Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 5
mu ci gaba?" Ga Ummakinsa kwalla ya gani a fuskarta, ba ta ce masa komai ba, a sanyaye ta soma tafiya har ta isa ga motarta ta shige, ta tayar. Yana kallonta ta tafi, duk sai ya ji ba dadi, so bai ce haka ba, ya yi mata abin da bai dace ba ko a musulunce. Ta yi juriyar kula shi, ya kyautu shi ma ya kulata, ya bi da ita ta sigogi masu kwantarwa ya nuna mata illolin da ke tattare da ita ba ta wannan hanyar ba. A can gida kuma abin da bai sani ba, a gaban idon Hajara ya shiga motar Humaida, tunda ta ga haka zuciyarta ke mata zafi, ta kasa zaune ta kasa tsaye, abubuwa kala-kala ta ke ayyanawa. Ta gama cika wa Malam baki, ta gama alfahari da cewar Mu'allim ba zai ba su kunya ba, ga shi tun kafin a je ko'ina ya nuna musu halayen zamani, shin ina Mu'allim ya kai tarbiyyar da ta dade tana ba shi? Ina ya kai ladabin da kowa ke yabonshi 26 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD a kai? Ina ya kai kunyarsa da halin da ya tsiro da shi? Ba ya cikin halin kamammun yara... "Assalamu alaikum". Mu'allim ya shigo cikin sallama. Kallo daya ya yi mata, yanayinta gabadaya ya nuna tana cikin matsanancin damuwa. Gabansa ya fadi, jikinsa ya ba shi lallai ta ga zuwan Humaida, musamman da ya ga ba ta amsa masa sallamar tasa ba. Sum-sum ya nufi kofar dakinsa. "Na gode wa Allah, a duk yanayin da na gan ni a ciki yadda na ke ganin ina sha'awarsu ni ima haka wasu ke ganina su yi sha'awar irin tawa ni'imar, burina a kullum shi ne Ubangiji ya kara mini wadatar zuciya". Ya san da shi ta ke, don haka ya dakata ya tsaya kurum. Ta dube shi cikin daure fuska, ya dago kai suka hada idanu, ya yi saurin dukar da kai. Ta ci gaba da fadin. 27 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Duk lokacin da na tsaya a gaban Ubangijina dukiya ita ce koma bayan abin da na ke roka a gurin Ubangiji saboda na gaskata cewa, rashinta ya fi samunta kwanciyar hankali. Ku san duk wanda ya ke kokarin ya same ta har abada ba za ka raba shi da bin kazaman hanyoyi da aka haramta ba, karya, ansar haram da zamba gami da hanci da dogon buri, wanda har abada ya ke hana shi godiya a kana bin da ya samu". Ta yi tattaki ta karasa gabansa ta се. "Mu'allim, da kai na ke, ka sauya daga akidar da muka dora ka, kwadayi da buri karshensu nadama, ka dai bi rayuwa a hankaii". Nan ta barshi tsaye motsi ya kasa yi, wata matsananciyar kunya ce ta kama shi, daga bisani ya sauke ajiyar zuciya ya juya kofar gida. 28 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Kin tabbatar kwatancen da ki ka yi mini daidai ne, kada ki sa ni wahala fa?" "Dad, haka ne mana, amma jikina yana ba ni kamar wani abu zai faru, amma ina son ka sani in har ka sake shawara a kana bin da ka tafi da niyya zan mutu, za ka rasa ni". Ya yi murmushi, ya се. "Baby, shirye na ke na so duk abin da ki ke so". Ta saki wata karar farin ciki. "Thanks Dad". Ya mike yana murmushi. "Zan wuce". "Dad a dawo lafiya". Da sauri ya sake kallonta cikin Ummaki, babu ranar da Humaida ta taba се masa a dawo lafiya sai yau. A harabar gida ya sami Hajiya Zainab ta tare shi cikin rashin walwala. "Shin da gaske ka ke yi, za ka je ka wulakantar da kanka ka nemi a auri 'yarka?" 29 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ya ce, "Ke ce wadda ta kamata ki fi kowa sanin halina, kin fi kowa sanin har abada ba na fatan wata mu'amala ta shiga tsakanina da talaka, ballantana in dauki jinina na ba shi, amma dai ki bari in je in dawo za ki ji yadda muka yi". "Haba ko kai fa, na ji ja'irar yau har a dawo lafiya ta ke maka, maimakon Dad a taho mini da katin waya, a taho mini da biskit". Ya kyalkyale da dariya. "Haka ne, shi ya sa na ke tsoron 95 yaron, lamarinsa azimun ne". A kofar gidan su Mu'allim Malam Musa ne ke ta faman kokawa da Yusuf mahaukaci (Kawu) kokari ya ke ya shigar da shi gida abin ya gagara, duk ya bi ya gama gajiyar da shi, ban da cizo da yakushi da ya sha, Yusuf ya ga in bai yi da gaske ba za a je a sake daure shi, dutse ya dauka ya buga masa a kafa, wata gigitacciyar kara ya saki, bai san sa'adda ya cika Yusuf ba ya 30 KA AURE NI=2 BILKISU N.MUND rike kafar wanda ya ke jinta kamar za ta karuye. Abinka da mahaukaci cikin gidan ya juya. Injiniya Sunusi ya fito daga cikin mota yana hange-hange yana neman wanda zai tambaya, idonsa ya kai ga Malam Musa, ya yi tattaki zuwa inda Malam Musa ke zaune rike da kafa. "Barka da rana bawan Allah". Malam Musa ya amsa ba tare da ya dube shi ba. "Gidan su Mu'allim na ke nema". Sunan Mu'allim da ya fada ya sa shi dago kai. Ya dube shi ya kawar da kai yana kokarin tuno inda ya san Alhajin. Injiniya Sunusi ya kara maimaita tambayar. Malam Musa ya nuna masa gidansa. "What? Kana so ka ce wancan mataccen gidan nan ne Humaida ke gaya mini? Amma Humaida na son tozarta ni!!!" 31 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Furucinsa ya sanya Malam Musa yi masa kallon tsaf, gabadaya yanayinsa suka sauya. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Ya dinga maimaitawa, ya yi kokarin danne 22ciyarsa amma a cikin zuciyarsa yana jin amkar ya makure shi. Injiniya Sunusi ya katse masa tunani. "Ba na jin zan iya karasawa gidan" Ya sa hannu aljihu, dubu daya ya dauko ya mika masa. "Ga wannan, ina son ka je ka yi mini sallama da mai gidan". kai. Bai amshi kudin ba, ya ce. "Ni ne mai gidan!" Ya sake dubansa sosai, yana gyada "Tabbas biri ya yi kama da mutum, yanayinka gabadaya ya nukna hakan. Kai yau na yi mugun gamo, ban da makanta har da talauci? Kai tunda na ke ban taba ganin mutum mara sa'a irinka ba. Da saurinka ka 32 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ke fadin kai ne maigidan ka dauka banza ce ta fadi ko? To ba haka ba ne, tsaya ka ji, zuwa na yi kawai na yi maka akshe di, ka ja wa yaronka kunne in bai rabu da diyata ba za ku karasa rayuwarku a kurkuku, ba zan taba raga muku ba, wallahi ban taba ganin mutumin da na tsana lokaci guda ba sai yau. Ba zan taba raga muku ba". Ya ja tsaki ya juya zai tafi. Malam Musa yana tsaye kawai kamar wanda aka dasa, yana son ya fadi inda ya tsani mutum ya kuma yi masa tunin abin da ya ke tunanin ya manta. Yana son ya tunasar da shi. Addu'o'insa kaf a kansa ya ke karewa, yana son ya gaya masa cewar bai san abin da a ke nufi da kiyayya ba sai a kansa, yana son ya gaya masa bai taba yi wa wani mahaluki mugun fata ba sai shi, yana son gaya masa abubuwa da yawa, yana son sanar da shi da yana da ikon kashewa da ya kashe shi. 33 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Sai dai ta ya ya zai iya sanar da shi duk wadannan abubuwan? Idanunsa suka ciko da kwalla saboda tasowar mikin da ke zuciyarsa ba zai barsa haka ba sai ya gaya masa ko da kalma daya ce don kada ya mutu da bakin ciki. "Ji mana!" Ya ce lokacin da ya ke kokarin shiga mota. Ya dakata da shiga motar yana Kankance idanu jin irin sigar da Malam Musa ya tsayar da shi a matsayinsa na talaka fitik. Malam Musa ya karasa kusa da shi, ya се. "Kafin ka tafi ina son ka sani, Annabawan Allah sun rayu a cikin irin wannan rayuwar talaucin, inda Ubangiji ya so da ya azurta su fiye da kowa ka da ka manta, arziki ya sa Fir'auna, Hamana da Lamarudu suka yi wa Ubangiji dagawa, ka manta ina Karuna wanda shi ma kudi ya saka shi ya yi wa Annabi kazafi ya nutse a 34 KA AURE NI=2 BILKISU N.MUND kasa ko rayuwar wadannan mutanen ka duba hakan ya ishe ka aya, don haka ka ji tsoron Allah..." Injiniya Sunusi ya katse shi ta hanyar daka masa tsawa. "Kai talaka me ka ke gaya mini haka, wa'azi ko maula? To bari ja hu kurwar diyata ta fi karfin taku". Malam Musa ya yi murmushin takaici. "Lallai iska na wahalar da mai kayan kara, kowane mutum burinsa ya hada zuri'a da gidan mutunci ba gidan masu halin dabbobi irinku ba, a kan na hada zuri'a da ku gwara in roki Ubangiji ya kashe dana kafin ganin hakan, yarona mai tarbiyya ne ba irin 'yarka ba, shashasha". Ummakin karfin hali irin na Malam Musa talaka ya hana shi motsi, kallonsa ya ke tun daga sama har kasa yana son ya shake shi, sai dai ya sa a ransa lallai akwai abin da Malam Musa ya taka. Bai iya yin 35 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD kwakkwaran motsi ba har Malam Musa ya shige cikin gidansa. *** *** *** "In har kana son samun albarkata kada na kara jin ka kalli yarinyar nan in har ka sake wata mu'amala da ita ko da ta magana ce ban yafe ba". Yadda ya ga Abban nasa ya birkice ya yi matukar Ummaki ya ci gaba da fadin. "Shekaru da yawa ina zaman lafiya na iya talaucina, don haka babu wanda ya tabа yunkurin wulakanta ni sai yau mahaifinya ya zo ya kare mini cin mutunci wanda babu wani da ya taba yi mini. Tashi ka tafi". Ya koma daki jiki a sanyaye, ya shiga rudu sosai. Adnan da Yasir sun dade tsaye a kansa suna magana, sai daga karshe sulka taba shi tare da neman gurin zama. Adnan ya dube shi. "Abokina gaya mini?" 36 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUND Mu'allim ya kada kai ya ce. "Abba ya tsananta a kanta, wai ya ce babanta ya zo ya ci masa mutunci, wai da ma Abba ya san shi ne, al'amarin nan na ba ni Ummaki". "Da ka ce ya goya maka baya, ya kuma saka zai sauya, anya babu masu kewayowa su zuga shi?" "Haka na ke zargi". Yasir ya ce, "Ni a tunanina tsoro ya ke ji saboda su masu kudi ne, ni dai shawarar da zan ba ka kada ka bari damar nan ta wuce ka. Ko don ka ceto Kawu daga halin da ya ke ciki, kana da tabbacin cewar kawu zai warke, ina ganin hakarka ta kusa cimma ruwa da zarar ka auri Humaida ka gama talauci". "Haka ne, sai dai matsalar Abba ba żai taba fahintata ba, kawu ya yi dawainiya da ni burina a duniya bai wuce in sama masa lafiya ba, ina son Ubangiji ya ba ni wannan 'damar ko da shi ne kadai abin da zan yi a 37 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD duniyar nan ina Kaunar Kawu fiye da kaina, zan jure duk wani kalubale daga Abba, na yi amfani da wannan damar da ta zo mini. Na yarda zai yi fushi da ni matsananci, zai yi Ummakin yadda yaro mai biyayya ya sauya masa, sai dai nan gaba zai gane abin da na ke nufi, musamman in Kawu ya sami lafiya" "Yaron nan ya fara ballo mini ruwan da cinye ni da yaki. Alhaji Auwal ka gaya mini ya zan 6illo wa al'amarin nan?" Alhaji Auwal ya fuskance shi, ya сe. "Humaida kadau ka mallaka, hakan ya sa tun farko ba kwa nuna mata abu mai kyau da mara kyau ku ka barta ta yi duk abin da ta so, ka ga yanzu kuwa ka ce za ka tilastata a kan barin wani abu zai yi wuya. Shawarata kawai ku amince mata tunda duk binciken da na yi a kan yaron ba shi da wani aibu, talauci da rashin aikin yi shi ne matsalarsa". 38 KA AURE NI=2 BILKISU N.MUND Injiniya Sunusi ya ce, "Wannan shi ne babbar matsala, zan iya juriya a kan komai amma ban da talauci na tsani talaka don haka kullum na ke neman tssari da talauci, duk inda ya ke ba na rabar gurin gudun kada ma ya waske ni". Alhaji Auwal ya ce, "Ina ganin haka ne ya sanya ayar Allah ta sauka a kanka gurin nuna maka ishara. Ina ba ka shawara kada ka soma ja da ikon Allah..." huci. "Ban fahince ka ba?" "Ina nufin ka bari ya aure ta". Zumbur Hajiya Zainab ta mike tana "Wallahi ba za ta sabu ba, wannan ba shawarar kirki ba ce ka ke ba shi. In talaka ba abin gudu ba ne mai ya sa da za ka aurar da Amina ba ka bai wa talaka ba? Ji na ke yi wanda ta ke so talaka ne amma fir ka ki amincewa ka dauke ta ka ba wa dan gidan " mataimakin gwamna aurenta...' 39 a KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Ji nan Hajiya Zainab, diyata tun farko ina tsaye a kanta na kan kwabe ta kuma in tirsasata ta yi yadda na ce ki da kuwa ba ta so, hakan ya sa ta amince da zabina, ku kuwa taku na sani ko da za ku yankata ba za ta bi ra'ayinku ba, turbar da ku ka dora ta a kai ke nan tun asali". Ai ko gabadaya ta hau jifansa da bakar magana. "Karya ka ke, da ma an ce munafikinka tabarmarka, gwara da ka yi a gabanmu..." Injiniya ya katse ta da fadin. "Ke Zainab! Ki san da wanda ki ke 99 magana Ya juya ga Alhaji Auwal. "Ka yi hakuri mu koma ofis mun karasa maganar a can". Suka mike za su fita, ta bude murya bakidaya. 40 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Ya dai tawa ce ba wani ne ya haifa mini ba, in kai ya shanye ka don ya dinga juya ka ni na fi karfinsa". Alhaji Auwal ya girgiza kai kawai yana murmushin takaici. gurin. "Injiniya Sunusi ya се. "I say stop it mana!" Ta ga ransa a bace ne ya sa ta barin Ya ga dai Humaida da gaske ta ke, ya dauki waya a kan tebur yana son kiranta, ya yi karfin halin lalubo layinta. Tana kwance a doguwar kujera ta ji wayarta ta dau ruri ta mika hannu kan tebur ta dauka, lambar Mu'allim ta gani, ta mike da sauti ta amsa kiran tare da karawa a kunne. "Talaka na ganinku?" Ta yi murmushi, "Wace ni, barinka na yi ka sha iska". Ya ce, "Iska kamar ya ya?" 41 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Та се, "Macen arziki namiji ke zuwa gidansu ba ita ta je ba, na damu da kai don haka na bi yadda ka ke so. Nasiharka ta sanya ni jure rashin ganinka". ya ce. Ya yi murmushin da ta jiyo sautinsa, "Allah sarki, Humaidata". Ta zabura a dokance, ta ce. "Me ka cе?" Ya ce, "Cewa na yi Humaidata Ta ce, "Sake fada na ji". Ya yi murmushi, "Humaidata! Humaidata!! Humaidata!!! Ya isa haka ko na ci gaba?" YBW "Ya isa haka Mu'allim, yau ka ba ni farin ciki ina tsoron zan roki wata alfarma a gare ka..." "fadi duk abin da ki ke so, na sadaukar da wannan ranar a gare ki". Ta yi shiru zuwa wani lokaci. "Ke na ke sauraro Ta ce, "Ina fargaba... 42 KA AURE NI=2 "Kada ki damu" "Ka ce mini za ka zo". BILKISU H.MUHD "Abin da ki ke bukata ke nan? In na ce zan zo ya za ki yi da Dad?" "Kada ka damu, ya yi nadamar abin da ya aikata maka". "Gaya mini, yaushe ki ke so na zo?" "In na ce yanzu ya yi?" "Ki yi mini uzuru zuwa gobe". *** *** *** "Kana da kudi in ka so za ka iya maida shi yadda ka ke so zai hau motoci zai rayu a babban gida kerarre, ta ya ya hakan دو zai yiwu, duk kai ne za ka mallaka masa". "Alhaji Auwal mai ke damunka, kana da lafiyar kwanya kuwa? Tun ina karami na ke bin hanyoyi iri-iri don na tsira daga talaucin da na yi karatuna babu wanda ya taba taimakona kai ma ka san wahalar da sha ta ya ya za ka ce na mallaka wa wai duk 43 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD wadannan abubuwa na sauya masa rayuwa dare daya? Ba zai yiwu ba!" Ya fada ciin kakkausar murya. Alhaji Auwal ya mike tsaye ya karasa gurin da Injiniya Sunusi ke zaune ya zube hannayensa a kafadunsa. "Kwantar da hankalinka mana, haba sai ka ce ba dan garin nan ba, bari in yi maka gwari-gwari yadda game din zai kasance" Tsawon mintina biyar yana gaya masa, Injiniya ya ce. "kana ganin hakan zai yuwu?" "Sosai kuwa". Suka yi dariya. دو" Kai mutumina ba ka da dama". A karo na biyu yau ma duk ta birkice sif da akwatina tana neman kayan da za ta saka saboda zuwan Mu'allim. Ta sake janyo wata akwati ta bude ta dauko doguwar riga English wears, ta bude shi tana kallo ta kada kai ta yi ciki da shi, ta sake dauko riga da 44 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD wando fakistan ta daga shi shi ma bai yi mata ba. Ta cije lebe ta mike ta hau ta kawo. Hajiya Zainab ta turo kofar dakin ta shigo. Ko'ina a birkice ta dube ta. "Humaida, me ye haka?" Cikin yanayin damuwa ta ce. "Mom please, ki taimaka ki gaya mini inda zan sami kayan hausa". Ta ja tsaki, "ban fahince ki ba". Humaida ta ce, "Ina nufin riga da zani da hijabi". "Me za ki yi da su?" "Mu'allim zai zo na kuma lura shigar da ya fi so ke nan ya ga ina yi". Ta tabe baki ta kuma kwaikwayi muryar Humaida cikin abin da ta се: "Mutuniyar wofi, har ki dinga kokarin faranta wa wani can kina muzanta mana in an yi magana Dad dinki ya ce kuruciya, ai ga irinta nan shaidaniyar banza". Ta yi tsaki ta fice a dakiln. 45 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Humaida ta rushe da kuka, "Mom bа kya sona tunda ba kyá son faranta mini". Ta yi waje, Mustapha ta tarar yana karatun alkur'ani ta yi masa sannu, ya bi ta da ido yana Ummaki, ya rufe alkaur'anin. Та се, "Mustapha ka taimake ni please Ya sanyaya murya, "Me ki ke bukata?" "Ina so ka samo mini riga da zani da hijabi". Ta mika masa dubu ashirin. "Ina sonsu a dinke nan da awa uku, please akwai tukwaici mai gwabi". Bai wani sami matsala gurin shiga gidan ba, tuni maigadi ya san da zuwansa, yana tsaye a harabar gidan yana laluben layinta. Tsaye a gindin madubi cikin shigar zani da riga tare da hijabi ta ke tana kallon kanta. Ta yi murmushi. 46 KA AURE NI=2 "Malama Humaida!". Ta kyalkyale da dariya. BILKISU H.MUHD "Babu laifi, na yi kyau sri dai zafi". Karar waya ya katse ta ta dauka ta manna a kunne. "Ka iso ke nan?" Ya amsa da, "Eh". Ta yi saurin katse wayar ta dauko turare ta feshe jikinta da shi, cikin sauri ta yi waje. Hajiya Zainab da jarida rike a hannunta tana dubawa. "Mom, ya ki ka gan ni?" Ta dago kai tana dubanta. "Ina za ki je?" Ta tambaya cikin daure fuska. "Haba Mom, sau nawa zan gaya miki? Ji na ke dazu na sanar da ke cewa 'zan yi bako?" Ta mike ta ajiye jaridar a gefe. "To ba za ki je ba". "Uhm Mom na sani wasa ki ke yi" 47 KA AURE NI=2 Cikin daga murya ta ce. "Ki koma daki na ce. BILKISU H.MUHD Ko dar ba ta ji ba ta dube ta. "Mom, ko Dad ba na tsammanin zai yi abin da ki ke kokarin yi". Ta kausasa murya tana fadin. "Ashe ba ki da mutunci Ta kama hanya za ta fita cikin kunkuni. Cikin zafin nama ta finciko ta. "Mom kina son wasa da rayuwata, ki cika ni ina fargaba kada na ba ki Ummaki. Idanuna sun rufe zan iya yin komai". Ta kwace daga hannunta ta fice daga sitroom din, Hajiya zainab ta koma ta yi yaraf a kan kujera, Humaida ta yi nisa ba ta jin kira, ya ya za su yi? "Kina da kyau, kin fita daban cikin mata Humaida, yau zan sanar da ke ina sonki, ina matukar sonki". Ta yi murmushi mai yalwa. "Sannu da zuwa". 48 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Lambu ta ja shi, ya dube ta yana murmushi. "Kin jima ba ki fito ba, Allah ya sa lafiya?" "Macen arziki in aka aika kiranta sai ta dan jima kafin ta fito, ba ta fito nan da nan tana rawar jiki ba". Ya shafa kai cikin jin kunya. Ya yi saurin basarwa. "Humaida ke nan, na same ki lafiya?" "Lafiya kalau, sai dai kewarka". "Da gaske ki ke?" Ta ce, "Sosai ma kuwa". "Amma kin ba ni Ummaki". "Kamar ya ya?" Ya ce, "Sai ana sonka a ke kewarka, ko kin mance kin ce ba sona ki ke ba, kina so ne na aure ki?" "Na rasa me zan kira abin da na ke ji a zuciyata game da kai, yadda na ke ji ya fi karfin so, shi so wataran ya kan rikide ya 49 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD zamo kiyayya, in ko na ce KA AURE NI, hakan na nufin ba zan taba kinka ba". "Babu namijin da zai dube ki ba tare da ya yi fatan ki zamo mallakinsa ba, ina donki tuntuni, to matsalar in na amince da me zan aure ki? Ba ni da komai". Hon da suka ji ne ya katse shi, a tsorace ya dubi Humaida. "Dad ne ya dawo". Bai san sa'adda ya mike tsaye ba. "Kada ka damu". Yana kallo ya fito daga mota, ga Ummakinsa gurinsu ya ke tahowa. Tuni ya yi mutuwar tsaye. "Please ka zama namiji, dad ba ya son 6acin raina babu abin da zai faru”. Lokacin da Injiniya Sunusi ya Karaso daf da su tsoro ya bayyana karara a kan fuskar da sauri ya durkusa cikin rawar murya. "Sannu da dawowa". Ya dube shi da fuska a sake. 50 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Kana lafiya, baby in kun gama sa: ya zo ya same ni ko?" Ya wuce ya tafi, ajiyar zuciy ar da ya saki ya sanya Humaida kyalkyala dariya "Haba irin wannan kidimewar haka taho mu je in. nuna maka inda za ka same. shi". "Ka dauke ni a matsayin uba, na kan so duk abin da babyna ta zo mini da shi tun farko da ka ga na ki na yi tunanin irin yaran nan ne mayaudara, masu gurbata tarbiyya da lalata sai dai da na gama bincike na sai na ga ba ka daya daga cikinsu don haka na ke son mu yi magana ta fahinta. Kana sonta ne ko samartaka kawai ka zzo ku yi?" Ya sunkuyar da kai cikin jin kunya. "Ina sonta, sai dai zan so a jinkirta mini har zuwa lokacin da zan sami aikin yi". "In dai wannan wannan ce ba wata matsala ba ce gobe ka same ni a kamfanina". Ya dauko card ya ba shi. 51 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Wannan Katina ne ka taho da takardunka don na san inda zan yi". Ya risinar da kai yana godiya. "No babu godiya a tsakaninmu, ai yi wa kai ne". Suka yi sallama ya fito. A kofar gurin ya sami Humaida. "Ya ku ka yi da Dad?" "Cewa ya yi kada na sake zuwa gurinki". Ta juya cikin sauri za ta shiga gurinsa, cikin kiran, "Dad! Dad!!". "Humaida! Kin san abin da ki ke yi kuwa? Wannan ai ba tarbiyya ba ce, in ba ki girUmma shi ba zai iya yiwuwa ni ma ba za ki girUmmani ba bayan na aure ki”. "Idanuna sun rufe, ka gaya mini me ya ce da kai". Ya mika mata katin hannunsa, gurin karba ya yi ido biyu da wasu irin farata masu kyau sun sha kunshi, sai dai sun yi tsayi da yawa. Ya gaza dauke idanunsa. 52 シ KA AURE NI=2 "Me ka ke kallo?" BILKISU H.MUHD Ya ce, "Rumfar shaidan na ke kallo". "Ban fahince ka ba". Ya ce, "Faratanki su ne rumfar shaidan". "Faratan nawa? Ka san kuwa nawa na ke kashe musu a duk sati? Haba Mu'allim kar fa ka zaci don na ce KA AURE NI hakan na nufin ba ni da sauran 'yanci ke nan ba" "Yanci? Mene ne 'yanci? Al'adun yahudu su ne suka zamo 'yanci? Humaida dole ne ki sauya duk wannan dabi'un, dole ki rage su. Ki je ki yi nazari ba zan dauka ba". Ya juya zai tafi, ta yi saurin shan gabansa. "Ga katinka". Ya ce, "Ba shi da amfani a gurina". Ta raunana murya, "Ka gaya mini me ka ke so?" 53 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Humaida ina son ki sauya duk wani 'yanci da ki ke tunanin kina da shi, ina son ki sauke shi ki koma saiti kamar yadda musulunci ya tanada, in kin amince da haka Humaida zan aure ki". Ya ci gaba da tafiya, ta sake shan gabansa. "Kada ka tafi ka bar ni". "Humaida zan tafi". Ta ce, "Ina ji a jikina Dad zai amince da batunmu me ya sa ba za ka amsa gayyatarsa ba?" "Zan amsa lokacin da za ki zamo macen bahaushiya sai anjima" "Mu'allim! Mu'allim!! Please kada ka tafi, ka saurare ni kada ka tafi”. Ko waiwayenta bai yi ba ya fice daga gidan. Gabadaya hankalinsu Malam Musa kya kwanta suna tunanin sun kashe matsalar Mu'allim, shi ma kuma ya iya takunsa, ba 54 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD ya taba nuna musu da akwai sauran alaka tsakaninsa da Humaida. Yau ya kawo musu labatin samun aikinsa, Hajara da Malam Musa sun kudiri aniyar daukar azumi don nuna godiyarsu ga Ubankgiji. Wata daya kacal da fara aiki rayuwarsu ta soma sauyawa, albashin farko kayan abinci ya jibgo musu da dai abin da ba a ra a. ara da Malam Musa a tsakar gida Suna ra cikin nishadi, malam Musa ya dubi Hajara. "Kin ga danki da rigima ko?" Ta kalle shi, "Wacce irin rigima?" "Ya dage wai lallai sai na daina likin takalmi". "Malam ai abin da kullum mu ke roko ke nan, U ngiji a kawo ranar da za ka .huta دو nan?" "Au ke ma kin na da goyon baya ke 55 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Gani ya yi ta yi shiru ya kira sunanta. Ta kalle shi. "Tunanin me ki ke yi haka?" "ina tuno Kawu Yusuf, lokacin da yana da lafiyarsa kullum addu'a ya ke yi wa Mu'allim, yau ga shi ba ya a hayyacinsa addu'arsa ta karbu". Malam Musa ya ce, "Amma kin san wani abu Hajara? Kawai na ji hankalina ya kasa kwanciya da Mu'allim". Та се, "Кamar ya ya ke nan? Haba Malam me ya sa ka ke haka? Takardun yaron nan fa a gurinka suke, ya zo ya amsa in ba aiki ba ne zai karba ne? Ko kana son ka ce sata ya ke yi?" "Ba na taba zargin yarona, sai dai zuciyata tana raya abubuwa da yawa, amma ina nan ina bincike, ko ma me ye zan ci gaba da gaya wa Ubangiji, koma me zai bayyanar da gaskiya". Ran Hajara ya gama bасі. 56 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Haba Malam in ba za ka fadi alheri ba ka yi shiru, kada ka yi masa baki ya fada kansa..." Sallamar Mu'allim ya sanya su yin shiru, ya durkusa yana gaida su, ya mika wa Hajara leda. "Me muka samu?" Ta tambaya. Ya ce, "Kaya ne na siya wa Kawuna". Malam Musa ya ce, "Allah ya yi albarka, Ubangiji ya sa ka fi haka, ba ka gajiya da hidima". Hajara ta ce, "Da izinin Allah sai kawunka ya samu lafiya ya tabbatar da fadawar addu'arsa a kanka". "Umma da izinin Allah ya kusa samun lafiya nan da wani kankanin lokaci komai zai zamo labari". "Ubangiji Allah ya tabbatar, amma kafin nan sai ka ayi aure ko?" Ya dan shafa kai. "Umma lafiyar kawu ne a gabana". 57 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Malam Musa ya bude ledar shaddoji ya

Chapter 2 of 5