Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 5
bari ai ni ma tamkar mahaifinka na ke, ni ne shugabanku, zan iya jagorantar komai a kan jama'ata. Wannan hargagin nasa na dan lokaci ne, da zarar an kwana biyu da kanshi zai sauka". Ya ji dadin bayanin mai unguwa sosai, bai taba yin tunani a kan maganganun mai unguwa ya ji yana yi don shi ma har kyauta ya yi masa. Bayan kwana biyar Alhaji Auwal ya sake dawowa a gidan mai unguwa sun dade suna tattaunawa da kwana biyu da rabuwarsa ya sake komawa gurin Malam Musa. "Malam Musa kada ka tauye wa yaro rayuwarsa don kawai kana mahaifinsa in ka yi haka ba ka yi masa adalci ba, yadda yaron nan ke maka biyayya bai kamata a ce ka yi biris da abin da ya zo da shi ba. Na kira yaro mun yi magana, ya nunan yana kaunar yarinyar". "Hakan ya ce maka?" "Kwarai kuwa". 89 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "To shi ke nan tunda haka ya ce ka yi masa ja gaba, amma ni kam in dai ni ne har abada". Mai unguwa ya yi dariya. "Tunda kai ka ba ni amanna zan yi י5 hakan, ai da na kowa ne. Hannu ya sa cikin aljihu ya dauko kati ya mika masa. Cikin rashin fahinta ya tambaya. "Me ye wannan?" Mai unguwa ya ce, "Katin daurin auren dan namu ne "Na yafe, ka rike kayanka Ya mike ya shiga ciki "Yau ni na zamto abin wolintarwa da wulakantawa a gurinka? Ni za ka tozarta ashe da ma ban isa da kai ba? To shi ke nan ka je ka yi, amma Allah ba zai bar ka ba. Bakin cikin da ka dandana mini da yardar Allah kai ma sai ka dandana" Mu'allim zuciyarsa ta soma karaya, amma son da Ubangiji ya jarrabe shi na 90 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Humaida yana jin in ya rabu da ita ba zai sake moruwa ba. "Abba ka yi hakuri, na ce ka gaya mini abin da suka yi maka ka ki ba ni hujjar da in na rabu da shi zan bayar inda ka gaya mini da.lili sai na sami madogara". Malam Musa ya harzuka sosai idanunshi sun kada sun yi jajir. "Ba zan gaya maka dalili ba, ka je ka aure to amma albarkar da ke cikin aure ba za kme shi ba". ra mike yana sharar kwalla ya fita. Shin mai ya yi zafi Abbansa na kuka abin da bai taba gani ba a rayuwarsa, duk jikinsa ya gama yin sanyi, sai dai har lokacin yana kan bakansa ko Hajara bai nema ba ya fita. *** *** *** "Adnan kaina ya kulle, ina tsoron Abba ya ambata mini abubuwa da yawa, yana gaya min magana mai kama da tsinuwa. Na rasa ya ya zan yi, yau Abba 91 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD kuka ya yi ban san mai mutanen nan suka yi masa ba, da zan iya da na rabu da Humaida, sai dai ina matukar sonta, ruhin soyayyata yana hannunta ka gaya mini ya ya zan yi?" "Yadda za ka yi kawai ka rabu da ita". Wani abokinsu ya fada, Adnan ya kalle shi. "Wai kai Ahmad me ye haka? Wannan ai nuna bakin ciki ne kuru-kuru, in da za ka sami irin wadannan su ce suna sonka kai ma so za ka yi". Ahmad ya ja tsaki ya се. "Irin wadannan idan za su kwanta in dinga taka su ina wucewa ba zan aure su ba, domin na san kwadayi da buri ne, kuma akwai nadama a cikinsa. Yarinyar da ba ta da cikakkiyar tarbiyya, su kansu iyayenta ba ta girUmma su..." "Wa ya gaya maka, ko da ma zama ku ka yi kuna gulmarsa a cikin unguwa?" Shi dai Mu'allim ya sa musu ido kawai yana jinsu, Adnan ya dube shi. 92 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Wallahi Ahmad yana daya daga cikin mahassadanmu, duk mutumin da bai yi maka murna ba makiyinka ne yana bakin cikin ka yi masa nisa za ka hau mota mai tsada, za ka shiga gida mai kyau, za ka yi harka da manyan mutane ai ba damuwa tunda tana sonka za ka iya sarrafa ta ta daina abin da ta ke yi". Mu'allim ya gamsu da maganganun Adnan ya kalli Ahmad yana son gamsar da shi, ya ce. "Wannan abubuwan da ta ke yi duk zan san hanyoyin da zan bi na sarrafa ta ta daina". "D Allah abokina kyale shi duk abin da ya ke yi kyashi ne da hassada". Ahmad ya mike, "Na ga zancen nawa ba za ku fahince shi ba, kun dau zafi da yawa, sai an jima". Ya dubi Mu'allim, "Ranar da nadama ta zo maka ina nan ina jiranka". 93 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Mu'allim na ga ka yi shiru tunanin me ka ke yi, kar fa ka dauki zancen wannan dan bakin cikin. Ka nutsu mu tsara yadda bikin zai tafi". *** *** Har ta iso gare shi ba tare da ya lura ba, gabadaya ya nutsa cikin tunani ta kai hannu tana shafa masa fuska. A hankali ya dago kai wani kamshi ya shaka, ya dora hannunsa a kan nata. Sun dade a haka, ya lumshe ido. "Humaida ina sonki, na ba ki duniyata". Ta yi murmushi kawai, ya zare hannunta daga fuskarsa. ki ba". "Yau ki ce mini kina sona ba in aure "Sau nawa ina ce maka aure shi ne gaba da so?" 94 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ya ce, "Na sani, amma furta ina sonka a gare ni zai haifar mini da wani yanayi mai dadi". "Uhm, amma ka san me?" Ya kada kai yana kallonta. "Mun dace da juna, ina alfahari da samun kyakkyawan mutum kamarka, ka gaya mini za mu dauwama da kai har Karshen rayuwa?" "Haka na ke bukata”. "Kuma ka san me? Zuciyata in ta dokanta da mutum na sati daya ne zan so abu kamar hauka, amma ba za mu yi cikakken wata ba abin zai fice min, sai dai kai na daban ban taba gajiya da ganinka ba, yau ga shi ka aure ni na gode da cika alkawari da ka yi min. mom ta shirya dinner har kashi uku ta ce duk za ka halarta, da fatan ba za ka ba da matsala ba? Ga kuma wannan kudi ne masu yawa duk sun ishe ka ka yi abin da ka ke so daga bangarenka, ka yi shiru kana kallona". 95 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Humaida ina tunani ne, ina tunanin ranar da zan dauke miki dawainiyata, ina son a ce yau ga shi ke ma kina alfahari da ni zan so a ce ke ce za ki sami duk wadannan abubuwa daga gare ni. Ina jin kunya duk lokacin da ki ka yi mini wata kyauta..." Ta katse shi, "Anya kuwa za ka ga wannan ranar don ina ganin ba za ka taba yi mini wata kyauta da ba a yi min ba, ba za ka taba yi mini abin da za ka burge ni ba. Duk abin da ka ke sa ran za ka yi min ina da shi, an taba yi mini. Dukiyar Dad yana nema ne saboda ni, a ka ke nan a karkashinsa don haka ka daina wannan tunanin, har abada kana a kasanmu". Ta dube shi tana murmushi, sakonta ya cika can cikin kwakwalwarsa har yana son tuna inda ta dosa... ta katse shi. "Babban abin da za ka faranta mini da shi, ka yi hakuri da ni, ka faranta mini ka da ka tada kosawa da ni, shi ne kawai". Ta riko hannunsa. 96 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Taho mu tafi gurin Momy za ku yi magana Tunda ya gaida ta ya ji ta amsa a ciki ya san sako ya isa gare ta, ba ta bukatar karin bayani. Ya sa hannu cikin aljihu ya dauko bandir din naira dari bibbiyu ya ajiye a gabanta. su". "Na me ye?" Ta tambaya. "Kudin da za ki yi na ki hidimar da Ai gabadaya ta suri kudin ta cilla masa cikin muryar kuka ta ce. "Mu'allim me ke damunka ne, ko me za ka samu a duniyar nan a bayan albarkar iyaye ya ke, anya ma kana son ganin da kyau kuwa? Kada ka bari fushin zuciyar mahaifinka ya kama ka, ka kwadaitu da neman albarkar addu'ar iyayenka, ka ji tsoron muguwar addu'arsu a kanka, domin kuwa kibiya ce da ba ta kuskurea. Ya kamata ka nutsu ka yi nazari". 97 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "To Umma na ce masa ya sanar da ni abin da suka yi ya tsane su haka ya ki, ya ku ke so na yi? Ina sonta in na rasa ta mutuwa zan yi". Ya fada a kufule. "Shin ke ma kina goyon bayan Abba ne? ke ce ya kamata ki fahince ni, amma ke ma kin kI". Duban Ummaki ta ke masa. "Tir da yaran zamani, tir da yaro irinka". Ta kada kai, ta kuma sanyaya murya, ta ce. "Dukkan zunubai Allah yana jinkirtar da su zuwa ranar alkiyama amma ban da cutar da iyaye, Yana gaggauta sakamako ga mai yin shi tun a nan duniya kafin mutuwarsa, ka ji tsoron Allah, ka ji tsoron faduwar masiba a akanka, ka lura da abin da ya faru ga masu cutar da iyayensu, wadanda suka gabace ka, kada ka maida kanka abin izina ga sauran jama'a, ka dubi irin annobar da ta lalata karshen rayuwarsu, ka dubi 98 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD yadda suka shuka tsiya suka cutar da iyayensu amma daga baya suka girbi kavar hasara da da na sani a hannasu 'ya'yan..." "Wai Umma me na yi ne? A karo na biyu ta sake duoansa cikin Ummaki, ashe wannan nasihar bai risinar zuciyarshi ba, lallai Mu'allim ya yi nesa. "Ba ka yi komai ba, babu abin da ka yi, wannan kudin ka diba ka kai ma mai unguwa tunda shi ya tsaya maka ku yi taron naku a can". "Umma!" Ya kira sunanta. "Haka za ki yi mini, in Abba ya ki ai ke mahaifiyata ce, a tunanina ba za ki wofintar da ni ba, kada ki yi mini haka, in kina tsoron Abba ne, ni zan dauke ki in nema miki wani gidan, kuma..." Ta daga hannu a zafafe ta tsinka masa mari. Cikin daga murya ta ce. "Mahaukaci, shashasha wanda bai gaji mutunci ba, Mu'allim ina tantama a kanka, 99 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ina tantama ma kai ba jininmu ba ne, kа tashi ka fita yau na tsane ka! Na tsane ka! Ka dauki kudinka ka fita". Ta dauki muciya ta yi kansa, da sauri ya dauki kudin ya yi waje. Bai zame ko ina ba sai gidan mai unguwa wanda ya riga ya zamo dan gidan don ko ba shi da shamaki da gidan duk lokacin da ya zo kai tsaye ya ke shiga. Mai unguwa ba ya nan sai matarsa yanayin da ta ganshi a ciki ne ya sa ta soma tambayarsa, bai 6oye mata komai ba. "Yanzu kai wannan shi ne ya sa duk ka fice a hayyacinka. Yanzu fa lokaci ne na farin ciki, ka kyale Umma, duk abin da kа ga tana yi ba yin kanta ba ne, Malam shi ya assassa komai, domin bai barta haka ba, ni na san komai, kafe ta ya yi a gidan babu wanda bai san wannan ba, don haka ka yi mata uzuri, yanzu ni zan tsaya maka ba ka da matsala duk abin da za a yi na hidima ni 100 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUND zan yi, zan kuma yi wa mai unguwa bayani Ya mika mata kudin hannunsa. Ta daddage ta rangada guda, tana ci gaba da zuga shi. "Ai muna nan da kai, Malam Musa da kansa zai neme ka, ita ma Hajara za ta dawo rakiyarsa, ka rubuta ka ajiye". Kullum abu na matsowa kusa, yau ga shi an wayi gari gobe za a daura aure duk gidan rediyon da ka kunna sanarwar daurin aure a ke, unguwa gabadaya ta dauka. Ango kai ya dau zafi in ya fita tun safe sai kwanciyar bacci, yana yawon raba aibi, sai yau ya sami damar ziyartar gidan da za su rayu a ciki shi da Humaida, ganin gidan ya gigitata tunaninsa, ya mantar da shi duk wani bakin ciki da ke karkashin zuciyarshi. Yanzu ne ya ke jin shi mutum ne. Yana zaga ko ina na gidan cikin Kasaita kansa ya gama kumbura, yana 101 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD rayawa a ransa duk mutumin da ya ke daure mishi gindi a kan wannan lamari ya zamo babban makiyinsa, to in haka ne iyayensa fa ya matsayinsu ya ke? Ya tambayi zuciyarsa, ya yi saurin kawar da wannan tunanin. Kayan da a ka zuba musu odarsu aka yi daga waje, ga masu gadi da masu yi musu wanki da guga duk sun gabatar da kansu gare shi, haka ya baro gidan cike da matsanancin farin ciki. *** *** *** gefc. "Hajara ina ki ka shiga?" Hajara ta fito daga bayi ta aje buta a "Malam ya na ganka da jaka?" A raunane ya ce, "Tafiya zan yi, ki kula da Kawu Yusuf ki dinga ba shi abinci a kan lokaci". Ta fara kuka, "La'ilaha illallahu, yau na ga ta keina, Malam in ka zauna akwai 102 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD wanda zai tursasaka ya ce sai ka halarci daurin auren nan?" "ki yi hakuri Hajara, kin ga gobe za a daura auren, jibi sai na dawo, muddin, na zauna akwai wadanda za su tursasa ni a kan halartar daurin auren, ni kuma zan ji kunyar gardama a gare su". "To yanzu ina ka nufa?" Ya ce, "Rano na nufa, na ji rade-radin za a yi taron bikin a gidan mai unguwa ban yarda ma waņi nawa ko naki ya taka gidan ba, ina kara gargadinki kada na ji labarin kin je in ko kin je kada ma ki dawo mini gida, ki yi SABI ZARCE kawai". Har Malam Musa ya jima da fita tana zaune tana faman kuka. Sallamar mutane ya sanya ta,saka wa zuciyarta lisilama, kowa ya shiga sai ya tambaya wai bikin Mu'allim ake yi amma ba a gayyace su ba? Ita kam sai ta rasa abin cewa, sai kawai ku yi hakuri ta ke cewa. 103 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Haka mata suka dinga sintiri ta san tsegumi ne ke kawo su, karshe gajiya ta yi ta kulle gida duk wanda ya zo sai ya yi zaton ba ta nan. Shi kam Mu'allim gabadaya ya ki zuwa gidan duk wasu shirye-shiryensa a gidan su Adnan ya ke yi. Washegari abokanansa suka hadu a gidan Mai unguwa daga nan motoci suka dinga dibarsu zuwa gidan Injiniya, mai unguwa ya yi amsa wakilci aka daura aure a kan sadaki naira dubu dari hudu wanda Alhaji Suwal ne ya ce ya dauki nauyi. Bayan an daura aure abokan ango suka wuce country mall walima, an ci an sha, kudin da aka kashe ya tsone wa kowa ido, haka aka fashe ana yi masa sam barka. Washegari unguwa ta dinke mutane cike a gidan mai unguwa, makada kala-kala, kowa ya yi Ummakin wannan al'amari, sanin halin mai unguwa ne ya hana kowa furta nasa batun. 104 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Bayan sallar magriba aka sake haduwa a wani katafaren gida inda Hajiya Zainab ta shirya nata dinnar, wai ba na kowa da kowa ba ne, sai masu ido da kwalli, sai kuma abokanan ango. Hajiya Zainab ba ta ji kunya ba ta ja hannun ango suka shiga filin rawa guri ya dinke da shewa, shi kam Alhaji Sunusi dolas ya dinga kika musu, shi ma babban amini ya shiga lika 'yan dubu-dubu, daga nan sai abokan ango suka shiga suna yi wa ango kara da dari biybbiyu, masu karfin halin ciki suka dinga likawa. Sai karfe goma sha biyu na dare taro ya watse. Washegari ma wani bikin akа tashi da shi a gidan Alhaji Sunusi, daga gefe Mustapha ne ya hangi Mu'allim da sauri ya nufo shi, ya mika masa hannu. "Ina taya ka farin ciki da auren kwadayi, wanda karshensa nadama ce za ta biyo baya". 105 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Da sauri ya zare hannunshi daga cikin nasa, "Kai ma?" Ya tambayi kansa wanda a tunaninsa a zuci ya yi maganar, yayin da a fili kuma ya ambata. "Ban fahince ka ba, kuma waye kai?" "A hankali wataran za ka gane waye ni, amma a zahirance kana da kirki, ina yi maka kyakkyawan zato, akwai kamala a tattare da kai, ga ka ingarman namiji, duk wanda ya dube ka zai yi maka kallon jarumta, in ko haka ne lallai abin ba a jiki ya ke ba". Kansa ya kara daurewa, zai sake magana Mustapha ya bar gurin, duk sai jikinsa ya yi sanyi. "Ina son Humaida, zan bai wa kowa Ummaki, zan jure duk abin da zai biyo baya". Yanayin da ya tsinci kansa a ciki bai barshi ya shiga gidan ba, komawa ya yi gida ya dade tsaye a kofar gidansu yana tunanin 106 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD yadda zai fuskanci iyayen nasa. Karshe ya juya ya sani yanzu suna cikin fushin zuciya. A can shagon gidan su Adnan sun dukufa shi da abokanshi suna faman kwantar masa da hankali, saboda yadda zuciyarsa ke yi masa kwan gaba kwan baya, gabadaya ya birkice musu da fadin, yana jin fasa auren zai yi saboda har yanzu babu wani sauki daga bangaren iyayenshi. Hajiya Zainab ce ta kira shi a waya, tana cewa za ta wuce da amarya ita da Alhaji Sunusi, ruwansa ne abokansa su yi masa rakiya... Ya katse wayar cikin 6acin rai yana yi wa Adnan bayani. "Ka tashi ka je abokina, kai ma ba ka bukatar rakiyar kowa, ka saki ranka wannan rana na da matukar muhimmanci a gare ka, wannan rana na daya daga cikin ranakuln farin cikinka. Da zarar ka ayi tozali da ita za ka mance duk wani bakin cciki. Ina yi maka fatan alheri". 107 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Wannan karon ma bayan ya bar gurin kofar gidansu ya koma ba tare da motarsa ba. Ya dade a tsaye kuka ya ke yi sosai yana kallon lokacin da Abbansa ya fito daga gida ya zauna cikin rafka tagumi cikin 'yar kuka tamkar yana a gaban Abban nashi. "K yafe mini, wannan aure mukaddeti ne kada ka zarge ni. Babu yadda ban yi don na tirsasa zuciyata akan bin umarninka ba amma na kasa, ji na ke yi tamkar rayuwata na hannunta ne". Da sauri ya juya yana sharar hawaye. GIDAN AMARYA Lokacin da suka isa gidan da ita lallashinta suka dukufa yi, saboda tsananin kukan da ta ke yi har ta sanya Hajiya Zainab kuka. Ta rike ta tamau wai ita ba za su tafi ba, a al'adance duk yarinyar da aka kai gidan miji sai iyaye sun yi mata nasiha yadda za ta bi mijinta, da yadda za ta ja 108 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD dangin mijinta a jiki, ita kam maimakon haka ita nata fadan shi ne. "Humaida son da muke yi miki ne ya sanya muka bari ki ka hada jini da talaka mara galihu, don mun aura miki shi ne ba mu amince ki bari ya raina ki ba, muna son ki dinga nuna masa ke ce sama, ba mu laminta ki saki jiki da 'yan uwansa ba a yi miki zugar dangi a cika miki gida da 'yan ba ni ba ni. In muka ji labarin wata mu'amala da hada ku da su za ki hadu da fushinmu. Daga karshe gobe za mu turo kuku, aikinsa girki da gyara miki daki, Allah ya sanya alkhairi". Suka mike za su tafi ta sake rungume ta da kyar suka lallaßata Injiniya Sunusi ya се. "Zamanki cikin gidan yau da gobe ne kawai zuwa jibi, hijabinki a yaye ya ke, kina iya fita ki je duk inda ki ke so, ki yi hakuri babyna, ban so kunshe ki a gida ba, sai don hakan ya zama dole". 109 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Yana maganar yana sharar hawaye, ta kada kai suka fita. Bathroom ta shiga ta yi wanka, ta zauna a bakin madubi tana shafe jikinta da turaren shu'umin humra, ta mike ta bude akwatin da aka zubo mata kayan bacci a ciki, riga ta dauko da wando ta saka, rabin cinyarta ba su rufe ba kayan masu sharashara kana ganin duk wani abu da ke jikilnta, ta koma ta kwanta a gado, bacci mai nauyi ya dauke ta. Karfe goma ya iso gidan maigadi ya risina yana yi masa sannu da zuwa, sai da kya yi tafiya mai dan nisa ya isa harabar gidan da ledoji rike a hannunsa. Ya dinga sallama yana kara yaba yadda gidan ya tsaru a zuciyarsa, ga wani kamshi mai dadi da gidan ke yi. Sai da ya kara zagaya gidan sannan ya nufi sashin da bedroom ya ke, ya san amaryar na can. A hankali ya ke tafiya, 'a wani kayataccen falo ya ganshi, wanda 110 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD bedroom din ke manne a jikinsa, kai tsaye ya nufi bedroom ya kutsa kai. Arba ya yi da ita ta yi shame-shame tana faman bacci abinta, shigar da ta yi ne ya tilasta masa saurin dauke kai, wannan wayewa ce ke nan? Abin da ya sani ko kuma na ce a al'adance lokacin da ango ya shigo dakin amarya zai tarar da ita a suturce cikin lullubi ko da idonta ba ta bari a gani. Ya kada kai kawai a hankali ya dinga kiran sunanta. Ta yi wani mika tare da wani irin juyi tamkar tarwada, da sauri ya kawar da kai tare da lashe lebe, wani irin yanayi ya ji shi a ciki. Ta mike zaune tana mutsika ido, ko kadan babu alamar kunya a idonta, ya kawar da kai. Ta sake wata mikar tare da hamma. "Yana daga cilkin al'adata, in na yi bacci ba a tashina, mancewa na yi ban sanar da kai ba". 111 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Yadda ta ke magana cikin murmushi ne ya zaci ko zolayarsa ta ke yi. Ya koma ya zauna a kusa da ita yana satar kallon kirjinta wanda ya fi komai daukar hankali. Ya shiga bude ledojin da ya shigo da su. "Na sani kacaniyar biki bai bari kin ci komai ba”. "Wa ya gaya maka? Ai ni ko a ina ba na sake da cikina". Ya jinjina kai. "Kin kyau mana, amma kin san wani abu?" Ta kada kai kawai. "Jina na ke yi na fi kowa sa'a a duniya. Humaida ina matukar sonki, ba zan iya rayuwa ba in babu ke". "Mu'allim kana burge ni don haka na zabi na yi rayuwa da kai, za mu zauna lafiya in har za ka bi ni babu mai jin kanmu". 112 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ya yi murmushi kawai har yanzu akwai kuruciya a tattare da ita. Ya maida kai jikin agogon da ke manne jikin garu. Karfe goma sha daya, ya mike. "Ya kamata mu raya wannan dare wanda na lakaba wa FARIN DARe, wannan dare yana da matukar muhimmanci a gare mu, bismillah taso ko". Ya karasa zancen cikin tattausan murya. "Abin da na sani angon da ke son kusantar matarsa shi ke umartarta da ta yi alwala don nuna godiya ga Ubangiji, da kuma fatan samun zama na gari". "Ni kam a sanina ban yi wannan aure don ka mallaki jikina ba". "Me ya sa?" Ya tambaya cike da zulumi. Ta ce, "Saboda cewa na yi kawai KA AURE NI, kuma ka aure ni saboda kana burge ni in sanya ka a gaba ina kallo wannan ne burina” 113 KA AURE NI=2 Mamaki ya kasa barinsa. BILKISU H.MUHD "Humaida!" Ya kira sunanta can kasan makoshisa. Da sauri ta dakatar da shi. "Please kada ka kawo mini kitabul ra'asi, babin glo da MTN ko ka taba jin na ce ina sonka?" Bai gama mamaki ba ta dora da fadin. "In ka fita ka turo min kofa, akwai dakin da aka ware musamman don kai" Ta juya ta kwanta. Humaida ce kuwa? Anya wannan Humaidarsa ce? Ya shiga zargi ko iskokai ne suka shige ta, ko kuma tana dan taба shaye-shaye ne? Zai yi mata uzuri zai kyale ta zuwa lokacin da za ta dawo daidai. Ya juya ya fita cike da tsananin tashin hankali. Cikin damuwa ya ke faman kai komo, ya koma ya zauna yana jin kansa na wani irin sarawa tamkar zai tarwatse. Ya sake mikewa kai tsaye ya nufi dakin da Humaida ta ke ya tura. Gam ya ji shi a kulle ko 114 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD motsawa ba ya yi. Ya koma ya mike a kan doguwar kujera ya daga kai yana kallon agogon da ke manne a jikin bango. Karfe uku, zuciyarsa ta shiga bugawa tunda ya ke bai taba ganin inda aka yi haka ba, kalaman Abbansa ya shiga dawo masa. "Ka je ka yi auren, albarkar da ke cikinsa ba za ka samu ba!" Zumbur ya mike cikin faduwar gaba tamkar wanda aka yi wa allura. "Azzaluma ce!". Ya sake tunowa a karo na biyu. Ya shiga zarya lokaci guda ya ji kamar an doddoke masa hakarkarinsa, kafafunsa sun gaza daukarsa, gabadaya ya zube, a kan doguwar kujera yana maida numfashi da ido jajir. Bai san iya tsawon lokacin da ya dauka a gurin ba, ji ya yi ana kwankwasa get, da sauri ya daga kai ya dubi agogo, karfe bakwai saura minti goma. Ya mike cikin rashin walwala. 115 KA AURE NI=2 "Waye?" Ya tambaya. "Ni ce". BILKISU H.MUHDYa dan yi jum, muryar namiji ne babu isasshiyar Hausa, ya ce. "Kai wa?" Ya ce, "John". Ya kai hannu ya bude get, ya yi arba da wan Raton mutum, murdadde yana sanye da riga da gajeren wando, hannunsa rike da faranti dauke da kwanuka a ciki. .Kan Mu'allim ya daure, fuska ya faffake, cikin kaurara murya ya сe. 2 "Lafiya?" "Ke ne majin ogana? Alaja ne ta turo ni, ni ce zan dinga yi ma Hajiya aiki". Ya fada cikin gurbatacciyar Hausarsa mara dadin sauraro. A zafafe Mu'allim ya karbi farantin hannunsa. "Ka koma ba ma bukata". 116 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Humaida wadda ke tsaye a bayansa ta gama jin duk abin da ke wakana, ta ce. "Me ya sa za ka ce haka?” Ya ji muryarta, da sauri ya juyo tana sanye cikin wasu makalallun kaya riga body fitted da wando iya gwiwa ya kama sosai, ta ci gaba da fadin. "An taba rayuwa babu tsaftace gida in ka ce ba ka bukata kai ne za ka yi? Don ka san ni babu abin da zan daga a gidan nan, ina gida ma ban yi ba balle yanzu da na sami gashin kaina". Ta maida kallonta ga John ta ce. "Welcome, come in. Ya ko wuce yana fadin. "Thank Madam, amma this your ago is not good". "Don't mind". Ta ce tana murmushi. Mu'allim ya yi mutuwar tsaye, ba ta bi ta kansa ba ta rufa wa John baya. 117 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Humaida kin sauya mini, kin shammace ni, ganin komai na ke tamkar a mafarki". Ya fada a zuci. Kwana biyu bai shiga shirginta ba, tunda ya lura da take-takenta ko kadan bai ma cika zama a gidan ba. Hutun sati daya da man ya samu a gurin aiki shi ke nan bin gidajen abokai ko ya je ya zauna a bakin get daga waje. Daga gidan su Yusuf ya dawo a gajiye ya riske ta kwance a kan doguwar kujera tana bacci, jarida kife a ruwan cikinta. Ya dube ta kurum ya kawar da kai, ga wani irin sonta a can karkashin zuciyarsa. Sashinsa ya ke kokarin shiga ya'ji motsi a can cikin uwar dakinta, kai tsaye ya nufi gurin. Ya daga labule, John ya gani yana gyaran gadon madam din tasa. Cikin wani mugun tashin hankali bai san sanda 118 KA AURE NI=2 BILKISU M.MUHD ya ci kwalarsa ba, ya fidda hannu ya tsinke shi da mari, cikin daga murya ya ke fadin. "Ashe kai dabba ne, mara hankali, waye ya ba ka izinin shiga dakin nan? Iyee waye?" John ya yi wuki-wuki da ido cikin rawar murya ya cе. "Madam ne ya ce na cala mata daki". Ya kara shako shi ya janyo shi

Chapter 4 of 5