Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 5
ciki a cikin aljihu, yayi waje jiki na rawa, ya shiga motarsa ya taka a guje ya nufi gidan likita, dakta Dattijo. Duk inda ya gibta sai an kalleshi,domin irin gudun da yake yi akan titi. Allah cikin ikonsa saboda rudewa, Alhaji na na cikin gudu bai san lokacin da ambulan din da wasikar da Jamila ta rubuto masa, ta fita daga aljihun gaba na rigarsa ba, ta yi waje, zuwa gabas, bai kula ba, burinsa ya cimma gidan dafta Dattijo. BABI NA HUDU Sha Biyu da rabi dai-dai na rana, Alhaji KarmaKarma ya taka burkin motarsa a kofar gidan likita Dattijo. Ya bude kofar ya fito, ya mayar ya rufe garam, ya sabe hannun babban rigarsa, ya soma takawa zuwa kofar gidan da take kulle. Idan ka debe manyan itatuwa,da iska dake kada ganyayyakinsu, da kuma kukan tsuntsaye, unguwar 44 babu kowa a wajc. Da zuwa bakin kofar, ya sa hannu ya soma kwankwasawa, ya dan yi shiru, yana sauraren takun sawu da ake zuwa domin watakila a bude masa. Aka murda"kofar ta ciki aka bude, sai ga likita Dattijo, wani dogon mutum fari mai farin gemu, fuskarsa 'yar karama, ga wushirya ta cikin jerin hakoransa. Suka hada ido da Alhaji, likita Dattijo yayi murmushi ta rashin sani, yana nuna bai gane Alhaji ba, shima Alhaji ya yi dariya irin ta karfin hali. Likita ya bukaci Alhaji ya shiga falon, yayi yadda aka ce, aka nuna masa wuri ya zauna. Likita ma ya zauna yana fuskantar Alhaji yana nuna damuwa ya ji ko me ke tafe da Alhaji'? shi kuwa ya gyara zama ya dubi likita. Ina ganin alamun ba ka waye dani ba ko? Likita ya gyara zama ya dan yi zurfin tunani, daga nan ya dubi Alhaji, lallai kam ban waye da kai ba, sai ka bani sani. Likita yayi shiru yana sauraren Alhaji. Yayi wata 'yar manafukar dariya ta karfin hali, ya soma yi wa likita bayani. Ba abin mamaki bane idan ka ce ba ka waye dani ba, a takaice nine Alhaji Karma-Karma, wannan da kake jin labarinsa a garí Ya kammala maganarsa cike da alfahari. Likita ya gyara zama ya tsurawa Alhaji idanuwa sosai yana nuna alamun razana da mamaki, Alhaji KarmaKarma? Ya tambayi kansa a cikin zuciya. Alhaji ya dube shi cikin alamun kasaita, kada kayi mamakin haka likita, ina fata za ka bani cikakken hadin kai akan abin da nake bukata. Ya kammala maganar yana kallon akwatin da ya zo dashi, wanda ya aje a gefe daya. Kafin likita ya ce wani abu, Alhaji ya sake duban sa yana cika baki, Likita wannan alfarma da zan tambaye ka, wata dama ce a gareka, da za kayi ban - kwana da talauci, ka fada tsundum cikin kogin arziki da wadata, 45 amma idan wannan alfarma tawa kayi watsi da ita,lallai kam ka zama maras rabo a duniya, abin da ya dace sai ka bar duniyan kawai> Likita yayi sauri ya gyara zama, ya dubi Alhaji, fuskarsa tana nuna farin ciki da kuma alamun tsoro, Alhaji ai ku namu ne, fadi duk bukatar ka, yanzu nan ayi duk abin da kace. Alhaji ya sa kafa ya shuri wannan akwati dake gabansa zuwa inda likita yake zaune, sannan ya daga kai ya dube shi suka hada ido, Likita bude wannnan akwati ka gani, idan ka bi umarni na, abninda ke ciki na ka ne, idan kuwa ka bijire......... Bai kammala ba yayi shiru ya girgiza kai. Likita yana rawar jiki ya bude, sai ga wazobiyoyi sabbi fil a dankare, Allah kadai yasan yawan su. Tun da yake aikinsa na likita bai taba ganin kudi masu yawa irin wadannan ba, musamman idan ya tuna albashin sa da ake bashi, wadanda duk yawansu a cikin aljihun wando yake zuba su. Nan take ya rude, ya dubi Alhaji. "fadi duk bukatar ka,wallahi zan yi ko menene, yana maganar idanuwan sa na kan wadannan kudin". Alhaji ya gyara zama yana mazurai, ya soma maganar sa tare da barazana da yaudara: Wata-kila ka san wata shara'a da ake yi a kotun ku,wadda ake tuhumar wani yaro Salim da yi wa wata yarinya Jamila ciki? Yayi sauri ya amsa,kwarai da gaske na sani Alhaji, hasalima ni aka ba wa bincike in gane idan da gaske Salim shine yayi wannan ciki ko kuma ana masa sharri ne. Alhaji ya girgiza kai, to me ka gano a binciken ka, shine yayi mata cikin ko kuwa sharri aka yi masa? Likita ya amsa cikin karfin hali, a gaskiya na yi bincike, wannan 48 yaro Salim ba shine yayi mata ciki ba, na riga na kammala rahoto na gobe kuma zan gabatar dashi ga alkali a kotu. Alhaji yayi murmushi, ya dan yamutsa fuska, abin da na ke so kayi min shine, wannan rahoto na ka na farko ka canza shi, ka bada rahoton cewa wannan yaro Salim shine yayi wannan ciki, ka nuna kada a zargi kowa sai shi. Idan kayi haka to wadannan kudi da kake gani sun zama naka har abada, idan kuwa ka bijire ko kuma daga baya kuma ka tona asiri, kaga makomarka. Sai Alhaji ya ciro wata yar karamar bindiga ya nuna masa. Likita yana rawar jiki, Alhaji wallahi an gama, na gane manufarka, zan yi duk yadda ka ce. Bayan kotu ta cika,kowa ya zauna a mazauninsa, magatakarda ya mike domin ya soma bayani. Yau kotun babu masaka tsinke, daga kowane lungu na garin mutane sun kwararo domin su ji sakamakon rahoton likita Dattijo. Idan shine za su ji yadda za'a yanke masa hukunci, idan kuwa rahoto ya nuna ba shi bane,za su ji yadda za'a fitar masa da hakkinsa. Shi dai Salim da abokinsa Abdul da mahaifiyarsa sun zo kotun da karfin gwiwa, da kuma alfaharin cewa gaskiya za ta bayyana, Jamila kuwa, duk da cewa ta san abin da ta kulla tare da Alhaji KarmaKarma, cikin ta ya duri ruwa tana tunani wata kila dabarar ta ta ba za ta ci ba. Alhaji Karma-Karma kuma ya turo domin ya ji yadda za'a kwashe ya kai masa rahoto. Lauyoyin wanda ake kara da kuma mai kara duk suna zaune suna saurare. Yayin da magatarkada ya mike, sai duk idanuwa suka koma wurinsa, ya bude wata 'yar gajeruwar takarda mai ruwan kwai ya soma karantawa, Yau ce ranar da aka umarci likita Dattijo ya bada rahoton da ya samo akan biniken da aka bashi, ya 47 tabbatarwa da kotu, idan da gaske Salim ne yayi wa Jamila ciki,ko kuma sharri tayi masa. Don haka kotu tana bukatar likita ya fito nan ya ba da rahoton sa. Likita garcki. Yana gama bayaninsa ya zauna, shi kuma likita Dattijo ya mike daga inda yake zaunc, ya soma tafiya zuwa inda aka ce. Shima aka bi shi da kallo, ya fito ya tsaya, idanuwa na kansa. Salim duk ya kagara ya tabbata shike da gaskiya. Likita ya bude wata 'yar takarda ya soma karantawa: Kotu ta bani umarni inyi bincike akan wannan al'amari. To kamar yadda na rantse cewa zan yi bincike na tsakani da Allah, to na yi, na auna jinin Salim da Jamila,kuma na tabbatar na gano cewa: salim shine yayi wa Jamila ciki, babu wata tantama akan wannan magana ta wa. Yana gama karantawa,sai Salim ya dube shi ya fada da karfi: Likita wallahi karya ka ke, Ka ci amana,wallahi ba ka yi gaskiya ba. Jamila tayi murmushi, gadar zaren da ta shirya ta ci nasara. Lauya filla - filla mai kare Salim ya girgiza kai ya bata fuska. Shi kuma lauya Sabulu mai kare Jamila yayi mumushi,aikinsa yayi kyau. Mahaifiyar Salim ta dubi, Abdul ranta a bace hawaye suka soma kwarara mata. Hajiya Asma'u kuwa mahaifiyar Jamila, da Alhaji Hamisu suka soma murmushi. Jama'a kuma 'yan kallo wannan ya dubi wannan, kowa na fadin albarkacin bakinsa. Likita Dattijo na tsaye ya sun kuyar da kai yana kallon kasa, ya san abin da ya kulla. Alkali ya gama rubuce-rubucen sa,daga nan ya dago kai ya tsawata sannan aka yi shiru. Ya soma bayanin sa: 48 Kotu ta ji bayanin Likita Dattijo, wanda muka tabbatar baya goyon bayan kowane bangare. Rahoton sa ya bawa bangaren mai kara galaba, don haka idan bangaren wanda ake kara sun amince da wannan rahoto, shike nan,idan suna da wata magana, sai mu ji. Daga nan yayi shiru. Lauya Filla-Filla yayi Zumbur ya mike, fuskarsa babu annuri, ya dubi alkali, ranka ya dade ina neman kotu ta bani izini in binciki likita, domin ban amince da wannan rahoto nasa ba. Da gama bayanin sa, alkali ya amince da bukatar sa,aka bashi izini. Daga nan ya fito farfajiyar shara'a ya dubi likita. Likita Dattijo kai ne ka yi bincike ka gano wannan bayani da aka bayar yanzu ko? To wacce hujja za ka bamu mai karfi wacce za ta tabbatar mana da gaskiyar maganar ka. Likita ya kalli lauya, Hujjar kenan,na bincika na gano gaskiyar lamarin. Lauya ya gyara rigarsa, ya sake tambayar sa, Likita a misali ka amince da mutum, ka tabbata ba zai ha'ince ka ba, sai ka gwada shi akan wani abu wanda kai ka riga ka san yadda yake, saikuma kaga wannan wanda ka amince masa ya ba ka rahoton da kake kokwanto a kansa,me za kayi? Likita ya yi gyaran murya, tana rawa, sai in ki binciken sa? Lauya Filla-Filla ya dube shi, to ni ma ban amince da kai ba, akan wannan rahoto naka, don haka ni ma zan bincike ka. Lauya Filla Filla ya dubi alkali ya soma magana, ranka ya dade, an nuna mana cewa ka bar abin da kake kokwanto, ka koma wanda ba ka kokwanto, don haka ni a matsayina na lauya filla-filla,ina so ayi ta fillafilla, kuma ina karar likita Dattijo akan cin amana da canza rahoto, don haka ina nema kotu tayi wani abu akai, yana gamawa ya koma ya zauna. 49 Sai lauya Sabulu yayi zumbur ya mike, ya dubi alkali yace, ranka ya dade, bayanin da lauya yayi yanzu,babu komai a ciki sai soki burutsu,domin kuwa, Likita wanda kotu ta amince masa shi yayi wannan bincike, kuma ya bada rahotonsa,don haka ina fata kotu tayi watsi da wannan shara'a,kuma ta dau matakin ladabtar da wanda ake kara,domin ya tabba shine yayi wa wannan baiwar Allah ciki. Yana gama bayaninsa shima ya zauna. Alkali yayi 'yan rubuce - rubucensa, daga nan ya dago kai ya soma magana, Kotu ta ji bayanai daga duk bangarorin nan biyu, abinda ya kawo mu nan shine mu tabbatar da adalci a tsakanin al'umma. Bayan rahoton da Likita ya kawo mana, wanda ake kara ya nuna rashin amincewar sa da haka. Kotu ta yi nazari, ta amincewa lauyan wanda ake kara ya binciki Likita. Amma idan bincikensa ya nuna Likita ya fi shi gaskiya, likita zai iya nema a bi masa hakkinsa. Don haka kotu ta dage wannan shari'a har sai sati mai zuwa. Ta amince likita ya tafi ba tare da beli ba, shi kuwa wanda ake kara kotu ta bada izini a kai shi ruman har zuwa mako mai zuwa. Wannan adalci ne na musamman na kotu. Yana gama bayaninsa, sai ya mike,jama'a ma suka mike, kotu ta dage zamanta. Abdul ya dubi mahaifiyar Salim wadda take faman kukan, bayan sun dawo daga kotu, yana ba ta hakuri akan abinda ke faruwa, "baba kada ki ki damu kan ki da komai,ni na yi Imani Salim ba shine ya aikata wannan al'amari ba, kokari dai ake a makala masa dole" Ta dube shi tana kokarin share hawaye, "Abdul kai dai kana goyon bayan abokin ka ne, amma ai ge likita ya bada rahoto cewa, lallai Salim ne yayi wa wannan yarinya ciki". Ta kammala maganar tana cewa, oh, ni na 50 shiga uku, yau ni a duniyan nan,ina zan saka kai na,dan kuka mai ja wa uwa jifa. Ta sake fashewa da kuka.. Ba haka bane baba, wallahi ni ina shakkar rahoton wannan likita, kin san halin duniya, za'ayi yin komai, domin a batawa Salim suna. Shi yasa ki ka ga lauya ya nuna bai amince ba, da akwai abinda ya lura dashi, kuma Allah ya kai mu sati mai zuwa, da yardan Allah gaskiya za ta bayyana. Bayan Abdul ya gama tausar zuciyar ta, sai ya sallame ta kafin ya dawo da yamma su tafi wurin Salim da ke zaman ruma. Ya fito waje, ya tura kekensa, ya haye, ya soma tafiya zuwa gida. Yana tafiya,ransa a bace, yana tunani, irin sharrin da ake so a kullawa abokinsa. Shi ya tabbata ba Salim yayi wa Jamila ciki ba, ba aikinsa bane. Da aikinsa ne, da kuwa ya sa ni, domin shekaru da yawa suna tare. Wata katuwar mota ta zo ta wuce shi fuuuu, iska ta buga, har takardu da sauran tarkace suka warwarse, ya ga wata doguwar ambulan mai kyan gaske, iska ya kada ta gaba kadan. Har ya wuce, sai wata zuciyar ta gaya masa ya kamata ya duba wannan ambulan din nan, wata kila yayi gamo da katar, wato kudi ke ciki, ko kuma wani abu mai muhimmanci. Nan da nan ya sauka akan keken, ya tokare ta gefe daya, ya soma takawa zuwa inda ambulamn din take. Da zuwa ya duka ya dauka ya soma dubawa, yayi mamaki da ya ga an rubuta a jikin ambulan din da manyan bakake kamar haka: ZUWA GA ALHAJI KARMA-KARMA. Ya fada a cikin zuciyarsa, Alhaji Karma-Karma, wannan matsayacin mai kudin da na sa ni? Ni kuwa sai na karanta na ga abinda ke ciki. Ya bude jiki na rawa, ya soma 51 karantawa cike da mamaki. Har ya kawo inda aka rubuta kamar haka: To na san watakila kana sane cewa na lakafawa Salim mai aikin gidan mu wannan ciki da kayi min, har sbin ya kai kotu, yanzu ma alkaliya bada umarnin likita ya auna mu, ya gane idan cikin da gaske Salim ya yi min, ka san kuwa dole zai gane ba cikin Salim ba ne. Idan haka ta faru kaga na ji kunya,kuma ya zama dole in fallasa ka cewa kai ne kayi min wannan aikin. Shawara anan itace ka hanzarıa ka sami ganin dakta Dattijo sanannen likitan nan mai yi wa kotu aiki, domin ku daddale dashi, ya canza bayani kuma ya lakafawa salim wannar ciki dole. Ka hanzarta Alhaji, kada dare yayi wa mai wankin hula. Nice Jamila. Abdul ya girgiza kai, wannan wasika ta daure masa kai kamar a mafarki,ya ma rasa abin yi. Sai kawai ya saka wasikar a aljihu ya haye kekensa, sai gidan fillafilla. BABI NA BIYAR Jiki na rawa, Abdul ya isa gidan lauya Filla-Filla yana tafiya yana tunani, watakila kaya ne ya tsinke a gindin kaba. Idan haka ne kuwa,lallai Ubangiji ba azzalumin kowa bane. Da zuwa kofar gidan, ya sauka daga kan kekensa,ya tokare ta ya je bakin kofar gidan ya kwankwasa, ya tsaya yana saurare. Lauya Filia-Filla ba shi da mata, shi kadai ne a cikin gidan. Yayin da ya ji aa kwankwasa kofa ya taso da sauri ya bude, suka vi ido hudu da Abdul cikin mamaki da annuri a fuska, ya dube shi, Abdul na ganka da rawar jiki ne, lafiya dai ko? Abdul ya rike masa hannu suka yi ciki, ba tare sun rure kofar ba, lafiya kalau, takarda ce na tsinía, nace bari na kawo maka wata-kila alheri ne. 52 Yana gama fada suka zauna su na kallon juna. Abdul ya mikawa lauya wannan ambulan yana murmushi, Lauya ina tafiya a hanya na tsinci wannan ambulan din, na bude na karanta, sai na ga kamar a mafarki yayi kama da hujjojin da muke nema akan maganar Salim da Jamila. Lauya yayi hanzari ya fisge, ya bude da sauri ya soma karantawa yana girgiza kai cike da mamaki ya gama karantawa, ya kai ya dubi Abdul cike da mamaki, Abdul ya aka yi ka samu wannan takardan, ko kuwa Allah yayi niyyar ya yanke mana wahala ne? Abdul ya gyara zama, lallai ina fatan haka, Lauya yayi ajiyar zuciya, lallai kuma zamu yi bincike akan haka, Allah yana tare da mai gaskiya. *********** ** Alhaji Karma-Karma,ya dubi na hannun damansa, Namuzu kawali,ransa a bace, yana ganin asiri zai tonu idan ba an tashi tsaye ba, abubuwa biyu ne suka daga masa hankali. Ga shi duk dabarunsa zasu tafi a banza,kuma ya jefar da wasikar da Jamila ta aiko masa. Yana bakin cikin idan ta fada hannun wadanda suke abokan gaba, shike nan asiri zai tonu. Namuzu wai wace hanya ce mafita, ka duba duk da yadda na kashe kudi na bawa likita Dattijo ya canza rahotonsa,tsinannan lauyan nan Filla-Filla,sai da ya dagula al'amuran, ka ga ya zama babban makiyi shima. Namuzu ya shafa gashin bakinsa, ya dubi Alhaji, Alhaji ai kowa ya ci tuwo da kai miya ya sha, ina ganin sai ka hada da daukar rai, wannan al'amari zai tafi dai-dai. Amma idan ka tsaya lakwa-lakwa ko tausayi, lallai asiri zai tonu, ya gama maganarsa yana nuna rashin tausayi. Alhaji ya gyara zama, yayi dan murmushi kwarai Namuzu, kayi tunani, ni ma ina ganin idan ba na raba 53 lauya filla-filla da duniya ba,zai kwance min zane a kasuwa. Kai! Kai! Kai! Namuzu ya amsa, ya ci gaba da cewa Alhaji ai ba lauya za ka kashe ba Alhaji,wanda lauya ke tuhuma za'a raba da duniya, wato likita Dattijo, domin yanzu idan ya sha wahala zai tona maka asiri, idan kuwa ya bar duniya,shi ma lauya babu wanda zai bincika,ka ga dole ayi amfani da rahoton likita da ya bayar da farko. Alhaji yayi farat ya amsa,kwarai Namuzu, tun kafin in yabawa aya zaki,kamata yayi ka shugabanta,aje har gida a raba likita Dattijo da duniya, mu ga wanda lauya zai tuhuma. Haka za'ayi a daren yau. Karfe biyu na dare, gari yayi tsit, baka jin komai sai haushin karnuka,da kukan tsanya, gari duk babu farin wata,idan ka debe Namuzu da sauran mutane uku da suke tare da shi suna sanda a kofar gidan likita Dattijo,babu kowa a unguwar ta turawa. Shi kuwa yana ciki yana sharar barci. Namuzu tare da sauran suka lababa ta baya, suka kama katangar suka haura, suka dira a ciki. Duk kofofin da zasu kai mutum inda likita ke sharar barcinsa a rufe suke. Namuzu ya tsaya yana tunanin yadda zasu yi. Wata dabara ta zo masa. Ya tsaya a bakin wata kofa, yana kwankwasa ta a hankali, sauran kuma suna labe. Likita yana barci ya ji kamar daga sama ana kwankwasa masa kofa yayi firgigi ya tashi ya zauna ya kunna lantarki, haske ya bi duk dakin ya tashi ya dau wata 'yar karamar bindiga tasa, yana sanye da doguwar riga ta barci, ya nuti zuwa kofa. Namuzu da sauran na kallon sa. Da ya je bakin kofar ya ci birki,wanene yake kwankwasa kofar nan? Shiru babu amsa. Namuzu dai yana labe, da wukarsa mai daukar idanuwa. Likita yayi karfin hali,ya kai hannu ya murda mukulli, kofar ta bude, ya soma turawa a 54 hankali,bindigarsa na rike a hannun damansa. Ya tura kofar ta bude a hankali. Bai sa ni ba, da fitowarsa, Namuzu ya shaki wuyansa suka soma kokawa, har ya harba bindigar sama, har masu gadi suka ji karar harbi, suka ji kuma ana cewa La'ILAHA ILLA LLAHU ku taimaka zasu kashe ni. Da jin haka, masu gadin suka tashi da gudu, suka nufi kofar gidan, su na haska tocilan. A dai-dai lokacin kuma, Namuzu da sauran wadanda suke tare, sun ci karfin likita Dattijo. Sauran suka danne shi da karfin tsiya. Namuzu yasa sharbebiyar wukarsa, yayi masa yankan rago. (Allahu Akbar). Allah ya raba mu da rashin imani, amin. Dai-dai masu gadin nan sun shigo. Nan fa aka soma dauki ba dadi. Namuzu da suaran su na neman su gudu, masu gadi na neman su cafke su, saboda ganin abinda suka aikata. Namuzu ya samu ya tsallake ya gudu, haka sauran mutum biyu. Mutum daya da ya rage, kafin ya samu ya gudu, aka samu cikin masu gadin, wani gwanin saiti ya auna kafarsa da bindiga, ji kake daram. Yayi kara, wayyo Allah, ya fadi yana shure-shure-. Likita Dattijo kuwa yana gefe cikin jini, ya riga mu gidan gaskiya. ********* ************ *** Duk gari, labari ya ba zu akan irin kisan gillar da aka yi wa likita Dattijo. Ba a san ko su wanene ba, amma an cafke mutum daya, wanda ake tabbatar da cewa za'a samu bayani daga gareshi. Za'aji wane yasa su, kuwa saboda wani dalili? s4 af4 ofe sfa sle Dja eja aha aft ahe ohe sje aje eje eje sfa Idanuwan Alhaji. Karma-Karma sun fito, musamman labarin da ya samu cewa an cafke daya daga cikin yaransa da suka je wajen kisan likita Dattijo. Shi 55 yana ganin laifin Namuzu ne, wanda bai ba su cikakken vadda za su yi ba. Alhaji ya tashi daga inda yake zaune jiki na rawa, ya nufi inda Namuzu yake tsaye, yayi tsuru-tsuru. Ya rike masa wuyan riga, ya daga hannu, ya sharara masa mari tas! Ya dube shi. "Mutumin banza da wofi, kai ne kayi sakaci, aikin ka bai yi kyau ba". Namuzu ya dubi Alhaji cikin fushi, ga ka nan matsiyaci, mutumin banza maci amana maras imani. Sai ya nufi waje, ya tsaya a dai-dai kofar fita, ya waiwayo ya dubi Alhaji, Na tafi, bani ba kai har abada, kuma asiri zai zai tonu. Ya juya ya wuce ya tafi. ********** A Ofishin 'yan sanda, jami'an leken asiri, suna ta binciken dalilin kisan da aka yi wa likita Dattijo. Tuni dai labari ya bazu ko ina da ina. Mutane sai zuwa suke su na ba wa idanuwansu abinci. Aka tura 'yan sanda suka dauko gawarsa aka kai mutuware. Shi kuwa wanda aka kama, bayan an kai shi asibiti anyi masa maganin harbin, ya samu sauki, hankalinsa ya zo masa. Daga nan aka soma bincikensa, ta hanyar amfani da wutan lantarki, da sauran hanyoyin horaswa. Bukata ita ce, ya bada bayanin wanda ya basu umurnin kashe likita Dattijo. Bayan ya sha bakar azaba, sai ya bayyana cewa Alhaji Karma-karma ne ya tura su. Koda jin haka, mamaki ya kama jami'an tsaro. Nan da nan, aka bada umurni ga wata bataliyan 'yan sanda su je su kamo shi. Shi kuwa yana gida hankalin sa ya tashi. 'Yan sanda ne ta ko'ina sun firfito daga cikin motoci guda biyar, duk sunyi wa gidan Alhaji Karma56 karma kawanya. Kowanne rike da doguwar bindiga, yayi balas yana jiran ko ta kwana. Da saukan su, wanda ke shugabantarsu, ya attakura yayi harbi sama. Ji kake daram! wanda ya gifta ko tsuntsu ne, idan bada izini ba a kakkabo shỉ. Alhaji Karma-karma yana zaune a falonsa, tare da matarsa, tunani ya dame shi, sai ya ji harbi Kofar gidansa. Zuciyarsa ta buga ras! Jiki na rawa, ya tashi ya bude wundo ya leka. 'Yan sanda ne iyakan ganinsa. Hankalinsa ya tashi, lallai yasan asiri ya tonu kenan, ya tabbata shi aka zo a kama. Ya waiwayo ya gayawa matarsa, ita ma hankalinta ya tashi. Yana wannan ya ji ana kwankwasa masa kofa, ya tafi da rawar jiki ya bude, suka yi ido hudu da shugaban 'yan sanda. Ba da bata lokaci ba, aka gaya masa an zo a kamashi ne, saboda tuhumarsa da akeyi. Koda yake yasan asirinsa ne ya tonu, amma sai ya tsaya barazana wai a dole shi mai gaskiya. Da 'yan sanda suka ga zai tsaya soki burutsu, sai shugabansu ya bada umarnin a dauke shi. Nan take aka yi cuku-cuku dashi, aka daga shi cak, matar tana kallo tana kuka da salati, aka yi waje dashi, aka jefa a mota. Dai dai za'a jefa shi a mota, sai ga dansa Faruku barazana ya zo a motar sa, ya fito da sauri, yana tambayar 'yan sanda dalilin kama mahaifinsa, amma babu wanda ya kula shi. Nan take aka tafi dashi, sai ofishin 'yan sanda. Da zuwa babu kakkautawa aka soma binciken Alhaji ya fadi dalilin da yasa ya bada umarni a kashe likita Dattijo. Da farko ya karyata, amma da aka kawo wannan da aka kama ya shaida cewa lallai shine ya basu umarnin su yi haka, sai Alhaji yayi tsuru-tsuru. Ana haka, Kwamishinan 'yan sanda tare da alkali mai gaskiya suka zo domin labarin da suka sınu. Da zuwa, duk 'yan sanda suka kame, suka sara domin girmamawa, Alhaji na zaune 57 ankwa kafa da hannu. Kwamishina ya dube shi cikin bacin rai. "Alhaji daman muna da labarin irin ta'asar da kake yi a garin nan, domin kana da kudi, kuma da yake kana ganin kamar kafi karfin doka al'amarin ya wuce lalata 'yan matan mutane, har ya kai ga zama dan ta'adda,mai bada umarnin ayi kisan kai. Kwamishina ya matsa kusa dashi, ransa ya bace, ya cakumi wuyan rigarsa, ya dago kansa, ya daga hannu ya sharara masa mari tas! Ya fada da karfi, ko kai ne kayi masa rai da ka sa aka kashe shi? Alhaji yayi shiru. Ina tambayar ka, ko kuma yanzu nasa bindiga in harbe ka, kai ma ka ji idan da dadi kisan. Kwamishina yasa hannu a aljihu ya ciro bindiga yar karama yayi saitin Alhaji. Za ka gaya min dalilin kisar ko sai na kashe ka yanzu nan? Daga bayan sa, sai ya ji ance, ranka ya dade kada ka kashe babban mai laifi, kamin a fitarwa da jama'a hakkinsu, ni ma ina karar sa! Kwamishina da sauran dake wurin suka waiwaya da sauri su ga mai maganar. Sai suka yi tozali da Lauya Filla-Filla tare da Abdul. Lauya na rike da wata doguwar ambulan. Nan da nan ya karaso, Abdul na bin bayansa, ya tsaya gaban Kwamishina, yayi masa ladabin da ya dace dashi. Daga nan ya ciro takarda daga cikin ambulan din ya soma cewa, ranka ya dade,wannan takarda da ka gani, wasika ce da wata yarinya ta aikawa wannan azzalumin da dalilin wannan wasika idan ka karanta, za ka ga ya dace da halin da ake ciki, domin kuwa wacce ta aika masa da wannan wasikar kara ta kawo cewa wani saurayi yayi mata ciki, amma sai ga shi an tsinci wannan wasikar, har ga inda ta aikawa Alhaji cewa ta lakafawa wannan saurayi ciki, don haka...... 58 Bai kammala ba, Kwamishina ya fizge takardar ya kammala karantawa. Ransa a bace, ya daga kai, ya dubi 'yan sanda, ya ba da umarnin a tafi a kawo masa Jamila, nan take aka bi umarninsa. Bayan kamar minti sha biyar sai ga ta tare da iyayenta an ingizo keyar su. Da ganinta cikin ta yayi girma, dole ko makaho zai gane. Da zuwa Jamila ta hada ido da Alhaji sai ta sunkuyar da kai kasa, shima ya sunkuyar da nasa. Kwamishina ya dube ta cikin alamu irin na tsoratarwa, ya bata wasikar nan, ta karba jikinta na rawa. Ko kin san wannan wasikar? Ta soma dubawa,ta daga kai ta kalleshi, ya daka mata tsawa, ba kallona nace kiyi ba,kin san wannan takardan nace? Tayi shiru bata ce komai ba. Mahaifiyar ta dube ta da nuna tausayi, Jamila ki gaya musu gaskiya, kin ga al'amarin sun dagule. Hawaye süka soma kwarara mata, bakin ta na rawa, ta dubi Kwamishina, Eh! na san

Chapter 4 of 5