by_
*_Zee Mmn khady_*๐Ÿ˜˜




1โƒฃ9โƒฃ2โƒฃ0โƒฃ
1โƒฃ9โƒฃ2โƒฃ0โƒฃ
1โƒฃ9โƒฃto2โƒฃ0โƒฃ



๐Ÿ–Š Tafiya suke Laraba na ri'ke da hannun angonta Habu, sai da sukayi nisa da gari
sun shiga gonaki, baka ganin kome sai duhun daji da kukan tsuntsaye,

kasancewar akwai 'yar tazara tsakanin gidan Hansai da gidan Laraba, sun shiga
cikin duhun ciyayi, Habu ya waigo ya kalli Laraba yace "Amma Laraba nayi mamakin
yanda kika san ina gidan Hansai, kodai wani ya gaya maki ina nan?

Shuru yaji tayi batada niyyar amsa mashi tambayar da yayi mata, hakan yasa ya juyo
ya kalleta, suna had'a ido da ita gabanshi yayi mummunan fad'uwa dan ganin ta yayi
ta d'ad'd'aure fuska yanda kasan tunda Allah ya halicceta bata ta6a dariya ba, ga
fuskar tata tayi duhu, ba alamar haske tattare da ita, kamar ba larabar da
yasaniba, kya'kyawar yarinya fara tas fatar ta kamar ka ta6a jini yafito, amma
lokaci guda ta sauya takoma ba'ka, ga fuskar ba Alamun fara'a tattare da ita.

Lokaci guda jikinsa yafara 'kyarma kamar mazari, yakasa matsawa daga inda yake, sai
da 'kyar yasamu ya iya daga baki yace La....la....Lara...ba, miya sa kika biyoni,
miyasa zaki tsoratar dani......

Kafin ya rufe bakinsa yaji ta gagga6e da wata irin mahaukaciyar dariya tace,

"Tambaya kake yanda akayi nasan inda kake, to ayni ba sai na tambaya ba, tunvdaga
ranar daka furta kalmar so gareni nake biye dakai, kuma kasani sai nazama
ajalinka..... Hhhhhhhhhhhhhhhhh, ta 'kara gagga6ewa da wata nahaukaciyar dariya
karo na biyu.

Habu kuwa banda 'kyarma ba abinda yake, yariga yagama sad'aukar da rayuwarsa, dan
yasan 'karshen rayuwarsa ne yazo, kwata-kwata kasa yin wata addu'a yayi dan
tsananin tsoro, sun kai kimanin minti ashirin tsaye gurin Laraba, tana tsoratar da
Habu.

Sai zuwa can Allah yabashi ikon furta kalmar *lnnalillahiwa,inna'ilaihirraji'un*
sannan yasamu 'kafar guduwa daga gurin,

Gudu yake iyakar 'karfinsa, domin yau ya tabbatar ma kanshi maganar da mutane ke
fad'a suna cewa Laraba *mayya* ce, a zuciyarshi yana cewa koma miye Nina jawoma
kaina, dama ance _(Wanda beji bari ba yaji hoho)_.๐Ÿ˜ฑ

Lokaci guda yahad'a wani uban gumi, ga tsabar tsoro ga kuma uban gudun dayasha, da
kyar yashiga gida ya maida 'kyaure yarufe, yana maida numfashi.
'Daki yanufa yana nishi yana goge uwar zufar data rufeshi kamar wanda aka watsama
ruwa,

Mutuwar tsaye yayi dan wani babban tashin hankalin daya tarar a gidan, yasan dai
yabaro Laraba a daji, amma kuma yanzu gata ya tarar da ita kwance kan 'yar
katifarta tana kuka.

Jin alamun shigowar mutum yasa Laraba tashi daga kwancen datake, ta d'ago da manyan
idanunta wanda suka kad'a sukayi jawur saboda tsabar kukan data sha.

Cike da mamaki Habu ke kallonta, a zuciyarshi yace "to wai miye ke shirin faruwa
dani ne, kodai ba Laraba bace wacce nabaro a daji.

Ganin bashida niyyar ida 'karasowa cikin d'akin yasa Laraba tayi magana "Sannu da
zuwa, tafad'a cikin zazza'kar muryarta mai sanyin sauraro.

"Yauwa yafad'a zuciyarsa na dukan ukku-ukku, "bari inje in dawo nayi mantuwa a
gida, cike da tsoro Laraba tace "miye kuma ka manta, nifa wallahi tsoro nakeji ni
d'aya gida, a zuciyarsa yace _"Ai kece abin tsoron laraba, ke yakamata aji tsoro
bake zakiji tsoron wani abu ba_

"Tinanin me kakeyine, ta tambayeshi dan ganin ya tsaya a gun bayada niyyar tafiya,

Yayi saurin dai-daita nutsuwarsa yace "a'a zanje bari intafi bazan dad'eba zan
dawo, sannan yasa kai yafice, cike da tsoro yafita daga gidan, zuciyarshi cike da
tunani kala-kala.

Tafiya yake bekoyi nisa da gidan ba amma wani mugun abun tsoro daya gani shine
yakusa sanya numfashinshi ya d'auke, dan Laraba yagani gabanshi, ta kashe d'an
kwali ta ri'ke 'kugu tana jijjiga jiki, suna had'a ido ta gagga6e da wata
mahaukaciyar dariya, sannan kuma ta d'aure fuska kamar bata ta6a dariyaba.

Tace "Habu kana gan-ganci da rayuwarka, inaso kafin nan da safiya ka gaggauta
yankema kanka hukuncin daze fitar dakai.

๐Ÿƒ๐ŸปDa gudu yayi baya yakama hanyar gidanshi, tashin hankali wanda ba'a samashi
rana ๐Ÿ˜ณ Laraba ya iske a tsakar gida tafito daga kewaye hannuta ri'ke da buta.

Wata irin gigitattar 'kara yasaki nan take yafad'i 'kasa kanshi yabugu da wani
dutsi dake tsakar gidan, aiko kan yafashe jini yafara zuba.

_Innalillahiwa'inna,ilaihirraji'un_ Laraba tashiga furtawa, tanufi inda Habu yake
kwance tana jijjigashi tana kiran sunanshi amma ba alamar numfashi tattare dashi.




๐Ÿ–Š Zee Elkaseem
Mmn khady ๐Ÿ’‹
[10/16, 8:10 PM] www.gidannovels.blogspot.com [24/08 2:03 pm] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡
๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡
๐Ÿ˜ญ *_ALHINI_* ๐Ÿ˜ญ
๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡


ยฎ```NWA```
_written by_
*_Zee Mmn khady_*๐Ÿ˜˜


2โƒฃ1โƒฃ2โƒฃ2โƒฃ
2โƒฃ1โƒฃto2โƒฃ2โƒฃ
2โƒฃ1โƒฃ2โƒฃ2โƒฃ


๐Ÿ–Š "wayyo nashiga ukku dan Allah habu katashi kada ka mutu, idan kamutu nasan bazan
'kara shan ruwa garinnan ba, dan Allah ka taimakeni, Laraba ce ke fad'in haka cikin
muryar kuka,
Yayinda habu yake kwance har yanzu besan inda kanshi yakeba, ga kuma inda kanshi
yabugu har yanzu zubar da jini yake,
"Ya salam laraba tafad'a "Lallai rayuwata tana cikin had'ari ya Allah ka fitar
dani, wasu sabbin hawaye suka gangaro kan kumatunta.

Lokaci guda jikinta ya mutu li'kis kamar wacce akayima duka
Ta tashi da sauri tanufi d'aki ta dauko wani tsohon zani cikin zannuwanta ta yaga
ta d'aurema Habu kanshi inda jini ke zuba, cikin ikon Allah kuwa sai jinin ya
tsaya, amma har yanzu ba Alamar numfashi tattare dashi,

Sai lokacin dabarar ta yayyafa mashi ruwa ya fad'o mata a arai, da sauri tanufi
randa ta d'ebo ruwa me sanyi ta yayyafa mashi, a firgice ya tashi yana "cewa "dan
Allah kiyi ha'kuri Laraba kada ki kasheni, Laraba ni me 'kaunarki ne bekamata ki
sakamin da sharri ba.

Wata irin 'kara Laraba tayi, cikin wata gur6atacciyar magana take cewa, Habu bazan
ta6a raga makaba, babu ragi ba ragowa tsakanina dakai, nariga na gaya maka kafin
gari ya waye ka nemama kanka mafita,

Cike da tsoro da firgici habu ya kalli Laraba, yaga fuskarnan tata ba Alamar
sassuci, tabbass idan yaci gaba da zama da ita ze iya rasa rayuwarsa, hakan yasa ya
yanke shwarar rabuwa da ita.

"Laraba"yakira sunanta,
Jiki a sanyaye ta juyo ta kalleshi, yace "kije na sakeki *Saki ukku*
Daga yau babu ni babu ke,

"Hhhhhhhhhhhhhh, wata irin mahaukaciyar dariya sukaji ta gauraye gidan, har tsawon
minti biyar sannan dariyar ta lafa, wata irin murya sukaji wacce basu San daga inda
take fitowaba ana cewa,

"Yaro kayi ta barka, ashe kana son rayuwarka, aka sake bushewa da wata dariya,
sannan sukaji d'if kamar anyi ruwa an d'auke.

Wani matsanauncin tsoro Yakama Laraba dan jin wani sabon Al'amari, da gudu tanufi
habu wanda shima jikinsa mazari kawai yake saboda tsananin tsoro tafd'a jikinsa ta
'kan'kameshi.

Cike da tsoro habu ya finciketa daga jikinsa, yajata kiiiiii, ya turata waje yace
"kije nace nasakeki *Saki ukku* ya maida 'Kofa ya rufe.

Laraba ta shiga bugun 'kyauren gidan, tana cewa "Dan Allah habu ka taimakeni ka
barni in kwana gobe sai intafi, haka ta rin'ka magiya amma bataji Habu yayi
maganaba, hakan yasa ta kalli gabas ta kalli yamma kudu da arewa, ba Alamar haske,
garin yayi duhu dind'um bakajin kome sai kukan tsintsaye, take wani mugun tsoro ya
dira a zuciyarta.
[24/08 2:38 pm] Zee Elkaseem: Wani irin haske ta hango daga nesa yana nufo

Please Login or Register in order to submit comment