Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 5
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels KA AURE N HAUSABООK.COM 2 KA AURE BILKISU H. MUHD Harafi Publlshers KaAure Ni BILKISUHAMUHD KA AURE NI=2 KA AURE NI-2 BILKISU N.MUKD a cе, "Kada ka sake Ytambayata, don babu abin da za ka ji daga gare ni, in har ka amince ni ne mahaifinka ka sa a ranka tamkar ba ka taba saninta ba, amma kafin nan ina so ka sani babu wani gado da ya fi kwaun hali amfani, kuma babu wata taska da ta fi ladabi duk abin da ya yi yawa ya kan yi arha, amma ban da kyawun hali. Shi yana kara yawa ne yana kara tsada, al'umma ta kan tabbata ne matukar kyawun halinsu ya tabbata, in kuwa dabi;arsu ta tafi su ma sun tafi da yawa mutane sukan mutu yayin da dabi'unsu suka mutu, sai ka ga mutane a raye amma matattu ne. Jikin Mu'allim ya yi sanyi sosai. Ya mike ya shiga gida. Wuni ya yi sur yana nazarin maganganun Abbansa, yana matukar son Humaida, ya zai ya tursasa wa zuciyarsa a kan ya rabu da ita? Bai taba tunanin sonta ya 4 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD yi zafi haka ba, yana jinta tamkar numfashinsa. Yana zaune a kan tsohuwar kujerar da ke dakinsa, lokaci daya ya mike ya shiga zarya har lokacin laluben mafita ya ke, damuwa ce karara lullube a fuskarsa. Wayarsa ta yi kara, ya dauka ya duba, Humaida ce, ya dubi agogon da ke daure a tsintsiyar hannunsa, karfe daya da kwata na dare, ya ja tsaki ya maida wayar ya ajiye, ya koma ya zauna defe da kai har ta gaji da ruri ta katse, kiran ya sake shigowa, hannayensa biyu ya saka ya toshe kunnuwansa, sai da ta sake katsewa ya sauke hannayen nasa ya kwanta. Ba a jima ba kiranta ya sake shigowa, a zafafe ya mike ya dauki wayar gabadaya ya kashe ta. *** *** *** Ta fito daga daki rike da mukullin mota, ko kallon inda su Dad suke ba ta yi ba, kokarin gota su ta ke yi, sun sa mata ido 5 KA AURE NI=2 BILKISU M.MUND kurum. Da Dad ya tabbatar fita za ta yi sai ya yi saurin dakatar da ita. "Humaida, ya kin an. Tana tsaye ba ta kallo inda suke ba, ta ba su baya. Ya yi murmushi cikin kada kai. "Zo ki gaya min waye ya bata miki rai?" Gabadaya ta juyo tana fuskantarsu, cikin muryar kuka ta ke magana. "Dad, ka daina ganin murmushi a fuskata!" Ya mike tsaye ya yi tattaki zuwa inda ta ke, ya се. "Murmushi ba zai taba gushewa a wannan kyakkyawar fuskar taki ba muddin ina raye, rashin murmushi alama ce na bakin ciki, ni kam burina a kullum in ganki cikin farin ciki, muddin kina da ni babu ke babu matsala". Wasu sababbin hawaye suka dinga sintiri a kan fuskarta, ta runtse ido ta bude. KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Ina son ka tabbatar mini da haka, don na gaji da gafara sa kullum zancenka guda daya ne, ban ga ka cika shi ba, ka dauke ni tamkar 'yar baby, Dad in har abin da ka ke fada na murmushi ba zai gushe a fuskata ba, ka amince min in aure shi". Ya kai hannu ya dafa mata kafada. "Zan yi yadda ki ke so, akwai nazarin 99 da na ke yi ne... "No Dad!" Ta ce da karfi, "Kana so ka rusa mini tsari na. "Wannan karon zan kara rokonki ki יי ba ni kwana uku kin ji?" Ba taice komai ba, ta janye jikinta ta fice tana sharar kwalla. "Please, ki fita daga rayuwata na huta, tunda ki ka shigo rayuwata farin cikina ya gushe, ke shu'uma ce mahaukaciya, ki je ki koyi hankali sannan na saurare ki". "Mu'allim!" Ta kira sunansa cikin muryar kuka. 7 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Saboda ina nemanka da alkhairi shi ne za ka samu damar ci mini mutunci, ashe ra'ayi yana zamowa laifi don na ce ina ra'ayinka shi ne duk ka janyo ka ke kirana da dabba, mahaukaciya?" Cikin rashin damuwa ya ce. "In kin je ki tambaya ki ji babu mutumin da zai sa ki a sahun masu hankali, don duk abin da ki ke yi na mahaukata ne, ki je ki tambayi bambancin hankali da rashinsa". Wata kara ta kwalla da sauri ta shige mota ta bar gurin. Adnan ya karaso inda ya ke. "Tabbas ba ka dara ba, na yarda abin a jininka ya ke". Ya dube shi a fusace. "Don Allah ka kyale zuciyata ta huta, ka rabu da ni". Ya yi tsaki ya bar gurin. *** *** *** 8 = KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Saboda ba ni da shi sai a turo mini kananan yara suna yi mini fitsara har suna jifana, sannan ki ce na yi hakuri? An dade ana yi min wadannan abubuwan ban taba daga kai ba, amma abin ya ishe nim wannan karon zan dauki mataki". Saudatu ta kada kai. "Ba za ki iya da su ba saboda ba ki da komai in ki ka doshe su mahaukaciya za su dauke ki". Ta dafa goshinta inda ya kumbure saboda jifan da yaron ya yi mata. "Shi ke nan Saude, na bar su da Allah, domin na san shi ne kadai zai bi mini hakkina". Ta fada tana sharar kwalla. "Ki yi hakuri, ga wannan babu yawa kin sayi magani". Ta mika mata naira dari biyu. "Ni zan tafi". 9 KA AURE NI=2 Da sauri Mu'allim BILKISU M.MUND ya ja da baya, Saude ta fito ya yi saurin rufa mata baya, ya koma ya sha gabanta. "Mu'allim kai ne?" Ya kada kai yana kallonta da idonsa jajir. "Ina son ki gaya mini waye ya aikata wa Ummata?" "Ka yi hakuri ba na son haddasa fitina". "Ba fitina ba ce, ina son kwatar mata 'yanci". Saude ta yi murmushi, "Mu'allim ke nan, akwai babban 'yancin d ya wuce ka mike ka nemi kudi ba za ka taba daina ganin kaskanci ba da kai da iyayenka har sai ka zama wani, me ya sa ba za ka zamo da na gari mai kishin iyayensa ba? Wallahi muddin ba ka yi haka ba kana tare da la'ana, bakin jama'a zai fada maka, ka ganka namiji har namiji amma sai dai ka kwanta a nemo ka ci, to in ba ka sani ba idanun jama'a а 10 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD kanka ya ke, kullum zagi da tsinuwa a kanka ya ke karewa. Ka ji tsoron Allah ka tashi ka nemi na kai a ko ina ne, muddin halali ne ka taimaki Hajara, ka ga yadda ta dawo". Ga Ummakinsa kwalla ya ga Saude na yi. "Wallahi Mu'allim da na haifi dan da ba ya tausayina gwara na zauna a haka, kа tabe ka gama tabewa". Da sauri ta bar gurin, jiri ne ya dinga - daukarsa, idanunshi suka rufe ya daina gani ya koma ya bi jikin bango ya zauna jabar dafe da kai. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Ya ke ta maimaitawa, da kyar ya samu ya dawo daidai, ya mike ya nufi gida. Da kumburarren goshinta ya fara arba, gabansa ya buga, da kyar ta ke iya bude idanunta. "Umma, waye ya aikata miki haka?" Ta yi kokarin kirkiro murmushi. 11 KA AURE NI=2 "Bugewa na yi..." BILKISU H.MUHD "A'a umma, kada ki gaya mini haka, kada ki 6oye mini don Allah". "Kai ka ji min yaro, wa ka ke tunanin zai yi mini haka?" Ya sani ba za ta fada ba, don haka bai tilasta ba. "Allah ya sauwake" Ya ce, ya koma dakinsa ya dinga zarya zuciyarsa na yi masa ciwo, abubuwa iri-iri ya dinga sakawa, Humaida ita ce damuwarsa, babu abin da ya tsana irin ya zamo mijin Hajiya, yana Ummakin mazajen da ke auren jaro, ya tsani irin wadannan mazajen, yau ga shi burinsa zai janyo ya bi sahun wadannan mazaje, dole ya amince da Kudirinta. Tun daga aruber gida ta soma kiran. "Dad! Dad!! Dad!!!? 12 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Har ta isa babban sitroom. Yana zaune shi da Hajiya Zainab, ya yi saurin mikewa yana duban ko'ina na jikinta, sai da ya tabbatar ba ta tare da wata matsala sannan ya sauke ajiyar zuciya. "Uhum baby ke na ke sauraroro". "Dad, ina son ka sanar da ni yau me ye hankali, me ye kuma yarinta? Mene ne bambancin hankali da rashinsa?" "Kafin na ce miki komai ki koma ki zauna, ki kuma daina kukan nan". Ta yi kamar yadda ya bukata. "Dad, ba ka ba ni amsar dukkan tambayoyina ba". "Humaida zan ba ki amsar tambayoyinki". Ta kafe shi da ido alamar shi ta ke sauraro, ya сe. "Hankali shi ne nutsuwa, wanda kuma tunaninsa bai jirkita ba bambancin hankali kuma da yarinta, kin ga kamar ke da Mustapha hankalinku ba daya ba, yanzu na 13 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD hana ki fita da yamma za ki iya ki yi ficewarki, ta yuwu fitar da za ki yi za a yi ta kawo mini kararki, wani fannin za a ce kin kade wane ko wance, ko kin ci kwalar wancan da dai sauransu. Amma shi Mustapha a wannan lokaci yana ina?" Ya karasa maganar yana kallonta. Та yamutsa fuska. "Na san ba zai wuce a ce yana can yana fama da carbi ba, ni ko tun farko kai ne ka hana ni ka ce in na yi ba zan dinga samun hutu ba". "Okey, kin gamsu da amsoshina, sai wacce tambayar za ki yi?" Ta kada kai, ta ce. "Ban gamsu ba Dad, asalima soki burutsu kurum na ji kana yi" Hajiya Zainab ta mike a fusace tana nunata da yatsa. "Ki minin shiru na ce ko na karya ki sakarya, shashasha kawai, wallahi... 14 と KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "A'a Zainab, kyale ta, in ba tambaye ni ba wa ki ke so ta tambava?" Ya juya ya kalli Humaida. ta "A karo na biyu kin ga hankali shi ne, kin ga yanzu an gan ki fes da ke kamar mai hankali, amma za ki ringa abu na kuruciya ...tsantsa وو Ta sake dubansa cikin rashin gamsuwa, ba ta kuma bari ya sarara ba, ta dora da cewa. "Dad kawai ka fito fili ka gaya mini ina abu na marasa hankali, domin Mu'allim ma kullum maganarsa daya ce a kaina". Cikin kuka ta juya dakinta. Hajiya Zainab ta dube shi ta ce. "Ka ga irin ta ko?" "I say shut up! Saboda haka sai na kamata na daka ki ke so ko? Ina gaya miki baby yarinta ce ke damunta..." "Haba alhaji, yarinya ta kai shekaru ashirin ka dinga kiranta da yarinya? Wane 15 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD mataki ne ba ta taka ba na imili, ashe ke nan ba za ta taba yin hankali ba?" Ta kada kai ta shige faki, shi ma ya tashi ya nufi dakin Humaida. Tana zaune a kan gado ta rafka tagumi, idanunta na ambaliyar da hawaye. Ya tausasa murya cikin tsananin tausayinta. "Kuka ki ke yi har yanzu? Tashi goge hawayenki mu yi magana, mai ya yi zafi? In kina son in dauki mataki a kan wanda ke kiranki da mara hankali sai na dauka..." "Dad, me ya sa ka gurbata min rayuwa ba ka sa ni a sahun masu hankali ba ka sa ni a sahun mahaukata?" Ya rude sosai, ya ce. "A'a, ba haka ba ne. babu wanda zai kira ki da mahaukaciya, duk wanda zai ganki sai dai ya yi da ma shi ne ke". "Dad, mutane da yawa na yi mini kallon haka". "Ke ki ke ganin haka, wadancan masu fadin haka ba su san zafin 'ya'ya ba, suna da 16 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD su da yawa, ke ko kin ga ni ke kadai ce gare ni, ke kadai ce a gidanku, ba ki ga bature ya bai wa kowa 'yanci ba, misali ba mun je Rasha da ke ba, kin gani ba mun je America da sauran kasashe kin gani ba? To me ki ke son ai miki?" Ta mike tsaye tare da juya masa baya. "Dad, ka yi hakuri da abin da zan gaya maka, ku kuka jawo mu mu zama rakumi ku akala mu ja ku mu tafi jahannama..." Da sauri ya katse ta da daka mata tsawa. "Ni za ki kawo wa rashin tarbiyya da rashin mutunci? Kina bin wadancan 'ya'yan talakawan suna gurbata miki tunani?" Hajiya Zainab ta shigo a sukwane, ta fidda hannu ta tsinka wa Humaida wani gigitaccen mari tana huci. "Ga irinta nan, yarinya ta kai tsaiko abin da kullum na ke jiye maka ke nan”. 17 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ita kam 'yar lele juyawa ta yi ta fita a guje cikin ihun kuka. *** *** *** "Ka yi hakuri tunda Abbanka ya ke bai san me ye dadi ba, don haka babu abin da zai dorar a rayuwar ya kare a talauci, zuciyarsa ta riga ta mutu ba zai taba ganewa ba, yakin naka ne duk lokacin da ka cire musu wannan tsatsar a nan ne za su gane ashe da su mutane ne su. Ka aure ta in sun yi fushi a hankali watarana za su gane gaskiya, talauci ya yi musu mugun kamu, ya zame musu illa kada ka bari yarinyar nan ta subuce maka. Ba zan gaji da ce maka ba in har hakan ta kasance za ka yi nadama, su fa yanzu su Abba rayuwarsu ta zo gangara yanzu kai ne ka ke tasowa in ba ka yi da gaske ba za ka yi rayuwa irin tasu, a wannan karnin in ba ka da shi ba mai tausaya makа. Jama'a gudunka za su dinga yi, 'ya;yanka su rainaka, ka zamo abin zolaya da tsokana 18 1 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD su da yawa, ke ko kin ga ni ke kadai ce gare ni, ke kadai ce a gidanku, ba ki ga bature ya bai wa kowa 'yanci ba, misali ba mun je Rasha da ke ba, kin gani ba mun je Americа da sauran kasashe kin gani ba? To me ki ke son ai miki?" Ta mike tsaye tare da juya masa baya. "Dad, ka yi hakuri da abin da zan gaya maka, ku kuka jawo mu mu zama rakumi ku akala mu ja ku mu tafi 99 jahannama... Da sauri ya katse ta da daka mata tsawa. "Ni za ki kawo wa rashin tarbiyya da rashin mutunci? Kina bin wadancan 'ya'yan talakawan suna gurbata miki tunani?" Hajiya Zainab ta shigo a sukwane, ta fidda hannu ta tsinka wa Humaida wani gigitaccen mari tana huci. "Ga irinta nan, yarinya ta kai tsaiko دو abin da kullum na ke jiye maka ke nan". 17 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD Ita kam 'yar lele juyawa ta yi ta fita a guje cikin ihun kuka. *** *** *** "Ka yi hakuri tunda Abbanka ya ke bai san me ye dadi ba, don haka babu abin da zai dorar a rayuwar ya kare a talauci, zuciyarsa ta riga ta mutu ba zai taba ganewa ba, yakin naka ne duk lokacin da ka cire musu wannan tsatsar a nan ne za su gane ashe da su mutane ne su. Ka aure ta in sun yi fushi a hankali watarana za su gane gaskiya, talauci ya yi musu mugun kamu, ya zame musu illa kada ka bari yarinyar nan ta subuce maka. Ba zan gaji da ce maka ba in har hakan ta kasance za ka yi nadama, su fa yanzu su Abba rayuwarsu ta zo gangara yanzu kai ne ka ke tasowa in ba ka yi da gaske ba za ka yi rayuwa irin tasu, a wannan karnin in ba ka da shi ba mai tausaya maka. Jama'a gudunka za su dinga yi, 'ya;yanka su rainaka, ka zamo abin zolaya da tsokana 18 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD cikin dangi, duk abin da ka yi ba ka iya ba babu wanda zai damu da kai, wannan sai ya fi ka daraja, wasu ma sa sur mai da kai karamin mahaukaci. Mu'allim, talauci na da zas na ban Ummaki in ba ka da shi kullum za ka kasance cikin kunci, shi kansa Abba talauci ne ya sanya ake kiransa da sunaye iri-iri, in yana da shi wannan makantar ba za a gani ba. Ka je ka yi tunani, kuma ma ai yarinyar ba ta da makusa. Daga karshe ina son tunasar da kai shi kansa shugabanmu ya се, mu nemi tsari da talauci don haka ka kyale su Abba, tunaninsu irin na mutanen da ne". "Adnan ina matukar sonta, ba don su wasu ba ne. yadda na ke jinta a raina zan iya zama da ita ko da ba kowa ba ce, sai dai matsalar yarinyar duk dabi'unta ba su yi ba". "Wannan ba wata matsala ba ce, muddin tana sonka za ka bi da ita ta yadda ka ke so sannu a hankali, kada ka yi saurin 19 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD mika kai ka kara jan aji. Sai fa ka jajirce a kan matsalar su Abba". Bayan ya koma gida ya shiga shawarwarin ya kira ta, sai dai yana jinjina abin yadda kya yi mata da kyar ne in za ta sake bibiyarsa. Ya ja tsaki ya janyo wayar tare da kura mata ido, ga Ummakinsa ya ji wayar ta soma ruri, kamar a mafarki lambarta ce ya gani. Ya ji wani sanyi a ransa da ita ce ta kira shi da kanta. Ya yi murmushi yana sani ya barta ta ci gaba da ruri har ta katse. Can wayar ta sake daukar ruri ya danna kore ya kara a kunne. Cikin kaurara murya ya ce. "Please and please, ki fita a rayuwata, kin takura min". Daga can 6angarenta, ta ce. "Na ji, zan yi yadda ka ce. Amma kafin nan ina son mu hadu, zan yi maka wata muhimmiyar magana". Ya ce, "Ba zan iya ba". Ta raunana murya cikin bayar da kai. 20 KA AURE NI=2 "Ka taimake ni". BILKISU H.MUHD Cikin daga muryar karfin hali ya се. "Wai ke wace irin mara zuciya ce? Kina son ne na yi miki karya?" Та се, "Ка yi hakuti, na riga na zo ina kofar gidanku". Ras! Gabansa ya buga, ya mike da sauri ya leka tsakar gida, Ummansa ba ta nan. Ya sauke ajiyar zuciya tare da yin kasa da murya. "Humaida, ki gaggauta barin kofar gidan nan, wai ke wace irin mace ce, me ya sa ki ke son ki dinga bata mini suna? Iye? Me ya sa?" "Da ma ka daina daga hankalinka. Duk wannan abin da ka ke yi ban san kana yi ba. Na dade ina shaida maka ban san bakar magana ba da ma ka bi komai a sannu, kuma na rantse in ba ka fito ba ni zan shigo". Da sauri ya katse wayar a guje yana fadin. 21 KA AURE NI=2 "Na sani za ta iya". BILKISU H.MUHD Hajara wadda ta ji tsiraru daga cikin maganganunsa ta shiga tararrabi, shin me ke faruwa? Hankalinta ya yi matukar tashi, musamman da ta ga yadda ya fito a hargitse. Daki ta koma ta janyo hijab a jikin kyaure ta nufa masa baya. Zaune a cikin mota kofar motar a bude ta zuro sam6ala-sambalan fararen kafafunta waje, cikin daure fuska ya ke kallonta. Bai yi magana ba ya zagaya daya bangaren ya bude murfin motar ya shiga. "Shigo na ce". Ya ce da ita. "Ina za ka kai ni?" Ta tambaya. Bai ce komai ba, ta zuro kafafun cikin motar, ya dan rankwafo ya janyo murfin motar ta inda ta ke da karfi har sai da ta firgita. Suka soma tafiya, sai da suka bar unguwar a can nesa ya yi fakin a gefen titi ya fito daga cikin motar yana faman huci. Ita ma ta rufa masa baya, ta ddube shi kawai tana murmushi. 22 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Zan tambaye ki, gaya mini me ki ke so? Me ya sa ki ke son jefa rayuwata cikin bala'i? Me ya sa?" Ta yi murmushi da nuna ko'inkula. "So na ke KA AURE NI!" Duk lokacin da ta furta wannan kalmar Ummaki ya kan kama shi, musamman in ya yi duba daga tsantsar kyawun da Ubangiji ya ba ta. Ya gaza furta komai. Ta kalle shi sosai, ta ga wani guri can ya ke kallo, ta maida kallonta gurin, wata budurwa ce ta zo giftawa sanye da hijabi har kasa. Ta koma ta dube shi. "Ni za ka kalla, ni ya kamata ka kalla ba ita ba, babu abin da ta fi ni da shi". Ya yi tsaki tare da kawar da kai gefe. "Akwai abubuwan da ta fi ki da su da yawa". Ta yi murmushin karfin hali, duk da kalaman nasa sun mata ciwo, amma ta sakaye abinta. 23 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Ni na sani, ka fadi son ranka. Ni na sani a cikin mata dubu da wahala a sami wacce ta dara ni, in akwai ka gaya mini". "Shi ya sa na ke kallon waccan mai hijabin, saboda ta fi ki komai". Meganarsa ya sanya ta sake kallon mai hijabin, baka ce mai jiki, tana da yankakken hanci, ba za a taba saka ta a tsarin kyawawa ba. Ta maida dubanta gare shi tana girgiza kai. "Da me waccan abar ta fi ni?" Cikin murmushi ya ke kallonta da alama ya soma ba ta haushi, ya cе. "Kin ga na daya, ta fi ki kunya, Saboda lunda ta tsaya kanta a kasa ya ke alamar mace ce mai kunya ke nan. Na biyu ta fi ki ilimi, saboda wani haske a fuskarta, ga shi ta sako hijabi alamar ta fito daga gidan kwarai, gidan mutunci. Da alamun kamun kai a tattare da ita. Na uku, ba za ta tari namiji a hanya ta ce ya aure ta ba, idan namiji ya ganta shi zai 24 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Zan tambaye ki, gaya mini me ki ke so? Me ya sa ki ke son jefa rayuwata cikin bala'i? Me ya sa?" Ta yi murmushi da nuna ko'inkula. '"So na ke KA AURE NI!" Duk lokacin da ta furta wannan kalmar Ummaki ya kan kama shi, musamman in ya yi duba daga tsantsar kyawun da Ubangiji ya ba ta. Ya gaza furta komai. Ta kalle shi sosai, ta ga wani guri can ya ke kallo, ta maida kallonta gurin, wata budurwa ce ta zo giftawa sanye da hijabi har Kasa. Ta koma ta dube shi. "Ni za ka kalla, ni ya kamata ka kalla ba ita ba, babu abin da ta fi ni da shi”. Ya yi tsaki tare da kawar da kai gefe. "Akwai abubuwan da ta fi ki da su da yawa". Ta yi murmushin karfin hali, duk da kalaman nasa sun mata ciwo, amma ta sakaye abinta. 23 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Ni na sani, ka fadi son ranka. Ni na sani a cikin mata dubu da wahala a sami wacce ta dara ni, in akwai ka gaya mini". "Shi ya sa na ke kallon waccan mai hijabin, saboda ta fi ki komai". Maganarsa ya sanya ta sake kallon mai hijadin, baka ce mai jiki, tana da yankakcen hanci, ba za a taba saka ta a tsarin kyawawa ba. Ta maida dubanta gare shi tana girgiza kai. "Da me waccan abar ta fi ni?" Cikin murmushi ya ke kallonta da alama ya soma ba ta haushi, ya ce. "Kin ga na daya, ta fi ki kunya. Saboda tunda ta tsaya kanta a kasa ya ke alamar mace ce mai kunya ke nan. Na biyu ta fi ki ilimi, saboda wani haske a fuskarta, ga shi ta sako hijabi alamar ta fito daga gidan kwarai, gidan mutunci. Da alamun kamun kai a tattare da ita. Na uku, ba za ta tari namiji a hanya ta ce ya aure ta ba, idan namiji ya ganta shi zai 24 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUKD je gidansu zance ba ita ta je ba, in ya aika ya ce ta zo sai ta dan jima kafin ta fito ba tana rawar jiki za ta fita ba. In ta fito din ma za ta tsuguna ta ce maka, ina yini ba tana tsaye kerere a kanka ba, ba kuma ita ce za ta ce ka zo a yi zancen aure ba, sai dai kai ka ce ki gaya wa iyayenki zan turo neman aurenki. Iyayen suna yanga ba kawai a hau zuba ba". Gabadaya yanayinta ya sauya, maganganunsa sun shige ta, cin fuska ne muraran ya ke gwada mata, yau ne ta ke jin wani abu a jikinta, wanda ga dukkan alamu ita ce wannan kunyar da ya gama goranta mata, me ya sa ba za ta hakura da wannan mutumin ba? Me ya sa ta bari ya samu damar da ya ke tozartata ya ke gasa mata magana yadda ya ga dama? Yanayin da ya gani a tare da ita ya tabbatar maganganun sun yi mata zafi, duk da ya ji ba dadi a zuciyarsa bai sa ya nuna alamar nadama a fuska ba. Ya dan yi murmushi, ya ci gaba da cewa. 25 Γ 1 1 KA AURE NI=2 BILKISU H.MUHD "Ya isa haka, ko

Chapter 1 of 5