Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 5
wannan takardan, ya girgiza kai, ya nuna Alhaji,kin san wannan mutumin? Ta amsa, Eh! Shine na aikawa wasikar. Da jin haka, gaba daya wurin kowa ya soma fadin albarkacin bakinsa. Shi kuwa Alhaji yayi tsuru-tsuru. Kwamishin ya dubi Alhaji, kai azzalumi maci amana, laifunka biyu manya a kanka, na haddasa kisan kai, ga nayi wa karamar yarinya cikin shege, don haka mu hadu a kotu. **** Faruku barazana da mahaifiyarsa, hankalinsu ya tashi, suna zaune a gida, suna tunanin dalilin kama Alhaji sai suka ji a rediyo ana labarai, ana cewa! 'yan sanda cun cafke Alhaji Karma-Karma, sanannen mai kudin nan dake nan garin, yayin da yake bada dalilin kamun, Kwamishinan 'yan sanda yace an cafke Karma-Karma ne 59 a dalilin haddasa kisan wani mutum, wanda yake likita ne a Kofun wannan gari. Koda fadin haka,sai Faruku ya gyara zama ya dubi mahaifiyar, ita kuma tayi tagumi. Daga nan aka ci gaba da labarai kamar haka, "haka kuma an sake kama Alhaji Karma-Karma da laifin ya yayi wa wata budurwa mai suna Jamila Alhaji Hamisu cikin shege,wacce ake kyautata zaton budurwar dansa ne, mai suna Faruku barazana,wanda ya shahara a fagen raina jama'a da rashin kunya a cikin garin nan". Koda jin haka,idanuwan Faruku suka firfito ya sake duban mahaifiyar,aka ci gaba da labarai ana cewa, yanzu haka gobe ne za'a shiga kotu, domin yanke hukuncin wadannan laifuka guda biyu,saboda haka ana gayyatar jama'a da su je su ba wa idanuwan su abinci. Da gama labaran, Faruku ya mike a fusace ya dubi mahaifiyar, Mama kin ji ta'asar da Baba ya dafka ko? Sai ya bugi wani teburi dake kusa dashi da hannusa. Ji kake gam!. Kotu ta cika Makil, babu masaka tsinke, jama'a sai tururuwa suke su ba wa idanuwansu abinci, kuma su ji yadda za'a kwashe. Asirin Alhaji Karma-Karma dai ya tonu,dubu ta cika, dukiyar ba ta hana ya fuskanci tuhuma ba. Daman kuma haka ake so ga masu mulki,kada su bambanta tsakanin mai kudi da talaka wajen tabbatar da doka da oda. Ga laifin haddasa kisan kai, ga shi kuma Jamila ta tabbatar da cewa lallai Alnaji shine yayi mata ciki, ba Salim kamar yadda ta lakafa masa da farko ba. Bayan da aka kawo Alhaji a motar nan bakar ashana, tare da yaronsa, daya da aka kama a wurin da aka kashe likita Dattijo, ga Jamila da iyayenta,Salim a gefe ga Faraku barazana da mahaifiyar sa, Ga alkali da sauran ma'aikatan kotu kowa yayi balas Jama'a kuwa iyakan ganinka,basu 60 , lissafuwa. Ga Lauya Sabulu mai kare Jamila yayi tsurutsuru, saboda sanin halin da ake ciki. Ga Lauya Linzami wanda Alhaji ya dauka domin ya kareshi wuri dai babu masaka tsinke. Da aka natsu, mai gabatar da kara ya mike ya soma bayaninsa kamar haka, Yau shari'i'on namu sune: Hukuma tana karar Alhaji Karma- Karma da haddasa kisan kai, wanda akayi wa likita Dattijo ranar sha hudu ga wannan watan, da misalin karfe biyu da rabi na dare. Haka kuma tana tuhumar sa da yi wa budurwa mai suna Jamila cikin shege,ya kuma sa ta lakafawa wani saurayi Salim wanda bai ci ba bai sha ba. Da gama bayaninsa, ya zauna,alkali ya gama 'yan rubuce-rubucensa, ya daga kai ya ce, yau ce daman muka sa za'a yanke hukuncin shara'ar Jamila da Salim, akan maganar ciki, to amma yanzu ta sake zane, domin kuwa inda aka za ta, ba'a nan take ba, an gane cewa Alhaji Karma-Karma shine ya aika wannan ta'asa, don haka magana ta juye,me lauyan wanda ake kara zai ce, wato lauyan Salim? Lauya Filla-Filla yayi zumbur ya mike, ya fito farfajiyar shara'a ya fuskanci alkali, ya dan sunkuya a matsayin ladabi, ranka ya dade, daman mu mun tabbatar ba Salim bane ya aikata wannan mugun aiki mai kama da kisan kai, amma wani lauya sukurkutacce, wanda bai san aikinsa ba, yayi karanbani, ya kare marasa gaskiya. Ranka ya dade tun da gaskiya ta bayyana mu ba mu da ja, sai abinda kotu ta zartas, mu dai mun san mune masu gaskiya. Yana gamawa, ya dan sunkuya, ya juya ya koma wurinsa yana barazanar samun nasara. Alkali yace, ko lauyan dake kare Jamila vana da ta cewa, sai lauya Sabulu ya mike, gwiwarsa a sacce, ya fito bagazan-bagazan, ya sunkuya a gaban alkali ya nuna ladabinsa, ranka ya dade 61 mun ji yadda ta kaya, kuma tun da an samu hujjoji cewa Alhaji shine yayi wannan ciki,to shi muke kara yanzu, kuma mun janye kara daga kan Salim. Kuma ina rokon ranka ya dade ka jawa lauyan wanda ake kara kunne, ya daina kirana da sukurkutacce, yayi aikinsa kawai in yi nawa. Yana fadin haka,sai duk jama'an dake nan suka kwashe da dariya, sai da aka tsawata sannan aka yi shiru. Alkali ya dube shi,ko me lauya zai yi ya wanke kansa ta yadda suka lakafawa yaro laifi, suka wahalar dashi, suka bata masa suna da lokacinsa, suka cuci lafiyarsa? Lauya ya girgiza kai, ranka ya dade ai rashin sani ya fi dare duhu, don haka muna neman ya yafe mana laifin mu. Alkali ya dubi lauya Filla-Filla,lauyan Salim ka ji abinda suka ce, kun yafe musu,ko kuwa kuna da ja dasu abi muku hakkin ku? Lauya Filla-Filla ya mike,ranka ya dade muna bukatar a fitar mana da hakkin mu yanzun nan kuwa, yana gama fadin haka, mahaifiyar Salim ta mike da sauri ta ce ranka ya dade, sai duk aka waiwaya inda take. Ta ci gaba da cewa, idan Salim da na ne, ni na haife shi,to ya yafe. Ai Allah ya fitar mana da hakkin mu, tun da ya nuna gaskiyar al'amarin. Tana gama bayanin ta sai ta zauna. Alkali ya bada umarni Salim ya mike. Bayan da ya mike aka tambaye shi idan ya yafe, shi kuma ya fada cewa tun da mahaifiyar sa ta ce ya yafe, bashi da wata magana. Alkali ya sake duban lauya Sabulu. "Lauya tun da wadanda aka yi kara sun ce sun yafe, ko kana da wani bincike da za kayi ga Alhaji Karma-Karma,wanda yanzu aka tabbatar shine yayi wannan ciki? 62 Lauya ya gyara rigarsa, ya amsa, kwarai da gaske ina da bincike da zanyi a kansa, don haka ina fata kotu ta bani dama. Nan aka ba shi dama yayi binciken sa,kuma aka rantsar da Alhaji akan zai fadi gaskiya. Lauya ya dubi Alhaji, a yayin da duk idanuwa sun koma gareshi, sannan ya soma magana, ban tambayar ka ba, sai dai kayi min yadda zan fahimta. Lauya ya sake kallonsa, abinda nake nufi anan shine, tun da dai Jamila ta ce kai ne kayi mata ciki, kuma daman can mun san halinka ne,me za ka iya cewa? Alhaji yayi shiru na wasu 'yan dakikoki, zai yi musu, amma sai ya dake ya dubi lauya, yace: Ai wannan al'amari abinda zan ce shine aikin kaddara ne. Lauya ya girgiza kai, ya zamu tabbatar da cewa wannan aikin kaddara ne? Alhaji ya sunkuyar da kai, "domin ya ri ga ya faru". Da kyau in ji lauya, bayan ya girgiza kai. Daga nan ya dubi Jamila, ko za ki iya tunawa da tsawon lokacin da kuke tare? Eh mun dai dade da shi. Lauya ya ce, yanzu da yake mun tabbatar shine yayi miki ciki, ga shi haihuwa yau ko gobe, ta wace hanya ki ke bukata a kwatar miki hakkinki? Jamila ta soma bada amsa, jiki na rawa, ni dai kawai idan na haihu ya amshi dansa, kuma a bi min sauran hakkina daga gareshi. Lauya ya girgiza kai, ko kina bukatar ki aure shi? Ta amsa da sauri,Allah shi kiyaye in auri wannan mayaudarin tsohon azzalumin. Daga nan lauya Sabulu ya waiwaya ya dubi alkali ya soma cewa, "ranka ya dade ya tabbata Alhaji KarmaKarma shine ya aikata wannan mugun aiki ga wannan yarinya. 63 Ranka ya dade wannan mutum a fili yake, ya lalatawa wannan yarinya rayuwa, domin 'yar wani ce, Kanwar wani, matar wani, uwar wani, kakan wani ko kuma wata,ko wasu. Ranka ya dade ina fata kotu za ta tsaya da cikakken adalcinta ta yi nazari ta fitarwa da wannan yarinya hakkinta, kuma ta ladabtar da wannan mutum domin ya zama ishara ga sauran masu hali irin nasa. Da gama bayaninsa ya koma wurinsa ya zauna. Alkali ya duka yayi rubutu na kamar rabin minti, sa'annan ya daga kai ya dubi lauya linzami mai kare Alhaji KarmaKarma, ko lauyan Alhaji yana da wata magana ko kuwa kariya? Lauya ya mike duk jikinsa yayi sanyi, ranka уа dade akan yi kariya ne idan babu wata hujja, amma a nan da akwai hujja. Hasali ma Alhaji ya amsa laifinsa, don haka ina rokon kotu wajen hukuncin ta, ta yi adalci da tausayi da sanin ya kamata, domin kaddara za ta iya hawa kan kowane daya daga cikin mu anan. Yana gamawa ya zauna. Shima alkali ya gama rubutunsa, daga nan ya daga kai yace: "Kotu ta ji bayanai daga duk bangarorin biyu, ta gama nata nazarin sai dai idan da akwai karin bayani sai ayi, domin yanzu yanke hukunci ya rage". Yayi magana, ya sake yi, amma babu wanda yace kanzil. Daga nan ya bada umarnin aje hutun rabin lokaci, daga nan a dawo ayi shara'a ta gaba, kuma a yanke hukunci. Ya mike, kuma kowa ya mike, jama'a suka soma fadin albarkacin bakinsu kafin a dawo. Da aka dawo, gabatar da kara ya mike, ya soma karanto bayanin shari'a ta biyu,yace, shari'a ta gaba,akan kisan da aka yi wa likita Dattijo ne. Daga nan sai ya zauna, alkali ya daga kai ya soma magana ya ce, shima wannan kisa ya tabbata cewa Alhaji ne ya sa aka yi shi. 64 Shi kansa bayan tsanadin bincike ya gayawa 'yan sanda cewa shine yasa aka yi kisan,kuma wai domin kada likita Dattijo ya tona masa asiri,a domin haka kotu ba ta bukatar wani lauya ya ba ta mata lokaci, domin gaskiya ta riga ta bayyana. Abu daya ne kotu za ta yi wa Alhaji, kafin ta yanke masa hukunci shine ta ba shi kamar minti daya ya roki afuwar da yake so ayi masa, don haka gareka Alhaji. Alhaji ya fashe da kuka, duk idanuwa suka koma kansa, ya ce ni dai bukatata ita ce ayi min rangwami kuma ba zan sake wannan aiki na kaddara ba. Daga nan yayi shiru, Alkali yayi kamar minti uku yana rubutu, duk kotu tayi tsit, shi ake saurare aji hukuncin da zai yanke ga shari'un nan biyu. Jim kadan ya daga kai ya soma cewa: Kotu ta tabbatar da laifin Alhaji na farko akan yi wa budurwa ciki. Mun tabbatar yayi mummnan laifi,don haka ba tare da bata lokaci ba, idan wannan yarinya ta haihu Alhaji zai bata kudi naira dubu hamsin,ta soma daukan nauyin abinci da magunguna,da suturu na jariri ko jaririya. Sannan zai bata wasu dubu hamsin,domin neman lafiyar ta,kuma zai ba ta dubu dari domin lalata mata rayuwa da yayi, bayan ya fita wayo da hankali. Sannan kuma kotu ta daure shi shekara uku, domin laifin cin amana da lalata rayuwar 'ya mace. Ita kuwa Jamila kotu ta ci tarar naira dubu goma, ko kuma daurin wata biyu, domin bata lokacin kotu da ta da bata wa Salim suna. Wadannan kudi idan su za ta bayar sai tayi alkawarin ba wa Salim da zarar sun bar nan. yi Wannan ita ce adalci ta kotu, yana gama fadin haka, ya buga kan sarki, wanda ya nuna cewa, ya yanke hukunci babu ja a kai. Ya ci gaba da cewa, kotu kuma ta daure Alhaji rai da rai. domin kisan da yasa aka yi wa bawan Allah likita Dattijo, babu wata afuwa akan haka, shi kuma daya daga 65 cikin wadanda aka kama a wurin kisan, kotu ta yanke masa hukuncin kisa ta hanyar bindigewa. Kotu tayi adalci bata bukatar wata magana kuma. Da gama fadin haka, Alhaji da yaronsa suka fashe da kuka suna rokon afuwa amma ko sauraren su ba'ayi ba. Nan take aka sa musu ankwa sai gidan maza. Ite kuma Jamila ta yi alkawari a rubuce za ta bawa Salim dubu goma,tarar da alkali yayi mata. Faruku barazana yayi ta kuka shi da mahaifiyar sa. Nan dai kotu ta watse jama'a na ta fadin albarkacin bakinsu. Iyayen Jamila sun ji kunya akan abinda suka yi wa Salim. Suka je har gida suka kaskantar da kansu, suka ba shi hakuri ya manta da komai, amma ya ci je sai da mahaifiyar sa ta sa baki, ta ce ya manta da komai, kaddara ce ta faru, kada Allah ya maimaita. Daga baya ya amince. Alhaji Hamisu ya ba shi jari ya sake amince masa. Ba'a dade ba, Jamila ta haifi da namiji. Sai dai babu wata murna. Da rana ta zagayo aka sawa yaron Dan Asali. Da ka ganshi kaga Alhaji Karma-Karm. Bayan 'yan kwanaki, sai jaririn ya ce ga garinku. Bayan ya rasu, sabon bakin ciki ya rufe Jamila da iyayenta, domin ta zama babu wani mai zuwa wurint ta, saboda bakin fenti da ta samu. Abin ya dame ta,ta rasa yadda za ta yi ita da iyayen suka kasa yi wa Salim magana ko zai aure ta. Rannan Salim ya zo gidan su, ya gaishe da iyayenta zai tafi. Sai da Jamila ta bari yayi waje, sai ta faki idon mahaifiyar ta ta bi bayansa, bai sa ni ba. Ta kira sunansa, ya waiwayo ya tsaya cik. Ya dube ta, lafiya? Ta yi murmushi ta dube shi, Salim wata magana ce zan gaya maka amma ina jin nauyi.... Yayi 'yar dariya, fadi maganar ki, babu komai. Ta soma magana, hawaye na zuba, Ni dai Salim kai nake so, ka m,anta da komai,ka ceci rayuwata daga 66 nakasa ka aure ni saboda Allah. Wallahi abin da na aikata a baya, ba komai bane sai laifin zuciya ta. Idanuwansa suka canza suna nuna alamun tausayi, ya dube ta, kada ki damu Jamila, na yarda zan aure ki muddin rai, ki kwantar da hankalin ki na amince. Tana jin haka, ta ruga da gudu ta rungume shi, suka sumbaci juna, hawaye na kwarara musu. GARGADI Ba'a yarda wani ko wata ko kuma wasu kungiyar mutane su sarrafa wannan littafin ba, ta hanyar yin fim, ko sake buga shi, ko wasan dandali, ko wasu abubuwan da suka yi kama da haka ba,sai da izinin masu hakkin mallaka. Copyrigh JAKARA 2005 67 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 5 of 5