Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 5
ta tashi tsaye ita ma ta dauke ta da mari ko da Hajiya ta ji saukar mari sai ta rike kunci, abin ya bawa Jamila mamaki sosai, lokacin Fiddausi ta kwacewa Hajiya zani da mayafin daek jikinta, Allah ya sa dai Hajiya akwai siket a jikinta. Fiddau si ba ta tsaya a nan ba, sai ta hankade Jamila ta je ta bugu da kujera ta fasa goshi, a lokacin Jamila ta soma kuka. Amma Hajiya ta kasa y in k omai ga shi yau ma Abba baya nan, kuma ga shi yanzu ta fi karfinta, a lokacin Fiddausi ta dakawa Jamila tsawa ta ce m aza ki hada min hita a bokiti zan yi wanka Jamila ta mike jini na diga ta sa ruwa ta wanke sannan ta hadawa Fiddausi ruwan, bayar nan Fiddausi ta waiga ta ce da Hajiya ke kuma maza ki je ki 32 kawo min abinci nan ta tashi ba ko musu ta tafi ta kawo wa Fidduai abinci Kuma dama abincin shi ya rage kawai. Nan Fiddausi ta ce ke Jamila dauki ruwan ki kai min bandaki, nan ko musu babu ta kai mata, to Fiddausi ita dama ba don babu ruwan zafin ba ne kawai dai don ta rama irin mu guntar da ake yi mata ne, kuma ta ce kada wanda ya ssoma cin sauran abincin nan. Sai a shiga wanka, bayan shigarta ba ta juma ba, sai ga Jamilu ya yi sallama yana shigowa koda ya hau sama sai Hajiya ta soma fada masa abin da Fiddausi ta yi musu Jamilu ya ce Fiddausin? Hajiya ta ce E" ran Jamilu ya baci ya ce yau ma sake dawowa ta yi a lokacin Jamilu ya ce yanzu tana ina Gaji ta ce tana bandaki tana wanka. Ya ce ina bulala, Hajiya ta bashi, ya tafi yana jiran fitowarta. Fiddausi sai ta fito su Hajiya suka bita da kallo Fiddausi ta shiga dakin mahifiyarta tana shiga sai su kai arba da Jamilu a falo sai ta huce shi ko kallonsa ba ta yi ba sai kawai ya dau bulala wai zai doki Fiddausi, koda ta ga haka sai ta rike daga hannu Jamilu sannan ta fisge abin ka da ragowar AIDS' sai nan da nan bulala ta dawo hannun Fi ddausi, koda ta zo hannunta sai ta dunga tsalalawa jamilu, tana cewa da kenan, amma yanzu na huce nan. Domin wu tsiyar rakumi ta yi nesa da kasa Yayin da ta ci gaba da dukansa, lokacin Hajiya da Jamila sai mu rma suke ba su san reshe ne ya juye da mu jiya ba don su a zatonsu Fiddusi ake `KILA" lokacin su ka shigo dakin baki daya koda su ka shigo sai su ka shiga dakin baki daya koda suka shigo sai suka tarar duk bayan Jamilu ya farfashe, kuma gashi nan a kwance. hajiya ta rike baki tana mamaki, nan dai ta dunga bawa Fiddausi hakuri amma ina Fiddausi ta ci gaba da tsalala mar, bayan Jamilu ya sami dama sai ya fice a guje. Suma su Hajiya suka arta a guje sukai waje bayan da suka fita Hajiya ta ce yau mun shiga uku, yau ya ya za mu yi da wannan shegiyar yarinyar, ni ban san wanda ya koya mata wannan rashin kunyarba. lalle bahaushe ya yi gaskiya 33 da ya ce komai ya yi farko ya yi karshe, to mu dai karshen mu ya zo kenan don na san ko Alhaji ba zai iyawa Fiddausi ba. Ni dai idan ya dawo sai in ce mu tashi, do min idan muka zauna to kashe mu za ta yi. Don haka idan dai ya sami kudin da ya je karbowa shike nan, don na ga ta fitsare sosai. Haka Gaji tai ta y in surutu ba ji ba gani, haka su ka kasance cikin wahala da bakin cikin Fiddausi lokacin da su ke azabtar da ita ai babu wanda yake jin tau sayinta, amma yanzu sa tausayawa kansu gashi ma suna neman mafita. Koda gari ya waye sai Fiddausi ta sa su aikin gida a wannan lokaci duk cikinsu babu wanda ya yi mu su domin yanzu tsoron ta suke sosai, haka su ka wanka gidan ta sa suka share shi tas! Suka goge leda, sannan inda kafet yake su ka kadae shi fes, haka Diddausi ta yi ta sa su aiki iri-iri. Gaji da 'yarta jamila abin du niya ya yi musu zafi, su kawai so su ke Alhaji Abba ya dawo ko ya yi musu maganin Fiddausi. Shi kuwa Jamilu tu n lokacin da Fiddausi ta zane shi ya kwanta rashin lafiya zaza!6i, ciwon kai, kumallo tare da gu dawa. Hajiya tana son ta kai Jamilu Asibiti, amma-saboda Fiddausi ta kasa domin Fiddau si ba-za ta bari ba. Du niya kenan wai yazu Hajiya се ke tsoron Fiddausi, dama masu iya magana su n ce abin da ya baka tsoro wata rana shi zai baka tausayi, dama can Jamila na shakkar yarinyar da su ka rainawa wayo, kuma suka wu lakanta. Kuma ba su taba zaton haka za ta faru a gare su ba. Bayan da aka sami mako daya da tafiyar Alhaji Abba, kwanakin Fiddausi kenan a gidan, har Hajiya Gaji ta soma rama saboda rashin kwanciyar hankai da tsabar aiki, а wannan lokaci Jamila ta fahimci cewar Fiddausi ba ta da niyyar barin gidan, sai ta ce Hajiya ni fa zan hada kayana na bar gi dan, koda Gaji ta ji haka sai ta ce to yanzu Jamila ni ba kya tausayina haka za ki tafi ki bar ni, wato ko mutuwa zan yi haka za ki min. Gaji t asoma hawaye, suna cikin haka sai kwatsam ga Abba ya dawo, ya yi sallama koda Gaji ta je sai 34 ta share hawayenta ta ce Allah na gde ma da ka dawo min da Abba, kun ji fa sai yau Hajiya ta tuna da Allah Hajiya ta leko, sai ta ga Abba rai bace ta ce wai mun shiga uku nan ma ai wani bakin cikin ka taras 'Abba ya hau sama, Hajiya da Jamila su ka bi shi su ka yi masa barka da zuwa ya amsa da kyar, Gaji ta ce yà ya me yake damunka, abba ya ce ai wahalar banza na sha domin asarar kudın tikiti na yi, don ban sam komai ba, amma ban sami ba ko alhaji Hamisu ne ya yi waya ya ce kada a bani. Ko kuma watakila Fiddausi ce ba ta sa hannu dai-dai ba domin yanzu ta zama tatacciyar 'ya kuma za ta hadu da ni bayan ya huta, sai Hajiya ta kawo masa ruwa kawai, koda ya ga haka ya ce to ina abincin, Hajiya ta ce ai Fiddausi ta hana a yi, kuma wallahi ta matsa mana sosai, dama ni so nake ka dawo mu bar gidan don har. dukana ta yi yanzu ga Jamilu can a kwance ta hana akaishi asibiti,don shi ma duka ne ya kwantar da shi ni dai kam ka san matakin da za ka dauka akan Fiddausi don kuwa tą takura mana. Sosai, Abba ya ce to yanzu ta tafi, Gaji ta ce tananan ba ta da ranar tafiya balle ma mu huta. Nan dai Gaji ta kwashe labari ta sanar da Abba. Ya yi mutukar bakin ciki ya zamar masa biyu. Yaje AMURKA kudi babu, ga kuma abinda Fiddausi ta shuka a gidan. nan ya fusata ya mike ya ce ian bullar nan har yaushe ta isa, ni ba ta isa ta yi min iskancin ba. Ina bulalar nan Hajiya ta ce ga ta, kuma baka ga jikin Jamilu ba, nan ya karba ya hau sama. Ya huce dakin da Jamilu yake kwance, Abba ya ce sannu Jamilu, a lokacin Jamilu duk ya rame ya soma kanjamewa. Dama ai Kanjamau ce ta kama shi don haka sai na ce Jamilu sai mun taho. Lokacin da Abba ya gama duba dansa, sai ya huce inda Fiddausi take, koda ya shiga ta ganshi amma ko magana ba ta yi masa ba. Abba wani ta kaici ya sake kama shi yayin da ya kai mata duka sai Fiddausi ta rike bulalar kamar yadda ta yi wa Jamilu, ta, fisge daga hannun Abba 35 sai da ya yi laryin faduwa, ta ce da kenan! Ka dake ni ka aki banza. Amma yanzu na huce haka a gurinku baki ya, Fiddausi ta dunga tsalalawa Abba bulala ba ji ba gani, da ya ga ba dama sai ya fito da gudu ba shıri. Ya yi kasa, dama Jamila da Gaji ba su bi shi ba don şun san da kyar zai yi nasara a kan Fiddausi, ko da suka ga Abba da gudu riga duk a yayyage sai suka ce gaba daya yau mun shiga uku, Abba ma ta gagare shi to waye zai yi maganinta kemaGaji ta ce wayyo! Ga shi Alhaji duk ya sayar da kadarorinsa ga shi gidansa ya bawa su GIZAGO da sai mu koma can muhuta da wannan bala'i. Haka dai Alhaji ya sauko ba shiri. Bayan kwana biyu' da yin haka Fiddausi ta sa su aiki sai Jamila ta yanke a hannunta jini yana zuba, a lokacin ta rasa yadda zata yi, da Fiddausi ta ga ba ta aiki sai ta daka matsa tsawa. Jamila ta nunamata sai tace ci gaba ai zai tsanene, Jamila sai hawaye ne ke zubo mata har suka gama. Bayan da suka gama sai ta ce su share yana ta ce kuną ganin duk gidan yayi yana, to ku share. Da zama za ku yi ai zama bai same ku ba, bayan sun gama sai Fiddausi ta ce ga kwakinan ku jika ku ce. don dama kai Abba sunanka (АВВА ЛКО) don daga yanzu sai ka fi kowa iyama'amala da kwaki. Haka nan suka dau kwaki suka jika ba ko sukari suka ci. Bayan gari yawaye jamila ta debe kayanta ta yi gaba. Dama ta kware a wajen iya iskanci, amma ita Fiddausi bat san ta gudu ba. Koda Abbada Gaji suka ga haka sai suka yanke shawarar abin da za su yi kan Fiddausi. Gaji ta ce ko gidan Hayane mu koma amma yaya zamu yadda yarinya take ci mana mutunci ni ba abin na ce ka je gidan su Hajiya ba, sun san gidan ta ne, kai ka ji fa ashe wuya ba dadi Lamarin. GIZAGO da yake hannun 'yan sanda to yanzu dai wuya ta yı wuya don yanzu ya fadi yanda aka yi 36 kuma ya fadi sauran da suka nadu suka yi wa HANYA ZAINAB kisan gilla ya kuma fadi wanda ya sasu. Alhaji Abbab abin ya zame masa goma da ishirin ya ya zai yi da ransa ga wannan ga wancan. Kun ga dai ramuwar da Fiddausı take yi, ga takaicin rashin kudi ga Jamilu ba shi da lafiya, ga Jamilata zama karuw ta yi nisa a karuwanci ga kuma hukunci zai hau kansa, to dama haka duniyatake wata rana a sha zuma, wata rana asha madaci, a lokacin da GIZAGO ya fadi komai sai 'yan sanda suka sa shi a gaba a inda suka bi shi ya nuna musu inda su NAMUZU suke, aka yi sa'a aka kamo su sannan yakai su har gidan Alhaji Abba baban mahadın. Koda suka isa suka yi sallama a lokacin Abba duk jikinsa kumfa domin wanki ya ke wa Fiddausi bayan an yi sallama da shi, ssi Fiddausi ta bi bayansa don ba ta amince ba ko guduwa yake son yi shima. Koda ta leko sai ta ga 'yan sanda sun sawa Abba ankwa a hannunsa. Sai ta ce da su ko lafiya ‘yan sanda suka ce tuhumarsa ake a kan laifin kisan gilla. Koda fiddausi ta ji sai ta gane cewar da hannun Abba a kisan da aka yi wa mahaifiyarta, a lokacin sai hawaye ne yake zubowa Fiddausi nan dai 'yan sanda suka hankada keyarsa aka yi gaba da shi zuwa ofishinsu ita kuwa Fiddausi sai ta yi sauri ta nufi gidan Kakanninsu don ta sheda musu komai. Amma Hajiya Gaji ko da ta ga Abba da Fiddausi sun daďe ba su šhigo ba, sai ta fita waje tatambaya sai aka ce ai an kama shi ‘yan sanda ne suka tafi da shi. Ta ce har da yarinyar suka de a'a, sai ta ce to ina kuka ga ta yi sai suka nunamata. Nan dai Hajiya ta koma ciki tana mai bakin cikin kama Abbaita ba abin ta þi shi ba ga Jamilu a kwance haka dai ta kasance kan takaicin wannan lamari da dana sani, don dma masu magana sunac cewa dana sani keya ce a baya take zuwa. Laokacin da Fiddausi ta isa gidan kakanninta. Abdullahi da mahaifinsa suka ga ba'a hayyacinta take ba, .37 sai suka ce yaya me yafaru, sa’a ba su labarin abin da yafaru ta ce ashe Abbane yayi sanadiyyar rasuwar hajiya, don gashi can an tafi da shi POLICE STATION. Lawan ya ce lalle biri ya yi kama da mutum, don bana mantawa Jokacin da aka gama zaman makokin Hajiya cewa na yi da dai ba shi da rai ne to ashe macuci ne don ya zalince ki ne to ni dai ban yaje masa ba, duniya da lahira, ai dama Allahba azzalumin Sarki bane don ga shi ya tona masa asiri, haka ma Hajiya Binta ta ce ita ma ba ta yafe ba. Lamarin Abbakuwabayan yasami mako daya a hannun 'yan sanda suna yi masa tambayoyi, haka.su Namuzu ma suka tabbaatar wa da 'yan sanda cewar shi ne ya sa su har yaba su kudi da gida wnda yake ciki a da bayan komai yadaidaita. Bayan an gama bincike Abba da su Gizago suka hallara a kotu, domin yanke hukunci a cikin jma'ar da suka hallara don ganew idonsu akwai Alhaji Abdullahi, Mustapha, Alhaji Lawan, Alhaji Hamisu da Fiddausi, don su jiyewa kansu hukuncin da za a yankewa su Abba, haka ma Hajiya Gaji ta jewai tana ta addu'a don mijinta yayi nasara ba ta son Allah ba ya zalintar bayins,kuma ba ya karbar du'ain azzalumi sai dai wanda aka zalinta. Bayan kotu ta cika makil da jama'a, sai mai shari'a ya iso. Koda ya iso sai duk aka mike don girmamawa agare shi, bayan ya zauna sai kowa ya zauna a lokacin mai gabatar da kara ya mike yafara karanto tuhumar da ake yi wa su Abba, lokacin mai shari'a ya nemı wadanda ake tuhuma sai suka mike gaba dayansu, mai shari'a ya ce to kun ji laifin da ake tuhumarku da shi, kafin kowa yayi magana sai Aba ya ce mun ji to amma ni sharri a kai min domin babu hannunaa ciki, kun ji Abba ba kunya bare tsoron allah ya ce shi bahannuns a ciki Lokacin mai shari'a ya ce ko kana da shaida wanda zai kare ka daga zargin da ake ma. Abba ya ce Allah yagafarta malam ni ba ni da shida sai mai dakina! 38 Mai shari'a ya ce ai matarka ba za ta yi shedarka ba. Abba ya ce tuba rake Allah ya gafarta malam don ni ba ni da masanıya akan wannan zargin. Mai shari'a yace ko za rakarantse da Alkur'ani akan cewar baka da masaniya akan zargin da ake maka, na kisan Hajiya Zainab. Abba yace tuba nake amma bazan rantse ba rantse ba. Mai shari'a ya nemi Gizago da ya yi bayan i akan abin da ya sani kan wannan tuhuma. A lokacin Gizago ya fara bayni kamar haka, wata rana ina zaune da safe sai ga Abba ya zo wajena sai ya nemi da mu kashe H ajiya Zainab akan kudi Naira dubu goma, tare da bamu gidansa wanda yake ciki, shi kuma ya koma gidan Alhaji Bello marigayi. Alokacin Gizago ya ba wa mai shari'a t akardun da Abba ya ba shi, alkali ya karba ya ga sa hannun Abba da wasu shedu. nan alkali ya tabbatar Abba shi ne makasudin kisan HajiyaZainab, Gizago ya ce shi ne abin da na sani akan tuhumar da ake yi mana. Alkali ya juyo gurin Abba ya ce ka ji abin da shaida na farko ya fada. Sannan alkali ya juyo kan Dansanabe, nan shi ma yaba da shaida kamar yadda Gizago ya bayar haka ma Namuzu, sannan alkali ya juyo kan Abba ya ce ka ji abin da suka ce ko kana da abin da za ka ce,. Nan Abba ya ce tuba nake, alkali ya ce to yanzu dai ka amsa laifinka na hada baki da kai a yi kisan kai don neman dukiya, ga kuma cin amanar 'yan'uwanka, don haka na yanke muku hukuncin daurin rai-da-rai gaba dayanku. A lokaçin aka iza keyar su Abbą zuwa gidan wakafi. Koda aka fita da su Abba da su Gızago, sai Alhaji Lawan da Alhaji Hamisu suka yi murna sosai, amma koda Hajiya Gaji ta ga an tafi da su Abba, sai ta dora hannu a ka tana kuka, sai ta koma gida, ko da ta koma gida, tana shiga sai ta tarar Jamilu rai ya yi halinsa. Koda Hajiyata ga haka sai ta yi waje tana kuka shikenan makasudin haukacewarta. Ga shi kuma Jamila an shiga. karuwanci, bata san halin da 39 ryayenta ke ciki ba bare mutuwar dan uwanta, wannan shi ne sakamakon da ya faru ga Alhaji Abba da iyalinsa to jama'a sai a lura a gane. Cutar maraya ba abu ne mai kyau ba, kuma hatta mugwayen makota masu yin tsafi ko wani surkulle ga makocinsu sai su gane, domin zaka ran da Allah ya nufa da cara.... Mu dai mun san tsintacciyar mage ba ta mage, don haka kowa da yarensa tur Allah ya rabamu da hali irin na su Abba. Sannan ga masu hali irin wannan su sani cewar ba za a bar mutum jiran duniya ba, domin ko wanne rai sai ya dandana mutuwa don haka a yi hattara wajan gujewa son zuciya da zalinci on h aka wnnan sai ya zama darasi ga masu irinw annan halaya hakı kuma ga cin amanar 'yn'uwa. to yanzu Abba ya ga sakamako akan wacce ya so ta mutu, ammaba ta mutu ba sai ga'shi shine ya zama matacce a tsaye, tun da an yi ma sa faurin rai-da-rai. To mu dai sai mu ce Allah ya kare mu da irinw annan zucıya irin ta su Alhaji Abba amin. Dama an ce son zuciya bacin zuciya don da bai so ransa ba, babu shakka haka ba za ta same shi ba. Lamarin Fiddausi kuwa babu abin da ya dame ta sai murna take da irin hukuncin da aka yanke wa Abba sosai. A lokacin Alhaji Lawan da iyalinsasukayi wa Allah godiya mai yawa bisa wannan sakayyada ya yi musu tun daga duniya. Ana cikin wannan murna, sai ga sako daga Katsina kan cewar Hajiya Na'ima tahaihu kuma an sami da namiji, murna, sai ta kasance biyu. Ga ta nasara da aka yi wajan su Abba ga kuma ta karuwa. haka dai al'amu ra sukai ta gudana a gidan Alhaji Lawn, bayan an sami nutsuwa sai ga Alhaji Hamisu da dattijo mai rikon amana ya yi sallama a gidan Allah ya bamu hali irin na su Alhaji Abdullahi ya fito, suka gaisa da juna. Sai ya ce da Abdullahi ko Alhaji Lawan yana nan. Sai Abdullahi ya ce ko Alhaji Lawan yana nan. Sai Abdullahi ya ce yananan a lokacin Alhaji 40 Abdulllahi ya yo magana da shi, bayan da ya fito, suka gaisa da Hamisu, ga kuma Abdullahi a gurin, sai ya се dama Alhaji Lawan zuwa na yi na baka dukiyar Fiddausi, domin ni ma akwai yara da yawa a gabana, kada na bar baya da kura domin saboda halin mutuwa. Domin gudun kada a zo ana rigima akan wadannan kamfanoni da kuma kudaden da suke banki na wannan marainiya. Don haka ga takardun kowane dukiya, kuma ga cek din banki a lokacin ya mikawa Alhaji Lawan, sai ya ce a'a shi ba zai karba ba, kuma Allah ya yi maka albarka, bisa rike amanr da ka yi kuma Alllah ya raya zuriyarka amin. nan dai Alhaji Hamisu ya dunga hada shi da-Allahakan ya karba, amma ina. Sai da Alhaji Abdullahi ya sa baki, ya ce shi ma ai Hamisun ya yi gaskiyaka san halin yau yadda yake. Sanan ya karba domin Alhaji ka san yanzu takarda ita ce sheda domin ka ga nan gaba idan babu taakardun to ba ka da hujja a kan komai nata, a lokacin Alhaji Hamisu yayi godiya mai yawa ya kuma ce zan kai ku duk inda kamfanoninta yake in nuna muku. Ya yi bankwana da su suna masu godiya yatafi. Washegari Alhaji Abdullahi ya ce shi zai koma domin a yi suna yana nan. Lokacin fiddausi ta ce ita ma za ta don a yi sunan tanan nan. Haka suka tafi, to bayan tafiyarsu da kwana daya sai iyayen Mustapha suka hada kaya suka aiko gidan Alhaji Lawan nan dai aka karba cikin aminci da karimci. Amma a can Katsinakuwa da ranar suna ta zo sai aka sawa yaro suna Muhammad Lawan, wato yamayar da sunan mahaifinsa. Don dama tuni ya riga ya sa sunan mahifiyarsa. Bayan da aka kammala harkar suna da wani lokaci sai ak fara shirye-shiryen biki. Aka sa Fiddausi a lalle, a lokaicn akai shagalin biki mai kayatarwa ga duk mutumin da ya halacci wurin, Alhaji Hamisu yayi wa Fiddausi kayan daki na gani na fada; don shi ne madadin Alhaji Bello marigayi. akai ta yi masa godiya d sa masa 41 albarka, ita kuwa Fiddausi suka yi zamansu lafiya da masoyinta. Dama wnnan shi ne burinsu gashi allah ya cika musu sai mu ce Allah ba da zuriya ta gari amin summa amin. Wannan shi ne karshen wannan littafi mai suna MAI RABON GANIN BADI, inda Hausawa suka ce wai ko ana dakawa a turmi sai ya gahi. Ai wuyaba ta kisa sai kwana ya kare to a nan zan takaita ni ce-'yar uwarku HAUWA ALHAJI BASHIR AYAGI, mawallafiyar SO SARTSE Allah ya ba shi kabuli amin. Bissalam, Allah ya ba mu alheim sa amin na barku lafiya. Lokacin da mutun ya fahimci cewar ya bi watą hanya wadda ba za ta kai shi ga alheri ba, to shi ne yake neman aimako ga Allah da ya nisanta shi da ita kuma ya kare shi daga sharrin shaidan da sharrin mutane da za'a yi musu azaba ranar kiyama. Kamar yadda wannan littafi ya kunsa, wannan dai a takaice muna neman shari'a ta gari daga gun Allah kuma muna so ya nisanta mu ga dukkan mai kawo fitina a duniya 'yan uwan shedan da shi kansa muna neman tsari da shi mutun kada ya yi tsmmani rayuwarsa ta kare bayan mutuwa, ita dai mutuwa tana raba shi da duniya ne kawai zai sake sabuwar rayuwa fil ba irin wadda ya yi a duniya ba wnnan rayuwakuwa zai sake yinta ne ranar lahira wwanda Iamni da shi da abin da yatattara na hisabi da sakamako yana shika-shikan Musulunci. Kuma babu wni maimulkia wnnan rana sai Allah, dubi Suratul Infidari aya ta 17/8/9 BAKIN CIKIN RAYUWATA NA BIYU A gaskiya Kairiya babu yadda za'a yi na daina sonki da kaunarki don duk lokacin da na kwanta da sunan bacci dare ko rana to wallahi tunaninki ba ya barin na yi bacci, 42 inda na ga wuni haka zan ga kwana, don haka Kairiya ki tausaya min. Ga irin sonki da ya mamaye min zuciyata don hka kada ciwon sonki ya hallaka ni, domin idan kika ce ba kya Kaunata lalle ciwon zuciya zai kama ni, domin idan bana kusa da ke to rayuwata bata da amfani. yake masoyiyata, Kariya ta kalli Sa'ad sai dai na ce ka yi hakuri kuma Allah ya ba ka mai kaunarka kamar yadda kake Kaunata. amma Kariya sai Jabir. Kadan kenan daga littafi na biyu, NA BAKIN CIKIN RAYUWATA. 'Yar uwarku HAUWA A. BASHIR AYAGI, Allahya bamu alherins amin summa amir. Na barku lafiya, na gode. BAKIN CIKIN RAYUWATA NA DAYA Wata rana Sarki Abdulhamid suna zaune shi da matarsa Hamida suna hira sai ta ga yana hawaye a lokacin hankalinta ya tashi ta ce lafiya Sarki ya ce yanzu nine a cikin gidan baban makiyina wanda ya raba ni da iyayena da dan uwana da matarsa saboda abin duniyaya sa ni bakin cikin rayuwata. nan Hamida ta rarrashe shi, ta ce abinda ya fi duk lokacin da muka yi sallah to muyi musu addu'a ga Allah ya yi musu rahama ya ce amin. nan suka ci gaba da hirarsu ta masoyan juna na zamantakewa ta aure, Sarki Abdulhamid ya kalli Hamida suka yi murmushi ya ce yanzuna farka da bakin cikin rayuwata. Kuma yanzu zan yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki da ya ba ni ikon samun masayi. Don jin yadda hirar za ta kasance nemi littafin don jin yadda za ta kasance. HAUWA A. BASHIR AYAGI MASOYINA NA DAYA Nafisa a gaskiya kin san cewar babu wanda ya fi wannan mu'amala da nisa ko in ce ganin nisa ga wanda ya hau giginya ya fado bai zarce ko ina ba sai cikin rijiya ina ganin wanda zai fi shi ba da labari game da nisa ko in ce da kai 43 ganinsa, don haka kar ki ji tsorn nisa game da mallakar junanmu a halal ce. (Aure) Fatana kuma shi ne ki rike alkawari, amana, ta numfasa ta ce kai nemi wannan labari `na UMAR akwai gwa-gwarmaya a ciki kafin a yi aure. Neme shi a kantin sai da littattafai na kusa. NA HAUWA A. BASHIR AYAGI. MASOYINA NA BIYU Lokacin da nafisa ta fito ta ga Aliyu ya ce ina son ganinki ta ce kai dakata ya rike baki ya ce baki sanni bane. Ta ce ban sanka ba don Allah ka tafi ka bani guri mara zuciya, mara tunani, jibeka wani "YABGI" da kai kamar mara hankali shashasha. Ni banasonka bana son mai sonka. Aliyu ya yi kasake yana kallonta, yace sai na aure ki in dai kudi ne suke aiki akwai su. nafisa ta kama hannu Umar suka koma cikin gida, suka bar Aliyu a tsaye yana cizonyatsa nemi wannan littafi ka ji karshen batun HAUWA A. BASHIR AYAGI. SO AJIYAR ZUCIYA Muhammad ban yi tsammani za ka yi min haka ba. Amma Muhammad ka ci amanata, kuma ka yaudare ni ka sani a cikin wani hali ka tuna alkawarin da ka yi min. Muhammad ka shiga zuciyata ka mamayeta domin ba wani mahaluki da yake cikin zuciyata in ba kaiba. Na kori jama'a da dama amma za ka yi min haka, haba Muhammad kaceto

Chapter 4 of 5