Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 5
hanya zan ba shi kyautarsa wallahi." Shima a fusace ya juyo ya ce "Banawa bane, gara ma ki nemi ubansa tun dare bai yi miki ba." Ta ke naji wata irin tsima ta kamani. Na ga falon na juyawa, na fara juyi ni kadai. Tuni Sadik ya zuro da 55 Amina A. Sharada gudu dan karfe only one daga hannuna domin in na fada kansa sai ya yi mugun jin ciwo. Kafin ya iso tuni an yi jifa da dan waje daya, ya yin da ni kuma na kifc kasa baki a datsc, ban san meke faruwa ba, domin bana cikin hankalina sam-sam. Sadik ya suri dansa cikin bacin rai. Bai lura ma da halin da na shiga ba ta dansa yake yi. Ya tafi gidan Mamy dan gaya mata abin da na yiwa dan domin a zatonsa nina ya da shi ina sani. Ni kuwa Daddy ne kife bisa kaina yana kuka "Umma ki tashi! Umma ki tashi!!" Ina ban san me ya ke fada ba. Mamy na jin abinda Sadik ya ce ta fada shi da fada tana cewa "Ai kadan ma tayi maka, inda ace ni ce abinda zan yi sai yafi haka. Kai yanzu in kana da kunya ka zo ka ce min wani abu? Haba Sadik, wai yaushe za ka yi hankali ne? Ace baka da wani abokin gaba sai matar da ka ke aure? wallahi anyi bitir!" Nusaiba ta karaso ta ce "Yaya tana ita kuma Hamdiyyar.?" Ya ce "Tana can akwance." "Akwance.!?" Inji Mamy. "Dukanta kayi.?" Ta kuma tambaya. Ya се "A'a ni ban taba ta ba, gani nayi kawai tayi jifa da shi ta fadi." Ta ce "Ai idan Hamdiyya batayi hankali ba sai bakin cikin ka ya kasheta wallahi." Ta dubi Nusaiba ta ce "Maza ki gani min abinda ke 56 Sharrin Jinni 3 faruwa." Nusaiba ta fisgi mayafi tayi waje da gudu, ya yin da shi kuma ya zauna Mamy tana ta yi masa fada akan abinda yake yi na rashin kyautawa. Akwance ta sameni rigingine bakina na kumfa, idona a tsaye kuma a juye. Da gudu ta fice bayan ta janyc Daddy ta koma gida a rude tana kiran "Mamy kizo kiga abinda take yi. Mamy ko mutuwa za ta ta yi?" Mamy ta fisgi hijabi ta fice, ya yin da shima Sadik yabi bayanta a hanzarce. Nusaiba ita ma ta dafa musa baya. Suna zuwa suka tsaya a kaina suna sallallami. Nan da nan Mamy ta yiwa Alhaji da Ibrahim waya suzo maza gida babu lafiya." Ba'a fi minti biyar ba sai gasu, domin dama suna tare, kuma a hanyar zuwa gida suke. Suna ganina Alhaji ya ce "Garin ya ya haka ta faru.?" Mamy ta ce "Gashi nan shi ya jawo. Ina gida yazo yake gayamin." Alhaji ya ce "To jiran me aka yi, sai a tafi asibiti. Suka dauk i sai mota. Daddy na ta kuka. A lokacin shekararsa audu, muka dunguma gaba ki daya. Ta ke aka bani gado gami da sanya min karin ruwa. Bayan gwaje-gwaje da aune-aune da aka yi min, amma ko kadan ban dawo hankalina ba. 57 Amina A. Sharada Likitoci sun kai bakwai akai kowa yana kokarinsa, amma lamarin yaci tura. Haka suka yi iya bakin kokarinsu, amma lamarin ya ci tura. Haka suka yi iya bakin kokarin su suka barni, domin hankalina bai dawo ba, kuma har wani lokaci bakina bai daina fitar da wannan farar kumfar ba. Ba wanda bai zubar min da hawaye ba har Alhaji. Shima Sadik a zaune yake ya yi tagumi yana tunani da dana sanin abinda ya yi min. Kwana bakwai a asibiti, amma kullum gobe ya jiya babu sauki babu dalilinsa. Dan haka Alhaji ya yanke shawarar aje can kauye a fadawa su Inna domin in ma cutar ta tafiya ce sa ganni ba sai dai suji mutuwa kwatsam ba. Dole Ibrahim me uake domin Sadik ba zai iya zuwa ba, shima a 'yan kwanakin nan har ya rame, ya jeme, ko abinci baya iya ci. Kullum sai kuka, a lokacin ne nadama ta zi masa, ya dinga tunanin wai me ya sa ma yake min irin wannan halayen ne. Shifa bai ga abinda na ke masa ba. Da abin ya yi masa zafi sai ya sa kuka kawai. Ya nufi gadon da nake ya fara sambatun cewa "Hamdiyya dan Allah ki yafe min kar ki mutu. Wallahi na daina." Ya dan girgiza ni wai lallai sai in tashi mu koma gida shi, ya daina bata min rai. Alhaji ya rarrasheshi yana cewa abinda nake gudun maka kenan kaki ji Sadik, gashi baka ki gani 58 Sharrin Jinni 3 ba. Lokacin da na ke maka fada gani ka ke kamar ba sonka nakc yi ba, gashi yanzu ka gani da idonka." Da kyar ya rarrashe shi ya fidda shi daga dakin. Da Inna da Baba Tasallah da gidan Dagaci gaba dayansu suka zo dubani. Suna ganina abin ya basu mamaki. Inna ta ce "Ya kamata amai da ta gida ayi mata maganin gargajiya." Alhaji yaki ya ce "A sauya wani asibitin dai." Hakja suka hakura aka sauya min asibiti. Can ma din haka aka yi ta fama, kullum kamar da dai. A haka har sati biyu suka shude, aka ga dai ba wani sauyi da aka samu. Sai aka yanke shara akan akoma dani gida kamar yadda Inna ta ambata. Aka koma gida. Nan ma sai da su Alhaji suka yi da gaske sannan Inna ya bari aka kaini gidan Sadik. Alhaji shi ya bada shawarar asamo Malamai masu rukiya, domin suna zaton wannan abu akwai hannun mutanan 6oye, domin sun nuna tun farko ba a sauraresu ba ne. Haka aka samo Malamai su hudu suka dukufa da karanta ayoyin rukiyya akaina, sai da suka yi kwana uku suna aiki ba tsayawa, sai ko sallah da cin abinci. Wani lokacin ma da dai-dai da dai-dai suke zuwa basa barina su tafi baki dayansu. 59 Amina A. Sharada Har izuwa yanzu babu wata alama da ta nuna cewa akwai Aljanu a tare dani. Abun ya bawa kowa mamaki, bar ma aka fara shawarar a hakura kawai asake wata hanyar. Sai daya daga cikin su ya ce muje mu gayawa Malam yazo da kansa, domin a zaton da muke yi akwai aljanin, kuma yana da matukar taurin kai, shaidanin gaske ne." Aka yarda da hakan, aka sami daya daga cikinsu yaje ya gayawa babban Malamin nasu suka taho tare Da zuwansa ya kura min ido. Sai ya yi murmushi ya ce "Zaka yi bayani yanzu, domin kuwa GABA DA GABANTA." Daga nan ya cafki dan yatsana babban na kafa ya matse da karfin gaske, ya ce da sauran yaran nasa "Ku ci gaba da karatu maza." Ta ke suka dinga kwararo ayoyin rukiyya. Suna cikin yi sai kawai aka ji wata irin kara da ta firgita duk wanda ke gurin. Amma banda Malam, domin su sun saba, kuma aikin su ne. Take Malamin ya ce "Kayi magana me ya kawo ka nan,?" Ya yi shiru. Ya ce "Kayi magana mana.?" Nan ma shiru. Malam ya dubi sauran Malam ya kauda kai. Tuni sun gane abinda yake nufi. Suka fara kokarin kona Aljanin. Da yaji azaba ta isheshi sai ya fara kara yana ihu. Malamin nan ya 60 Sharrin Jinni 3 ce "Ku kona shi in har ba zai yi magana ba. Suka hau aikinsu. Tuni ya ce su tsaya zai yi magana. Malamin ya ce "Su dakata." Sannan ya ce "Daga ina ka ke? Kuma kai waye.?" Ya yi shiru. Ta ce "Au raina mana hankali zaka yi? Za fa mu kona ka yanzun ." Ya dubi sauran. Su kuma suka ci gaba da nan. karatu. Ya kuma kwala ihi mai razanarwa. Ya ce "Su tsaya zai fada. Suka ki dakatawa. Sai da ya jigata sosai sannan suka yi masa magana. Sannan ya amsa musu a wahale. Karshe ma kawai sai ya fice ba tare da sun ji wani cikakken bayani a wajen sa ba. Malamin ya ce "Ya fa gudu da ya ga halaka." Alhaji ya ce "To fa lafiyar ita yarinyar.?" Malamin ya ce "Ai shine, kuma zamu binciketa yanzu mu gani domin bamu tantance ta inda ya fita ba." Suka sa Sadik yajo ya jijjigani da karfi. Ya kira sunana a hankali. Na bude ido gami da amsawa. Na jima ina jujjuya ido kafin in shaida mutane. Daga can na gane Sadik. A firgice na tashi na matsa daga inda yake, na ce cikin kuka "Ina Daddy.?" Aka ce gashi. Na kama Daddy na rungume ina kuka kawai. Ba wand abai tausaya min ba. Su Mamy cewa suke yi "Kiyi hakuri Hamdiyya, in Allah yazo za'a rabaki da wannan alakakai din.' Na yi saurin dago kaina na kalli Mamy, na ce 61 Amina A. Sharada "Wayc.?" Ta ce "A'a ba komai, kije ki kwanta ki huta baki da lafiya." Na ce "To." Na koma kan kujera. Malaman suka ce za su tafi, da zarar anga ya komo sai a sanar da su da wuri." Su Alhaji suka yi musu godiya mai tarin yawa, aka sallamesu suka tafi. Suma sun jima a gidan sannan suka tafi ba tare da sun sanar dani abinda ya faru ba. Sadik na zaune ya hada kai da gwiwa yana ta tunani. Sai naje kusa da shi na zauna, na kalleshi idanuna taf da hawayc, na ce "Yanzu Sadik haka zaka yi min? Irin sakamakon da zaka yi min kenan? Ka tuna fa saboda kai na kusa na salwantar da rayuwata, amma ka rasa wanda zaka yi wa sharri sai ni. Wai ka ce Daddy ba danka bane? Kai ko wanne irin laifi nayi maka haka har da zaka yi min irin wannan mummunan sharri.?" Kansa a sunkuye ya ce "Kin ga ni dai ban ce ki sake tayar da wannan maganar ba. Ya ya abu ya wuce sai ki dinga tada shi.?" Na ce "A wajen kane ya wuce, amma a wajena bai wuce ba" Ya ce "Haba Hamdiyya, na ce kiyi hakuri kın k, to ya ya kike son in yi miki ne.?" Na yi shiru (an na ce "Wannan fa magana ba ta shiru ba ce, saboda haka sai na bari gani ga ka ga Mamy sannan in fada." Ya ce "To shi kenan. Ni kuma zan ce sharri kika yi min." Na ce "Koma mai zaka ce sai na fada in Allah 62 Sharrin Jinni 3 ya so." Ya yi murmushi. "Su ma ba za su yarda ba." Na ce "Ai sun ga alama tun daga farko." Ya lakuce min hanci. "Baki da hankali, kina so ki kuma jawo mana wata rigimar daban." Na cе "Wacce rigima ce kuma." Ya yi murmushi "Ai ke sai dai a lalla6a ki, domin duk wanda ya takura miki na fuskanci ba zai ga da kyau ba." Na tabe baki na ce "Na fahimci kaima ka shiga canfe-canfen nan na tsofaffi." Ya ce "Wanne irin canfi kuma banda wanda na gani da idona? Wannan ai ya wuce tunda har jikina ya gaya min." Na ce "A'a ba zancen wasa ba Sadik, wai dan Allah akwai wani abu da yake faruwane da ni sabanin wanda na sani.?" Ya cе "Akwai kuwa." Take ya warware min komao na dangane da zuwan Aljanin nan kaina, da kuma yadda aka yi ta fama da shi. Na yi matukar mamaki, na yi tagumi kawai zuciyata cike da fargaba. na ce "Wato dai tana kasa tana dabo kenan ko.?" Ya ce "Ato daga dai yanzu ko wanne lokaci zai iya dawowa, domin guduwa ya yi bai tsaya ya yi magana ba." "Innalillahi wa'inna ilaihi raju'un." Abinda na ce kenan. Take hawaye ya zubo min. Na ce "Kai ni dai na shiga uku. Take mafarkin da nayi ya fado min a lokacin da ina asibiti. Na yi shiru kawai ina tunani. Sadik ya rungumeni ta baya, ya ce "Ki 63 Amina A. Sharada manta da komai, Allah zai yi mana maganinsa ne." Na yi murmushi, "To Allah gamu gareka." Yanzu komai ya zame mana kamar da, tsakanina da Sadik kamar wata husuma bata taba hadamu ba. Ya dawo da al'amuransa gareni. Nima kuma na watsar da komai, tunda naga yanzu Sadik yana son Daddy fiye da kowa, kullum suna tare kamar ya hadiye shi. Yanzu sun ma fi rigima da Sadik karami, domin in mun shiga dakinsa zai masa ta'adi sai ya koreshi, kuma sai ya gudu waje yana dariya, in kuma barna ya yi masa ya dan dakeshi ya yi kuka sai in ce "Kayi hakuri, ka san sha'anin mulki hawa da sauka ne. Wannan karon Daddy ne ya dane kujerar." In na fadi gaka Sadik ya yi ta dariya. Hatta unguwa tare suke tafiya, dinki iri daya, hula iri daya, kai komai nasu iri daya. Tun Daddy bai saba da shi ba har yazo ya saba. A yanzu kwanciya ce kawai take rabasu, itama din sai ya yi barci nake daukeshi in kai shi makwancinsu. A takaice dai shi ya komo mowa, ya yin da little ya dawo bora. *** Kwanci tashi ba wuya, domin dai an kusa daura aurer Tbrahim da Haulatu. Ana ta shiryeshiryen biki, duk da ta zama faccalata kawancanmu sai abin da ya yi gaba, domin a yanzu ne ma muke 64 Sharrin Jinni 3 Eawance, duk abinda ta saya na auranta dangane da wanda zata saya da kanta yana gidana, tare muke fita kasuwa ta siyo, in sayo, mu hadu mu Soye ba wanda ya sani. Lefenta ma tare muka hado, ta kuwa tubure nima sai an hada min lefe, na ce "A'a bena so." Ta ce "Wallahi baki isa ba." Ibrahim ya ce "Ai uwargida ce sai a hada mata." Suka yi ta zolayata shi da Sadif. Da yake duk inda za su suna tare, muma muna tare abinmu. Sai tazo tayi kwanaki a gurina ba tare da gidan s Ibrahim din sun sani ba ma Yau ce ta kasance ranar daurin aure. Dangi daga ko ina sun hallara maza da mata. Da yake zarcewa zaayi da biki duk mutanen Kauye sun zo mazansu da matansu. Da yake gidan Alhaji na da girma, sai ya kasance komai a wadace ba matsuwa. Mata suna bangaren su, mazama haka. Ni kuma ina can gida da tawagata muna ta faman namu sha'anin a nawa Gangaren. In kuma mun gaji da nan sai in debosu mu dunguma gidan Mamy. Sadik ma ba zama shi da ango, suna ta faman shirye-shiryen daurin aure. Duk abin nan Daddy na manne da shi, in na ce ya kawo min shi baya baya yarda. Sai na kyalesu suna tare, ko yana gurin Ibrahim ko yana gurin Sadik. Har nake tsokanar Ibrahim ma da cewa sun sami dan zaman daki Ibrahim ya ce "Yaushe za ku yarda ku bani, yadda 65 Amina A. Sharada kuke makale da su ba kwaso ya matsa daga gareku." Muka kalli juna da Sadik muka yi dariya muka tafa. Ya ce "Rabu da shi maga yadda zai yi nasa kawa zucin." Shi ko Sadik karamin yana gurin Mamy, duk wannan kujiba-kujiban da shi take yi. Shi yasa nake yawo na zagargar abina. Hatta su Inna da Baba Tasallah suna gidana sun zo bikin. Yau ranar lahadi, ita ce ranar da aka daura auren Ibrahim da Haula a can garin mu, wato Kauyen Zanzari. Bayan an dauro auren an dawo su Dagaci suka biyo bayan angwaye. Jerin gwanin motoci kuwa abin ba magana, har nan gidan Alhaji. Falon Alhaji cike da manyan baki 'yan uwa da abokan arziki masu zuwa taya shi murnar auren dansa da ya yi. Mu kuma muna falin Hajiya ana ta faman shagalin biki da murnar daurin auren, mun cika makil, domin su Inna ma nan suka taho. Su Aunty da kawata Safiyya ta gudo daga gidan kawaye wai wallahi ta gaji da zirga-zirga. Inna tayi mata tsiya. Na ce "Ashe ba zaki fatin ba gashi a Hotel din da kike so za'ayi. Wato CONG COНТ НОТEL." Ta ce "Zuwa kai. Ta6dijam! Ai damu za'a rabashi." Na ce "Yar iska, ko ki fidda miji abu ya gagara." Та се "Wa ya ce miki ban fidda miji ba.?" Na ce "A gidan uban wa kika fitar.?" Tayi dariya. "Sorry Aunty na 66 Sharrin Jinni 3 yi miki karya." Na ce "Wacece Auntyn ta ki.? Ke fa baki da mutunci." Ta cc "Ai gani nayi har kinyi haihuwa biyu ni ko auren banyi ba. Nan gaba kuka kara ta uku wallahi Mama zan ce miki." Na kai mata duka. Muka fito falo da gudu muna dariya. Sai ga Sadik yace "wanna wanne irin abune wannan kuma? Sai ka ce yara.?" Na ce "Wai ce min take Aunty." Ya yi dariya. Ta ce "Wallahi Sadik ta tsufa, gara ka sami wata 'yar shana-shana ka aura." Ya ce "Haka ko za'ayi Safiyya. Ki samo min yarinya karama." Tayi dariya, "An gama Sadik." Na ce "Za ki ci ubanki wallahi. Ki kiyayeni." Suka kwashe da dariya. Na ce "Na san irin zaman da zan yi da ke." Ta ce "Afuwa kawalli da wasa na ke." Na ce "Kin tsira." Muka yi dariya baki dayan mu. Ta karbi Daddy daga wajen Sadik tayi gaba ta barmu a gurin. Na nemi guri ha zauna na ce "Wash Allah Sadik! Kaina ciwo yake yi." Ya ce "To tashi mu koma gida." Na ce "A'a, ai da nan da can din duk daya ne." Ya ce "To muke wurin Mamy ki karbi magani." Na ce "To." Muka fito tare. A sako muka sami Mamy a zaune tana lallaба Sadik karami yana son yin barci. Sadik ya ce "Baiwa Hamdiyya maganin ciwon kai." Tа се "Anya kanki ne ke ciwo? Sannu Allah ya sauwake. Wallahi hayaniyar bikice. Bari in kawo miki 67 Amina A. Sharada magani." Ta mike ta tafi dauko maganin. Ni kuma na kwanta ina hutawa. Sadik na zaune, sai ji ya yi na kwala Kara. Ya zaburo da guru gurina ya ga abinda ke faruwa. Tuni na koma gidan jiya. Wato bakina ya datse yana kumfa, idanuna a kafe. Nan da nan dakin ya cika da jama'a dan jin karar da na kwala. Mamy kuwa bata san ma yadda aka yi tazo dakin ba, ko maganin bata dauko ba. Nan da nan ta tura aka fadawa Alhaji, ya taho da sauri. Yana ganin halin da na ke ciki sai ya fita da sauri. Bayan ya kira Sadik. Basu fi minti arba'in da biyar ba sai ga su da Malaman nan da suka taba yi min rukiyya. Suna ganina sai suka ce a dawo dani falo. Cak Sadik ya daukeni ya ajiyeni a tsakiyar falo. Nan suka dukufa kan yi min rukiyya. Amma Aljanin nan ko gezau bai yi ba. Hasalima sai ya fara bugani da jikin kujerun falon yana gurza kaina a kasa. Kafin ka ce meye wannan? Ya yi min jinajina. Hankalin kowa ya tashi a gurin. Mata sai kuka. Sadik ransa ya 6aci, idanunsa suka yi jajawur kamar gaushin wuta. Ya dubi Aljanin ya ce "Kai sakarai mara zuciya, ai wannan abin da kake yi ba so bane, kuma yanzu na tabbatar kai matsoraci ne. In þa dan haka ba ka yi magana mana a san ko kai waye, kuma daga ina ka fito? Kuma meye hadinka 68 Sharrin Jinni 3 da ita, in ma fafatawa ne sai mu yi domin aga mai karfi tsakanin ni kai." Ya yi shiru yana ta huci kamar kububuwa. Aljanin ya yi dariya, ya ce "Yauwa jarumin maza, yanzu na san cewa kai namiji ne, kuma zamu kara da kai akan Hamdiyya." Malaman nan suka ce "Ba za ka fita ba kenan.?" Ya ce "Ai gurin zamana ne nan." Suna cikin haka sai ga daya babban Malamin nan da ya taba zuwa ya fara illata Aljanin a wancan karon. Yana zuwa ya damki goshina ya fara karanto ayoyi masu zafin gaske. Ya ce da sauran suma su kifu akansa." Nan da nan sai ga Aljanin nan ya fara ihun wahala yana jin azaba. Gashi duk sun toshe wata kafa da zai gudu. Da dai yaji zai hallaka, sai ta ce da su su dakata zai yi bayani." Sai da suka kara wahalar da shi sannan suka tsaya. Ya yin da shi kuma ya soma bayani dalla-dallah kamar haka. "Ni sunana Shu'umanu dan Shaidanatu. Ina zaune ne a wani daji mai suba Darbuba akan dutsen Jal'ura. Ina da shekaru dari bakwai da arba'in da biyar a duniya. Asalin haduwa ta kuwa da wannan yarinyar ba ita na taba so ba. Akwai wata kakarya ta bakwai a cikin iri-irin danginsu wandanda suka gabata tun zamanin da can kimanin shekaru dari 69 Amina A. Sharada uku da sittin. Ita wannan mata Allah ya bata baiwar kyau da babu kamarta a wannan lokacin. Tun da na ganta na jarabtu da kaunarta, ya yin da wani dan sarkin wannan zamanin shi ma ya kamu da ciwon sonta. Ba yadda banyi ba in raba su na kasa, domin irin tsarin dake jikin su. Haka itama na yi-nayi in shige jikinta na kasa, domin mutanen wannan lokaci basu da shagalalliyar zuciya kamar na wannan zamanin, dan haka har ta koma ga mahaliccinta ban sami damar rabar jikinya ba. Na yi bakin cikin wannan abu. Tun daga wannan lokaci nake bibiyar danginsu daya bayan daya ko zan dace a cikin irinsu in sami kamarta. Ban samu ba sai akan Hamdiyya. Tun tana jaririyarta nayi ta lura da ita domin naga ta debo yanayi da ita waccan tsohuwar budurwar tawa. Na shiga lura da ita sosai gudun kar wani abu ya taba min ita. Tana girma kamaninta na kara fitowa. Sai da ya kasance babu wani banbanci a tsakaninsu. Nan zuciyata ta afu akan ta. To itama na auna babu damar shiga jikinta saboda akwai yanayi na wancan tsari a nata jikin. Dan haka na kyaleta ina dai lura da ita har lokacin da ta isa munzalin mutane. Shi ne na shiga bayyanar mata kaina a yanayin dan Dagaci, wato Abubakar (Sadik). Dukan da ake yiwa 'yan matan nan ma na kauye ba kowa bane face ni. Domin na sha alwashin hukunta 70 gharrinJinni 3 wani mai sha'awar tabata. Ko da wasa ma uwar ta haifeta ma in zata iya yunawa a duk lokacin da doketa in tayi mata ba dai-dai ba sai taga ba daiiba. A takaice dai duk abin daya faru a garin nan ne ummul'aba'isi. Ni nayi sanadin kulla siyayya akanin Sadik da Hamdiyya domin su shagala in mi damar shiga jikinta. Amma ban samu ba, Jomin iyayensu suna tsaye a kansu har soyyyarsu ta ama gaskiya, wadda ba zata kankaru ba. Ni ne Juma na taimaka mata a lokacin da ta tafi nemansa akin dajin nan ta shallake hadura. Shi kuma ni na uro wannan micijin ya sareshi domin rama mata vahakar da ta sha a wajen nemansa. Ni ne wannan maharbin da ya taimaka musu, kuma nine na daukosu amota na kawo su gida. Bayan anyi auren anaga zama ya yi dadi, sai na shiga hadasu, domin gu bata tunda naga suna more rayuwarsu ba abin da ya damesu, ni kuma ina fama da bakin cikin ashinta. Sai na dinga kammanni da Ibrahim domin inyi amfani da wannan damar in jefa zargi a zuciyar Sadik. Na kuma yi nasarar yin hakan, bayan kuma n farkon tariyarsu na hansu kwanan farin çiki a wannan ranar. Da ta haihu sai na cusa kiyayya da zargi a uciyar Sadik domin ya ki dan da ya dinga sammanin na Ibrahim ne. Haka kuma aka yi, l'amarin da ya haddasa musu tsananin 6acin rai da 71 Amina A. Sharada rigima. Na yi sa'a na sami yadda na ke so suka dinga tafka rigima tun ba'a sani ba har aka sani. Kuma ya mareta na rama mata. Na kuma dinga tunzura masa zuciya domin kar su sami zaman lafiya bare su dinga farantawa junansu. Nan ma nayi nasara samun haka, har ya ce da yaron ba dansa bane adai-dai lokacin da na samu damar shiga jikinta. Wanna shine takaitaccen tarihina da dalilin da ya sani shiga jikinta. Kuma ina rokonku da kar ku konani ku kyaleni, ku kyaleni zan fita, kuma na yi alkawarin ba zan kara shiga jikinta ba. Kuma na dau alkawarin in har wani ya musguna mata zan dau mataki akansa." Malaman nan suka ce "A'a ba wannan ake so ba, sai dai ga mugaye masu muguwar manufa akanta ba kowa ba." Ya ce "To naji nabi." Suka ce "Kayi alkawari ba zaka sake shigarta ba." Ya ce "Nayi." Sai da suka nanata sau uku. Sannan suka ce ya fita ya kyaleta ta huta domin ta galabaita." Ya ce "To zai fita." Suka ce "Ta ina?". Ya ce "Ta baki." Suka ce "To kafin ka fita muna so mu san wanne addini ka keyi.?" Ya ce "Ni bani da addini." Suka ce "To muna so ka karbi addinin musulunci, domin shine addinin gaskiya wanda Ubangiji ya yi umarni da abi." Ya ce "Naji ina so a shigar dani cikin wannan addini na musulunci." 72 Sharrin Jinni 3 Ta ke suka biya masa kalmar shahada ya maimaita. Suka ce ya sauya suna, domin wan can sunan nasa ba suna ne da musulunci yazo da shí ba." Ya ce "To ai shi bai san irin sunan da za'a sa masa ba. Amma in Sadik ya yarda tun da ya zama abokinsa ya zaba masa suna." Take Sadik ya ce "Sunanka Usmanu." Ya cc "Yaji ya karba." Sannan ya yi musu sallama. Da zai fita ya dubi Dagaci ya ce "Ka mikowa Hamdiyya gadonta da ka cinye, domin ba halak cinka bane. In kuwa kaki ji ba kaki gani ba." Yana gama fadin haka ya fita. Suka ji shiru. Guri ya yi tsit ana ta mamakin abin da ya faru. Ni ko nayi shiru ina tsakiyar mutane ban san me yake faruwa ba. Naji dai ana yi min sannu. Na mike da kyar zan fita. Sai Sadik ya ce in koma gidan maza yanzu yana zuwa." Na ce "To." Na tafi. Anan na bar su Inna. Ina zuwa gida nayi wanka na shirya nayi kwanciyata. Jim kadan sai ga Sadik ya shigo da Daddy ya ce "Dama binda yasa nake son mu kaďai ce shi ne. A bayanin Aljanin nan na karshe, ya ce wai Dagaci ya biya ki hakkin ki na gado, shi ne nake son jin dama akwai wani hakki naku da Dagaci ya karba.?" Na yi murmushi, na ce "Ya fi kyau dai kaje ka same shi ya yi maka bayani cikin nutsuwa." Ya ce "Shi kenan bara inje." Na ce "A'a 73 Amina A. Sharada ka kyaleshi sai an gama biki kaje har gida ka same shi ya yi maka bayani." Ya ce "Ina ai ba zan iya jurcwa ba. Ni yanzu zanjc." Yana gama fadar haka sai ya tashi ya fita. Ya yi sa'a kuwa dakin da Dagaci yake ba kowa, daga shi sai Alhaji. Ya gaishesu, sannan ya ce "dam abinda yasa na zo, naji aljanin nan ya yi maka magana ne ban fahimce ta ba." Da Dagaci yaji haka sai ya ce "Maganar gadon nan ce fa ta bayan gari. Kai ma ka san da maganar." Sadik ya ce "Ai ni cewa dani kayi siyar maka suka yi." Dagaci ya ce "A'a ni ban gaya maka haka

Chapter 4 of 5