Reading AURE KO BOKO 3 BY TAKORI Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shigar sa. Bai san cewa Halimah na ganin rubuce-rubucensa ba, kuma ta shigar da zancen cikin labarin da ta bai wa Zarah.
Mahaifin Zarah kuma tsohon babban dan siyasa ne, wanda ya yi gwamnan Bauchi har sau biyu, ya yi sanata dinta ya yi minista. A halin yanzu shi ne shugaban jam'iyyar NRC, jam'iyya mai farin jinin da babu kamarta a Najeriya.
A yadda ya ji labarin Hashim daga bakin Zarah da 'determination' dinsa, sai ya ga kwarai yana bukatar irinsa matuka a siyasa, musamman a wannan lokaci da siyasa ke gabatowa. Ya gama tsara abubuwa da yawa a kan Hashim tun kafin ya zo, albarkacin Halimah da Zarah. Yana so yarinyar ta samu 'future' mai kyau albarkacin sadaukarwarta da gudun duniyarta.
Don ta kara jin tsoron Ubangiji ta san cewa wanda ya tsorace Shi ba zai tabe ba. Ta kara zage damtse wajen biyayyar aure, ta manta da rayuwarta ta baya.
Kudin motar zuwa Bauchin ma Halimah ce ta yi fafutukarsa da kyar da sudin ludayi daga cinikin kwan kajinta. Ya shirya a ranar asabar ya kama hanya, bayan Halima ta bi shi da addu'a da fatan alkhairi mai dumbin yawa.
*****
















BAUCHI
Hashim ya sauka a Bauchi lafiya da yamma lis, a matukar gajiye da takure da zaman bus, ya kira lambar da aka ba shi, mutumin ya gaya masa daidai inda zai tsaya ya ce zai iso nan da minti goma sha biyar.
Wata 'discussion contineous' ce ta yi parking a gaban Hashim. Mutumin ya fito ya ba shi hannu tare da karbar jakar hannunsa ya bude masa kofa ya shiga ya rufe, sannan ya zagaya mazauninsa ya tada motar.
Har suka zo unguwar 'Fati Mu'azu Links' inda gidan su Zarah yake suna hira shi da mutumin wanda ya ce sunansa Marzuq, shi ne babban yaron Alh. Datti Giade, wato mahaifin Zarah. Bangaren saukar bakin gidan su Zarah ya nufa da shi, ya bude masa daki ya ba shi mukullin, ya ce ya huta zuwa gobe ne zai gana da His Excellency, za a kawo masa abinci yanzu.
Hashim yana yin sallah, kafin yayi komai Halimah ya kira ya gaya mata saukarsa lafiya, ta hada shi da Safiyyah suka sha hirar su. Da kyar suka yi sallama cike da kewa da kaunar juna kamar kar su rabu, sannan ne ya ci abincin da aka kawo masa. Yayi wanka ya canza kayan jikin sa.
Da daddare ma kafin ya kwanta sai da ya sake kiran su. Washegari da safe bayan ya yi wanka ya kimtsa, Marzuq ya zo tafiya da shi wajen Alh. Datti.

Cikin nutsuwar sa ta halitta Hashim ya yi sallama a tankareren falon, Alhaji Datti ya amsa a mutunce, tare da cewa,
"Shigo ka zauna nan kusa da ni Mallam Hashimu".
Cikin matsanancin ladabi Hashim ya gaishe shi. Ga mamakin Hashim sai ya ji ya ce da shi.
“Yaya Halimatu da Safeeyyah? Ina fatan ka kira su bayan isowar ka?”
Kansa a kasa ya amsa da cewa, yanzu ma kafin ya shigo nan sai da ya kira su, sun tashi lafiya dukkan su.
Alhaji Datti ya fara jan sa da hira, cikin sakewa da hila irin ta manya, har sai da Hashim ya fara sakin jiki da shi ya daina nuku-nuku, labarin siyasar Najeriya yake ta bashi da mulkin soja dana farar hula na tun kafin a haife shi. Yana comparing dinsa da wanda ake ciki a yanzu. Yace "ratar dake a tsakanin siyasar da data yanzu mai tsananin fadi da girma ce Hashim, yanzu majority ana siyasa ne kawai don a yi kudi dare daya, yayin da shuwagabannin baya mulki suke don gina al'ummar su selflessly'. Shi Hashim yadda Alhajin ya sakar masa fuska da zuciya kamar ya dade da sanin sa har mamaki yake bashi. Duk zurfin ciki irin na Hashim dole ya saki jikin sa suka fara hira sosai da baban Zarah. Sai da Alhaji Datti ya tabbatar ya kama kurwar Hashim sannan ya sallameshi. Yace gobe da safe zasu gana sosai.
Washegari din kuma bai samu ganin sa ba sai azahar. Hashim na shigowa falon yace "koma ka dauro alwala mu yi jam'in sallahr azahar" Hashim yace "ai da alwala ta" "to kai zaka yi mana limanci, bisimillah".
Da suka idar da sallahr kuma Alhaji Datti yace "ban ci komai ba Hashim mu fara cin abinci ko?"
Tare suka ci abinci bisa ledar cin abinci wadda aka shimfida aka jera abinci nau'i-nau'i. Da suka kammala yace ya raka shi unguwa, Hashim ya fara tunanin Alhaji Datti bai kira shi don komai bane sai don ya zame masa abokin hira.
Tare suka tafi ofis din Alhajin, ya taimaka masa kan wasu ayyukan sa, sannan suka dawo gida.
Suna sauka a mota yace Hashim ya wuce masaukin sa sai Allah ya kaimu gobe.
Haka yayi ta jan Hashim a jikin sa kamar dan cikin sa, kulawar yau daban data gobe, don ya lura in ba da hakan ba bazai samu ya yarda da taimakon da yake son yi masa ba. Ya farfado da matacciyar zuciyar sa akan nasarar rayuwa. He already assumed shi bai zo duniya da sa'a ba. Ya riga ya karbi rayuwar sa a yadda take, baya bukatar wani sauyi a cikin ta.
Hashim na so ya koma gida amma kullum Baban Zarah cewa yake sai gobe zamu tattauna.

****

"Cheriè, sai yaushe zaka dawo ne?"
"Ba ke kika jawomin ba Halima tunda nazo babu wata kwakkwarar magana sai hira da debe masa kewa da taya shi yawo a mota, anyway, he's a nice father. Kuma ina jin dadin zama da shi sosai saboda yawqn ibadarsa. Amma na kusa runtse ido in ce masa zan tafi wajen Halimah ta".
Halima tayi dariya tace "ka daure baban Safeeyaah, haka kawai bazai kira ka don kuyi ta hira ba, mu kam dai kada ka damu damu lafiya sumul muke. Ga Sa'adatu ma jiya ta zo mana wuni mun sha hira, ta kawo ma Safeeyah kuli-kuli mai suga tana ta ci tun jiya". Da haka Halima ta kalallame shi ya yarda zai cigaba da zama har Alhajin ya sallame shi.

Ilai kuwa washegari Baban Zarah ya kira shi, yau kuma kai tsaye cewa yayi, yana so ya fara ba shi tarihin iyayen sa da na rayuwar sa gabadaya. Domin shi dai ya riga ya samu Da (yana nufin Hashim din). Hashim yayi murmushin nan nasa mai ratsa zuciyar Halima, sai ya samu kansa da kasa musanta bukatar Alhaji Datti Giade, wani abu da bai taba tattaunawa da kowa ba a duniya bayan Halimah.
Ya sunkuyar da kai ya gaya masa komai a kan mahaifinsa wanda Ba-Kano ne gaba da baya dan Yakasai, da kuma Innarsa, wadda ita Basudaniya ce. Aurota yayi ya zo da ita Najeriya.
Yadda ya yi dukkan karatunsa da taimakon mahaifiyar sa, bayan rasuwar mahaifin su, samun aikinsa da NCC da taimakon Halimah. Bayan ta kade shi da mota. Zuwan su Holland da yadda soyayya ta kullu tsakanin su. Sallamar su da Prof. ya yi bayan auren su, amma ya dan sakaya wasu daga wahalhalun da suka sha a rayuwa ko wadda suke ciki a halin yanzu. A wurin sa fadin halin kunci daka ke ciki ga wani bayan mahaliccin ka, tamkar rashin godiyar Ubangiji ne.

Cikin mutuwar jiki Alhaji Datti ya ce ya ba shi takardun sa ya duba, ya ciro su daga jakar goyonsa ya ba shi cikin ladabi.
Ba abin da ke fita bakin Alhaji Datti sai, “Excellent… Mimtaaz… jamilan Jiddan!”.

Ya dubi Hashim da murmushi ya ce, “Ashe tare da Dr. Of Philosophy nake zaune ni ban sani ba? Dr. of Telecommunication Engineering. Dr. Hashim kana son aiki a jami’ar Bayero? Ko Igbinedeon University? Ko Northwest University ta Kano, ko kuwa ba ka son aikin jami’a ka fada min duk wani industry da ka ke son yin aiki da shi a Najeriya?”
Hashim ya sadda kai yana murmushi cike da kaunar karimin dattijon, bafullatanin Giade, ya ce, a ha kali muryar sa ke fita inda ya ce.
“Babu ko daya, bana sha’awar aiki ranka ya dade! All the aspirations on it has gone”.
Alhaji Datti ya yi murmushi domin ya tsammaci jin hakan dama, ya ce, “Kana son international business kenan?”
Nan ma Hashim ya ce, “lala!”.
Alhajin so yake ya fada masa da bakinsa ga abin da yake so, yake da buri akai, shi ya sa yake ta zagayewa. Amma Hashim ya ki fada sabida zurfin cikin sa. Yana son ya kara tabbatar da wannan determination din daga bakinsa kamar yadda ya ji daga bakin Zarah, kada ya zamo cewa ya yi pushing ra’ayinsa ga shiga siyasa, wanda wannan ba shi ne abin da yake so ba. Don haka ya ce,
"To Hashim gaya min, me ka ke so to earn a living, tunda magidanci dai mai iyali bai zama ba tare da neman na kansa ba, kula da iyali abu ne mai matukar wuya, wanda dole sai da kwakkwarar sana’a mutum zai iya shi cikin sauki’.
Hashim ya kara yin kasa da kai. A karo na farko ya ji yana son fadin wannan burin nasa a fatar baki, ba don yana da hope na cewa zai same shi ba, wanda bai taba bayyanawa kowa ba sai alkalamin sa da littafin sa. Ko Halima bai taba bude baki ya gaya mata ba, ya dauki abun ne a matsayin mafarki (dream), which will never born alive. Wanda ba zai taba zama reality ba.

“Ni burina kawai siyasa ce ranka ya dade, ina son shugabanci kuma ba ni da hanyar shigar sa ko samun sa. Babban mission dina na son shiga siyasa shi ne; inganta rayuwar matasa marasa aikin yi, kawar da rashin aikin yi (unemployment) wanda ke maida su marasa amfani, marasa imani, kawo sauyi a kan yadda ake mulkar talaka da zama shugaba mai fada da cikawa ba irin shuwagabannin da ke ci yanzu ba. I want to curve POLITICAL DICHOTOMY.
Ka ga kuwa buri na zai tabbata a mafarki ne kawai daga nan har gaban abada, tunda ba ni da wata hanyar kaiwa gare shi”.

Wani tattausan murmushi ya subucewa Alhaji Datti, ya dubi Hashim da ke duke a gaban sa da manyan idanun sa irin na manyan shuwagannin da suka sha gwagwarmaya a rayuwar siyasa suke kuma da experience na su waye masu leadership motivation ko a kwayar ido. Jin sa yake a ran sa kamar 'yar da ya haifa, Zarah. A sati guda kacal da yayi tare da shi ya gama lakantar duk abinda yake son laqanta akan sa. Wato duk wasu (leadership qualities) ya mallake su har da kari.
“Ka zo gidan siyasa Da na, kuma ka shige ta ka gama. Irin ka muke nema ruwa a jallo masu patriotism, sannan masu jini a jika da dimbin ilmi a kananan shekaru, wadanda za su gaje mu tunda mu mun kusa ja baya.
Welcome to the NRC (Northern Region Congress party). Gobe za mu wuce Abuja tare in gabatar da kai ga shuwagabannin jam’iyyah. Insha Allahu Hashimu ka shigo da kafar dama, domin akwai rikici da ake yi tsakanin mutum biyu da za mu ba wa takara, zan raba gardama da kai duk su hakura domin kuwa ka fi su cancanta ta kowane bangare, welcome on board!".
****




















Hashim ya koma masaukin sa a daren ranar yana jin komai dake faruwa kamar a mafarki. Ya kasa hadiye wannan magana a ransa ba tare da yayi sharing din ta ga Halimar sa ba. Ya dauki waya ya kira Halimah wadda ke yiwa Safeeya shirin barci a lokacin.
"Cheriè, baka kwanta ba?"
Sassanyar muryar Halima ta tambaya.
"Ina zan kwanta Sweetheart, ban ji lallausar muryar ki mai tada tsigar jiki na ba? Baki yimin goodnight kiss ba? Bamu yi sallama mun gaida juna ba? Rabona da ke tun safiyar yau. Ga rayuwa na kokarin canzawa incredibly! Kin san wani abu?
Daddy yace gobe zamu tafi Abuja ya sanya ni a jam'iyyar su, jam'iyyar NRC dai da kika sani, he sounds kamar dama can ya san buri na kenan a yadda yake magana".
Halima tayi murmushi ta canza position din rikon wayar ta, daga dama zuwa hagu, a lokaci guda tana lullube Safeeyah da bargo, bata ce masa ita ta gayawa Zarah ba don bai san ta karanta rubuce-rubucen sa ba. Tace.
"Idan wannan shine alherin mu, Baban Safeeyah Allah ya tabbatar da shi, ya hada mu da dukkan alkhairin da ke cikin sa, ya dawo min da kai lafiya".
Hashim yayi kasa da murya cikin jin matsananciyar kewar matar sa, ya ce "i'm missing you, Sweetheart, anya zan iya kara wasu kwana bakwan a nan gaba ban zo na gan ki ba, na kuma ga apple of my eyes (Safeeyah)? This is too much for me to bear" Halima ta kara kankame wayar hannun ta, cikin tsananin shauki tace.
"Daurewa zaka yi Cheriè, suffer till you succeed. Nothing good comes easy…Halima is there for you forever"
"I so much love you Leemah....." ya fada a raunane.
"And Leemah loves you more!". Ta fada cikin karsashi.




ABUJA
Sai ga Hashim tsakiyar jiga-jigan ‘yan siyasar Najeriya a washegarin ranar Alhaji Datti na gabatar da shi. Sosai ya samu karbuwa a wajen dattijan, sabida kwarjini da kamalar da Allah ya zuba masa. Gami da kwalayen ilmin da ya tara a kananan shekarunsa. Duk da baza'a rasa wadanda zuwan nasa ta hannun Alhaji Datti bai musu dadi ba, don shine shugaban jam'iyya komai ya saka ta zauna. Musamman matasan cikin su. Masu shekaru tsararrakin na Hashim din.
Hashim kallon komai yake kamar a mafarki lokacin da Alhaji Datti ya zaunar da shi a gefensa, a kusa da shi ‘yan takarar gwamnoni ne na jihohin Najeriya wadanda ke karkashin NRC. Lokacin da Alhaji Datti ya tashi yin bayani a matsayin sa na shugaban jam’iyyar NRC bakidaya sai yace,
"Na raba gardamar da ake yi tsakanin mutum biyu, wadanda ke son karbar takarar gwamnatin Kano, wato Aliyu Sardauna da Inusa Zango, na maye gurbinsu da Hashim Ismael Yakasai, ya kawo hujjojinsa a kan cancantarsa da tsammanin da yake da shi na cewa zai fi su yawan mabiya tunda shi ba dan kowa ba ne, sannan matashi ne mai shekaru arba’in kuma haifaffen birnin Kano ne wanda ya zauna a cikin matasa daban-daban mazauna cikin gari (tsakiyar birni) yake kuma cikin irin rayuwar da suke yi.
Ya ci gaba da kawo musu manyan dalilansa da misalan sa na baiwa Hashim wannan takara har sai da dukkaninsu suka gamsu, cewa Alhaji yayi don cancanta ne ba don son kai da nuna fifiko na sanayya ba, banda Aliyu Sardauna da Inusa dake ganin son kai ne karara Alh. Datti yayi don Hashim yana dan uwansa. Amma in ba haka ba ta yaya su da aka yi fadi-tashin kafa jam'iyya dasu rana daya za'a hambare su a bawa bako matsayin su?
Dattijan kam sun gamsu da cewa Hashim din shi ya fi dacewa da tsayawa primary election idan lokaci ya zo.

Abu kamar wasa karamar magana ta zama babba, cikin dan lokaci fastocin Hashim suka soma yaduwa a jihar Kano da kafafen yada labarai, wadanda komai daga aljihun Alhaji Datti dana jam'iyya yake fita, musamman da yake jam’iyyarsu ita ce jam’iyya mai farin jini a wurin talakawa. Sunansa ya soma fita a hankali a kafafen yada labarai. Matsayin dan takarar gwamanatin Jihar Kano karkashin Northern Region Congress party. Watanni uku da fara campaign ganin irin karbuwar sa yasa jam’iyyah ta ba shi gida da full security a unguwar Nassarawa GRA.

Halima da Safiyyah suka tare yau a sabon gidansu karkashin rakiyar makwabtanta na arziki da Sa'adatu da Dr. Rabiah yayin da komai ke zuwar wa Halimah kamar a mafarki. Kamar ire-iren mafarkan data saba yi tana farkawa ta ga komai bai faru ba.
Ta rasa irin godiyar da za ta yi wa Zarah da ta maida mafarkin Hashim reality, tabbas Zarah ta cika masoyiya ta hakika.
Hashim ya zagayo da hannayensa zuwa kafadun Halima, yana sanye da wata lallausar shaddah light pink, 'yar ciki da wando kawai, ya aje babbar rigar bisa kujera. Halima ta sha ado da swiss lace ruwan zuma dinkin bou-bou, sai kamshin davidoff ke tashi a jikin ta. Falon ya kawatu da english furnitures farare kal komai a saukake, amma yana da matukar girma, ta yadda kujeru seti biyu ya dauka, kowacce kala daban da 'yar uwar ta. Suka hade goshin su wuri guda, dogon karan hancin su ma wuri guda yana zungurar na juna. Sai shakar numfashin juna suke, mai cakude da sanyin turaren jikin kowannen su.
"Cheriè, pls, in mafarki nake ka taimake ni in tashi" " Halima ba mafarki kike ba, gidan ki ne da jam'iyyah ta baki halak malak, ko mun fadi zabe ya riga ya zama naki".
Safeeyah na zaune akan leather tana ta lallatsa kujerar da hannun ta tana shafawa tace "Daddy, nan ina muka zo ne? Kujerar su akwai laushi" dariya suka yi su duka biyun suka isa gareta suka durkusa a gaban ta.
"Safeeyah this is your new humble abode. How i wish you can open your eyes and see its serenity?". Ya sumbaci kuncin ta. Safeeya tace "Daddy idona a bude yake amma bana ganin komai, sai duhu". Halimah kasa tsayawa tayi a wurin ta nufi dakin da ya zam nata tana share hawayen tausayin Safeeyah. Ta bar Hashim yana lallabata yana gaya mata watarana zata gani idan Allah ya nufa.
Saida ya kai Safeeyah dakin ta, yayi mata addu’a ya rufe ta da lallausar bargo, yarage mata wuta, sannan ya shafa kanta ya bar dakin.
Ya tadda Halima a tsaye jikin mudubin jikin bango tana karewa kanta kallo, cikin dan lokaci ta fara ciccikowa, ta fara tada komadar ta, kasusuwan da suka yi mata sarka a wuya sun ciko, ta fara komawa hayyacin ta, duk da yawon kamfen kauyuka da birane bai barin ta hutu sam, kuma tun daga wancan lokacin kawancensu ya farfado da Zarah, dari-darin da ta ke da Zarah duk ta bari. A hankali zuciyarta ta ke budewa daga tsukewar da ta riga tayi a baya, ta fahimci ashe dai tana bukatar 'yar uwa mace wadda zata dinga kaiwa matsalolin ta bayan Hashim, ta soma karbar canjin rayuwar da ya same su tana adopting din sa gradually da budaddiyar zuciya yanzu.
Tana wannan tunanin taji Hashim ya zagayeta cikin hannayensa, ya sumbaci dokin wuyan ta ta baya, tace "Hashim!" Yace "...Halimah-Leemah, me kika tanadar min a daren yau?" Ta juyo gabagadi ta fuskance shi, sannan ta maida masa sumbar da yayi mata, tace
"Duk abinda kake so, whatever…special Baban Safeeyah!".
****




Yawon kamfen da hada-hadar siyasa da ke sa ‘yan siyasa mancewa da iyalansu idan siyasa ta matso, wannan ba haka yake a wajen Hashim Ismael Yakasai ba, duk inda ya shiga, duk runtsin da yake ciki sai ya ware kansa ya kira iyalinsa ya ji muryar diyar sa Safiyyah ya tabbatar ba su da damuwa a kullum, sannan hankalinsa yake kwanciya.
Hatta miskiniya Safiyyah da ba ta da idanu ta san sun samu sauyin muhalli, sauyin abinci da sauyin atmosphere.

Zaben farko wato (primary election) na kara karatowa, abubuwa na kara yi wa su Hashim zafi, ta yadda zaman gida ya karranta gare shi. A daidai lokacin ne Halima ta bada kaimi wajen addu’ar nasara wa mijinta dare da rana yini da safiya addu'a take yi tana sadaqa, Dr. Rabi'ah gabadaya ta janye adawar data ke yi da Halima sai shishshige mata take, Halima bata taba canza mata fuska ba dai-dai da rana daya, sabida ko kare ne in dai daga dangin Hashim yake tana girmama shi balle Yayar sa uwa daya uba daya. Ta dauki abinda Dr. Rabi'ah tayi mata a matsayin ajizanci irin na dan adam, saidai bazata taba hada matsayin ta da na Sa'adatu ba a zuciyar ta;
Wanda ya soka a lokacin da duniya ta juya maka baya shine masoyin ka, ba wanda ya zo don ya rabi ni'imar da Allah yai maka ba.
Halima na tsananta addu'ah ne domin amsuwar Hashim Yakasai a Kano farat daya a wajen Kanawan Dabo, ya ja hankalin abokan hamayya kwarai da gaske a kansa, wadanda a baya ba su damu da shi ba, kasancewar sa bako a harkar siyasa. Amma yadda ya samu karbuwa farat daya ya gigita jam’iyyar adawa, musamman da aka buga primary election

Please Login or Register in order to submit comment