Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 5
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels MAI RABOD.GANIN BAD2 Hanua A Bashir Ayagi MAI RABON GANIN BADI NA BIYU NA HAUWA A. BASHIR AYAGI GODIYА D ukkan yabo ya tabbata ga Allah Madaukakin Sarki tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabinsa (S.A.W) da Sahabbansa da wadanda suka yi riko da da Sunnarsa har zuwa ranar sakamako. Ina mika godiyata ga Allah da Ya azurta ni da basirar cigaba da rabu ta wannan littafi MAI RABON GANIN BADI na biyu. Yanzu ga shi cikin ikon Allah har littafin ya fito, ina gdiya ga mutanen da s uka taimaka min kamar mai gidana Alhaji BASHIR AYAGI, da BABA INUSA SANI MAINAGGE TIJJANI ADO, da kanina RABI'U MUHAMMAD DISO, da kanwata LAMI ALHAJI BASHIR AYAGI da aminiyata HALIMA SHEHU GWALE KANO. da kawata HAЛYA HAUWA K ULU MUSA GWALE, KANO. Daga karshe ina mika godiyata ga duk mutumin da ya taimaka mini ta kowace hanya. Allah Ya saka musu da alherinsa, Amin Summa Amin. HAUWA A. BASHIR AYAGI HAKKIN MALLAKA (M) HAUWA A. BASHIR AY AGI,. MAI RABON GANIN BADI. AN FARA BUGAWA - 1996. 1I DOKA Ba a yarda wani ya buga ko ya juyi wani sashe daga 6angare wannan littafi ba sai da izinin mai shi wadda hakkin mallaka ya rataya a wuyanta. WASU DAGA CIKIN LITTAFAN DA NA WALLAFA SUNE:- 1. SO SARTSE I & II 2. MASOYINA I & II 3. BAKIN CIKIN RAYUWATA 1. MASU FITOWA NAN GAВА SO AJIYAR ZUCIYA, NA DAYA DA NA BIYU 2. RAYUWAR SOYAYYA NA DAYA DA NA BIYU. 3. GIMBIYA SALWA DA YARIMA SAYID. 4. BAKIN CIKIN RAYUWATA NA BIYU. 2 Ana iya samunsu a wadannan wurare:- 1. GARBA MUHAMMAD BOOKSHOP SABON GARI MARKET NO 222. 2. SAUKI BOOKSHIP NO 96 JAN BULO SABON GARI MARKEТ. 3. NASIHA BOOKSHOP KASUWAR KURMI. 4. JAKARA BOOKSHOP 25 JAKARA KANO. 5. NASIBI BOOKSHOΡ JUMΑ'A MOSQUE KANO III ra san mai karatu ba zai manta cewa littafi na daya a Nkwana a inda Fiddausi, ta bar gidan Alhaji Abbe kuma ya ke nemanta amma bai same ta ba. Koda Abba ya yi nema har ya gaji sai ya koma gida inda Hajiya Gaji ta ce, "Yaya ba labar?", Abba ya cе Babu! Ba inda ban zaga ba amma babu labari." Gaji ta ce Ita kuwa wannan yarinya ina ta shiga?" Abba ya ce, "То wa ya sani!" Haka dai suka kasance a ciin wannan halite tunani. Ita kuwa Fiddau si koda ta bar gidan Alhaji Hamis sai ta nifi gidan Kakanninta wato Iyayen Hajiya Zainab marigayiya, bayan ta yi sallama Hajiya Binta ta amsa Fiddausi ta gaida kakarta, Hajiya ta ce,"Lafiya?" Nan Fiddausi ta kwashe labari duka ta sanar da ita hade da iria bakar wahalar da take sha duka ta sanar da ita. Fiddausi ta ce, "Don Allah Hajiya ku taimakamin k rabani da masifar Abba da Hajiya Gaji." Lokacin da take wannan jawabi, hawaye ne yake zuba daga idanun Hajiy Binta. Ranta ya baci kwarai da jin wannan magana. Lokacih Binta ta rarrashi Fiddausi ta ce, ``Ki yi hakuri, alhaji ya dawo za'a san matakin da za'a dauka, domin ba zan yarda da h akea ba, wato an kashe mahaifiyarki wato kema so ake a kashe ki kenan. To idan ba zai rike ki tsakani da Allah ba, to sai y fada. ai wannan rashin Imani ne da tu nani." Haka dai Hajiy Binta tai ta fada lamarin ta kenan. 2 Alhaji Abba kuwa kulum sai ya fita neman Fiddausi domin kada Alhaji H amisu ya zo ya tarar Fiddau si bata na kuma gashi kenan ba zai bada kudin ba, don da a ce zai bayu ko da a ce bata nan, to ba abin da zai sa shi wahalar da kans gu n neman Fidddausi, haka Abba ya kai cigiyarta gidan "REDIYO" da Jaridu haka kuma ya kai hotunanta gidan Talabijin don shi Abba ya'manta cewar Fiddausi tana d 1 Nakanni a garin shi ne bai ko kawo cewar tana can ba. Yau kumanın kwana biyar kenan da batan Fiddausi Alhaji Abba abin duniya ya dame shi yana zaune, domin kullum sai an yi cigiya amma babu labari, kwatsam sai ya tuna Mustapha sau rayin Fiddausi wanda ya yi masa korar kare kuma gashi dan Alhaji Hamisu ne, sai ya ce, "To ko wajansa ta tafi ne," ko da ya tuna sai ya mike ya ce da Gaji, "Zan je wajan Mustapha ko tana can" Sai ta ce, "Af! Kaga kuwa mantawa na yi, amma da tuni ma ba'a je ba." Abba ya ce, "Ni ma ai tunawa na yi," Gaji ta ce, "To y anzu yaya za kai kenan wajan samunsa a kadaice, kada ka hadu da alhaji Hamisu fa." Abba ya ce, "Kada ki damu, ai ba a gi dan y ake ba, domin ki n san gida yake warewa duk 'ya'yansa. Hajiya Gaji ta y i wa Abba a dawo lafiya, ya fito ya nifi gidan su Mustapha, lokacin da ya isa ya yi sallama, wani lokaci matsakaici, sai Mustapha ya fito domin ganin mai sallama. Koda ya fito sai ya ga Alhaji Abba, Mu stapha ya yi mamakin ganin Alhaji Abba kwarai da gaske, ya gaida Abba ya yi tsammanin cin zarafin da ya y i masa ne, babu abin da ya fito daga bakin Abba sai cewa ya yi, "Ka ga Mustapha maza ka fito mini da yarinya, zaka wani gaisheni, do min yau kwananta biyar kenan da gu du, kuma na san ba i nda zata sai wajenka." Mustapha da ya ji haka sai ya ce, "Wallahi Alhaji bata zo ba." Abb ya kada ya raya, amma Mustapha ya ce bata wajansa. Alhaji ya y i bakin ciki, koda Gaji ta ganshi ba Fiddausi sai ita ma ranta ya 6aci, ta ce. "Ba ta nan?" Ya ce, "Bata nan." Alhaji Abba yana huci ğayin da ya ce, "Wallahi darajar Alhaji Hamisu ya ce, don da a ce ba fansa bane, da sai ya raina kansa don da sawa zan yi a yi masa lilis kuma sai ya fadi inda take." Gaji ta ce, "Wannan gaskiya ne, kuma ai ya riga ya sanka da bai sanka ba da sai ya fadawa aya zakinta." Haka dai s ukai ta hira akan Fiddausi. 2 Ita kuwa Fiddausi tana can hankalinta a kwance babu abin da y ake dam unta ta murmure sosai. Wata rana Abba yana zaune abin duniya ya ishe shi, ba CUWA-CUWA, an fara kada masa "SUMBUKA" sai ya tuna da mahaifin Hajiya Zainab. Nan ya tuna da cewa, Fiddausi fa tana kaka a duniya, sai kawai ya mike ya ce, zan tafi gidan Alhaji Lawan domin yana zaton ma Fiddausi na can. Koda Gaji ta ji sai ta ce, "Ai k uwa ai ba za'a rasata can ba., Tun da har an yi cigiya an gaji, kuma ka san ko tana can ba za su dawo da ita ba. Domin batun yanzu ya so ta dawo gurinsa ba ai sai ka hanzarta ka gani don na san tana can." Abba ya ce, "Ai kuwa idan na same ta sai na lahira ya fita jin dadi, don kuwa sai na mata dukan kaskanci, ku ma sai na ciwa Kakan nata mutunci yadda baya zato." yi Lokacin da Abba ya ita a fusace, bai zarce ko ına sai gidan Alhaji Lawan a inda da isarsa ya take burki kura ta tashi fau! Ya fita, ya shiga ya yi salama aka amsa. A lo kacin ya yi sa'a kuwa domin ya tarar da Alhaji Lawan, ya fita ya ga Abba, ya ce, `"Alhaji Abba!" ya mika masa hannu suka gaisa, gama gaisuwarsu ke da wuya sai Abba ya ce, "Ko Fiddausi ta zo?" Alhaji Lawan ya ce, "E, ta zo, yau kwananta ashirin da daya, don na ga ba wanda ka aiko ne, sai a rediyo nake jin cigiya shi ya sa ban dawo da ita ba. Na ce sdai ka zo da kanka don ka sanar da mu, amma ba ka tu ro ba ni kuma shi ya sa na yi "Duf!!! K uma abin da kake wa yarinyar nan kai da mai dakinka ba ku kyauta ba, kuma na zo har gida na yi muku nasiha kan ku sasssauta amma ba ku fasa ba. Ka tuna fa kuna da 'ya'ya kuma abin da kuka yiwa dan wani haka za a yi wa naku, ka tuna da karin maganar Hausawa da suke cewa MAI RABON GANIN BADI TO FA KO ANA DAKAWA A TURMI SAI YA GANI." Kuma aı wuya ba ta kisa, kuma abin da k a shuka lalle shi za ka girbe. Azabtar da itan da kuke yi shi zai sa ta mutu, domin na lura da cewar ba 3 son rayuwarta kuke ba. Kuma ka ci amanar dan'uwanka, da ana m utuwa a dawo da an ji kunya. Ba karama ba, kuma abin duniya mai karewa ya barka da mutum to ka ji tsoron Allah, duniya ba matabbata ba ce." Ko da A Lawan ya kawo nan, sai Alhajin Abba ya ce, "To dakata ka gama." Alhaji Lawan ya ce, "E" "To na ji shiga ka fito m in da ita. Ai da ka san wa'azi za kai sai ka shiga ka fito da turmi ka zauna ko ya fi shiga kunnen wanda kake wa.. A wannan lokaci ne Alhaji Abba aka wani karkace a kai wani doro a kace cikin mamaki, yanzu har kai ne za ka gaya min Allah! Kai ka manta abin da ka yi har za ka yi wa wani wa'azi, to bari na gaya maka, to babu wanda ya shiga kunnena kuma wallahi idan ba ka hanka. ba sai mu au rimin gafiya m un fado a na 6era. Kuma ka shiga taitayinka ko ka san ko shari'a muka shiga ni zan yi rinjaye. Kuma da ka ce da ana mutuwa a dawo da an ji kunya to ai sai ka dawo da shi don na ji kunyar, kuma da ka ce na ci amana to kai ma idan ka samu ci za ka yi, wannan ai shi ne haushin rashi, wai da aka ce wa makaho ga ido, haka dai Abba ya yi ta maganganu marasa dadi. Alhaji Lawan ya ce, "Ai nasihar da na yi ma shi ne ranka ya 6aci, dama an ce gaskiya dacі gareta kuma idan an ki ji ba a ki gani ba. Abba ya ce na ji shiga ka fito min da ita. Alhaji Lawan ya ce, "Ai babu inda za ta su kukc ku kasheta. To ba za ta koma ba, ai ta zo k enan, Abba ya yi murmushi ya ce, "Wasa kenan, haka Alhaji Lawan ya dage kan Fiddausi ba za ta k oma gidan Abba ba, shi k uma ya dage kan cewar nan duniya babu wanda ya isa ya, karbcta daga hannunsa, haka su kai ta bugawa har makotan Alhaji Lawan su ka sa baki, su ka ce ai wata rana za ta dawo ne muddin bai fasa yi mata abin da yake yi mata ba. Alhaji Lawan ya yi dan Jim! Ka sancewarsa mai daukan banbaki, ya ce, to wallahi don kun sa baki ne da ban ga `KAFARGEN BANZAN" da ya isa ya fitar da Fiddausi daga 4 gidan nan ba, sai ya shiga gida, Hajiya Binta ta ce yaya ta tafi, ya ce a'a, ina Fiddausin ta ce tana wanka, bayan jimawa kadan ta firo, alhaji ya ce, maza ki sa kayanki ki zo ku tafi. H ajiya ta ce ina? Alhaji ya ce gidansu yayin da ya ci gaba da yi mata bayanin yadda suka yi da Alhaji Abba, ita kuwa Fiddausi koda jin cewa za ta koma ai sai ta sa kuka Hajiya tana rarrashinta tare da bata hakuri, haka Fiddausi ta sa kayanta, ya ce ga ta sannan ya mikawa Alhaji Abba hannu, amma Alhaji Abba ko dubansa bai yi ba bare ma ya mika m asa hannu, ita kuwa Fiddausi sai hawaye ne yake zuba daga idanunta sai bata hakuri da rarrashinta yake yi haka Abba ya saka Fiddausi a mota a suka vufi gida. Nan ne Alhaji Lawan ya ce a sauka lafiya, amma shi Alhaji Abba ko waigowa bai yi ba bare ya ce wa Alhaji wani abu. Bayan da suka isa, Abba ya kashe mota Fidausi ta fita ta shiga gida suka y i sallama, Hajiya Gaji ta amsa, a lokacin ta leko sai ta ga Abba da Fiddausi sun shigo, bayan da suka hau sama Hajiya Gaji ta y i wa Abba bark da zuwa, ta ce ai ca nake ba ta can, abba ya shiga bawa Gaji labarin yadda s uka y da Alhaji Lawan ya fada mata a lokacin Fiddausi ta gaida Hajiya, maimakon ta amsa sai kawai ta tashi ba ta amsa ba koda ta shiga daki sai kawai ta fito da bulala ta m ikawa Alhaji abba koda Fiddausi ta ga haka sai ta soma kuka tana basu hakuri, amma idan sun yi mata magana to haka kai da baka nan sun yi ma. Haka Abba cin karfi ya kama yarinyar nan da duka, ya yi mata dukan kaskanci ya sassamamata kamanni. Bayan Fiddausi ta ci na j aki, sai Abba ya ce go be ma ki sake fita ba da izinina ba Sai na yi miki wanda ya fi haka, koda Fiddausi ta ci dúka sai jikinta ya soma cíwo, zazzabi ya rufeta, sai ta kwanta rash in lafiya, babu mai kula da ita balle ma ya bata magani. Bayan kwana biyu da kwanciyarta kwatsam sai rannen Alhaji Hamisu ya yi sallana, ko da su ka ji muryarsa ai sai 5 nan da nan Gaji ta koma kusa da Fiddausi ta zauna, shi k uma Abba ya yi wa Alhaji Hamisu barka da zuwa, ya amsa, yana hawowa sama Abba ya mikawa Alhaji hannu, a lokacin ya ce ina Fiddausi, abba ya ce tana daki ba ta jin dadi ne! alhaji Hamisu ya tambaya an kai ta HOSPITAL kuwa. Abba ya ce dama yanzu nake cewa zan kaita. Alhaji Hamisu ransa ya бaci sosai a lokacin ya shiga dakin Fiddausi, ko da ya ganta sai ransa ya kara baci, nan Gaji ta gai da shi ya amsa a yankwane! Bayan ya amsa sai ya yi wa Fiddausi sannu, to a lokacin saboda zafin ciwo ba ta iya amsawa ba. Nan da nan Alhaji ya fita ya samo wasu kawayen Fiddausi inda suka kamata aka fita da ita. Koda Abba ya ga haka, sai ya ce gani ga Hajiya! Amman a rasa wanda zai kamata sai ka nemo wasu, nan dai aka fita da Fiddausi, aka dunguma HOSPITAL, Abba da mai dakinsa su ma suna ciki kamar gaske. A inda aka ba ta kwanciya haka Fiddausi ta ci gaba da karbar magani kuma Alhaji Haisu shi da kansa ya kula da ita. Lamarin Jamilu dan gidan Alhaji kuwa dake Amurka! Yana can yana sheke ayarsa, amma wai a masayin karatu ya tafi, to dai a halin da ake ciki yanzu Jamilu ya kamu da shegiyar cutar nan mai karya garkuwar jiki wato "AIDS" domin sakamakon ya biyo baya ne a karkashin binciken da aka yi masa ne a wani HOSPITAL dake "Washington" aka gano cewar yamu da wannan cuta, don haka Jamilu ya sanar cewar zai dawo gida don ya san mutuwa ce ba tantama, to dama haka duniya take ta ishi kowa, shi dai Jamilu ya san Lahira ko ba t aya, ga shi kuma ta hanyar banza. Lamarinsa kenan. Fiddausi kuwa an sallameta domin ta ji sauki, bayan komai ya nutsa ta ci gaba da bauta kamar yadda ta saba. Wata rana da misalin karfe goma sha biyu na rana sai kawai ga Jamilu ya dawo daga Amurka, kasar da ya je ya "Tsuga" ya kuma "Tsumu" ya kuma sheke ayarsa a tsanake. Yana ko 6 tare ne da wani abokinsa koda su ka yi salkama aka amsa, Hajiya ta daur muryar danta Jamilu ai sai nan da nan ta shedawa Alhaji Abba cewar ga Jamilu ya dawo, koda Abba ya ji haka sai murna da murmushi ya taryi Jamilu ya rungume shi yana murna, wai shi m ai da! Shi kuwa Jamilu ransa a bace don ya san h alin da yake ciki. Hajiya da diyarta Jamila suka sakko daga sama, su na murna da dawowarsa, bayan sun yi masa barka da isowa, sai Jamilu ya ja abokinsa su ka shiga dakinsa. To a lokacin da su Jamilu suka shigo, Fiddausi tana ban daki to amma tana ji ana cewa Jamilu ya dawo, koda ta fito daga bandaki sai ta nifi fakinsa don yi masa sannu da zuwa bayan ta yi sallama ya amsa sai ta shiga ta durku sa ta gaishe su baki daya ta ce and awo lafiya, ya ce lafiya lau, ta yi waje, ko da fitarta sai wannan aboki nasa mai suna Tahir ya ce wannan fa! Jamilu ya ce,Yar aike ce, ka ji wulakanci bay an da bazarta s uke rawa, baki daya bama shi ba har iyayensa ai duk inuwarta "Suka laбa-6a" suke samıa nutsuwa. Amma saboda rainin hankali ya ce wani 'yar aikinsu ce. Tahir ya ce ki amma fa tana da kyau, sosai. Kuma ina so ka hadani da ita, idan mun daidaita sai mu je wani `"hotel" mu gana. Ko ya ka ce, Jamilu ya ce, "Wannan gaskiya ne yayin da suka tafa. To Allah ya kare mu da h ali irin na su Jamilu amin. Yanzu dai gashi Jamilu "AIDS" ta kama shi, amma bai sadeda ya koma ga Allah ba. Har yanzu bai fasa ba, domin abokin tafiya yake nema domin idan `AIDS" ta kama ka ba ta da magani sai kabari. Amma shi Jamilu ba zai tuba ba balle Allah ya yafe masa, a lokacin Jamilu yà ce ai za ta kawo mana abinci na baku guri ku gana ko kwa daidaita ka ji rashin mutunci za'a jawowa Fiddausi gagaru ma don k uwa shi har yarzu so yyake ya yi mata sharri shi ya sa ya ce mata 'yar aike ce. Don da ya ce 'yar uwarsa ce Tahir ba zai ce zai yi mata maganar banza ba. 7 2 Lamarin Fiddausi kuwa koda ta koma sai Alhaji Abba ya ce ga riga ta nan ki goge min sawa zan yi na fita, sai Fiddausi, ta dau rigar tana gogewa,, bayan ta juya bayan dutsen ya yi zafi ta dora shi a gaban tana dannewa sai Hajiya ta yi kiranta, saboda tsoron da take wa H ajiya sai ta fita da sau ri ta manta b a ta 'au ke dutsen ba, tana zuwa ta durkusa, Hajiya ta ce ga abinci ki kaiwa su Jamilu, Allah Sarki Fiddausi sai t a dauki abincin da sauri ta nifi can dakin su Jamilu domin ta yi maza ta yi wa Abba aiki da ya bata, koda ta isa sai ta yi sallama suka amsa, Tahir da jin muryar Fiddausi sai ransa ya yi fari kamar wanda aka yi wa gafara. Fiddausi koda ta tura ta shiga sai Jamilu ya mike ya yi waje, inda ya ja kofa Fiddau si ba ta lura ba, sai ta ajiye kayan abincin ta juya, Tahir ya ce saurin me kike yi ne sai ta ce wallahi Abba ne ya ba ni aiki shi ne nake sauri kada ya yi min fada. Sai Tahir ya ce ai ya kamata ki saurari abhin da zan fada, a lokacin Tahir ya ce ni dai sonki nake a lokacin ya taso daga kan kujera sai ya iso gare ta koda Fiddausi ta ga haka sai ta yi baya Tahir 'yana murmushi yana cewa tsorona ki ke ji ne ita dai Fiddausi ba ta ce komai ba kuma gashi ya tare kofa balle ta fita kuma gashi Abba ya sata aiki kuma ta tuna lale cewar dutsen a kunne yake, can dai ta yi kukan kura ta banke Tahir. A lokacin Jamilu ya turo kofa da ya ga Fiddausi rike a hannun Tahir sai ya koma ya kirawo Hajiya da Alhaji da Jamila ya sanar da-su wai ga Fiddausi tana k okawa da Tahir ka ji munafiki. Ita kuwa Fiddausi sai kuka take yi a lokacin ne Alhaji ya ce ke Fiddausi! Sai nan da nan Tahir ya saketa, Fiddausi tana kuka ta ce Abba ka raba ni da wanan haka nan daga kawo abinci ya rike ni, Abba ya ce shin ina aikin da na baki, a lokacin Jamila ta ji kauri sai ta yi waje, Fiddausi ta ce ai ina cikin yi sai Hajiya ta yi kirana. Tana ru fe baki sai ga Jamila ta dauko riga duk ta kone, abba 8 yana ganin haka sai kawai ya kama Fiddausi da du ka ya zane ta Jamila da Jamilu sai dariya suke mata. Tahir a wannan lokacin da ya ga irin dukand a ake Wa Fiddausi sai tausayi ya kama shi, Tahir a zuciyarsa ya y alkawarin ba zai sake irin wannan aikin ba, Allah Sarki ka wanda yake da dan sauran tausayi da imani. Kuma ya y fatan daga wannan allah ya shirye shi haka. A wannan rana haka Tahir ya sami kansa a cikin tunane-tunane irin aikin asshan da suke aikatawa. Bayan ya sami kamar kwana uku sai ya ce shi zai koma gida domin ya zo ne don ya ga gidan Bayan ya gama shi ryawa Abba ya yi masa alheri mai yawa Tahir ya yi godiya, Jamilu da Abba sukai masa rakiya lig filin jirgi ya tashi sai KADUNA daman shi fan jahar Kadun ne. Bayan sun ga tashinsa sai suka juyo zuwa gida. Bayan komai ya nutsa a gidan Abba! Amma Jamilu bai gaya musu abin da yake ciki ba. Domin a lokacin bai fara kanjamewa ba, babu wanda ya sani sai shi sai Allah. Lamarin gidan su marigayiya Hajiya Zainab kuw yayanta ya zo ziyara daga Katsina don shi dama can Allah ya yi zamansa. Kuma nanne inda yake aiki amma duk sanda y sami hutu ya kan zo ya gai da 'yan uwa da abokan arziki. Sh dai wannan wa na Hajiyą Zainab ubansu daya kuma mahaifiyarsu ma daya Sunansa Alhaji Abdullahi. Kuma yana aiki ne a ma'aikatar gidaje ta Jahar Kátsina" koda ya kofar gidansu sai ya kashe mota ya shiga ya yi sallamaH ajiya Binta ta amsa a lokacin ta ce sannu da zuwa, ta yi mag shimfida ya zauna, bayan ya zauna ya gaishe ta amsa. Ta gidan su na nan lafiya ya ce lafiya lau. Na'ima ta ce gaısheku, Hajiya Binta ta ce muna amsawa, ya ce ya kanı hakuri ta ce hakuri sai Annabi to Allah ya ji kanta amin in Hajiya Binta. Ta ce amman ka dade ba ka zoba kuma bak yo aike ba, da har na shirya zuwa don na zo na gani ko lafiy Abdullahi ya ce wallahi lafiya lau hutu ne bans amu ba d و har zan aiko to shi wanda nake aikowa ya yi tafiya ne shi ya sa ban aiko da sako ba. Kuma yanzu ma hutu na samu shi ya sa na zo. Ta ce to ai ba komai ya ce ya su Fiddausi ta ce suna nan lafiya ya ce yaya baba bai dawo ba ta ce ai yanzu bai isa dawowa ba amma da an jima za ka gan shi haka su kai ta y in hira amma ba ta fada masa halin da su Fiddausi take ciki ba Don ta san shi mai zuciya ne yanzu sai ya tada hankalin mutane don haka ta yi shiru da bakinta bayan sun dade suna hira irin ta da da mahaifi, sai

Chapter 1 of 5