An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
Documented by H.M.G
🧕UNAISA🧕
*A*
✍️Ayshatuuu
Na sauke wayar daga kunnena tareda sakin Murmushin jin dadi, bayan shekaru da na dauka Ina jiran wannan lokacin se gashi yazo, komai lokaci ne sede jiran se me karfin Imani. Na kalla gidan da komai na ciki Wanda nawa ne, na Kara kallon hoto Na sanye da Ash din Abaya ta idon duniya, fuskata dauke da Murmushin da ko kana bacin Rai ka kalla se kayi murmushi, Yana tsaye a bayana sanye da dakakiyyar shadda Ash sede nashi Ash din yafi nawa duhu, yayi kyau karshe Yana murmushi, na saki ajiyar zuciya Ina hamdalan cikar buri. Na aje wayar Jin ana kwankwasa kofa, cikin sauri na Nemo veil Dina dake ninke akan cushion gefe Dani na lulluba sannan na nufi kofa bayan na zura slippers a kafata, dama na aje ne saboda ko ta kwana. Seda na leka Amma banga ko waye ke knocking ba kawai se na bude, a take wata Mata da Kuma karamin yaron da Bai wuce shekara biyar ba Suka bayyana. Fuskar ta dauke da murmushi, matar ta girme ni sosae nesa ba kusa ba, kana kallonta kasan ta manyanta Kuma Yar gayu ce ta gani ta fada, nikam a rayuwata Ina son Yan gayu, take naji ta burgeni, ni din Yar gayu ce ta bugawa a jarida, ko lokacin da bamu da komai bamu da gata bamu da Mai taimako a hakan idan ka kalleni ba zaka taba kawowa a cikin wahala nake ba. I always mind how I look. Na Bata guri ta shigo tana fadin
" Amarya Bata laifi ko ta kashe Dan masu gida!"
Nayi murmushi tareda ayyana kada dai na kashe din. na karaso ciki na Mata tayi ta zauna tana fadin
" Ammar come and sit, baka gaida Anty ba"
Yaron ya zauna Nima na zauna Ina murmushi nace
" Zo nan boy"
Ya make kafada tayi dariya, na gaida ta ta amsa da faraar da tunda na bude take a fuskar ta, na Mike na shiga kitchen na dakko ruwa da juice, se su alkaki a karamin plate, na jera Kan tray sannan na kawo musu. Ta dubeni tace
"A'a harda wahala! Nagode sosae"
Nayi murmushi anxiously Ina jiran tayi min bayani
" Sunana A'isha, ni neighbor din ki ce ta baya, megidan ki yayi ma megidana maganar zuwan ki, shi ne na lallabo mu gaisa"
Na Kara fadada murmushi na ina shafa Kan Ammar da ya dawo gefena Yana Wasa da throw pillows din da na Gama jerawa, nace
" Naji dadi sosae Anty, sunana Unaisa. Nagode da ziyarar ki"
Tayi murmushi jin nace Mata ta ci abinda na kawo Mata, karshe tayi min bayanin yaranta uku bayan Ammar daya Tana karatu a Alqalam katsina, me bi Mata Yana UAE Yana karatu, se me bi Masa tana secondary ita anan cikin anguwar mu take yi.
" Amma Anty boarding Kuma? Na zata nan Bayan mu makarantar take"
Tayi murmushi tace
" Ai dukka boarding sukeyi, Kinga Ammar ma se yayi"
Nace
" Allah ya kaimu har na fara jin tausayin shi"
Kafin ta bani amsa se wayata dake Kan side table ta fara ringing, na saka hannu na dakko, jikin screen din kamar yadda nayi saving King, shi ya bayyana, saboda a duniyata shi din sarki ne, shi ke mulkin zuciyata. Na saki murmushi jin tace min
" Daga Kiran ki Mana"
Na Kara a kunne na Amma maimakon naji muryar shi se naji akasin hakan, naji wata muryar daban. A take yanayin fuskata ya canja nace
" Ina me wayan? Me ya same shi?"
" Hajiya idan Zaki iya zuwa kizo nan general hospital yayi accident ne"
Shi ne amsar, amsar data gigita ni, Bai jira me zance ba ya kashe wayar, already Anty Aisha ta iso inda nake saboda yadda hannuna ke rawa, kirjina Yana sama da kasa alamar Neman iska nake, ta riko hannuna tana fadin
" Me ya faru ? Me ya sameshi?"
Na dunkule hannuna Ina panting sosae, nace
" Anty shi ne Yana general Wai yayi accident"
Ta saki salati ta Mika min veil Dina tare da rike min hannuna Amma Ina tashi numfashi na ya fara sarkewa Ina Jan shi da kyar, nasan definitely I'm having an attack. Innanlillahi! Hakan da ta gani ya Kara rikitar da ita, inhaler ta na dakko Dake aje inda na dakko wayar Dan dama tun safe nake jin alamar attack din, shiyasa na kawo ta na ajiye. Nayi puffing inhaler na samu ya Dan lafa, zuwa lokacin fuskata tayi kacakaca da hawaye, hannayena Banda gumi Babu abinda suke, ita ta kulle gidan sannan ta zaunar Dani ta dakko mukulin mkta, gani nayi ta Dade Bata dawo ba, hakan yasa na Mike na fara tafiya, ban masan Ina nake wulla kafata ba, kawai dai Fata daya da nakeyi na tsinci kaina a emergency unit na general.
" Anty kina sauri"
Naji muryar Ammar Yana fada min se lokacin na gane Ashe hannuna na cikin nashi, nayi nisa naji an tsaya da mota a gefena, Anty Aisha ce ta fito ta saka ni gefen ta sannan taja motar tana fada min na dinga maimaita " Innanlillahi wa inna ilaihil rajiun!!" Haka nata maimaitawa har muka Isa asibitin. Ya Rabbu! Ban taba ganin tafiya me tsawo irin wannan ba, ban taba ganin kafata na rawa ba se wannan ranar, cikin mintina kasa da Sha biyar na gigice na fita a hayyacina, kamar ba amaryar da tayi kwanaki uku gidan miji ba. Dukka na canja a lokaci kankani. Tana parking muka fito na nufi kofar shiga unit din gabana Banda faduwa Babu abinda yakeyi, zuciyata kamar zata fito ta kirjina Haka nake ji. Nayi shiru ina kallon yadda ake ta zirga zirga,mutane nata Kai kawo, marasa lafiya wasu akan bench sunata hankoran ciwo, ga nurses na ta Kai kawon ganin sun kula dasu. Na tsaya rooted to the spot Ina jin maganganun sun danyi nesa dani.
" Dan Allah accident din da aka kawo dazunnan? Ko zamu iya ganin shi?"
Anty A'isha ta tari wani Male nurse dake zaune a station Yana clerking patient. Ya dubi wani officer Dake cike Abu cikin log book yace
" Officer inaga familyn victim din sun zo"
Nayi saurin kallon su nace
" Yana Ina? How's he? Tell me he's ok please"
Na fada muryata na rawa Ina hade hannayena waje guda alamar roko, hawaye wani na bin wani, hannuna Anty Aisha ta Kama muka bi bayan su zuwa cikin casuality din, tundaga yadda ake Kai kawo naji kafata ta sage, I'm part of the family nasan menene a janyo sunction machine da oxygen. He's in critical condition kenan! Kamar zombie Haka na cigaba da daga kafafuna har muka Shiga ciki, Yana kwance Kan couch din ciki, hannun shi infusion na shiga ta cikin cannular, hancin shi sanye da oxygen, Haka Kuma ana sunctioning din shi. Wani irin jiri naji Yana Neman kwashe ni ya yar a kasa, gaba daya ya canja kammanni, farar shaddar jikin shi ta jike da jini, Wanda ya tabbatar min yayi bleeding sosae, kafar shi anyi packing tare da daure ta Amma still jini na ratsowa ta bandage, Haka Kuma fuskar shi ta bubbugu, na karasa Ina jin wani mummunan tashin hankali da bazai misaltu ba Yana mamaye ni. Ya ilahil alamin! Na karasa gurin hawaye wani na bin wani na Kama hannun shi se Naga Ashe jini ake Kara Masa banma lura ba, na saki kuka Ina fadin
" Ya Allah! What happened to you"
In charge din ya fara min magana cikin lallashi har ya samu na yadda na zauna Amma zuciyata Allah kadai yasan irin abinda ke ciki, Anty Aisha na ta tausa ta tare da fada min nayi Masa addua. Hope kowa ke bani akan zai tashi, why se sunyi min karya, zuciyata ta karye, bana tunanin he's going to make it, Police din yazo ya bani wayar shi da wallet dinsa da Kuma wristwatch dinsa, na kalla wristwatch din ni na siya Masa kyauta wani zuwa da yayi gurina, shi ya saka ranar daurin auren mu! Ya Allah ka tashi kafadun shi, kasa ya Mike kada na rasa shi! Shi ne abinda nake maimaitawa cikin kaina. Rike wayar shi ya tuna min Yana da wani family Bayan ni, Kuma hakkin su ne Susan meke damun shi. Hakan yasa na cire lock din wayar, Wanda kawai swiping ne. Na fara lalubo number dinta " First Lady" Haka yayi saving a wayar bugu daya ta dauka tana fadin
"Ango kasha kamshi!"
Na ayyana a raina Ai Jin muryar ta se hawaye ya kubce min na fara shehsheka, Jin Haka se hankalin ta ya tashi ta fara tambayar wacece? Lafiya? Amma na kasa Bata amsa seda Anty Aisha ta karba ta Mata bayani Ina jiyo salatin ta tana fadin Anty Aisha ta fada Mata gaskiya idan ya rasu! Fadar hakan yasa na dago kaina na kalleshi, se kawai Naga ana zare masa nasal prongs din hancin shi, na dubi kirjin shi yayi flat, ga oximeter da aka saka ta tafi flat Babu alamar pulsation a jikin, se Kara take alamar Babu pulse ba oxygen saturation, Wani yawu me dacin gaske ya gauraye min bakina, na Mike Ina ganin idanuna suna rufewa da budewa spontaneously na karasa gurin. Naji ance
" Time of death 4:05pm!"
" Ya rabbul alamin"
Na furta da karfi, na nufe shi shi dinne a kwance ya rasu, farin cikin rayuwata, haskena, savior Dina ya rasu. Anty A'isha ta riko ni kowa a gurin na bani hakuri, se kallon tausayina suke dan Anty Aisha ta fada musu kwanan mu uku da aure, to duk sun sani ma, tunda yawanci sun ganeshi, idan ka kalla hannuna lalle ne, jikian kamshi amarci yake, Haka fuskata haibar aure a tattare da ita. Ya rasu! Se asthma Haka aka Jani mutane sun taru kowa na maida yacce akai, aka nebulizing Dina Amma da kyar ta sauka aka min allura Wanda da kyar na tsaya Danni gani nake mafarki nake, gani nake hakan bazai yiwu ba, a lokacin imanina baya kusa Dani. Da kyar Anty Aisha ta zaunar Dani tana lallashina itama hawaye na bin fuskarta. Ya Rabbu wannan wacce irin kaddara ce me zafi ka jarabceni da ita? Nasan baa questioning Allah Amma a lokacin banma San me nake fada ba, nayi nisa da hankalina. Ina nan na fara addua
" Allah Dan Allah kasa na farka a wañnan mummunan mafarkin da nake! Allah Dan girman Allah kasa ba gaske bane"
Funny ko? Yadda nayi adduar na yadda duk Wanda Bai taba wannan adduar ba Bai shiga masifa yadda ya kamata ba.
Love and fighting
Accusing denying
I can't imagine a world with you gone
Drawing and choas, demons we're made up
I feel so lost when you left me alone
Can you hear me screaming please don't leave me
Hold on I still want you
Come back I still need you
Lemme take your hands I'll make it right
I swear to love you all my life!
UNAISA is not free, pay N300 to 3091721807, A'isha kwalam Hassan first Bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258
[5/11, 5:55 AM] Hauwa Galadima: 🧕 UNAISA 🧕
*B*
✍️ Ayshatuuu
Mijin Anty Aisha yazo, aka Kuma sanar da Governor se gasu an aiko daga fadar shi, aka dauki gawar da taimakon masu zaman jinya harda staff din da securities, sannan aka rike hannuna muka fita, na jingina kaina da headboard din kujera motar Ina jin wani irin abu na bin jikina, I was scared, I was hoping ya tashi yace min April fool! Wasa yake Babu abinda ya sameshi, how I wish a movies ne ace ya shiga cardiac arrest ne! But wannan da gaske ne na rasa shi, shi din ya mutu. Wayar shi Dake hannuna ta fara Kara se Naga " Daughter" nasan Aseey ce hakan yasa na dauka na Kara a kunnena, cikin kuka take fadin
" Unaisa a wani asibitin kuke zamu taho?"
Hawaye ya cigaba da gangaro min nace cikin dashewar murya Dan ta riga da ta Jima da dashewar saboda kuka nace
" Ya rasu!!"
Seda tayi shiru na kusan mintina daya, either she's in shock ko Kuma kokarin digesting abinda na fada take, se kuwa ta saki kuka tana fadin
" That can't be Unaisa! Ki duba carotid artery din shi. He can't die just like that"
Allah sarki ita ta fini sakin layi, Jin bance komai ba se ta Kara sautin kukan Wanda ya Kara dagula min lissafi na jiyo ta tana fadin
" Mamaaa wallahi Abiey ya rasu! Unaisa tace ya rasu. Innanlillahi wa inna ilaihil rajiun!!"
Na kashe wayar Ina Kara sakin kukan rashin sanin halin da nake ciki, rashin sanin madafa. Kafin wani lokaci Kira ya dinga shigowa Amma bazan iya dauka ba, se Kuma Wanda suke da number ta Suka ta Kira na Amma na mutum daya na dauka wato mahaifiya ta
" Unaisa me ya faru da me gidan ki?"
" Ya rasu!"
Na fada Mata a hankali, ban Kuma Jin me tace ba, na rutse idanuna se Kuma ga Kiran Dada, uwata wadda ta kasance tare dani a dukkan halin da nake ciki, na dauka Amma banyi magana ba se sheshekar kuka da nake, hakan yasa ta saki salati tana fadin
" Yallabai da gaske ya rasu, ku Kira zuhra mu tafi"
Anty Aisha ta karbe wayoyin a hannuna, duk Wanda ya Kira se ta dauka ta bada amsa, a wañnan halin muka karaso Kano. Allah yasa nasan gidan shi Haka na kwatanta muka Isa, an taru sosae abinka da Dan siyasa da yake akan mulki. Aka shiga Dani ciki shima Haka gawar tashi. A makeken parlon kasa Mata ne a zazzaune kowanne da carbi a hannunsa, I began to think Ina Suka samu ko dama sunsan zai mutu ne, already Dada da Zuhra da Badi'a har da Yaya khulthum sun karaso, Zuhra na ganina ta mike ta nufo ni ta rungume ni, Haka kukan mu ya tsananta, seda Dada ta janye ni ta rungume ni tana buga bayana a kunnena tana fadin
" Sabr Unaisa"
Na kankame ta inajin kamar zuciyata zatai bindiga Dan abinda nakeji yafi gaban misali. zaunar Dani tayi aka dakko min hijab na yaye mayafin Dake jikina, Allah kadai yasan tururin da zuciayata take. Babu jimawa har an Gama shirya shi, aka shigo dashi akan muyi masa addua, kafata har sarkewa takeyi saboda jiri da nake ji. Na tsugunna gefen shi, ga Mamaa wato First Lady, Asiya, Muhammad da Kuma Ahmad se ni, mune ahalin nashi. Banda kuka Babu abinda nake Yi seda Mamaa ta dubeni tace
" Kiyi Masa addua Unaisa ita yake bukata"
Na kalleta, she sure is a strong woman, na saukar da kaina Kan gawar shi Sannan na fara nema Masa gafara, ina saka ran zai huta a kabarin shi saboda shi din mutumin kirki ne. Muna kallo Haka aka fita dashi zuwa makwanci, na saka kaina cikin hijab kamar Raina zai fita, ban taba sanin Haka zafin ka rasa wani yake ba, ko lokacin da mahaifina ya rasu naji Babu dadi nayi kuka Amma Bai Kai ko kwatan abinda nake ji yanzun ba. Ana Kiran sallar maghrib Anna ta karaso hankali a tashe, suka shigo Muna hada idanu da ita na Kara sakin kuka, ta janyo ni jikinta tana fadin
" Kiyi hakuri! Ki Masa addua"
Seda nayi shiru sannan ta matsa gefen Mamaa suka yiwa juna gaisuwa, Suka gaisa da Asiya sannan Dada da sauran Yan uwan shi Suma, a hakan se kallon banza ake wurga Mata. Se bayan ishai aka sarara, ya rage bamu da yawa. Dada tasa aka kawo Mana abinci, Amma Babu yadda batayi ba naki naci, se kuka kawai nake na rashin madafa da Kuma tausayin kaina. Wannan yasa Mamaa rike hannuna ta fara kuka itama, tunda nazo Naga tana hawaye daga baya se ta daina, she's trying so hard to be strong for us. Asiya ma se ta biye mu, Haka Muhammad da shigowar shi da abokan shi zasu Mana gaisuwa. Dada ta dinga Mana nasiha da matan gurin, Sega wata dattijuwa me Kama dashi tasa mu da fada tana fadin
" Idan bakuyi hakuri ba ya zakuyi? Kowa yaji mutuwar nan Amma kukan ya Isa Haka, ke Hajiya Talatu idan kina kuka Unaisa da Asiya su mutu kenan? Dan Allah kuyi hakuri"
Aka taru ana bamu Baki se kukan ya lafa, Anna ta mike tace zata tafi gobe zata dawo, Dada da Mamaa suka ce basu San magana ba, Dole ta zauna dan a wañnan lokacin Ina bukatar support, Dole Anna ta zauna ga Anty Aisha, se kannena Mata su biyu Nuzla da Hunainah, Dan Dada tace ma Badi'a ta tafi gidan ta tunda Yaya Man yazo tafiya da ita. Acan bangaren muka koma, duka Suka fara Shirin kwanciya Amma Ina zaune saman carpet nayi shiru tare da tsirawa guri daya idanu, Anna ta zauna gefena itada Zuhra ba tareda tace komai ba, wannan Daren guangyadi kawai nayi. Da safe labari ya bazu sosae cikin kawayena da Yan uwan Kai kasar Baki daya, ko Ina ka duba hoton mu ne na ranar daurin aure, Yana sanye da bugaggiyar shadda blue wadda akai riga da Yar ciki, se katuwar babbar riga ta farar shadda, ni Kuma Ina sanye da dandatsetsen lace Blue irin shaddar shi, nayi kyau har na gaji, fuskar mu dauke da madaukakin annuri, Wanda ganin shi kawai se ya saka murmushi, hoton ma iya soft copy ne ya karaso Dan hardcopy Bai zo ba, "he died after three days of wedlock" shi ne caption din.
Tun asuba nake kuka bayan nayi sallah, Anna ta dinga bani Baki da Anty Aisha, yayinda Hunainah da Zuhra ke tayani kukan. Anty A'isha tasa nayi wanka Amma Babu ma kayan da zan saka, se kawai na maida Wanda na cire Dada ta shigo lokacin Ina saka socks a kafata saboda bana son iska a kafar, ta zauna gefena na gaishe ta cikin dasashiyar murya
" Ya hakurin mu? Allah ya jikan honorable"
Ta fada na amsa da Amin Nima na Mata gaisuwa, ta dubi su Anna Suka gaisa sannan aka shigo da abinci, tea ta hada min me kaurin gaske tace na daure nasha, se na fara hawaye Amma yadda take min bazan iya Mata musu ba, Haka na kafa Kai na Sha baifi rabi ba na aje, ba Wanda ya sani se na karasa Suka barni sannan ta kamo hannuna muka dawo can parlon Dan karban gaisuwa. Haka har seda akai kwana uku sannan Anty Aisha ta tafi, Anna da sisters Dina ma Suka tafi tunda Zuhra na nan, Dada Kuma na zuwa. ya rage daga mu se shakikan shi, nawa dangin da kawayena sun min Kara nasha waya kowa na min taaziyya, wasu ma nasan Basu Gama warware gajiyar bikina ba.
Da yamma Ina zaune a daki ni da Zuhra, a Rana na hudu, Asiya na parlor zaune tana waya Mamaa ta fito daga daki tana fadin
" Ku saka hijab zaa shigo"
Nikam dama da hijabina a jikina Dan Haka Asiya kadai ta zura nata, Anty Uwa ta dubeni tace
" Unaisa Banga Hajiya ba?"
Na dube ta nace
" Ai ta tafi tun dare Baku hadu ba?"
Tace
" Ina can Ina magana, Amma ai da ta zauna dake"
Bance komai ba na cigaba da Jan carbina kawai. Babu jimawa Ahmad ya shigo shi tunda akai rasuwar Bayan ankai shi banma Kara ganin shi ba, ya rame ya to duhu na kalleshi shima ni yake kallo, ya karaso ciki ya zauna Dan nesa Dani muka gaisa muka yiwa juna gaisuwa sannan yace
" Ina Mamaa? Bakin zasu shigo"
Kafin na amsa shi se gata ta fito da carpet na Mike, na karba na shimfida sannan Ahmad ya fita se gasu sun shigo,mutum daya na sani Abba, ya zauna da mutanen da suke tare muka gaisa sannan Suka Mana gaisuwa. Sannan Abba yace
" A ganina Babu amfanin a zauna ana Jan magana, lawyer company din shi yazo Hajiya talatu zamuyi proceeding da compiling dukkan dukiyar shi a Raba gado"
Haka fa abun yake, ka Tara dukiya kana rasuwar zancen gado zaa fara, Babu Wanda ya damu da Kai se na kusa da Kai, hawaye suka gangaro min. Nasan Mamaa lawyer ce Kuma ya fada min dukkan takardun shi a hannun ta suke. Ta mike ta dakko katon file ta aje sannan tace
" Amma hanzari ba gudu ba, Baku ganin a Dan Kara lokaci Koda zai kasance Unaisa nada ciki!"
Anty Uwa Dake gefe tace
" Ciki Kuma? Auren kwana ukun haba ke kuwa Hajiya Ladidi"
Abba ya dubeni nidai kaina a kasa yace
" It's very possible, ni tunanin hakan Bai ma zo minba. Ahmad how early ake iya detecting ciki?"
Ya dubeni sannan yace a kalla da komai na mallakin dukiyar shi, tun ana lissafi Ina ganewa har kaina ya daina dauka, addua kawai nake Masa Allah ya gafarta masa. Anan aka ware abubuwan da ya riga ya mallaka Mana, ce Kar a raba gado dasu. Malamin dake zaune ya kissima yaga eh Bai Shiga yadda musulinci yace kada ayi considering ba. Gidan da ya saka ni ya mallaka min babu a gado,akwai wani gida na Mamaa ne, se wannan gidan ya barwa yaranshi kada a raba dashi.
Unaisa is not free, pay N300 to 3091721807 Aisha kwalam Hassan first Bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258.
[5/11, 5:55 AM] Hauwa Galadima: 🧕 UNAISA 🧕
*C*
✍️ Ayshatuuu
Haka na cigaba da Zama da Mamaa a gidan, yanayin zaman ya banbanta da abinda nayi tunanin ganin, na dauka baza mu taba maganar arziki da ita ba, yadda ta dinga fadawa Dada ta tabbatar idan Zan shigo na shigo da wasiyya ta Dan kuwa se ta min azabar dazan bar gidan da kaina, Amma ko kadan ko kallon banza Bata taba min ba, hasalima kallon da take min me dauke da tausayi ne. Har mamakin yadda muke