Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
gani kala biyu dinkakku. Ya dubi Mu'allim. sai "Ubangiji ya aba ka masu yi maka". "Amin Abba, bara na ci abinci in huta na yi masa wanka na sanya masa. Sun sake sosai'cikin soyayyarsu, yau shi ne ta ja shi wancan guri, gobe ta ja shi wani guri, gidajen abinci kam kala-kala Mu'allim ya sani, dawainiyarta gare shi ya wuce misali, gabadaya ya sauya tamkar ba shi ba, duk irin suturar da ta ke ra'ayin ta ganshi a jikin da namiji ta siya masa, da zarar ya dawo daga kamfani gidansu ya ke wucewa, Hajiya Zainab tun tana tsanarsa har ta watsar, kyawawan dabi'unsa ya sauya mata kiyayyarsa musamman da yanzu ya soma sauya rayuwar 'yarsu za ta iya cewa Allah ya dora shi a kanta, duk wani tsiwa da dagawa ta kan ajiye shi muddin suna tare da shi. 58 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Yau tunda ya iso kimanin mintina talatin yana zaman jiranta har ya soma sha'awar tafiya daga can nesa ya hango ta, ta taho sanye cikin kananan kaya, ta yane kanta da dan siririn gyale kan nan nata ya sha karin attach. Tana tafe da Kyar tamkar tana tausayin kasa, a sace ya ke kalionta yana jin kansa cikin wani irin nishadi, Ubangiji ya yi masa baiwa da ya mallaka masa Humaida. Yana sonta tamkar ransa, haka kya sa wani fanin ya ke kasa tsawatar masa a kan duk wani tabararta, ya lura wasu halayyar tata sun riga sun zame mata jiki, musamman tara farce, karin gasji, shagwaba da rashin iya magana. "Hello". Ta ce da shi a daidai, saitin kunnensa. Ya ji tsigar jikinsa na tashi musamman da ya shaki wani shu'umin turare ya lumshe ido ya bude ta zauna a kujerar kusa da shi tana murmushi. "Kina da kyau". 59 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ta shiga yi masa kallo mai lumshe idanu kallon da a duk lokacin da ta ke masa shi ya kan ji tamkar ya rungume ta. Ta daga masa gira. "ba ka gajiya da yaba mini?" "Ta ya ya zan gaji da yabonki?" Ta ce, "Amma ka san wani abu?" "Sai kin fada". "Wallahi Mu'allim ka fi ni kyau, don haka na ke kishinka, ina yi maka kallon fure, ba zan taba hin kunya ba yayin da na nuna wa duniya mijina, don haka na сe KА AURE NI”. Ya so ya yi mata wata tambaya ya dai basar, ya се. "Ina rokon alfarlma mai ya sa ba za ki adana kwalliyar nan ba har sai kin je gidana? Wannan kwalliyar ni ne kadai ya dace na gani". "Haba ai a gidanka kuma ba zan yi wannan shiga ba, akwai irin shigar da na tanadar maka". 60 KA AURE NI=2 Farcenta ta ga yana kallo. BILKISU H.MUHD "Ba ka son wayewa, ni a ckikinta na taso, domin ba haramun ba ne. To ma me ye wayewar?" Ta daga hannu tana kallon faratanta. "In yi wanka, in ci abincin da na ke so, in hau motoci masu tsada, mai kuma matsalata? Ji na ke yi wannan ita ce wayewar ko ba su ba ne?" Tunda ta soma maganar ya kasa janye idanu daga kanta har sai da ta bushe masa ido, ta kai hannunta za ta riko nasa, ya yi saurin janyewa. "Please, sorry Mu'allim". Ta ce. Ya sake dubanta. "Kada ka dauki rike hannu a matsayin wani abu daban, na kan rike hannun abokaina, wannan ra'ayina ne, so kada ka damu". Ya yi murmushi kawai. Mustapha ya zo wucewa ya yi masa sannu da zuwa. 61 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Amma kuna yanayi da shi". "Uhm haka a ke cewa, kanin Dad ne". "Kaninsa ne?" "Eh, kana Ummaki ne?" "A'a ba na yi, ni zan wuce". Ya mike ta rufa masa baya. A harabar gidan suka hadu da Injiniya Sunusi. "Mu'allim da ma kai na ake zaman jira, ga wannan makullin”. Ya mika masa, ya durkusa ya karba. "Motarka ta iso". Gabadaya kansa ya kulle. Injiniya ya fahinci hakan, ya ce. "Ina nufin mota ce na siya maka, yanzu haka da ita za ka wuce gida". "Wow! Dad thanks". Ta rike hannunsa tana murna. Ya nuna musu motar, a gaban Dad din ta janyo hannunsa. "Taho mu je". 62 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Godiya ya dinga rangadawa ta ja shi, Injinkiya na yi mata dariya ko a jikinsa kama hannun kato da 'yarsa ta yi. Hakika talauci bai yi ba, ji yadda Mu'allim ya sauya, tabbas 'yarsa ba ta yi zaben tumun dare ba, ta samu namiji tamkar da dubu. Ya gama yi ta ko'ina. Ta bude masa motar tana nuna farin cikinta, hannunsa nade a kirji. "Dad ya siya maka mota mai kyau kamar kai Dad ya san duk abin da ya dace da kyakkyawan mutum. Okey, shiga ka tafi". Har lokacin Ummaki ya kasa sakinsa, yana jin komai tamkar a mafarki, da kanta ta karaso gabanshi neman riko shi ta ke yi, haka ya san ya yi saurin shigewa motar, haba wani sanyi da kamshi ya ji ya dinga rige-rigen ratsa shi. Ya ji wsani nishadi ya rufe shi, ta rufe masa kofar tana daga masa hannu. 63 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD A can gida Malam Musa da Hajara sun dunguma kofar gida kallon mota tare da sanya albarka. "Abba ai shiga za ku yi mu zaga gari da ku". "Ba shakka Malam kanaji fa?" "A'a Hajara ina ni ina shiga wannan babbar mota? Ai sai yara". "Malam gaskiya fa yaro ya fada shigarmu shi ne sanya albarka". "Sai dai ke ki je in ba dole ba ba son shiga mota na ke ba, kin fi kowa sani ina ba so ku ke ku dawo da ni magashiyan ba". "To ni kam zan saka albarka". Tuni ta shige motar, Malam na faman yi musu tsiya, ta kame a gaban mota tana jin wani matsanancin farin ciki na ratsa ta. Ba ta san sa'adda ta fashe da kuka ba. A hankali ya gangaro gefen kwalta. "Umma me ke faruwa?" "Mu'allim kukan dadi na ke yi, ashe za mu sami irin wannan 'yancin? Ubangiji 64 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD na gode maKa. Wallahi ko yanzu na koma gare ka zan mutu ina mai farin ciki da godiya yau burina ya cika, Ubangiji ya yi maka albarka" Ta dinga jero masa addu'a bai maida ta gida ba sai da ya yi mata soyayya sama da dubu hamsin tukunna suka dawo. Da kanshi ya taya ta suka share mata daki, ya shimfida mata leda tare da alwashin zai sauya musu gida. Su kansu su Adnan sun san abokinsu ya samu, domin sam abinshi ba ya rufe masa ido, musamman zai siyo kaji ya sa Ummansa ta dafa musu a zuba su kwashi gara, alheri tsakaninshi da su ba ya yankewa haka ya sa a kullum suke kara kwarara masa gwiya. Yau ma kamar kullum suna zaune a shagon shi Adnan ya kalli yadda ya sauya komi na shagon, ya с 65 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Lallai komai na son gyara, ka ga shagon nan tamkar ba shi ba, wallahi abokina ka gama shan kwana". Mu'allim ya kada kai, "Ka san wani abu yanzu ji na ke yi ina son na juya fiye da wannan dukiyar, yanzu ko da za a janye dukiyar zan iya ci gaba da sonta "A'a abokina kada ka zafafa saboda gudun matsala, dole fa ka dinga dannewa, haka ne zai sa ka zamo jajirtacce muddin ba haka ba kai ne za ka zamo macen bayan an yi aure, duk runtsi ina son ka dinga nuna mata kai ne shugaba, in ka bari ta samo lagonka za ka gama yawo, don na ganta 'yar rainin hankali ce". Gabadaya suka yi dariya. "Adnan abin kuma har da sharri?" Ya ce, "Sharri ko gaskiya?" "Zan fa gaya mata?" "A'a rufa min asiri". *** *** *** KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Sister, kina ganin yadda gabadaya Alhajinku ya maida hankali kan wannan kan ta wayen kina kallo har da saya masa waya, kina kallo har da saya masa mota? Ni ka mina cikin gidan nan bai taba siya min ko da keke ba". "Amma da bai saya maka ba wacce irin mota ce ba ka hawa? Babu motar da aka yi maka shamaki da hawanta, ka gode wa Allah mana". "Sister, ko yau Alhaji ya fadi ya mutu na yi imani daina hawa zan yi, ko kuwa bai hana ba wannan fitananniyar Humaida za ta hana..." "Dakata Aminu me ka ke fadi ne? Humaida diyata ce ba ta kishiya ba, ka budi baki ka kira ta fitinanniya a gabana? A gaskiya ka sake da yawa "In ita 'yarki ce ni kuma kaninki ne, ina kuma da ikon da zan gaya mata ko me ye". 67 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Ba ka da shi, domin ba kai ne ka haifa mini ita ba". "Okey, daure mata gindi shi ya sa in rashin mutuncinta ya tashi a kanki ya ke karewa, kuma za ta ga ni sai na kunno mora wutar da za ta kasa kwacewa, ba dai ita soyayya ba? A tafin hanuna ta ke, na san yadda mahaifin yaron ya ke kinta za a yi auren in gani". Ya fice yana faman surutai marasa kan gado. Hajiya Zainab ta hada kai. "Tabbas ba ka hayyacinka, zan daga maka kafa sai ka dawo daidai in karta maka rashin mutunci, wanda za ka ji a jikinka, yanzu ko da na yi ba za ka fahinta ba, dan iskan karya". Shi kam Adam tunda Mu'allim ya shiga rayuwar gidan ya soma tausaya masa, ko da labarin siyen motar ya riske shi ya yi mamaki, kodayake ya sani akwai abin da Injiniya ya taka, ya kan yawaita yi wa 68 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Mu'allim addu'ar tsira daga sharrin 'ya'yan nasa sau tari in Mu'allim ya zo ya kan ji tamkar ya tsare shi ya ba shi labarin mugun hali na Alhaji, sai dai in ya dube shi ya akan gano tsantsar son Humaida kwance a idanunshi ya yi imanin ya riga ya yi nisa, don haka kurum ya zamo dan kallo shi dai yana gefe zai ga zuwan lamarin da dawpwarsa, sai dai kullum fatan alheri ya ke bin Mu'allim da shi. Kamar yadda malam Musa ya saba kafin ya tafi masallaci sai ya daura alwala a kofar gida, yau ma hakan ce ta kasance a can nesa da shi. Mudansir da abokinsa, cikin daga murya suke hira, abokinsa ya ceе. "Gaskiya yaron gidan can ya sami kudi, tabbas dare daya Allah kan yi bature, kai ka ga motar da ya ke hawa?" Mudansir ya ce, "Haka ne, amma ai baban budurwarsa ne ya mallaka masa duk 69 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD wadannan abubuwan, ciki har da sama masa aiki a kamfaninsa.. Abokin ya ce, "Haka ne, caf in ko haka ne bai kyautawa kansa ba, ka ce shi auren kwadayi zai yi?" Mudansir ya ce, "Kai di bari, ba giringirin ba tai mai, in dai wannan mutumin ne sharri ne zai biyo baya, muna nan za ka gani". Abokin ya ce, "Auren kwadayi babu abin da ke biyo baya sai tsantsar nadama". Malam musa ya ji wani jiri na dibarsa, ya mike da kyar, masallacin da bai iya zuwa ba ke nan, sai a gida ya yi sallah. Yana zaune a kan darduma, magana ya kasa yi. Hajara ta dire masa abinci shinkafa da miyar naman kaza sai kamshi ya ke, na gama girkin. Ya dube ta. "Ki dauke abincin nan ba zan ci ba, ba zan sake ci ba har abada kin ji ko". 70 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ya fada cikin daga murya, ta dube shi. "Allah ya ba ka hakuri mai kuma ke faruwa, ji na ke yi yanzun nan ka ce mini kana jin yunwa in wannan abincin ne zai dauke mini yunwa ta na muu, malam na shiga hudu, ka gaya min abin da ke faruwa". "Yaron nan yana tare da wannan yarinyar". Ta ce, "Yanzu har yanzu ba ka daina zarginshi ba?" "Babu zargi, shi ne ya ke ba shi duk wani abu da ju ja ga ya mallaka, yana kuma aiki ne a karkashinsa". Ta shiga tafa hannu. "La'ilaha illallahu, yanzzu bain da yaron nan zai yi mana ke nan?" Ya tashi ya koma kofar gidan yana jiran dawowar Mu'allim, har bayan sallar magriba bai dawo ba, zuciyar Malam Musa tamkar za ta fashe, a can nesa ya hango shi yana tafe rike da manyan ledoji guda biyu. 71 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Da sauri ya mike, ya tsaya a dokin kofar gida yana faman huci. Sannu a hankali ya karaso. "Sannu da gida Abba". Bai ji ya amsa ba hakan ne ya sa ya dube shi, ras gabansa ya buga. "Abba lafiya, ina Kawu?" Yunaninsa Kawun ne wani abu ya same shi, kokarin ratsawa ya ke ta gefenshi. Ya daka mishi tsawo. ya ce. "Ina za kaа?" Cike da Ummaki ya се. "Ciki zan shiga'. Cikin kakkausar murya Malam Musa "Da wannan kayan?" "Abba ai kayanku ne na siya muku don ku yi amfani da shi". "To ka juya ka maida su". Ya yi turus, "Amma Abba ban fahince ka ba? Na ce ka juya ko ba ka ji ne?" 72 S KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ya durkusa, "Abba na tuba ban san me na yi ba". Cikin zafin nama ya kai hannu ya cizge ledojin ya watsar da su, suka tarwatse kayan shayi ne sai gasassun kaji da sabulun wanka da na wanki. Yana huci ya ce. "Daga yau ban lamunci ka shigo min ko da kwallin shinkafa ne in ko ka kawo ko da ba da sanina ba, ba zan yafe ba". "Abba ban san me na yi ba, hukuncin ya yi mini tsauri, ka yi hakuri na tuba". Ya ce cikin rawar murya. "Ka nuna mini ban isa ba, ka ci amanata ka kuma tozarta ni, amma ba komai akwai Allah". Ya juya ya shiga gida; Mu'allim ya mike cikin tsananin damuwa ya rufa masa baya. Hajara tsaye a tsakar gida fuskar nan a daure tamau. "Ina shakku a ce wannan Mu'allim dina ne, Mu'allim mai jin tausayinmu yau 73 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD shi ne ya rikide zai zamo silar tarwatsewar farin cikinmu. Ka yi hakuri ka sani Malam ne kadai gatanmu, ba ni da kowa idan ka haifar masa da wani ciwon ya ya zan yi? Ina Kara umartarka ka gaggauta rabuwa da wannan yarinyar, ka rabu da ita". "Ummi ku yi hakuri ni ban ga aibun yarinyar nan ba zargi kawai ku ke yi a kai ba kamammiya ba ce, rayuwarsu ce a haka da zarar na aure ta zan maida ta yadda ku ke 39 so... Zuruf Malam Musa ya fito daga daki, ta inda ya shiga ba ta nan ya ke fita ba. "Wallahi Hajara da ya auri wannan yarinyar gwara ya auri tantiriyar karuwa, da ya aure ta gwara ya auri gawurtacciyar 'yar fashi saboda na san wata rana Allah zai shirye ta, in kuma karuwa ce mutane nawa ne ke aurensu kuma karshe dalilin haka su sami shiraya". Ya dabi Mu'ailim da ido jajir. 74 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Wallahi da ka auri wannan yarinyar gwara ka mutu, da na ga aurenku da ita gwara na roki Ubangiji ya dauki raina, in kuma ban mutu ba zan haukace, dzan dawo kamat yadda kanina ya ke". Kuka Mu'allim ya saka wanda bai san lokacin da ya kwace masa ba. "Abba ka sanar da ni, me suka yi maka ka sanar da ni zan rabu da ita". "Ni ne na haife ka ba kai ka haife ni ba, zan iya tilasta ka a kan komai ba tare da na gaya maka dalili ba, in har ni ne mahaifinka dole ka bi abin da na ke so ko da kuwa abin zai zamo ajalinka"/ Ya juya ya fice daga gidan. Ya durkusa a gaban Hajara. "Don Allah Umma ki gaya mini kada ki boye mini, kada ki 6oye mini me mutanen nan suka yi wa Abba ya tsane su haka? A da na yi zaton irin abin da na hanga na rashin kamun kanta ne ya sa ya ke nuna kyamarsa gare ta, sai dai na lura ba haka ba 75 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ne. Umma ki nusar da Abba ba zan iya rabuwa da ita ba, ban san yadda aka yi sonta ya yi nisa a zuciyata ba, ki tausaya mini wallahi ba ta da wani mugun hali". Hajara ta dube shi kawai tana kada kai, yau Mu'allim ne ke ambato mata yana son wata, yaro mai kunya da kawaici, wannan al'amari abin duba ne. Ta sanyaya murya tana girgiza kai. "Malam na da kafiya fiye da tunaninka, tunda ya kafe ka yi hakuri, ina tsammanin akwai abin da ya hanga..." "Umma na fahinta, Abba ya fi son ya gan ni cikin wahala da tozarci. Umma zuciyar Abba ta mutu, wahala ta raunana tunaninsa, shin kina son dawowar rayuwarki na da shin me ya sa Abba zai nuna bakin 99 cikinsa da abin da Ubangiji ya bai wa... Ji ka ke tas! Tas!! Tas!!! Hajara ta hau marinas ta ko'ina. "Mu'allim ka haukace? Wallahi ka gama yawo, mahaifinka ka ke gaya wa 76 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD wadannan maganganun saboda dan abin da ka soma samu? To in har kudi zai sauya ka, na roki Allah ya barka a haka". Ta juya ta shiga ciki tana sharar kwalla, shi ma ya juya ya koma dakinsa. Yana zaune a gado jin zuciyarsa ya ke tamkar ta lfashe, ba ya taba tunanin zai iya rabuwa da Humaida, yana sonta sa'annan yadda ya dandani wannan daular ba zai yi saken dawowa gidan jiya ba, don me ya sa za su dinga ja masa jafa'i? shin da ma akwai iyayen da ba su son ci gaban 'ya'yansu? Wallahi yanzu na fara son Humaida". Ya fada a fili. Daga nesa suka hanfo Mu'allim ya fito daga mota rungume da wasu takardu, Alhaji Auwal ya dubi Injiniya. "Ya kamata. ka yi wa yaron nan magana ya turo manyansa, ina tsoro kada wani abu ya gilma, saboda mahaifin nan nashi ba shi da dama". 77 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Ni ma tunanin da na ke yi ke nan, amma ina ga yaro ba wani cikakken dangi ne da shi ba, iyayensa duk suna kauye". Alhaji Auwal ya ce, "Duk da haka a bai wa uban hakkinsa a matsayinsa na mahaifi". Shigowar Mu'allim ya katse su, ya durkusa yana gaida su, ya mike zai tafi injiniya ya dakatar da shi. "Lokaci ya yi da ya kamata ka turo magabatanka ko?" "An zo gurin". Ya fada a ransa. "Ka yi shiru, ko akwai wata matsalar ne? Okey, shi ke nan zan je gurin mahaifin naka da kaina na fahince ka, tashi ka je". *** *** *** Sun dade tsaye a kofar gidan kafin su sami yaron da za su tura. Wata yarinya za ta wuce suka kira ta. "Maza shiga nan gidan ki ce ana sallama ada maigidan". 78 31 KA AURE NI=2 ya ce. BILKISU H.MUHD Bayan shigar yarinyar Alhaji Auwal a "Yaro-yaro ne, in ban da Humaida mai za a yi da mutumin da ya ke rayuwa irin ta wannan, don Allah ji wani gida ko Kauye ba karamin matalauta ne ke jure rayuwa a cikin irin wannan gidan ba, gida rube, a lalace, Allah sarki Mu'allim". a "Wai yana zuwa". Yarinyar da suka aika ta idar musu da sakon. Injiniya ya mika mata dari biyu, ta karba tana tsallen murna, eh waye. Ya nufo su cikin rashin gane ko su "Ku ne masu salláma? "Mu ne Malam. Injiniya ya fada. Da sauri ya daga kai ya dube su. "Oho kai ne ka dawo Alhaji Haruna?" dan odlnjiniyasyas yiamurmushi mai ciwo, enwannandtsohon yana tofo shi da jafa'I, ya kanne tare da kokarin danne zuciyarsa, don yadda ya ke jinsa kamar zai shako 'shi.ss 08 79 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Mun zo ba ka hakuri ne da neman iri". "Wannan karon kuma da abin da ka zo ke nan? Aniyarka sai ta bi ka, kuma wannan irin ya fi karfinku saboda dana ba irin 'yarku ba ce". Mu'allim zai shiga gida ya hango su, Ummaki da tsoho suka bayyana a fuskarsa, PYLya so ya yi baya sai dai Malam Musa ya riga ya gano shi cikin kakkausar murya ya kwala masa kira. Ya taho cikin rashin kuzari musamman da ya gano irin kayan da ke jikinsa. Ya siya masa kaya bila'adadin bai san me ya sa ba ya sakawa ba, duk kunya ta kama shi, ya durkusa ya gaida su Injiniya. Cikin daga murya ya ce. "Mu'allim, kafin na dauko wuka ka yanka ni muddin ba ka fita daga shirgin wadannan mutanen ba sai na tsine maka, wallahi ko da za ka tattaro duka mutanen Kano a kan na amince da wannan auren ba zan amince ba". 80 KA AURE NI=2 Ya dubi Injiniya ya cе. BILKISU H.MUHD "Da nawa ne, ni na haife shi, na fi klowa iko da shi, ba zai auri 'yarku ba, in kuma kuna ganin za ku ja mu zuba ku gani... kai shige mu je". Ya finciko Mu'allim cikin zafin rai suka shiga gida. A cikin gida suka maida wa Hajiya Zainab abin da ya biyo baya bayan zuwan su gidan su Mu'allim, hankalin Humaida ya yi matukar tashi, Injiniya ya dube ta. "Kada ki daga hankalinki baby, zan yi amfani da karfin dukiyata don na ga wannan auren ya yiwu. Yanzu na fi ki bukatarsa". Hajiya Zainab ta ce. "Yana ikirarin ya fi kowa iko da shi har yana cewa ku zuba, Alhaji ya kamata ka nuna masa kudi na maganin komai”. Ya yi murmushi, ya cе. "Ban taba ganin kazamin matsiyacin talaka irin wannan dattijon ba, sai dai har -81 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUND gobe ina tunanin me ya taka, domin ko kadan ba shi da tsoro". Alhaji Auwal ya ce, "Da me ya ke takama kuwa in ban da tijara? Jira ya ke kawai ka taba shi ya bingire salon ua jaza mana bala'I". Gabadaya suka tuntsire da dariya. "Burinsa mu rabu da yaronsa". Injiniya ya ce, "Ai ba zai yin wannan saken ba, Zainab yaron nan bai yo jinin ubansa ba, yana da kashin arziki, tunda ya soma aiki a kamfani na ke ganin ci gaba". fadin. Alhaji Auwal ya amshi maganar da "Haka ne, shi ya sa na ke so mu bi ko ta wace hanya don mu mallake shi, ka ga zamowarsa sirikinmu shi zai ba mu damar yin hakan, inya so mu ga mai iko da shi tsakaninmu". "Amma Auwal kana ganin aure zai yiwu ba tare da sa hannun iyaye ba?" "Ka bar komai a hannuna" 82 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Duk wanda ya kwana ya tashi a unguwr su Mu'allim ya san halin mai unguwa yana da matukar son bin duniya, in ma bai fahinci kana da shi ba sam ba ya hada hanya da kai. Yana da son karya ga hadama da zakin bakiduk lokacin da aka ce ana sallamada shai sai ya tura yararea 3 gano mai kiranda alama yana da mauko ko ya ku bayi ne, yau da gobe ta fi karfin wasa, da zarar ya yi baki yaran har sun sanin ba su ga alamar danshi ba da kansu suke cewa, Abbansu ba ya nan kafin ma su sanar masa saboda su sani ba fitowa zai yi ba. Yana zaune yana cin naman kaza gasasshiya, daya daga cikin yaransa ya shigo gida da gudu ya zube a gabansa yana faman haki, ya ma kasa magana. "Jabiru mai ke faruwwa haka? Wa ya biyo ka?" Mai unguwa ya tambaya. Yana haki ya ce, "Bako kayi Abba a cikin wata katuwar mota". 83 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ai tuni ya tura naman gefe ya mike bai jira karin bayani ba, takalmi ma da ya saka wari da wari ne, sai matarsa Binta ce ta lura tana kiransaya zo ya sake, ina bai bi ta kanta ba. Akofar gida ya riski Alhaji Auwal, ya mika masa hannu suka yi musabiha, sai fada ya durkusa masa jikinsa har rawa ya ke. "Shigo ciki mana, ai muna da gurin saukar baki". Binshi kawai Alhaji Auwal ya ke da kallo suka shiga wani shago wanda aka shimfida shi da kafet. "Bara a kawo maka ruwa ko?" "A'a mai unguwa na gode, a kan hanya na kee". Cikin nutsuwa ya warware masa abin da ke tafe da shi, mai unguwa ya jinjin kai. "Hakika Musa makaho zai aikata amma ku bar mini komai a hannuna zan same shi ban da tsiya irin tasa kana wannan hali arziki na binka kana gudu? Ji yadda 84 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD yaron nan ke yi musu hidima, billahil azim ba za ka sha Ummaki ba sai in ka san uwar a da ka kuma ganta yanzu ba za ka yarda ita دو ba ce... "Wannan kuma wani abu ne daban, ni dai ka yi mini kokari". Ya sa hannu cikin aljihuya dauko kudi ya kirgo dubu hamsin. "Ga wanan somin tabi ne kafin mu ga yiyuwar abin". Ya dade yana samun tukwici da kyautuka amma bai taba samun kamar wannan ba, godiya ya dinga zumbuda masa. Sun rabu da sharadin zai dawo bayan kwana biyar, ya raka shi bakin motarshi yana wani takun takama da jin kanshi shi wani ne, ko ba komai ganin wannan hamshakin zai sanya jama'a su fara kiyayarsa. Yana son hulda da irin wadannan ko da ba za su ba shi rakan na kore yawa ba. Ai kuwa Alhaji Auwal na jan motarsa ya yi 85 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD kwana zuwa kofar gidan Malam Musa, daga kofar gida ya dinga kwada sallama. Ya gane waye da sauri ya fito. "Yallabai da kanka ai da sai ka turo ni na zo". Mai unguwa ya cee, "Komau kamawa ya ke yi". "To ina zuwa. Komawa ya yi ciki ya dauko tabarma ya dawo, ya shimfida masa suka zauna suna kara gaisawa. Mai unguwa ya ce. "Kai Malam Musaya ya abin da a ke nema ya tarar da kai har gida ka yi wa Ubangiji butulci?" "Ban fahince ka ba". Ya ce da shi. "Wannan attajirin Injiniya Sunusi suka zo mini da maganar yaronka na soyayya da 'yarsu... Da sauri ya katse shi. "Oho ta nan kuma suka billo? To bari ka ji mai unguwa, ina ganin kimarka don 86 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Allah don Annabi kada ka sa kanka cikin wannan maganar". "Malam Musa me ya yi zafi? Ban san ka da kafiya ba, a sanina kai mutum ne adali mai saurin fahinta tunda yaron na son yarinyar mai ya sa za ka ja da yin Allah? In fa ka ce za ka ci gaba da kafewa sai rabo ya kashe ka". "Bari ka ji mai unguwa, wallahi mutuwar za ta fi yi mini kwanciyar hankali a kan yin wannan aure". "Ya ilahi, shin Malam me ya yi zafi haka?" "Ka ga mai unguwa, yaro dai dana ne na ce ba zai aure ta ba, ka gaya musu wannan naci har ina?" Lallashi da ban bakinsa bai sa ya rusuna ba, karshe suka rabu baram-baram. Ya zauna a kofar gidansa yana huci, ba zai bari wannan arzikin ya wuce shi ba. Ya mike zumbur ya nutsa cikin unguwa yana neman Mu'allim har bayan 87 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD magriba babu shi, karshe ya je ya nemi guri a kofar gidan Malam Musa inda ya cі alwashin sai ya gana da Mu'allim yau komai dare. Bai shigo unguwar ba sai karfe tara da rabi, ji ya yi ana kwala masa kira, ya karasa inda ya ke jin muryar, da sauri ya risina yana gaida mai unguwa. "A kan maganarka da 'yar gidan Injiniya Sunusi ne, shin me ke faruwa, mai ya sa mahaifinka ba ya son ci gabanka? Shin ba ka sonata ne? Ka yi mini magana ta yadda zan fahince ka, na san yadda 6illo wa mahaifinka". "A kwanakin nana bin da na sa a gaba ke nan don na fahintar da shi, amma ya ki ganewa ban san mai ya sa ya hana lamarin nan ba, da ban sonta da na hakura da ita". "Lala kada ma ka soma, Malam Musa tunaninsa ya tafi, ba ka ganin girma ya kama shi, duk mutumin da ya kai wannan munzalin sai hakuri don tamkar mahaukaci 88 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ya ke zamowa, ka

Chapter 3 of 5