Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 5
falo, da kyar yana faman huci. "Humaida! Humaida!!" Ya dinga kiran sunanta cikin daga murya. Ta bude ido ta mike zaune tana hamma tare da mika. "Me ye ka ke tashina haka?" Ta fada a kufule. "Humaida, ki ji tsoron Allah, wannan wace irin rayuwa ce ki ke son tsiro da ita? Irin wannan rayuwar ko a tatsuniya 119 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ban taba ji ko ganin an yi irinsa ba, ta ya ya za ki ce wannan murdaden gardin ya shiga dakin bacci ya gyara miki?" Ta yi murmushi cikin kada kai. "Wallahi har ka sanya gabana faduwa haba mijina kwantar da hankalinza babu komai a ciki, an kawo shi ne saboda irin haka... A zafafe ya katse ta. "Ke! Rufe min baki, wallahi ba zai yiwu ba". Ya maida kallonsa ga John. "Daga yau na kara zuwa na ganka a dakinta sai na mika ka ga 'yan sanda". Ya yi tsaki ya hankada shi, ya shige dakinsa. Da gudu Humaida ta rufa masa baya. Ta zauna a gefensa idanunta cikin nasa. "Na fi son kullum in ga murmushi a kan fuskarka, na fi son na ga kana walwala". 120 リ KA AURE NI=2 Ya buga mata harare. BILKISU H. MUHD "Irin wannan rayuwar da ki ka tsiro ban taba ji ko ganin inda a ke yi ba, ki gaya mini ya sunan wannan auren namu? Humaida kin sake, kin sauya, ina tartama wannan ba Humaidata ba ce. A yau na yi tir da auren wannan Humaidar". Ta yi matukar sanyaya murya. "Irin wannan rayuwar duk wani dan Adam ke fatan cimmawa. Na taso a gidanmu ban san don me ya sa ka kasa fahintata ba. Haba mijina ka zauna za yi nazari". Ya mike a fusace. "Nazarin me ki ke so na yi? Babu wani abin da zan yi in ba ki gyara ba, komai zai iya faruwa tsakaninmu". Ya ja dogon tsaki ya yi waje yana faman mita. Binsa ta yi da kallo kawai cikin tabe baki. "Lallai akwai rigima a gaba". 121 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ta ga alama Mu'allim namijin duniya ne, sam ba shi da alamar risinawa a gare ta a matsayinta na 'yar gata yana son tun ba a je ko ina ba ya nemi dora mata hawan jini. *** *** *** "Ango ka sha kamshi”. Kirarin da Yusuf ya dinga yi masa ke nan, ya ci gaba da fadin. "Ai ni ban sa rai da ganinka nan zuwa wata daya ba, anya ka kyauta wa amarya kuwa?" "Haba, zaman gida sai mata". Mu'allim ya fada. "Ban da abinka abokina, ai kai kuma ana nema maka hutu kana nuna kai dan wahala ne, ai Alaji kawai ka nade a dafa a kawo maka ka ci ka tada kai, ka tsoma biyar ka cire goma". 122 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Murmushi kurum Mu'allim ya yi, ringin din wayarsa ne ya katse Yusuf. Lambar Dad ya gani, wato surukinsa. Ya kara a kunne bayan ya danna malatsin amsa kira. Muruar surukin nasa ta ratsa dodon kunnensa, da sauri ya dan risina kamar yana gabansa. "Barka da yamma”. "Barka ka dai Mu'allim, ya Humaida?" Ya ce, "Tana nan kalau”. "Da kyau, am Mu'allim ya kamata gobe a fito ofis". Iya abin da ya fada ke nan ya kashe wayar. "Yusuf ni zan wuce". Da sauri Yusuf ya sha gabansa. "Haba Alaji ai ba ka isa ba, ka mance yanzu ka girma hakan ni ma a dan jika ni". 123 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ya dube shi shekeke da wani uban takaici. "Me ka ke so na yi maka?" Ya tambaya a kufule. "Ina nufin ni ma ka dan dandala min... O.k bari na yi maka gwari-gwari, wallahi garin ne ya yi zafi". Ya rasa wacce irin amsa zai bai wa Yusuf, domin shi kansa rabonsa da ya ga naira dari a hannunsa tun kafin a daura aure. masa. "Yusuf ban fito da komai ba". Ya sa hannu cikin aljihu yana nuna "Ka yi hakuri”. Haka suka rabu Yusuf na faman mita. Kai tsaye ya nufi gidansa. John ya gani zaune da rimot a hannu yana kallon talabijin. A fusace ya karaso inda John ke zaune, murya a kausashe ya ce. 124 KA AURE NI=2 ko?" BILKISU H.MUHD "Ba ka ji kashedin da na yi maka ba Yà kai hannu ya damko shi tare da mikar da shi tsaye, ya kai hannu ya tsinke shi da mari ya kuma tankada shi. Ya yi taga-taga zai fadi, ya yi saurin dafa bango. "Wa ke wa mutane ihu haka?" Humaida da ke kokarin fitowa daga kicin ta tambaya. "Don Allah ka saurara masa, kana son takura wa mutumin nan me ya za ba za ka yi harkarka shi ma ya yi nasa ba?" Bai saurare ta ba idanunsa sun yi jajir, jikinsa har tsuma ya ke, yana huci. "Ka fita na ce". Ya ce wa John cikin daga murya da nuna masa kofa. Ita ma ta bude murya bakidaya. "Koma ka ci gaba da kallonka, babu inda zai fita ka ga Malam wai me ka ke nufi ne? Ni yanzu John ya fi ka amfani a gurina, domin zai gyara kuma ya dafa in 125 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ci, kai ko Dad shi ne kadai na ke wa amfani in kuma ka musa ka banar da amfanin me ka ke yi min, wallahi ka yi magana ka yi shiru babu ke nan ko to tunda babu ka bar mini mai aiki ya sake". Zuciyarsa ta dinga tunzurashi a kanta, ya kai hannu kamar zai mare ta, ya fasa ya maida hannun yana maimaita. “Innalillahi'. A zuciyarsa, ya juya a fusace ya bar gidan, ita ma ta shige nata dakin shi ko John ya hau doguwar kujera ya mike abinsa. A can harabar gidan ya zauna rike da kai komai ya kunce masa, son Humaida ya zame masa illa, da zai iya da tun yanzu ya tsinke igiyoyin aurenta. Yanzu kam yadda ya ke ji ba zai iya rayuwa babu ita ba, ko da a ce babu daula zai iya jure duk wani tijararta. 126 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Wai ashe haka so ya ke da zafi? Sonta ya sanya ba zai iya zartar da kowane irin hukunci ba. Ya dinga kada kai. "Humaida kin yaudare ni, kin shammace ni". Bai koma ciki ba sai daya tabbata ta yi baci. Lokacin da ya doshi gidan gabansa ya ji ya tsananta bugawa, ya yi sallama cikin rashin kuzari. Kawu ne mutum na farko da yake burin son dora idanu a kansa. Umma na zaune a tsakar gida, tankaden gari ta ke. Da sauri ta dube shi tana kokarin ajiye rariyar, ta mike tsaye tana yi masa wani irin kallo. "Me ya kawo ka gidan nan? Ka fita ba mu bukatar ganinka, mun dade da bar wa duniya kai". Ya rude ya dube ta. 127 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Umma kuka ki ke yi? Don Allah ki daina, zan fita amma kafin nan ki saurare ni don Allah". Da sauri ta daga hannu ta nuno shi. "Dakata! Kada ka soki zuciyata sau biyu, ya zama dole idanun iyaye su zubda kwalla don sun zama cikin bakin ciki saboda cutarwar 'ya'yansu". Gabadaya jikinsa ya gama yin sanyi, ya yi tattaki zuwa gabanta ya durkusa ya yi bala'in kaskantar da kaicikin sanyayyar murya. "Umma ina son ki sani Allah ya tsara Humaida matata ce in ba haka ba ban taa ketare abin da Abba ya tsara mini ba. Ke ce shaida, ke ce ya kamata ki fara fahintata, ban yi niyyar na ketaremaganarsa ba, don Allah ki fahintar da shi ke ce kawai za ki fahintar da shi ku yafe min". 128 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ta juya masa baya ta sarke hannayenta a bayanta ta yi dan tattaki ta sassauta murya. "Babana mahaifiyata kalmomin da suka fi dadin fadi aMebe, babu wani matashin kai komai taushinsa da ya kai tausayin uwa balle lallashin uba, hakika su kan rasa bacci don kai ka yi, sukan koka don kai ka dara". Ta juya gabadaya tana fuskantarsa, ta yi matukar kaurara murya. "Yau na tsane ka na tsani ka kira ni da wannan sunan Umma ko mahaifiya, saboda ba ka amfana mana komai ba lokacin da muke neman ka janye wata bukata taka ka juya mana baya". Kukan da ya ci karfinta ya sa ta dan dakata da maganar. Maganganunta sun gama rikita shi, ya girgiza matuka, zai yi magana ta katse shi da fadin. 129 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Biyayya ga iyaye fitila ce da ke haskaka hanya zuwa aljanna, rana ce da ke haska farin ciki a zukatan iyaye, kuma biyayya ga iyaye na debe maka kewa yayin da ka tsufa". Ta sauke ajiyar zuciya tana kallonsa cikin cizon lebe, ta sake numfasawa. "Duk ka rasa wadannan, ka rasa Mu'allim, ka shiga uku! Tun tasowa ta ban ga dan da ya sanya mahaifansa zubda kwalla ba sai kai, dan da mu ke tutiyar mun ba shi tarbiyya, tir! Ka kuma tashi ka fice kada Malam ya dawo ya riske ka a gidan nan, ka fice na се". Ta sake fada cikin daga murya, yadda ya ga tsanarsa a kwayar idonsa ya tabbata in kukan jini zai yi ba za ta saurare shi ba, tilas ya bar gidan. 130 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ta maida kai gurin duba agogon da ke manne a jikin bangon sitroom, karfe tara na dare, ta koma zanceń zuci. "Shin ina Mu'allim ya shiga, ba dai tun fushin jiya ba ne? Kai karfin sona ba zai bar shi ya yi fushi ba". Ta nufi daya sitroom din, John ta gani ya mike a kan kujera yana kallo. "Sannunka madam za ka fita ne?" John ya ce da ita. Ji ta yi kamar ya tunzurata, ta hau yayyafa masa ruwan bala'i ta inda ta shiga ba ta nan ta ke fita ba. Ya zuba mata ido kurum yana kallon ikon Allah. Karshe ya ga abin ba na kare ba ne ya mike. "Madam please, ka yi hakuri..." Ta watsa masa wata uwar harara. "Ka yi mini shiru ka kuma fice min daga gida ba na son ganinka yanzu”. Sum-sum ya yi waje. 131 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ta dauki waya a kan talabijin ta shiga laluben Dad dinta. "Dad, Mu'allim shiru har yanzu bai dawo ba". "Shi ne duk ki ka tada hankali haka? Yana tare da ni, aiki ne ya sha masa kai, kuma zai ci gaba da dawowa a irin wannan ララ okacin. Ta shagwabe murya kamar za ta yi kuka. "Haba Dad, ya za ka ce haka? Shi ke nan ba shi da lokacina sai dai na zauna ni kadai? Haba! Gaskiya ni ban yarda ba, wannan ai shiga hanci da kudundune ne, ni da mijina a raba ni da shi?" Dad ya yi murmushi irin mai cin rai, ya koma yа се. "Ina kayan kallo, ina jaridu, ina kuma John duk ba su ishe ki hira ba?" Ta yi saurin cewa. "Dad me ka ke so ka ce mini?" 132 KA AURE NI=2 Ya daka mata tsawa. BILKISU H.MUHD "Ki yi mini shiru, kina tunanin zan dauki diyata na ba shi ya ci bulis? Ko kadan ba na tunanin yin haka". Ya ja tsaki ya katse kiran a zuciye. Ta cillar da wayar ta dora hannu a ka ta kwalla kara ta koma ta zube a kan kujera tsawon lokaci ta kasa motsawa. Motsin tahowa ta ji, ta yi saurin mikewa ta nufo bakin kofa. Mu'allim ta gani, ta yi saurin shan gabansa. "Ina ka shiga, me ya hana ka dawowa da wuri?" Bai bi ta kanta ba ya wuce abinsa ya zauna a kan kujera, ta tsaya kawai tana dubansa, komai na Mu'allim mai kyau ne, duk sai kallonsa ya gama kashe mata jiki, ji ta ke kamar ta je ta fada jikinsa, sai dai tana tsoron aikata haka, zai sa ya rainata, ta matse lokaci daya ta daure fuska ta nemi 133 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD daya daga cikin kujerun ta zauna ta yi bala'in basar da shi. Ya mike ya nufi firij ya dauko tuwa ya koma ya zauna, ya tsiyaya a kofi ya sha ya koma ya kwantar da kai a jikin hannun kujera, sam ba shi da niyyar kulata saboda abin duniya ya sha masa kai, ya rasa komai na farin cikinsa. Tilas ta karya billenta cikin shan Kamshi ta ce. "Mu'allim magana fa na ke maka, ka bude baki ka ba ni amsa. Ya ja tsaki ya mike tamkar bai san da zamanta ba, bedroom dinsa ya shiga. Da gudu ta mike ta rufa masa baya. A tsakar dakin tsaye suke carko-carko. "Mu'allim kana son maida ni 'yar iska a gidan nan, kana neman ka raina min hankali, kana neman wuce makadi da rawa, saboda tsabar rainin hankali ina yi maka magana kana wani tafiya? To ka sani 134 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ko Dad na ke wa magana ba ya yi mini irin abin da ka ke yi min! Yau ka 6ata min rai". Takaici da bakin ciki gami da dariyaа gabadaya suka dinga cinsa, a fusace ya ce. "Ki je ki tambayi mahaifinki!" Ya yi saurin barin dakin. Yana zaune a kan mota yana faman lallatsa waya, wasu muryoyi ya ji a kusa da inda ya ke. Jin ana fadin sunansa ne ya sa shi maida hankali ga abin da suke fada. Samari ne su biyu ba su wuce sa'anninsa ba, daya yа сe. "Me' ya sa ba za mu latsa Mu'allim ba, na san ba zai hana mu ba”. Dayan ya ce, "Kai don Allah rabu da shi, ba ya mikawa sai yawan gaisuwa". Dayan ya sake cewa, "Kada mu yi saurin yanke hukunci sanin da na yi masa mutum ne mai son yin alheri". 135 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Whm da ke nan, lokacin da bai san dadin kudi ba, amma yanzu ya dandana ya san zakinsu". "Me ya sa ka ce haka?" Dayan ya sake tambaya. "Kai kanka ka dube shi ka gani, da da yanzu daya ne? Wanne ya fi kyan gani? Dubi fa yadda ya fige ya lalace lokacin da yana talaucinsa bai yi irin wannan ramar ba".. Ya sato kallon gurin da Mu'allim ya ke, da sauri Mu'allim ya basar, ya maida kai ga abokin nasa. "Tabbas na yarda da kai, to amma abin da ban mamaki”. "Ba abin mamaki ba ne, yawanci dogon buri ne wanda har abada ya ke hana su gode wa Allah a kan abin da ya ke samu, idan kuma ya fara samu za ka same shi mai kyamar jama'a, kuma shi kansa mawahalci ne ba ya iya daukar wani abu 136 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD daga cikinta don ya wadatar da kansa da iyalinsa, wai duk don gudun kada dukiyar nan ta kare". "Na yarda da kai, tabbas Mu'allim ya sauya a da mutum ne shi mai yawan fara'a, ga son jama'a yanzu kam kullum in ka ganshi za ka ga fuskar nan a daure tamau". Daya matashin ya dora da fadin. "Wannan shi ne dalilin da ya sa a ke samun wadansu attajiran suna fama da yunwa abin da ya fi muni duka shi ne idan ka ki yin amfani da dukiyar nan ta hanyoyi masu kyau yana yiwuwa bayan ka mutu a batar da ita wajen aikin banza, babu shakka kuwa komai ka bari gobe kiyama za a tambaye ka bayanin hanyar da ka bi כל ka samu abin nan... Bai iya tsayawa jin karashen maganganunsu nasa ba ya dimauce ya gigice, tabbas ba wannan ne karo na farko 137 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD da ya taba jin ire-iren maganganun nan ba, amma yau abin ya yi muni. Ya diro daga kan mota ya shiga ya tada ita, da kyar ya ke iya ganin gabansa, ikon Allah ne kurum ya kai shi inda za shi. Kamshin da ya dinga shaka ne ya tilasta masa kutsawa bedroom dinta, tana zaune a gefen gado sanye da rigar bacci.zumbur ta mike tana kallonshi. "Lafiya?" Bai ce komai ba ya maida kofar zai rufe, ta dako tsalle sai ga ta a gabanshi. "Me ka ke son aikatawa?" "Na zo gurin matata don karbar hakkina". Ta dube shi shekekeş ta ce. "Hakki? Wane irin hakki kuma?" Ya ce, "Ke ba karama ba ce, kin san abin da na ke nufi". Ya fada yana kallonta. 138 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Humaida na gaji, ke halalina ce ba zan iya ba, please". Ta dan ja da baya. "Ai na gaya maka ban aure ka don wannan abin ba, shi ya sa ma na zabi na zauna da kai a ganina ba za ka taba tirsasa ni ba, ka gane ko?" "Me ya sa za ki yi min haka Humaida? Kin sauya mini tamkar ba ke ba". Ta murguda baki cikin yanayin tsiwa. "A rayuwa babu abin da na tsana irin haihuwa, ban shirya mata ba, ba yanzu ba. Har nawa na ke? Ba zan iya ba". Ya katse ta da fadin... "Humaida, kina da ilimi, kin san abin da aure ke nufi..." "Mu'allim na ce da kai ka kyale ni, me ya sa ka ke son maida ni wawuya? Ni fa ban yi aure don namiji ya juya ni yadda 139 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ya ga dama ba, yauwa kai kanka ka san na fi karfin ka zo min da wannan rainin, ka bar ni na mori rayuwata ni kadai ba tare da wani yaron ya rage mini jin dadinsa ba,ba kuma na bukatar wani guri a jikina ya sami tawaya, ba zan haifa ba balle na shayar, ka gan ni kawai ka kalle ni na burge ka, ka dinga jin ka fi kowa sa'a domin ka tsinci dami a kala. Yanzu in na haihu kai kanka ba za ka so kallona ba, yanzun nan zan tsofe na yakune, da fatan ka gane nufina?" Ta gama kular da shi karshe, cikin daga murya ya ce. "Saboda haka na ce da ke, ke mahaukaciya ce tuburan, sam ba ki da hankali, ke gabadaya ma ba ki cikin jerin mutanen da za a kwatanta su da masu hankali, ke jahila ce wadda ba ta san me ta ke ba, banza! Bailagaza! Sauna! Kuma ki ji da kyau, wallahi ba ki isa ba, dole ne na juya ki, dole ne na yi yadda na ga dama da 140 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ke, don ni na ke aurenki ba ke ki ke aure na ba. Bari ganin ina daga miki kina duk iskancin da ki ka dama, ba wai ba zan iya tsawatar miki ba ne, ina so ne ki saba da rayuwar a hankali, amma tunda na lura kwalwar kifi ce da ke zan saita miki دو zama... Kusan daskarewa ta yi a gurin saboda tsananin mamaki, ta nuna shi da yatsa. "Mu'allim ni ka ke ci wa fuska haka? Ni ce jahilar? Wace irin tarbiyya ce iyayenka suka ba ka da ba su koya maka tattalin mace ba? Ko haka ka ga tsoho na y... Tabdijan! Humaida ta ballo ruwan dafa kanta. Mu hadu a littafi na uku don jin yadda za ta kasance. Bilkisu H. Muhd. 141 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD DANDANO DAGA 'YAR BABBAN GIDA Ya kutsa kai dakin da yake jiyo kukanta, ya hango ta a takure a sakon gado lamarin ya yi matukar taba masa zuciya musamman da ya yi mata ganin a hargitse babu gyara. Kwalliyar nan tata mai jan ra'ayinsa yau kamar ba a taba yin irinta ba a jikin Sa'adah ba, tun kayan barci ne na daren jiya. Fuskar nan ta koďe ta jeme, idanuwan sun yi luhu-luhu, ga ruwan hawaye da ya y kaca-kaca a fuskarta, gabadaya yanayinta ya sauya sai ya ke ganinta kamar ba Sa'adan tashi ba 'yar kwalisa mai iya daukar kwalliya da iya zuba dressing irin na daukar hankali ba. Tausayinta mai yawa ya tsirga masa, tabbas an shiga babin da zai iya salwantar da rayuwarta, ta sha fada masa. "Wallahi Mahmood gara na mutu kafin na ga ranar da za ka yi min kishiya". "To wai wa ya ja? Ita ce silar komai". Ya zauna gefenta cikin tattausan lafazi ya ke magana a gare ta. "Me ya yi zafi har irin haka Sa'adah? Ashe ke din ba za ki daure ki zamo jaruma a cikin mata ba? Yanzu saboda Allah irin wannan da ki ke yi me sunansa? Wa zai dube ki a yau ya fahinci ke ce Sa'adahr nan ma'abociyar ado da kyalkyali? Dube ki yadda ki ka mayar da kanki dalilin wani abu 142 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD da bai taka kara ya karya ba har ki ke neman sukurkurta kanki, ki ke son ki zamo abar kallo da nuni a wajen sauran mata...?" Ya sa hannu ya ke jawo kanta da ta tura tsakankanin cinyoyinta, ya ke fada mata. "Ki sa hakuri da juriya a ranki, ki zamo jaruma sai ki ringa rayuwa shi wannan din wani lamari ne mai girma da ya zo gare ni daga Ubangiji, ba wai niyyar kaina ba ne, ko nufin muzanci a gare ki, a'a yi wa lamarin kallon shirin Allah ne. In ba Allah ba Sa'adah shirin ya zo daga gare Shi ya ni da na ke da kamar ke zan jawo wata cikin rayuwarmu? Haba! Haba! Ai wannan da gani kin san ba yina ba ne, yin Allah ne. saboda haka maza share hawayenki, ki zamo mai hamdala a gare Shi, don ba mu sani ba kila wata rahamar ce ya yi shirin yenta a gare mu, shi ya sa ya aiko da hakan a gare mu". Ya sa hannu yana share mata hawayen. Tа ture hannayensa daga jikinta, ta ke magana a gare shi da muryarta da ta dushe don azabar kuka. "Babu wani furucinka da zai yi tasiri a gare ni, domin na riga na gama fahintar lamarinka game da ni, nid in na zamo abin ki a gare ka..." Da sauri ya katse ta. "Wa ya fada miki ke kin zamo abin ki a gare ni?" "Kai ka tabbatar min da haka tunda har za ka iya raba soyayyata zuwa ga wani fangaren". Ya fada 143 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD mata cikin lallami. "Ki dauki aurena kaddara Sa'adah, ba wai wani batu da ke fita a bakinki ba". Ta juya kafada da girgiza kai ruwan hawayen na ci gaba da kwaranya daga idanunta, ta ce. "Babu batun kaddara a maganar kishiya, ka ci zarafina irin wannan ka zauna a gabana kana fada min wai Kaddara? Ina! Wannan sam ba kaddara ba ce, son zuciya ne kawai da son muzanci a gare ni". Ya ce, "To idan ma ba kaddarar ba ce Sa'ada wa ya ha? Kar ki mance fa komai ya faru ke ce sanadi, da a ce kina tare da ni a kan kowane ra'ay nawa kina biyayya a gare ni, da yin rayuwa kyakkyawa irin ta sauran ma'aurata ta ya za a yi irin wannan ya faru? Amma ki yi duba ki ga mene ne na Gatanci bai faru daga gare ki zuwa gare n da tallafin mahaifnki ba..." Ta katse shi da alama ranta ya kara hauhawa a 6aci. "Na yi maka alkawarin gyara halayena da binka sau da kafa, da yi maka duk yadda ka ke bukata, amma kai ma ka yi min alkawarin bayar da saki aa gare ta tun kafin ta kai ga shigowa cikin gidan nan". Murjanatu Muhammd Dan-Guru 144 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 5 of 5