Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
don haka na yanke wa kaina hukuncin komowa nan. Fiddausi ta ce hatta Jamila sa'a ta cе amma saita zage ni ta do ke ni. ba ni da ikon ramawa domin Hajiya da Abba sun daure mata gindi, dubi gadon bayana duk katakore ne "bell' na injin nika da shi ake ba ni kashi. Haka Fiddausi ta yi ta ba su labari suka tausaya mata. Alhaji Abdullahi ya ce ai sam ba zan yarda da haka ba. Kuma ya Kara da cewa, kuma duk wulakancin da su kai miki sai kin rama kuma idan wulakancin ne kowa ya iya kuma namu ya fi nasu kuma da hannunki za ki rama babu wanda zai rama miki. Alhaji Abdullahi ya yi t a fada tare da cin alwashin cewar sai ya ga dalilin da ya sa ake ta bautar da wannan marainiyar yarinya haka domin abin ya huce misali Wata rana bayan an sami lokaci mai tsaho da maganar Fiddausi kan irin matslar da take ciki, kwatsam sai ga Mustapha ya yi sallama a gidan Alhaji Abdullahi, ko da Fiddausi ta dau muryar masoyinta sai ta leko,......Sai suka hada ido hudu da masoyinta, ta yi masa sannu da zuwa ta ce bari na fada cewar ka zo, Mustapha ya ce ba ji Fiddausi ta koma ta shaidawa Anti Na'ima cewar ta yi bako daga Kano. Anti ta ce maza a dau mukulli a bude masa sttitum, bayan ta bude suka shiga tare da Mustapha, ya zauna Fiddausi ta koma ta kawo masa lemo ta dire a tebirin da yake gabansa, wanda a wannan lokacin Fiddausi ta sake yı masa barka da zuwa ya yi da shi kuma yana zaune ne a kan kujera, ta kuma gaida shi gaisuwa kuwa irin ta ma'abota 21 soyayya, koda Mustpha ya amsa sai ya ce kai amma na sha hanya, Fiddausi ta ce kwarai kuwa domin ni ma lokacin da na zo haka na gani, don naza ta tafiyar ba ta da nisa, Mustpha ya ce ni ma banaiya irin wannan tafiyar a mota, amma da yake garin masoyi ba shi da nisa, ga shi na zo saboda ke, a lokacin Fiddausi ta ce ai ni ban zaci kwanan nan za ka zo ba. Mustpha ya ce ai kin san idan ba ganinki nake kusa da ni bato ba na jin dadi Duk da yake dai Abba ya hana ni zuwa to amma ai muna haduwa. Fiddausi ta yi murmushi mai tada hankalin-mai bege, Fiddausi ta ce ka ci abinci kada ya huce ka ga yanzu aka gama. Mustpha yace ko ganinki ya isa ya sani na koshi, Fiddausi ta ce bari na fita ko ka daina ganina ka ci da yawa. Mustapha ya yi murmushi ya soma ci har ya koshi ya yi hamdala sannan ya sharuwa ya sha lemo, Fiddausi ta ce bari na koma ciki ko ka huta, nan ta mike ya bita da kallo dimin ya ga kamanninta sun canza kamar ba ita ba, idan ba wanda ya gani da idonsa ba, ba wanda zai ce ta taßa wahala, don shi a lokacin gani yayi har ta fi da kyau sosai, a lokacin Mustpha ya yi tasbihi ga Mahalicci da- cewar sarki ya tabbata ga Allah Madakakin Sarki, Allah Subhanahu wa Ta'ala da ya shirya gabban wannan yarinya alokacin ya mike a doguwar kujera yana mai tunani da addu'ar Allah va tabbatar da aureps da Fiddausi. Lokacin da Fiddausi ta koma cikin gida sai Anti Na'ima ta ce waye bakon namu Fiddausi ta ce Mustpha ne, Anti ta ce ni kuwa ban san shi ba, amma ba dan uwanku ba ne. Fiddausi ta ce ai dan abokin Babana ne. Anti ta ce ko dai saurayinki ne, Fiddausi ta yi shiru, nan dai Anti ta gane cewar Mustpha biyo Fiddausi ya yi. Tana rufe bakinta sai ga Alhaji Abdulllahi ya dawo, nan Na'ima da Fiddausi suka yi wa Alhaji sannu da zuwa ya amsa Fiddausi ta kawo wa Alhaji abinci, don yanzu it take yin abinci kasancewar Hajiya Na'ima na da tsohon ciki, Alhaji 22 ya soma cin abinci, bayan ya gama, sai Hajiya Na'ima take gaya masa cewar mun yi bako yake cewa daga ina ta ce sirikinmu ne daga Kano. Alhaji yayi jum yana tunani, sai Hajiya ta ce to saurayin Fidddausi ne ya zo gaishe mu ka san garin masoyi ba ya nisa in ji Hausawa Alhaji ya се wanna gaskiya ne, Alhaji ya ce ko yana ina! Ta ce ashe baka kula ba ai yana sitirum, Alhaji ya ce amma na ji dadi da kika karrama shi, a lokacin ya yi kiran Fiddausi, ko da tazo ta durkusa ta ce gani ya ce maza kirawo min bakon da muka yi Fidausi ta nifi inda bakon yake wato Mustapha, ta ce ka zo Baffa yana kira koda Mustapha ya ji haka sai ya tashi da sauri suka yi cikin gida, da isarsu saí Mustapha ya durkusa ya gai da Alhaji da mai dakinsa, Na'ıma, bayan sun amsa Alhaji yace saukar yaushe Mustpha yace dazun nan naiso, Alhaji ya ce na ji dadin zuwanka, Alhajiyа се yaya mutanen gida Mustpha ya ce suna na lafiya lau. Alhaji ya ce lafiyanaganka ko Alhaji ne ya aiko ka Mustaphaya ce a'a, ni dai abin da yake tafe da ni shi ne na zo neman auren Fiddausi ne domin tun muna Kano ni ne nake sonta. To bayan da muka dade ina nemanta da aure, har ya kasance mun fahimci juna to sai wata rana na je Abbaya ce da ní ko da na sake zuwa ya ci mutuncina ya ce wai ya raba mu. Kumaya kara da cewa muddin ya sake ganina a kofar gidansa sai ya sabar min. Wata rana Fiddausi ta bar gida sai Abbaya zo har gida yayo sallama da ni, kp da na fito sai naga Abba a tsaye sai na durkusa na gaishe shi ya amsa da kyarya ce wai nafito masa da 'yarsa Fiddausi. Na yi masa rantsuw da Allah akan bata wajena amma ina Abba baiyarda ba, ya ce wai da a ce ni wani bare ne da sai ya ci mutuncina ya sa an taran gajiya. Nan dai na bi shi a hankali muka rabu lafiya. Domin kowa ya san halinsa shi yasa ban yarda hakan ya jawo wata illa a soyayyata da fidddausi ba. Na lallaba shi muka rabu lafiya. Shi ne muka 23 ci gaba da soyayya boye har ta taho nan. Domin lokacin da za ta taho nan sai da ta shedamin cwear za ta taho nan. Shi pe na yi mata alakawarin lale tana jika domin ba nisa ga garin masoyi, bakin zaren maganar shi ne zan ziyarce ta, to wannan shi ne dalilin zuwana kuma na ji dadi da na sami kyakkyawar maraba. Alhaji ya ce kai amma na ji dadi kuma ka kwantar da hankalinka in Allah ya yarda komai zai yi daidai. Alhaji Abdullahi ya ce ni ma daman ‘yan shiryeshirye nake domin za mu Kano. In ji dalili da ya sa Abba da mai dakinsa da ‘ya'yansa suke gallazawa Fiddausi sukai musayar kallo, suka yi murmushi. A lokacin Mustapha yace Allah ya kai mu lokacin don ni koda yaushe a shirye nake Alhaji yace amin. Alhaji yace da Mustapha ya koma masaukinsa, nan Mustpha ya mike tsaye tare da girmamawa a gare su, lamarinsu kenan. Amma a can Kano abin ba’a cewa komai domin Alhaji Abba ya kai Alhaji Lawan kara don yana gani shi ne ya foye Fiddausi, koda suka je kotu sai mai shari'a ya tashi mai kara don yayi jawabin karar da yake kan Alhaji Lawan. Alkali ya ce ka ji abin da mai kara ya ce Alhaji Lawan ya ce na ji Allah ya kyauta yin mallam, ko yana da sheda wanda ya ga 'ya a gidana, lokacin Alkali yajuyo gurin Abbaya ce ko kana da shaida Abba yace ni ba ni da shaida, sai dai akwai wani lokaci da ta je gidansa ya hana ta dawowa, don da na je sai da muka kai ruwa rana, shi ne ya sa nake zarginsa don sai da makotansa suka sa baki sannan ya bani ita. To shi ne yanzu na nemeta na rasa. To shi ne nake zaton tana gidansa, mai shari'a ya ce ko ka san zato zunubi ne, koda ya kasance gaskiya, don haka na yanke wannan shari'a taku, domin babu shaida Alhaji Lawan yi tafiyarka. Na sallame ka. Ya yi godiya ya share. abbaya koma gida ba gwiwa. hajiya Gaji ta ganshi ransa abace, ta ce yaya ko ba sa'a ne haushi ya sake kama shi ya 24 ce lalle wannan maı shari'ar ko alhaji Lawan ne ya gans shi don na ga ni shari'ar ba tai min ba. Gaji ta ce E" Lalle haka ne abin da ya fi to kawai ka sake kotu. Ko ka shigar da sabuwar kara ko ka sami rinjaye don na san babuinda Fiddausi in ba gidansa ba amma da yake munafiki ne ka ji ya dage kan cewa ba ta gidansa. Amma ai matarsa ba ta sanni ba. zan shirya naje gidan da daddare domin ka san ko aike ne ba za su aiketa ba a wannan lokaci, ka ga ko ni na ganta na isa shaida. Tunda idona ya nuna min. Shi kuma Abba sai ya amince ka ji, SAHON JAHILI. Ko da dare ya yi sai munafukar matarsa Gaji ta yi shiri ta nifi gıdan Alhaji Lawan, koda isarta ta yi sallama ta ce da Allah tambaya nake ko nan ne gidan Alhaji Abba, sai Hajiya Binta ta ce ai ko ba nan bane, bama a nan unguwar yake ba. Kuma da 'yar tazara zuwa inda yake, sai Gaji ta ce kai amma na wahala tun safe nake neman gidan, sai Gaji ta ce da man mai unguwa ne ya iko ni, Binta ta ce daman a nesa kike, Gaji ta ce a nesa nake can Koki, dama wata yarinya aka tsinta ta ce sunan babanta Abba, Hajiya Binta ta ce ita kuwa yaya sunanta, Gaji ta ce sunanta Fiddausi, kuma ta gayan wani suna idan ban sami gidan ba sai na tambaya sai na manta sunan. Ko da ta ji cewar Fiddausi take neman iyayenta sai ta ce ko dai Alhaji Lawan. Sai Gaji ta ce yawwa can, ko nan ne sai Binta ta ce nan ne ba ki ga neman da mukai ba amma ba'a same ta ba. Kuma shi Abban har karar mai nan gidan ya yi domin, sun zato tana nan, mu kuma ko gidan nan ba ta zo ba, amma watannin baya da ta zo, ya zo ya dauke tato shi ne yake zaton tana nan. Hajiya ta ce gashi kuma Alhajin ba ya nan da sai ku tafi a dawo da ita, kuma da za ki kwana da saiki yi kwanciyarki da safe kи je a dawo da ita. Gaji ta ce ai ni ba zan kwana ba domin za'a neme ni a gida, na san ba zai kasa sanin Koki ba idan Ailah ya kai mu sai ya zo ya tafi da ita. Gaji ta ce to ni 25 4 Hajiya zan koma sai an kwana biyu, Binta ta ce to madalla an gode Binta ta kuma kawo kudi ta ba ta ta ce ga shi kin shiga mota. Gaji ta ansa ta yi godiya, ta fita ranta a 6aсе ganin ba ai nasara ba,don da a ce Fiddausi na nan to zaman da ta yi ya isa a ce ta ganta. Nan dai ta koma gida ba gwiwa, ita kuwa Hajiya Binta sai Allah-Allah take Alhaji Lawan ya dawo ta ba shi labarin ganin Fiddausi, bayan wani lokaci da tafiyar Hajiya Gaji sai ga Alhaji ya dawo bayan ta yi masa sannu da zuwa sai ta soma ba shi labarin abin da ya faru cewar yanzun nan wata mata ta zo daga gidan mai unguwar Koki fitarta kenan. Alhaji ya ce lafiya, wai Fiddausi aka gani a can baka ga dadewar da ta yi baa nan, tana jiranka, amma ba ka dawo ba. Amma ta-ce gobe da safe ka je ka taho da ita, Alhaji ya yimurna sosai ya ce Allah ya kai mu, wannan shi ne abin da yafaru a gidan. Lamarin Gaji munafukakuwa tana isa gida ta tarar Abbayana jiranta, ta yi sallama Abba ya amsa yana ta murna tana zama, Abba ya ce yaya tana can Gaji ta ce ba ta nan, Abba ya yi takaicin rashin samun Fiddausi. Sannan kowa daga cikinsu ya zauna yana zulumi tare da bak cikin rashin ganinta, domin hanyar kudi t toshe rashin zamanta da su kenan. Bayan gari yawaye sai Alhaji Lawan yashirya ya nifi Koki don dauko fiddausi ba su san makirci ne Gaji ta kada musu ba. Koda ya ısa ya nemigidan mai unguwa suka gaisa sai Lawan ya ce don Allah tambaya nake, mai unguwa ya ce Allah ya sa na sani, Lawan ya ce wata yarinya Budurwa na zo karba, don jiya wata ta zo gidana daga gidanka ta ce tanan nan an ganta, wai ana peman iyayenta, don lokacin da ta je bananan, to shine na zo yanzu, amma da tun jiyan za mu taho. Mai unguwa ya yi shiru sannan ya ce wata mata? Lawan ya ce E" Mai unguwa ya ce shi tun da ya hau kujerar nan bai taba aika wani yaje nemo iyayen yara ba. Toballe mace, mai unguwa 26 ya ce shi sam ba daga gidansa ba, a lokacin yasa aka fito masa da duk yaran da suke gidansa ya duba, ko Allah ya sa ya same ta. Lokacin da Alhaji Lawan ya ji wannan batu, sai ya ce to lalle duk yadda aka yi wani makirci aka shiryamasa, a lokacin ya cewa mai unguwa na gode madalla, snnan aka fitoda batattun yaran ya duba yaga sam ba Fiddausi. Don haka ya yi ban kwana da mai unguwa ya koma gida,, ya shedawa mai dakinsa cewar lalle wannan mata karya take akwai dai abin da take nufi da mu domin idant an biya ma Abbane ya turo a gani ko tana nan. Ni kona same ta ma ba wanda ya isa ya sa na sake ba shi ita domin wata rana idan ana haka ganinta ma ba za a yi ba muddin aka sake mai da ita, haka suka kasance. Bayan wasu kwanaki, Alhaji Abdullahi ya shirya suka taho Kano da shi da Fiddausi da Mustapha, koda suka iso Kano lafiya sai Alhaji ya nifi gidan mahifansa, suka yi sallama Hajiya Binta ta amsa, tana lekowa sai ta ga Alhaji Abdullahi da Fiddausi ta yi musu barka da zuwa, inda ta yi musu shimfida bayan sun zauna Alhaji y gaida mahaifiyarsa, sannan Fiddausi da Mustapha suma suka gaishe ta, Hajiya tana fara'a da ganin dawowar Fiddausi, ta ce Fiddausi daga ina, Fiddausi ta ce Katsina na je, kuma yanzu daga can muke domin Baffa ne ya ce mu taho na yi ramuwar abin da Abba da mai dakinsa Gaji da 'ya'yansa suka yi min. Amma da ba zan dawo ba. Koda Fiddausi'ta yi shiru, sai Abdullahi yafara shaidawa hajiya abin da Fiddausi ta gaya masa, kuma yace don Allah me ya sa lokacin da na zo ba ku gayan ba ai da komai ake ciki da tuni an gama. Don ni ba zan yarda ba, don haka yanzu daukar fansa muka zo yi, a lokacin Hajiya ta ce yanzu ya za'a yi ta iyarama abin da sukai mata, ni daia ganina kawai a barwa Allah shi ya fi. Domin shi zai saka mata, Alhaji ya ce dama Hajiya ba du za ta rama ba, ai wani abin 27 ma ta manta, amma kin san ramuwar gayya, taf ta gayya safi Don haka ko kadan sai la rama A lokncn yn gии Mustapha, Hajiya la ce ai na san shi ha tun унн bн. Миужн sunsaii wani lokaci mat tsaho suna hira s Alhaji wn ya dawo Abdullahi, Mustapha da Fiddaust sukиi barka da zuwa ya asн Ya ce lafiya na g ku suke dawowи ya ce I, sannan ya Kara da cewa a nи ун gаno Fiddaue? Abdullahıya ba shi labarin duk yadda ta kиsance yu gaунми uban Shi ma uban ya ba shi labarin yadda suka kwashs An Abba, yace yanzu Fiddausi can ta je Abdullahi yu ee at tama dade a can Sannan ya ce kawo ta na yi, Albaji Lawan sam ba za ta k oma gidan Abbaba abdulllahiya ce ai ba can zan kai ta ba dama zuwa na yi tayi ramuwa, Lawan ya ee lalle wannan shi ne abin bida, gaskıyane an yi dai-dai allah ya yi maka albarka! Amin in ji HajiyaBinta, a lokacin Mustapha ya ce ni zan tafi sai an kwana biyu Abdullahi yace to madalla, ka gaida Alhaji ka ce ni ma na zo ni da Fiddausi, kuma zan zo har gida na gaishe shi. Mustapha yace to zan gaya masa. A lokacin ne Alhaji Lawn da Binta suka ce ka gaida gida. Sanan Fiddausi ta yi wa Mustapha rakiya har kofar gida, ta ce sai yaushe yace zan zo byan kwana biyu, ta ce to na gode. nan dai suka yi ban kwana, ta ce don Allah ka gaida Baban da Hajiya, Mustapha ya ce sa ji da haka suką rabu, ta dawo gida. A inda Alhaji Abdullahi yake cewa anama ban ji dadi ba da na zo watannin baya ba ku gayan ba. Ai da tuni na dau matakin da zan dauka, Alhaji yace ai ba komaika san tashin hankalibabu dadi yanzu ba gashi ka ji ba. Haka dai suka yi ta yin hira. Amma shi kuwa Mustapha bayan ya isa gida, yayi sallama Hajiya ta amsa Mustapha ya shiga ya gaishe ta, ta ce har ka dawo ya ce E" Ta ce yaya ka baro su ya ce lafiya kalau, kuma ai tare muka taho haddda Alhaji kuma da Fiddausi domin 28 ramuwa ta zo yi, Hajiya ta yi murna kuma duk sun ce gaisheku, Hajiya ta ce muna amsawa. a Bayan an kawan biyu da zuwan Abdullahi sai ya ce to Bab, yau fa mu za mu je gidan Abbaa lokacin Alhaji da Binta sukai musu a dawo lafiya suka ce amin, suka fita suka shiga mota suka nifi gidan su Fiddausı sai suka tsaı da motar, Abdullahi ya ce maza ki shiga ki yi min sallama da Abba, a lokacin da ta yi sallama suna sama dukkaninsu, sai da ta hau sannan suka ji tana shiga inda suke, sai dukkaninsu suka juya sai suka ga Fiddausi, sai mamaki ya kama su, ganin Fiddausi ta sake kama ta sake kyau sosai, nan dai su kai cak suna ta tunani wai ko fiddusi ce koba ita ba ce, Fiddausi d ta ga haka, sai ta ce wai ana sallama, nan dai Abba ya tashi yana mamaki bai cew kowa komai ba ya fita. Domin yasha jinin jikinsa cewar ba banza ba Fiddausi ta shigo kai tsye ba, kodaAbba ya daga kan kujerar da yake kai, sai Fiddausi ta dare. Yayin da ta ga kwanukan abinci a jere sai kawai ta soma ci. Ba tare da ta yi wa kowa magana ba, koda Hajiya Gaji ta ga haka sai wani sabon mamaki ya kama ta, ta kasa cewa komai, su Jamila 'yan duniya yau ana gida. Ta ce hajiya kina ganin abin da Fidausi take yi kuwa, Hajiya za ta yi magana sai Fiddausi ta mike ta cewa Jamila daman wajankina zo, munafika. Sai Fiddausi- ta ciro almakashi daga cikin jakarta ta datse gashin kan Jamila koda Jamila ta ga ta zama Gwai-gwai sai ta dunka kuka tana cewa Hajiya kina ganinta ko, Hajiya Gaji ranta ya 6асі sosai a lokacin ta daga hannu zata mari Fiddausi, sai ta ce "Ahir kika kuskurakika taba ni, yanzu nayi kasa-kasa dake munafuka, koda Gaji ta ji haka sai jikinta ya yi sanyi. Ga shi Abba ya fita yayi zamansa kuma dama Fidausi ta fi Karfin Jamila daman don da ana mulkkin kama karyane shi yasa Jamila ke rawa da bazar su Abba, to dama an ce ramuwar gayyata fi ta gaya zafi. Lokacin dasuke mata 29 azaba, sun manta cewar wata rana za ta rama ne tn da dai Allah bai dauki ranta ba. Koda Fidddausi ta rama yanke ga shi da aka yi mata sai ta sauka ta bar banzaye biyu 'ya da uwa azzalumai. Gaji munafuka sai ta bita da kallo. Bayan Fiddausi ta fito sai ta tarar da Alhaji da Abba suna magana. Domin shi Abba a zatonsa Abdullahi dawowa ya yi da Fiddausi, don shi har ya shiryaabin da zai mata idan ya koma, sai kawai ya ga Fiddausi ta fito. A lokacin shi Abba ko godiya bai masaba. Don Abdullahi bai nuna masa komai ba. Sai Fiddausi ta ce baffa na fiito mu tafi ta shiga mota Abdullahi ya tashi.ya bar Abba a zaune ya yi sallama da shi, Abba ya kasa cewa komai saboda mamaki shi kuwa Abdullahi ya shiga mota sukai tafiyarsu, lokacin Abba ya koma ciki yana bakin cikin abin da Abdullahi ya yi masa, koda ya hausama, sai ya taras da Jamila tana kuka yaya lafiya Abba ya tambayi Gaji, a lokacin nan Gaji ta hau masifa tana wallahi ni ba zan yadda da haka ba, domin ba zanyadda 'yar ciina ta dunga yi ***min rashin kunyaba, kawai ka je ka yi zamanka a wajc ai da kana nan da ba tai mana hka ba, kaiAbba da abin ya zame masa biyu, ga takaicin abin da Abdulahi ya yi masa ga kuma shi Gaji tana yi masa fada, shin wai me aka yi ne ni na tambaye kini ba ki bani amsa ba kuma gashi sai fada kike ta yi min, ta ce ai dole nena yi ma fada mana wai yarinyar nan Fiddausi har ita za ta iya zuwa har nan gidan ta yankewa Jamila gashi, wai har ni take cewa za ta yi kasa-kasa da ni, idan na kuskura na taba ta, Abba wani sabon bakin ciki ya zo masa, ya ce ai wan Hajiya Zainab ne ya sa ta ta yi komai, Hajiya ta ce ba dai wanda ya zò kwanakin baya ba, ya ce shi mana! Gaji ta ce ashe ba shi da mutunci, Abba ya ce ai ni ma sai yanzu na sani ashe da ta bar gidan nan ta je gidan Alhaji Lawan can ya tura ta, ya ce amma ba komai i wata rana za ta ske dawowa za ta san lahira babu dadi kai Abba kenan! 30 To ai lahira ita ce mai dadi ga wadanda sukai aiki na gari, domin sun fi son ma lahirar a kan duniya, a lokacin Abba ya ce da Gaji ki yi hakuri ya kuma rarrashi Jamila, ya ce to yanzu kin ga wan Hajiya Zainabya soma zuwa kuma yasan komai, to mai yiwa a karbe dukiyar Fiddausi daga gun Alhaji Hamisu shi ya ce zai a jiye a hannunsa, to ammaidan yasan wata ai bai san wata ba, kin san kafin fiddausi ta bar gidan ta samin hannu a takardun banki, to amma na je sun hana ni, amma zan je bankin Amurka na karbo na can, idan na dawo nan sai na sake gwada wa ko za su ba ni, ko yaya kika gani, to a lokacin Hajiya dai ranta a 6ace yake amma koda ta ji maganar kudi sai ta murmure yake to amma fa ki yi dabara tun da dai mu ne ba'a son mu ci arzikinta, to mune masu ci ko an Ki ko an so. Al'amarin su Abdullahi kuwa bayan sun koma ida yake tambayar Fiddausi in ce ko kin fara ramawa kuma ina mai yi miki gargadin cewa kada ki ji tsoron kowa, kuma duk abin da kika san an yi miki ki rama kin ji ko. A lokacin Fiddausi ta ce ai na soma ramawa Baffa, kuma babu wanda zan ji tsoro a gidan daman rashin wayewa ne ya kawo haka da kuma halin yarinta, amma yanzu za su dandani kudarsua wajena sosai, nan dai sukai ta yin hira. Lamarin gidan Alhaji Abba lokacin da gari ya waye sai Alhaji abba ya yi shirin tafiya AMURKA, Hajiya ta yi wa Abbafatan samun nasara. Kai ina ruwan wahalalle haka kurum ba ka ajiye ba ba ka bawa wani ajiya ba, ka shirya ka ce wai kai kudi za ka karbo. Alhaji Abba ya niif filin jirgin MALAM AMINU INTERNATIONAL AIRPORT. A inda ya tashi zuwa Amurka, byan rana ta daga kamar fiddausi ta sani sai Alhaji Abdullahi ya kawo ta, ta ce baffa yau kwana zan yi. Ya ce to a lokacin ya sake gargadinta cewar kada ta ji tsoron kowa, kuma idan ta ga ba sarari ta dawo gida, fiddausi ta ce, to, alhaji ya tafi, Fiddausi ta shiga ta yi sallama Jamila 31 a amsa ba ta san Fiddausi ba ce, a wannan lokacin Hajiya Gaji tana daki tana sharar barci, a lokacin Fiddausi ta hawo sama koda Jamila ta ganta sai gabanta ya fadi ji kake ras, Fiddausi ta wuce ba tare da ta yiwa Jamila magana ba sai ta aifi baranda koda ta isa, sai ta sami kujcrar da Abba ne kawai, ke hawanta lokacin da yake nishadi sai kawai ta yi ramanta a kai, ita kuwa Jamila sai ta biyo Fidddausi ta ga abin da za ta yi, koda ta ga Fiddausi a kan kujerar Abba ga shi kuma Gaji tana sharar barci. Sai Jamila ta ce wannan ai iskanci ne yaya kujerar da Abba yake hawa za ki hau don wani sabon rainin hankali da kika sake, koda Fiddausi ta ji haka sai ta mike ta ce ba za a tashi ba, a lokacin Fiddausi ta Kwace zanin Jamila da mayafin da dan kwali gaba daya, ko da Jamila ta ga haka sai ta shiga daki da sauri tana kuka har sai da Hajiya ta tashi ta ce yaya me ya faru? Ta ce kin ga abin da Fiddausi ta yi min kuma ga ta can a kan kujerar Abba wai don na ce ta tashi shi ne ta yi mn haka koda Hajiya ta ji haka sai ta ce yau ma dawowa ta yi Jamila ta ce E" Hajiya Gaji ta tashi a fu sace ta n if inda Fiddausi take, koda ta iso inda Fiddausi take sai k awai ta ganta Gaji ba ta yi wata-wata ba sai kawai ta dauke Fiddausi da mari, nan Fiddausi

Chapter 3 of 5