ma a maganar dansa Faruku, wanda ya ci mata
mutunci ita dai a karshe ta gano dabara.
***** **************
Sati daya kenan Salim yake cike da mamaki, ta
yadda Jamila ke jan sa a jiki. Ta sakar masa jiki, iyakar
saki. Hatta idan za ta ci abinci sai ta kirashi, ko kuma su
raba dare suna hira. Idan ya tambaye ta dalilin da yasa
take masa haka, sai tayi dariya ta dubeshi da manyan
fararen idanuwanta, ta ce, uhum Salim, menene kuwa, sai
Kauna?
Shi kuwa ya saki jiki tana ta yaudararsa, domin ta
samu hujja a kansa. Ta san cewa ba da dadewa ba, bakin
alkalami zai bushe za'a gane tana da juna biyu, kuma za'a
ce ma ta ta fadi wanada yayi ma ta, sai ta lakafa
masa.Haka suka ci gaba har zuwa wani dan lokaci kafin
Salim ya samu sabon sauyi a rayuwarsa.
Da daddare wata juma'a Salim yayi doguwar hirn
da Jamila har misalin sha biyu, daga nan ya sellameta ya
tafi. Bayan tafiyarsa da kamar minti goma tana kwance
akan gado, al'amuran duniya na ci gaba da damunta,
musamman gashi cikinta ya kai watanni biyar, amma babu
wanda ya gane. Tana cikin wannan tunani, sai ta soma
ganin jiri, dakin ya soma juya mata, nan da nan sai tari,
sai amai, ta kasa tashi, duk amai ya bata zanen gado.
Hajiya Asamu'u, tana daki ta ji kakarin amai, tare
da kuka, nan da nan ta fito da sauri, zuwa dakin Jamila.
Da zuwa ta tura kofar da karfi ta shiga, ta samu Jamila
babu inda take. Ta fashe da kuka, hawaye na zubo mata;
Lal'ilaha Illallahu.... Jamila me ya sameki, na
shiga uku, ga shi dare yayi babu wanda zai kai ki asibiti.
Jamila ba ta iya magana; ta mikawa mahaifiyar
hannu, tana fada a hankali;
Mama a kai ni asibiti. Zan mutu!
Hajiya ta sake rudewa, tayi waje gidan makota, ta
shaida musu abinda ake ciki. Nan da nan aka taimaka, aka
dauki Jamila a cikin mota, sai asibiti. Da zuwa babu bata
lokaci, wani likita ya soma duba ta, domin ya gano abinda
ke damunta. Hajiya Asama'u tana gefe duk hankalinta a
tashe, ta kagara ta ji abinda ke damun Jamila.
Bayan kamar awa guda, likitan ya waiwayo ya
fuskanci hajiya wacce take zaune, tayi tagumi.
"Hajiya a gaskiya 'yarki ciki gareta wata biyar,
kuma babu dama a zubar dashi, idan kuwa aka ce za'a
zubar lallai za ta mutu, dole sai dai ta haihu".
Hajiya ta mike da sauri ta yi salati, jiri ya debeta,
ta yi kamar zata fadi, sai da likita ya rike ta. Ta soma
magana; La'ilaha Illallahu; Ni kuwa wanene ya bata min
rayuwar yata? Amma ko wanene ya gama damu, yanzu
me zance wa mahaifinki Jamila? Sai ta fashe da kuka da
karfi har dakin yana amsawa.
********* *soje * en ejn ***** ** **** ****** *
Hajiya Asama'u ta dubi Jamila tana niyyar ta yi
mata magana. Koda ganin Hajiya kasan ta fita daga.
hayyacinta. Tsakanin daren jiya, zuwa safiya da suka
dawo gida, ta zama kamar wacce ta shekara babu lafiya,
annurinta ya canza, tayi baki, duniyar ma ta yi mata baki.
30
'Yarsu ta jawo musu abin kunya abin fadi, abin gori, abin
tir da Allah wadai. Menene abin yi yanzu? Sai ta tambayi
Jamila wanda yayi ma ta wannan aika-aika, domin daukar
mataki a kansa.
Hajiya ta dubi Jamila, wacce take zaune ta
sunkuyar da kai tana kuka;
"Ba kuka za kiyi ba, ba lokacin kuka bane yanzu,
da kinsan za kiyi kuka da baki saka kanki a cikin wannan
rayuwa ba, yanzi ki gaya min wanda ya aikata miki
wannan danyen aikin kafin babanki ya dawo musan nayi,
kaddara ce ta faru babu yadda za'ayi".
"Jamila bata kulata ba, sai kuka take yi. Koda
yake kuka ne na munafunci, domin tasan shirin data yi,
sai gabatarwa ya rage"
Jamila da ke nake, ko kuwa. Za ki ci gaba da bata
min rai ne, bayan bakin cikin da kika jawomin, ki gaya
min nace miki!
Ta kammala maganar, tana nuna damuwarta a fili,
idanuwanta na kawo kwalla.
Jamila tayi karfin hali, domin ta gabatar da abinda
tayi niyya!
Tana gamawa ta sake fashewa da kukan
munafunci.
Hajiya ta mike da sauri jikinta na rawa tayi salati,
ta sanar da Ubangiji. Ta kalli Jamila cike da mamaki da
alamun razana. Kina nufin Salim direban mu? Eh Mama,
shine; Jamila ta amsa cike da karfin hali.
Hajiya ta fashe da kuka; tayi salati; wayyo
Aliah,amma Salim ya ci amana, gaskiya daman yake
shisshige miki. Tana gama fadin haka, Salim yayiі
sallama ya daga labule ya shigo ya tsuguna ya gaishe da
Hajiya. Bata amsa ba, sai dai ya ga ta fashe da kuka, ta
kalleshi.
31
"Salim ka ci amanar mu, Allah ya isa ya saka
mana, ashe duk yadda muka rike ka da amana, shine za ka
yiwa Jamila ciki, Allah ya isa. Salim ya mike tsaye da
sauri, makullin mota da ke hannunsa ya fadi kasa, ya kalli
Jamila, kanta na sunkuye, ya kalli Hajiya suka hada ido,
ya soma magana bakinsa na rawa. Hajiya da gaske kike
ko wasa? Cikin lafiya sai đai ayi min sheri wallahi. Ya
kammala bakinsa na rawa, idanuwansa suka kawo kwalla.
Da rufe bakinsa, sai ga Alhaji Hamisu ya daga
labule ya shigo. Gaba daya dake cikin dakin, akayi tsurutsuru. Jamila kanta na sunkuye.
Alhaji ya dube su bi da bi;
Lafiya na ga anyi tsuru-tsuru, ku gaya min mana,
kada ku boye min komai.
Hajiya ta fashe da kuka ta soma gayawa Alhaji
halin da ake ciki.
Da ta gama gaya masa, sai akwatin dake hannunsa
ya fadi kasa, ya dubi Salim, wanda ya sunkuyar da kai.
Salim me yasa ka ci amanar mu, ka gaya min
gaskiya in san abinda zan yi asiri a rufe.
Salim ya tuma ya rantse da Allah bai san wannan
labari ba. Aka tambayi Jamila, tace ita shi ta sani. Da
Alhaji ya ga ya bi ta lalama amma Salim bai amince da
nauyin da ake so a dora masa ba, sai ya fusata, zuciyarsa
ta rika tafarfasa. Bai san lokacin da ya daga hannu ya
tsinke Salim da mari ba tas!
BABI NA BIYAR
Bacin rai da tsananin tunani sune suka sa Salim
duk ya lalace, domin tunanin halin da yake ciki. Ya
gayawa Alhaji Hamisu gaskiya cewa ba shine yayi wa
Jamila ciki ba,amma ya ce sam bai yarda ba, musamman
da Jamila ta shafawa idanuwanta toka tace ita shine yayi
mata. Alhaji yayi fushi da Salim sosai, domin a ganinsa
32
shine ya aikata wa Jamila wannan abu, har yana ce masa
ya ci amana. Ba tare da dogon bincike ba, Alhaji ya kai
Salim ofishin 'yan sanda domin a tuhume shi, ya amsa
laifin da aka ce yayi. Tun jiya yake tsare, a dakin kulle
masu laifi na ofishin 'yan sanda, babu abinda yake yi sai
kuka yana tunanin yadda aka kala masa laifin da bai yi ba,
ba tare da wani bincike ba. Mahaifiyarsa da ta samu
labari, ta je musamman ta roki Alhaji Hamisu arziki ya sa
a fito dashi, domin a sasanta, amma ya ce fatau ba za'ayi
haka ba, domin Salim ya ci amanarsa, don haka ba zai
kyaleshi ba. Aka ci gaba da tuhumar Salim, shi kuwa yace
sam bashi bane.
Salim na zaune akan siminti a cikin dakin da aka
kulleshi a ofishin 'yan sanda, zarnin fitsari da wari duk
sun dame shi. Domin wuri ne mai kazantar gaske, ga
kudin cizo ga masifaffun sauro, ga shi babu sakewa, baka
da wani 'yanci, sai yadda akayi dakai. Kai Allah ya raba
musulmi da shiga wannan wuri, albarkacin Annabi
Muhammadu (S.A.W) amin.
Salim na daga kai, sai ga mahaifiyarsa, tare da
wani abokinsa na kusa mai suna Abdul sun zo, wani dan
sanda dogo, mai faffadan fuska, wacce ba ta da annuri,
shine yayi musu rakiya. Abdul na rike kwanon abinci,
mahaifiyar Salim na binsa a baya. Salim na zaune, ya
hada kansa da gwiwoyi, sai ya ji ance; Salim.
Ya daga kansa da sauri, sai yayi tozali dasu. Ya
dafa bango ya mike, ya tashi yayi 'yar tafiya, ya zo ya
tsaya. Dogayen karafuna da akayi katanga dasu sune ke
tsakaninsu. Ya hada ido da mahaifiyarsa, sai kwalla suka
cika mata idanuwa, ta dube shi.
"Salim kaga abin nan yayi karfi, don naji ance
gobe kotu za'a kai ka, idan kasan kai ne ka aikata wannan
abu ka gaya min gaskiya in je in ba wa Alhaji hakuri,
domin kada aci mana mutunci, kaga bamu da wani a
33
mataimaki sai Allah. Ta fashe da kuka, Abdul ya rika bata
hakuri.
"Haba Mama,ai ya kamata yayi kiyi shaida ta.
Salim ya soma mayar mata da amsa, hawaye na kwarato
masa; ya ci gaba; "Mama ba wai ina alfahari bane, amma
da ace ina wannan harkar, dakin sani, ko kuwa da kin ji
labari. Ya kammala maganarsa yana cewa; waliahi Mama
gaskiya dokin karfi ne, Jamila ta yi min sheri. Iyayenta sun
amince da haka babu bincike don haka mu sa musu
idanuwa, Allah baya barci, zai fallasa maras gaskiya.
Yana gamawa yasa rigarsa ya share hawayen dake
kwararo masa.
Mama kada ki damu, na yarda da Salim na
amince masa, Abdul ya amsa, ya ci gaba da maganarsa
yana jaddadawa.
Mama Salim ba shi yayi wannan abu ba, kuma
Allah zai bayyana mai gaskiya, Allah ya kaimu goben, aje
kotun wa ya ke tsoro?
********
Tunda sanyin safiya, mutane daga cikin gari suka
soma kwarorawa zuwa babban kotun daukaka kara dakе
kan titin 'yanci, domin su saurari yadda wannan shari'a za
ta kwashe. Labari ya watsu ko ina cewá Jamila, 'yar gidan
sanannen tsohon ma'aikacin gwamnatin nan Alhaji
Hamisu. Da yawa mutane da suke fadin albarkacin
bakinsu sukan ce: ai babu mamaki.
Da yawa da suka san Salim, idan suka ji ance
shine yayi wa Jamila ciki, sai su cika da manaki, domin
sanin halayensa masu nagarta. Za ka ji suna cewa; "Allah
Sarki ta lakafawa Salim, irin su sun fi talka ta'asa"
ta Ko wasu jinsi da nasu ra'ayin, shi yasa ake
tururuwa a zo kotu a ji yadda za ta kare. A nan ne zaka
gane mutanen duniya, idan abun alheri ya samu saboda sins is a
34
bakin ciki da hassada, ba za ka ji ana labarin ba, amma
idan sheri ya samu mutum, sai ka ji duk labari ya bazu a
gari wasu na dariya, wasu na shewa. Ashe haka duniya
take, duniya mai wuyar gane hali, abokinta da shi za'a
kulla a cuce ka. Lallai mu yi takatsantsan.
Alhaji Karma-karma yana gida ya samu labarin
halin da ake ciki. Hankalinsa ya tashi domin kada magana
ta yi zafi Jamila ta tona masa asiri. Amma kuwa daga
baya ya kanne, domin idan haka ta samu, sai ya karyata
idan yaso ayi ta tafka shari'a. Shima Faruku barazana
wannan labari ya zo masa. Koda yake yasan ba shine ba,
amma hankalinsa ya tashi, kada Jamila tace shine, gashi
kuma an kawo wani alkali sabo, wanda baya amsar cin
hanci sai dai tabbatar da gaskiya. Asabe naira ma, da
Bilkisu kwandala sun yi bakin ciki, musamman saboda
shakuwar da suka yi, jikinsu kuma yayi sanyi. Kai labari
duk ya bi ko ina da ina a cikin gari.
********* ************ ****
Aka shigo da Salim cikin kotu, wani ramammen
dan-sanda na binsa a baya. Jama'a suka bi shi da kallo.
Aka shigo dashi wani wuri da aka zagaye da katako, ba'a
ganin komai nasa, sai daga kirjinsa zuwa kansa. Aka kira
Jamila, ta ttaso daga inda take zaune tare da iyayenta. Ta
taso tinkis-tinkis. Mutane suka bi ta da kallo. Sai nan da
nan mutanen suka soma kallon junan su, suna 'yan
kananan maganganu. Ita ma aka shiga da ita irin wannan
wuri da aka shiga da Salim. A can daga sama, alkali mai
gaskiya shine yake zaune, yasa wani farin gilashi, gabansa
da wasu manyan littafai, ga suturun alkalai ya sanya.
Daga kasa kuma a gabansa, magatakarda ne, da mai
gabatar da kara, suke zaune akan kujeru a gaban wani
bankamemen teburi. Daga hannun hagu kuma, lauyoyi ne
su biyu. Daya shine wanda Alhaji Hamisu ya dauko haya
domin ya kare Jamila, daya kuma wani abokin Abdul ne,
35
shima kwararren lauya ne, domin ya tsayawa Salim. Shi
kansa Abdul da mahaifiyar Salim suna cikin jama'a sun
zauna, su ji yadda za'a kwashe.
Sajen gishiri, wani kakkauran dan-sanda, mai
bakar fuska, ga gashin baki da jajayen idanuwa, kayan
sarkinsa duk sun kode, shine mai gabatar da kara. Ya
mike ya soma karanta karar yana cewa:
Ranar lahadi, ashirin da biyu ga watan Octoba na
shekarar alif dari tara da casa'in da biyar, Jamila 'yar
gidan Alhaji Hamisu, ta kawo rahoton cewa Salim
Kallamu, wanda yake musu aiki a gida yayi mata ciki,
amma ya ce ba shine yayi ba. 'yan sanda sun kawo shi
ofis, anyi bincike shi kuma ya karyata, shine mai kara ta
ce a kawo maganar kotu domin a fitar mata da hakkinta;
yana gama karanatawa sai ya koma ya zauna. Alkali ya
sunkuyar da kai yayi wasu 'yan rubuce-rubuce, sa'annan
ya dago kai, ya dubi wajen lauyoyi;
Lauyoyin mai kara da wanda ake kara kun ji
bayanin mai gabatar da kara, ko da akwai me wata
magana?
"Lauya Sabulu, lauyan mai kare Jamila yayi
zunbur ya mike, mutane duk aka bi shi da kallo, shi kuma
ya dubi alkali; ranka ya dade ina so kotu ta bani izini in
gabatar da wani bincike akan wanda ake tuhuma. Yana
gama maganar ya zauna.
Lauya filla-filla, wanda ke kare Salim da ake
kara, shima ya mike; ya dubi alkali;
"Ranka ya dade, a dokar shari'a ta kasa, lauyan da
ke kare wanda ake kara shine ya kamata ya soma
bincikensa ga mai kara, don haka ina fata kotu tayi watsi
da bukatar da lauya yayi yanzu, ta bani dama inyi bincike
na musamman a kan mai kara.
Yana gamawa, sai ya zauna. Alkali yayi 'yan
rubuce-rubucensa, ya dago kai yace, "kotu ta bada dama
36
ga lauya mai kare wanda ake kara yayi bincikensa ga mai
Kara.
Koda fadin haka lauya falle-falle, ya mike jama'a
suka bishi da kallo, ya soma tafiya zuwa farfajiyar
bincike, rigarsa ta lauyoyi tana jan kasa, da yake gajere
ne. Da fitowarsa, sai magatakarda ya mike, rike da wata
'yar doguwar takarda, ya nufi wajen da Jamila take, ya
kalleta, ya ce ta daga hannunta na hagu, kuma ta ce duk
abinda ya ce. Ta yi yadda ya ce. Shi kuma ya ce; ni Jamila
Alhaji Hamisu, na yi rantsuwa zan fadi gaskiya, a gaban
wannan kotun, babu abinda ba gaskiya ba, Allah ya
taimakemu amin.
Da ya gama rantsar da ita, sai ya koma ya zauna
abinsa. Lauya falle-falle ya soma takawa a hankali, ya
nufi inda take, ya dafa murfin dan dakin katakon da take
ya daga kai ya kalleta, suka hada ido, ta yi sauri ta
sukuyar da kai.
Jamila ke musulma ce, kuma wacce tayi imani da
Allah ko? Ki bani amsa.
Jamila ta amsa ba tare da ta daga kai ta kalleshi
ba.
Eh ni musulma ce mana.
Aauya ya sake dubanta, domin ya ci gaba da
bincikensa.
Shin kin san ko wanene Salim, kuma ya kuke da
shi?
Ta dan dago kai ta kalli jama'a ta ga, duk ita ake
kalloni ta sunkuya da sauri, ta soma ba wa lauya amsa.
Na san Salim, yaron gidan mu ne, shi muke aike,
kuma yana mana 'yan aikace-aikace. Shikenan sanin da ki
kayi masa, babu wani abu?
Ta dan dago kai ta kalleshi, a yayin da take wasa
da 'yan 'yatsunta. "Shike nan sanin da na yi masa mana".
37
Lauya falle-falle, yayi kamar yayi dariya, sai
kuma ya sha kunu, ya waiwayo ya kalli alkali, wanda ya
dukufa yana ta rubutu, ya kuma kalli jama'a ya ga duk su
ake kallo da saurare. Daga nan ya sake fuskantar Jamila.
Wato dai kina tabbatar ma da wadanda basu sani
ba cewa ashe ma salim yaron gidanku ne kawai, ba wata
tsiya ba.
Jamila ta amsa da sauri, cikin karfin hali. kwarai
da gaske! Lauya ya girgiza kai.
To ya akayi kuma yaron gidanku wanda babu
wani abu a tsakaninku har yayi miki ciki?
Ta amsa da sauri; ai kuma saurayina ne! Tana
fadin haka, sai jama'a da ke kotun kowa ya soma fadin
albarkacin bakinsa, duk wuri ya rude sai da aka tsawata.
Da aka yi shiru, lauya Falle-falle ya sake duban Jamila.
Ko kina da wata hujja, wacce ni da alkali, da
sauran jama'ar dake nan zasu amince babu tantama cewa
lallai Salim saurayinki ne?
Jamila tayi shiru tana tunani na wani dan lokaci,
kowa ita ya zurawa ido, ta dau misalin minti daya ba ta cе
komai ba.
Lauya ya dubeta, ko baki da hujjar da muka
tambaya? Ta sake yin shiru.
Ko Salim ya taba baki hoto, ko kuma wata wasika
tun da kuka soma soyayya? Bai taba bani ba, ta amsa tana
rawar murya.
To ke wacce hujja za ki bamu komi kankantar ta
cewa shine yayi miki ciki? Ta amsa ma lauya, kanta na
sunkuye. "cikin da yayi min shine hujja ta".
Koda Jamila ta fadi haka, duk kotun aka fashe da
dariya, har na kamar rabin minti, sannan aka sake yin tsit.
Lauya Falle-falle, da ya gama bincikensa, sai ya
waiwayo, ya dubi alkali, ya soma cewa; Ranka ya dafe,
ka ji ma kunnuwanka irin wannan al'amari. Jamila ta gaya
38
mana cewa Salim shine yayi mata ciki. Mun san kuwa
idan mutum ya ce anyi masa wani abu dole ya kafa hujjoji
masu karfi, domin masu saurare su amince.
Lauya ya sake matsawa kusa d gaban teburin
alkali, ya kalleshi, Ranka ya dade babu wata hujja wacce
mai kara ta kawo da zai tabbatar mana da cewa shine yayi
mata ciki. Abinda muka sani shine yaron gidansu ne
kawai. Ya waiwayo ya dubi jama'a kamar zai yi musu
lacca.
Kuma jama'a kun shaida, kuma na san za ku
tabbatar Salim salihi ne, babu laifi a kansa.
Ya sake waiwayo, ya dubi alkali. Ranka ya dade,
ina bukatar kotu tayi watsi da wannan karar, kuma ta bi
wa Salim hakkinsa, domin bata masa suna da lokaci da
aka yi.
Da ya zo nan ya dan sunkuya, a gaban alkali ya
mike ya nufi inda yake da farko ya zauna. Jam'a duk anyi
tsit ana sauraren yadda za'a kwashe.
Lauya Sabulu mai kare Jamila yayi zumbur ya
mike, ya dubi alkali. Ranka ya dade lauyan da yayi
bayani yanzu babatu kawai yayi, ya manta da wasu
ka'idoji na aikinsa, don haka ina fata alkali ya bani izini
in binciki wanda ake kara, kada a tauyewa yarinya
hakkinta.
Yana zuwa nan yayi shiru, yana, jiran umarni.
Alkali ya nuna masa alamun ya fito. Nan da nan jiki na
rawa ya fito ya tsaya. Magatakarda ya tashi ya je ya
rantsar da Salim ya dawo ya zauna.
Lauya Sabulu, ya matsa kusa da inda Salim yake,
ya daga kai ya dube shi.
Ko kasan Jamila? Na santa mana!
Lauya ya sake tambayarsa; Wane irin sani kayi
mata, na fili ko kuma na boye? Salim ya dan yi shiru na
wasu dakikoki yana. nazarin wannan tambaya, da
39
mamakinta. Daga nan ya bada amsa. Ni sanin fili nayi
mata, bana 6oye ba.
Menene matsayinka a wurinta? Ni mai aikin
gidansu ne.
Bayan lauya Sabulu yayi wa Salim tambayoyi na
ya akayi aka haifeka, sai ya waiwaya ya dubi alkali, yayi
surutu, yayi babatu, ya nuna bai amince ba, ayi bincike
mai zurfi. Da ya gama ya koma ya zauna.
Da alkali ya gama rubuce-rubucensa, ya dago kai,
ya soma magana, yana cewa "kotu ta ji bincike da bayanin
lauyoyi, don haka a karshe ta yanke shawarar cewa,
likitan da ke wa kotu aiki zai bincike Salim da Jamila ya
auna su, domin ya tabbatar mana da gaskiyar lamari, ta
haka ne kawai wannan matsala za ta warware muna fate
likita zai yi bincikensa saboda Allah ya gabatar mana da
rahotonsa ranar ashirin da takwas ga wannan watan, da
misalin karfe tara na safe. Masu kara da wadanda ake kara
sai su halartoa wannan rana, dai-dai wannan lokaci. Kotu
za ta bada belin wanda ake kara ga kowane tsayayyen
mutun mazaunin wannan gari idan ana bukata.
Da gama bayaninsa, sai ya mike, kowa kuma yа
mike, kotu ta tashi.
BABI NA SHIDA
Jamila na zaune a daki, duk abin duniya ya dame
ta. Tun jiya da alkali ya bada umurnin a binciki jininta
dana Salim, hankalinta ya tashi. Ta yi imani gaskiya zata
bayyana, kuma zata ji kunya, domin likita zai tabbatar a
gaban alkali da sauran jama'a cewa ba Salim ne yayi mata
wannan ciki ba. Idan aka gane haka, lallai alkali zai yi
mata mummunan hukunci, domin kazafi da 6ata suna da
ta yi bawan Allah. Hankalints ya tashi duk ta fita.
hayyacinta. Ita dai ba za ta yarda da tona ma kanta asiri ta
ce Alhaji Karma-Karma ne yayi mata ciki ba. Ai abin da
40
kunya. Dabara dai ta rage ga mai shiga rijiya. Iyayenta
Alhaji Hamisu da Hajiya Asama'u bakin ciki da kunyar
duniya duk ta rufe su.
Bilkisu Kwandala tayi sallama ta daga labule ta
shigo, bayan da ta gaishe da Hajiya Asma'u a tsakar gida.
Jamila na zaune a gefen gado tayi tagumi, da ganinta ka
ga mai juna biyu, duk tayi haske tana kyalli, kafafuwanta
da hannayenta sun zama manya, fuskarta ta kumbura. Da
ganin Bilkisu Kwandala ta yi murmushi irin na karfin
hali, suka gaishe da juna. Bilkisu ta samu wuri ta zauna,
suna fuskantar juna.
kenan?
Bilkisu ana ganin ku a duniya kuwa idanuwan
Jamila tayi maganarta cikin karfin hali, tana
kokarin gyara zama. Bilkisu ta sake yin murmushi, mai
nuna alamun ta ji kunya.
Uhum, ni dai Jamila sai dai kiyi hakuri abinda zan
iya cewa kenan. Jamila ta kalleta, suka hada ido,kada ki
damu Bilkisu haka al'amura suke tafiya.
Nan hira ta tsinke,mai tsawo. Bilkisu ta nuna
matukar rashin jin dadinta ga wannan kaddara da ta samu
Jamila. Ita kuwa Jamila tana ta kuka. Bilkisu ta dubi
Jamila cikin alamun tausayi, ba kuka za kiyi ba
Jamila,kada ki damu da komai, tun da kin tabbata Salim
shine yayi miki wannan ciki, ai koda ya karyata dole a
gane, tun da alkali ya umarci likita ya binciki jininku ai
babu damuwa, ta gama maganar, tana ci gaba da kallon
Jamila.
Jamila tayi gwauron numfashi, tayi wani dogon
tunani ba ta ce komai ba, har Bilkisu ta sha jinin jikinta ta
yi niyyar ta tambaye ta.
Jamila ko da akwai wata magana ce da ki ke so
kiyi na ga alamun haka?
41
Jamila ta sake yin ajiyar zuciya, ta kalli Bilkisu,
wallahi Bilkisu ke kawata ce, na amince miki da akwai
amana a tsakanin mu, na tabbata miki ko kisan kai na yi
ba zaki tona min asiri ba.
Bilkisu ta girgiza kai, amma ba ta yi magana ba.
Jamila ta ci gaba da cewa, a gaskiya zan gaya miki wata
magana, ni dake ce, amana idan ki ka tona min asiri Allah
ya saka min. Wallahi Bilkisu in gaya miki ba Salim ne
yayi min wannan ciki ba, Alhaji Karma-Karma ne baban
Faruku.
Bilkisu tayi zumbur ta mike, har daurin zanenta
yana kwancewa, ta dubi Jamila, wai da gaske kike Jamila
ko wasa, kina nufin Alhaji Karma-Karma baban
Saurayinki Faruku?
Shi fa, Jamila ta amsa cike da karfin hali.
Bilkisu ta rike baki, ta koma ta zauna a dai-dai
lokacin da take salati. Amma Jamila kin yi kuskure, shine
kuma kika lakafawa Salim bai ci ba bai sha ba? To
menene dalilin ki na yin haka?
Jamila ba ta boye mata komai ba, ta kwance mata
bakin jaka, ta gaya mata yadda aka yi ta gamu da Alhaji
Karma-Karma da yadda ya yaudare ta,da abubuwan da
suka biyo baya da kuma dalilin da yasa ta lakafawa Salim.
A karshe ta nemi shawarar Bilkisu, musamman ta yadda za
ta kaucewa binciken likita. Ta tabbata likita zai kwance
mata zane a kasuwa,kuma kashin ta ya bushe, menene
mafita yanzu?
Bilkisu jikinta yayi sanyi tausayin Jamila ya
kamata, ta yi niyyar za ta taimake ta komi wuya, sai dai su
mutu tare. Ta dube ta hawaye na zuba, Jamila kada ki
damu zan taimake ki muddin rai, kuma na gano hanyar da
zamu bi har a karya kudirin likita, ta yadda zai ba da
rahoton karya ga alkali,ai idan sun san wata basu san wata
ba. 42
Jamila ta yi 'yar dariya ta dubi Bilkisu, wace
hanya ce wannan kawata,don Allah gaya min.
Bilkisu ta ce, "kin gane ko Jamila, kamata yayi ki
rubuta wa Alhaji Karma-Karma wasika, ki gaya masa
halin da ake ciki,da sunan likitan da aka bawa aikin
wannan bincike, na san idan Alhaji ya ke zasu sasanta
komai. Ni ki rubuta koda yake bai san ni ba, sai in kai
masa in yi masa bayani".
Da gama fadin haka, Jamila ta taso cikin murna, ta
rungume Bilkisu, ta dube ta suka hada ido, da kyau
Bilkisu kawata,na gode kin taimake ni, wallahi na gode.
******** *********
Alhaji koda yake baka waye dani ba, amma nine
Bilkisu kuma Jamila ce ta aiko ni da wasika na kawo
maka. Tana gama yi wa Alhaji Karma-Karma bayani, ta
mika masa wasikar da Jamila ta rubuta,wacce take cikin
wata amdulan. Jiki na rawa ya amsa, ya san kwanan
zancen, ya soma karantawa, yana girgiza kai kamar haka:
Zuwa ga Alhaji,
Da fatan kana lafiya, Allah yasa, Alhaji ka lalata
min rayuwa, amam babu abinda ya dame ka a cikin
zuciya. To na san watakila kana sane cewa na lakafawa
Salim mai aikin gidan mu wannan ciki da kayi min, har
abin ya kai kotu, yanzu ma alkali ya bada umarnin likita
ya auna mu, ya gane idan cikin da gaske Salim ya yi min,
ka san kuwa dole zai gane ba cikin Salimba ne. Idan haka
ta faru kaga naji kunya,kuma ya zama dole in fallasa ka
cewa kai ne kayi min wannan aikin. Shawara anan itace
ka hanzarta ka sami ganin dakta Dattijo sanannen likitan
nan mai yi wa koti aiki, domin ku daddale dashi, ya canza
43
bayani. kuma ya lakafawa salim wannan ciki dole. Ка
hanzarta Alhaji, kada dare yayi wa mai wankin hula.
Nice Jamila.
Alhaji Karma-Karma ya mike, fuskarsa duk ta
canza ya soma tunani a zuciya, lallai karya za ta kare,
za'aji babbar kunya idan ban yi aiki da abinda yarinyar
nan tace ba, kamata yayi na hanzarta zuwa in samu ganin
wannan likita kamar yadda tace.
Zan bashi ko nawa ne domin ya canza rahotonsa.
Idan kuma bai amince ba fa? To lallai ya shia uku, domin
ba zai samu daman kai rahoton sa ba, don zan sa 'yan iska
su je har gidan sa su murde wuyansa. ya mutu murus, idan
ya so komai ta tafasa ta kone.
Da gama wannan tunani, Alhaji ya sallami
Bilkisu, ya bata wasu kudi ta kaiwa Jamila, ita ma ya bata,
a matsayin toshiyar baki. Shi kuma nan da nan ya saka
ambulan din nan wacce wasikar Jamila ke