Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
kawai ta gyara ni zanyi mata afuwa." Alhaji ya ce "To ke kinji, tunda yaki fadar laifin da kukai masa sai ki kintata ki gyara kinji ko.?" Na ce "Wallahi Alhaji ba wani laifi da nake masa, kuma yanzu a gabana ne ya fadi wannan, in ka tafi ci gaba zai yi. Gara kawai ayi ya kare." Alhaji ya ce "Kaji abinda tace, kuma ya kamata ace ka bayyana mata laifinta dan a kori gaba." Ya yi shiru. Sai Alhaji ya ce da Nusaiba "Ke tashi daga nan. Ana magana kin tsare mutane da ido." Sum-sum ta mike ta fice. Sannan Alhaji ya се "To sai kayi mata bayani." "Shi kenan kawai Alhaji, zan yi mata bayani, amma sai ni da ita." Ya ce "To shi kenan, ke kinji, amma ki kiyaye gaba, in har kinyi masan. Haba karku bani kunya mana, ku duba fa kuga irin gwagwarmayar da kuka sha, babu hankalin wanda baku tasa ba, amma daga baya kuma tun ba'aje ko ina ba zaku fara raba abin fada? Ya kamata kuyi wa kanku fada tun kafin ma ace wani ya sani. Kai Sadik kaine babba, in kaga ba dai-dai ba ba shiru zaka yi ba ka kullaceta, sai ka sanar mata tunda 38 Sharrin Jinni 3 wuri ta gyara. Gashi Allah ya bada rabo, nan gaba ba'a san iyakacin ba, in har kuna wanann in kun tara yara suka yi wayo sai ku dinga rabawa taranku hankali, in suna ganin bakwa zaman lafiya, suma kansu ba zai taba haduwa ba, kuma ba za su taба samun nutsuwa da kwanciyar hankali ba. Saboda haka ku saita halayyarku tun daga yanzu, kar kuzo kuna da kun sani gaba." Dukkanmu muka yi kasake muna sauraronsa. Sai da ya kawo nan ya mike. "Ni zan koma. Ina dada jan kunnenku karku sake." Muka ce munci in Allah yaso haka ba zata sake faruwa ba." Ya yi mana sallama ya fita. Sadik ya rakashi sannan ya dawo. Tun dafa fadan da Alhaji ya yi manalan yanzu Sadik ya dan sauko kadan, dominn nayi abinci zai ci, sannan in na gaisheshi zai amsa. Duk dabaya tsayawa ya yi hira dani, kuma baya shiga dakina, Kowa makwancinsa daban ne. Duk da haka ban damu sosai ba, tunda har awo yake kawoni, in na gama ya daukeni ya dawo dani gida. Kuma da ya samu aikin gwammanti ya sanar dani har lokadin da zai fara zuwa. Na yi farin ciki sosai. *** Mutanen da suka tsare Sadik a dajin nan tuni an gurfanar da su gaban shari'a domin hukuntasu. 39 Amina A. Sharada Take Alkali ya yanke musu hukuncin dauri shekara biyar-biyar da tarar kudi ta dubu dari biyu-biyu, saboda irin tsare Sadik din da suka yi, suka rabashi da gida kuma suka gana masa azaba. Suna jin haka suka ce aiko sai dai a hada har Ibrahim, domin duk abinda ya faru shi ya sa su. Take kuwa mai shari'a ya bada umarni da Ibrahim. Aka kuwa zo aka kama shi aka tafi da shi. Abin bakin ciki, sanadi kadan ya jawo masa shiga babbar matsala. Alhaji da Mamy damu baki dayanmu munyi bakin cikin abin da ya faru. Sabanin Sadik da naga abin ko a jikinsa. Ya dai jajanta a gaban Alhaji, amma a bayan idonsa murna ya dinga yi komai ya sa oho. Kwanci tashi cikina ya isa haihuwa. Dan haka Nusaiba ta dawo gidana da azma ko da haihuwar zata zo cikin dare, ta taimaka min mu tafi asibiti. Haka kuwa akayi, domin dare nayi bayan zuwanta da kwana biyu, sai Allah ya kawo nakuda. Da sauri na tasheta. Ta je ta sanarwa da Sadik a dakinsa. Ya fito da mota muka yi asibiti. Bamu jima da zuwa ba Allah ya kawo haihuwar. Nan da nan na haifi dana sankacece kyakkyawan gaske. Kowa ya ganshi ya ga Sadik, domin suna matukar kama sosai. 40 Sharrin Jinni 3 Tun a daren Nusaiba ta gayawa su Mamy. Kuma a daren suka taho. Anna muka kwana da su. Shi ko Sadik da ya kawomu gida yayi komawarsa abinsa. Wannan abu ba karamin bakanta min rai ya yi ba. Hatta Nusaiba sai da taji ba dadi. To amma sai taja bakinta ta tsuke gudun kar ta nuna bacin ranta. Hankalina ya kara tashi fiye da da. Su Mamy suka zo suka ga jariri har Alhaji ya tambayi inda Sadik yake. Nusaiba ta ce "Ai tunda ya kawo mu bai dawo ba har yanzu." Ya ce "To ya san ta haihu.?" Ta ce "A'a bai sani ba." Take Alhaji ya yi masa waya ya sanar da shi haihuwar. Ya ce kuma tun daran suke a asibitin." Sadik ya ce "To gashi nan yana zuwa." Shiru har kusan azahar bai zo ba. Shi ko dama Alhaji tafiya ya yi tun da safen ya bar su Mamy da Nusaiba. Sai Mamy ta ce "Tunda lafiyata kalau a sallamemu. Nan kuwa aka bamu sallama muka taho gida. Tun a hanya nake ta faman kuka ina rokon Mamy ta kaini gidanta, ni kar a kaini gidan Sadik. ta ce "Bani da wannan izinin sai kiyi hakuri in munje ai za'ayi masa fada ne." Akan dole na hakura muka isa gidan. Muka kuw ayi sa'a yana nan a zaune a falo ya yi tagumi. Yana ganinmu sai ya tashi ya gaishe da Mamy. Zai shige ciki sai Mamy ta ce ya dakata tana son 41 Amina A. Sharada magana da shi. Ya komo ya zauna yana sauraron abin da zata ce da shi Fa ce nima in dakata. Nima na zauna. Ta karbi jaririn daga hannun Nusaiba, ta се "Wai wannan waye.?" Ta tambaye shi. Kallo daya ya yi wa jaririn ya ce "Jinjiri ne." Ta ce "To dan waye.?" Ya sunkuyar da kai. Ta ce "Ba za ka fada ba.?" Ya ce "Danta ne." Ta ce "Dan wa." "Dan Hamdiyya." Ya yi shiru. Ranta a bace ta ce "Da wa kuma?". Y ace "To wai Mamy wannan tsarewa da akai min ni fa ban gane haka ba. Haka kawai a dinga takurani.?" Yana gama fadin haka sai ya mike abinsa ya fice. Ina ganin haka sai na rushe da kuka ina cewa "Na shiga uku Mamy na lallace! Kar dai ace Sadik yana nufin wannan ba dan sa bane.?" Ta ce "Haba ya ma isa? Ya ma soma.?" Ta kirashi, amma ya ki zuwa. Ta cc "An shiga uku jama'a, wai meke damun Sadik ne? Gaskiya akwai magana mai karfi ma kuwa. Barin Alhaji ya dawo sai ayi tufkar hanci tun kafin iyayen yarinyer nan su zo su san abinda yake wakana." *车华 A zaune nake a daki nayi tagumi ina tunanin abinda ke kaiwa da komowa. Na yi shuru zuciyata kamar ta tsage dan bakin ciki. A raina na ce "Yanzu 42 Sharrin Jinni 3 irin sakamakon da Sadik zai yi min kenna? Duk abin da na yi mishi da irin kaunar da make nuna masa duk bai gani ba? To me yake nufi da nine.?" Na tambayi kaina. Ba amsa. Na ce "To a gaskiya ya kamata in san abinyi, ba zan zauna hawan jini ya kamani a banza ba wallahi." Ban san san da hawaye ya fara zubo min ba. Na yi ta kuka a hankali dan kar Nusaiba taji ta tashi asirina ya tonu, gashi gobe suna, gida ya cika da baki. Na dauki jariri n na zuba masa ido ina ta kallonsa. sai naji tausayinsa ya kamani. Na girgiza kai, wani hawaye mai dumi ya zubo min. Tun da aka haifi yaron nan Sadik bai taba daukarsa ba ko sau daya, tun dai sa'adda Mamy ta mika masa shi. Mamy tayi fadan, Alhaji ya yi fadan, amma abanza. Alhaji ma har fushi ya yiwa Sadik. Kayan barka kuwa duk Alhaji ne ya siya. Haka ragon suna ma sai Alhajin ne ya yi. Shi yasa ma Alhaji ya ce ranar suba ba za'ayi wani taron suna ba gudun tashin wata hatsaniyar kuma daban. Haka dai aka yi sunan aka watse ba wani armashi. Aka sawa yaron sunan Alhaji, wato Lawansa, sai muke ce masa Daddy. Duk wannan abu bai dada Sadik da kasa ba. *** 43 Amina A. Sharada Ina zuane a falo ni kadai nayi tagumi Daddy na hannuna yana shan nono. Duk wanda ya kalleni ya san cewa nayi matukar ramewa sosai, domin lamarin na Sadik yafi gaban magana sai dai addu'a. Ina nan zaune ya dawo daga aiki, ya wuceni kwan-kwan-kwan abinsa. Na bishi da ido, domin har na gaji da yi masa sannu da zuwan da bana samun amsa daga gareshi. Na shareshi. Shi kuwa ya shige dakinsa. Jim kadan ya komi ya shiga kitchen domin hada abincinsa, yaje ya tarar ban girka ba. Ya dawo ya tsaya kawai, kamar ya yi magana, amma ko mai ya gani oho sai yake kawai ya koma dakinsa gami da dauko dan mukullin motarsa ya fice. Na bishi da kallo, a raina na ce "Indai ni ce wallahi yanzu zan fara shirya maka nawa taceccen rashin mutuncin. Kwanci tashi har Daddy ya kai kimanin shekara biyu. Ba shi ba Sadik kama ba dan sa ba. А koda yaushe gidan Alhaji nake kaishi ko Nusaiba tazo ta tafi da shi gidan su. Ba zai dawo ba har sai ya yini. Wataran ma a can yake kwana. Shi yasa ma Alhaji ya ce ayayeshi sai Mamy ta daukeshi ta barshi a wajenta, domin suna tsammanin Sadik haihuwarce baya so shi yasa yake wadannan abubuwan. Nima dai abinda na ke tunani kenna, shi yasa ma na hakura aka dauke shi din domin in gani 44 Sharrin Jinni 3 ya zaiyi in baya ganinsa. To da yake dama yasaba da su sai ya yi zamansa a can din. Rannan ina zaune ni kadai sai ga Sadik ya shigo, na yi masa wani kallon sha tara na dauke kai kawai na buga tsaki. Har ya kai bakin kofa sai ya tsaya, ya juyo ya kalleni. Na murguna baki gami da hararacsa na tashi abina zan tafi. Sai ya ce "Dakata." Sai na tsaya domin inji abinda zai ce. Sai yazo dab dani ya tsaye, ya ce "Wai wa kike yiwa tsaki." Na ce "Da kai nake." Ya ce "Karki kara yi min tsaki, in ba haka ba jikinki zai yi tsami." Na ce "Nayi, kuma na kara sai kayi duk abinda ka ga dama." Ya ce "To ki kara ki gani." Nan take na kuma daka masa tsaki Mst! Sai kuwa ya sharara min mari. Na dafe kuncina gami da fadin "Ka mareni. Wallahi sai kayi danasanin marina da kayi." Ina rufe bakina, me zai faru? Kawai sai naga Sadik ya yi kara ta fadı. Ga karar mari ana ta faman kifa masa. Banga mai marin ba sai dai karar marin. Shi kuwa yana ta tuntsurawa yana ihu. Kafin kace meye wannan bakinsa yana ta tsiyayar jini, fuskarsa kuwa ta kumbura suntum saboda tsananin mari. Ni kuwa saboda tsananin firgita ban san lokacin da na nufi gidan Alhaji jikina babu ko mayafi ina ihu. Da gudu na karasa cikin gidan. Mamy na zaune Alhaji baya nan ya tafi wajen 45 Amina A. Sharada Ibrahim ya gano shi ya kai masa wani dan abin masarufi kamar yadda ya saba duk karshen wata. Momy tana ganina ta tashi aguje tana tambayar lafiya? Domin a zatonta dukana Sadik ya yi. Nan da nan ranta ya бaci. Ta ce "Zauna Alhaji ya dawo. Wallahi yau sai anyi tufkar hanci." Ta fuskanci a firgice nake nake. Sai ta kamani ta zaunar tana tambayata ina Sadik.?" Na ce "Yana gida." Ta ce "To wai me yake faruwa ne.?" Na ce "Ni dai naga yana faduwa yana ihu yana wani irin abu." Mamy ta suri mayafi tayi waje tana cewa "Kice abin ba karami bane?". Tayi waje, nima nabi bayanta muka isa gidan. Da shigarmu muka sami Sadik a kwance shiru kamar matacce. Nayi saurin zuwa inda yake na dafashi. Ya dago kai da kyar yana kallona fuskarsa a kumbure, idanunsa duk sun nutse. Ya tashi da kyar. Mamy ta karaso inda yake, ta ce "Sadik me ke faruwa?". Ya ce "Wallahi Mamy ban san abinda ya faru ba sai ji nayi ana ta marina haka kawai. Ji bi yadda fuskata ta kumbura. Amma nafi zaton wannan abun da muka gani a gidan nan ya komo." Mamy ta ce "Ai sai a yiwa Alhaji way ayazo a sake kawo Malaman nan, amma fa ina ganin lamarin ku akwai wani bakon al'amari. Anya kuwa rashin jituwar nan taku bata da nasaba da halin da 46 Sharrin Jinni 3 ka shiga yanzu.?" Sadik ya ce "Ba wani nasaba da wannan, ni bana so ma a dinga yi min wanann maganar." Ta ce "To shi kenan, Allah dai ya daidaitaku. Amma ai abin akwai mamaki, dole kuma a dauki tsatstsauran mataki akan wannan abin. *** Satin Alhaji daya da zuwansa gurin Ibrahim sai ga Ibrahim a gida. Cikin tsananin rudani Alhaji ya mike ya ce "Ibrahim me ya akwoka? Ya akai ka fito? Wato gudowa kayi daga gidan yarin ko?" Ibrahim ya samu guri ya zauna, ya ce "Alhaji kwantar da hankalinka in baka labarin abinda ya faru, in baka yarda ba sai muje da kai a tambaya." Alhaji ya ce "Kai nake sauraro." Ya ce "Da mai girma gwamna ya ziyarci gidan maza a irin ziyarar da yake kaiwa wurare a kasan nan, shi ne yau Allah ya nufe shi da zuwa inda muke, ya taramu aka dinga karanto masa laifin kowa. Ma'ana aka dinga sallamar masu laifuka kananu, yana kuma ragewa wasu shekarun da aka dibar musu abisa adalci da kaunar talakawa. Wallahi Alhaji abin ba karamin dadi wannan abu ya yiwa al'umma ba. Hakan ne ma ya sa muma muka zamo daga cikin wadanda aka yafewa shekaru ukun, kuma kasan mun haura biyu ma.?" Ya ce "Haka ne.? To amma ba zan yarda ba 47 Amina A. Sharada sai naje ad kaina naga zahiri." Ya ce "Muje tare ma kaji yadda aka yi." Alhaji ya tusa Ibrahim gaba har ofishin Alkalin da ya yi musu shari'a. Alkalin ya tabbatar musu da wannan magana haka take, sannan hankalin Alhaji ya kwanta, domin da mai da shi zaiyi ayi a kuma yi masa hukuncin laifin da ya yi dai-dai da laifin nasa. Yanzu tsananina da Sadik abu ya sauya ba kamar da ba, domin tun daga ranar da ya sha mari yake dan rangwantamin, domin ya gane dalilin marin da ya yi min ne aka hukuntashi. Yanzu zamu zauna muyi hira da shi, zamu ci abinci tare, makwancin mu daya. Komai dai ya sauya. Nan da nan zuciyata tayi sanyi. Sai dai abu guda da har yanzu baya kula Daddy, in ya ganshi sai ya daure fuska. Haka shima Daddy in ya ga Sadik baya sakin jikinsa da shi. To irin wannan lamarin ne yake bakanta min rai. Wai ace kai da danka ya zame maka abokin gaba. To amma sai in' daure zuciyata domin gudun kar in yi masa magana mu koma gidan jiya, inzo kuma ina tada zaune tsaye. shi yasa ma In na ga muna zaune da Sadik Daddy ya taho, sai in maza in aikeshi daki dom in kar ya ganshi ko kuma yazo inda muke. Da yake yaron yana da jin magana, da na ce ya tafi sai ya juya da gudu ya tafi ya kwanta shi kadai a daki abinsa har sai sa'ilin da 48 Sharrin Jinni 3 na je. Hakanne yasa nake yawan kai shi gidan Mamy. Rannan na tashi bana jin dadin jikina, sai na fadawa Sadik. Ya ce in shirya to ya kaini asibiti." Haka kuwa muka yi, ina gama shiryawa ya daukeni sai asibiti. Anan likita yake sanar dani cewa ina da shigar ciki na wata biyu. Anan naga ikon Allah, domin Sadik murna ya dinga yi kamar ya hadiyeni. Da muka zo gida da kansa yaje ya gayawa su Mamy. Suma sun yi farin ciki matuka, kuma sunyi mamaki cikin abin nan sosai. Tun daga wannan lokaci na zamo 'yar lelen a hannun Sadik, domin irin gatan da yake nuna min ko ada ma bai nuna min shi ba. Da na ce "Wash!" Yanzu ya kidime. Daddy kuwa sai kace agola na zo da shi. Hakan ne yake sani tunanin ko Sadik yana tunanin Daddy ba dansa bane? Take na kauda wannan tunani, na sako wani domin ba shi da wani amfani. A haka har ciki ya isa haihuwa. Mamy ta ce Nusaiba tazo ta zauna a tare dani tunda batayi tafiyar ba (da yake za ta tafi Bauchi bautar kasa) domin tace sai tayi karatu mai yawa sannan zata yi aure. Da Mamy ta gayawa Sadik haka, sai ya ce a barni kawai, shi zai lura da ni. Mamy tayi mamaki, 49 Amina A. Sharada musamman da ta ga ya dauko wata likita tana dubani yana biyanta. Dan haka da haihuwar tazo ma ita ya yi kira ta kar6i haihuwar. A gida Allah ya saukcni. Allah ya sake bani saurayin kyakkyawa, shi kuma kamar mu daya da shi. Da ranar suna ta zo aka radawa yaro sunan Sadik, wato Magaji da Rai. A wanann karon Sadik ya yi buduri na ban mamaki, domin irin ta'adin kudın da ya yi abin ba bayani. Bai bar Alhaji ya yi komai ba sabanin haihuwar daddy da sai Alhaji ne ya yi komai. Kayan barka ma sai da na nuna бacin raina sannan Sadik ya daina jidowa. A wanann karon kai lamari ya yi sosai, ga kaunar dan da Allah ya zubawa Sadik. Domin 'yan barka ma idan sun zo a hannunsa suke karbarsa. Wasu ya bayar, wasu kuma ya yi bara ayi hakuri a ganshi. In an kwana biyu abin har kunya ya dinga bani. Ranar suna kuwa dauke dansa ya yi wai kar jama'a su jagwalgwalashi yazo yana ciwon jiki. Sai da Mamy tayi masa fada tana cewa "Wai kai a ina ka taba ganin irin wannan rashin mutuncin? Ya mutane za su zo tayaka farin cikin karuwa ka dinga hanasu suga dan.?" Nan dai tayi masa tatas! Ta cе ya bata dan ya bar gidan, in ba haka ba ta hada shi da Alhaji. Sannan aka sami sa'ida. Bayan munyi arba'in ne naje gida na dawo. Ina zaune da Sadik little wanda Sadik naji yana kiransa 50 Sharrin Jinni 3 na je. Hakanne yasa nake yawan kai shi gidan Mamy. Rannan na tashi bana jin dadin jikina, sai na fadawa Sadik. Ya ce in shirya to ya kaini asibiti." Haka kuwa muka yi, ina gama shiryawa ya daukeni sai asibiti. Anan likita yake sanar dani cewa ina da shigar ciki na wata biyu. Anan naga ikon Allah, domin Sadik murna ya dinga yi kamar ya hadiyeni. Da muka zo gida da kansa yaje ya gayawa su Mamy. Suma sun yi farin ciki matuka, kuma sunyi mamaki cikin abin nan sosai. Tun daga wannan lokaci na zamo 'yar lelen a hannun Sadik, domin irin gatan da yake nuna min ko ada ma bai nuna min shi ba. Da na ce "Wash!" Yanzu ya kidime. Daddy kuwa sai kace agola na zo da shi. Hakan ne yake sani tunanin ko Sadik yana tunanin Daddy ba dansa bane? Take na kauda wannan tunani, na sako wani domin ba shi da wani amfani. A haka har ciki ya isa haihuwa. Mamy ta ce Nusaiba tazo ta zauna a tare dani tunda batayi tafiyar ba (da yake za ta tafi Bauchi bautar kasa) domin tace sai tayi karatu mai yawa sannan zata yi aure. Da Mamy ta gayawa Sadik haka, sai ya ce a barni kawai, shi zai lura da ni. Mamy tayi mamaki, 49 Amina A. Shurada musamman da ta ga ya dauko wata likita tana dubani yana biyanta. Dan haka da haihuwar tazo ma ita ya yi kira ta karbi haihuwar. A gida Allah ya saukeni. Allah ya sake bani saurayin kyakkyawa, shi kuma kamar mu daya da shi. Da ranar suna ta zo aka radawa yaro sunan Sadik, wato Magaji da Rai. A wanann karon Sadik ya yi buduri na ban mamaki, domin irin ta'adin kudın da ya yi abin ba bayani. Bai bar Alhaji ya yi komai ba sabanin haihuwar daddy da sai Alhaji ne ya yi komai. Kayan barka ma sai da na nuna bacin raina sannan Sadik ya daina jidowa. A wanann karon kai lamari ya yi sosai, ga kaunar dan da Allah ya zubawa Sadik. Domin 'yan barka ma idan sun zo a hannunsa suke karbarsa. Wasu ya bayar, wasu kuma ya yi bara ayi hakuri a ganshi. In an kwana biyu abin har kunya ya dinga bani. Ranar suna kuwa dauke dansa ya yi wai kar jama'a su jagwalgwalashi yazo yana ciwon jiki. Sai da Mamy tayi masa fada tana cewa "Wai kai a ina ka taba ganin irin wannan rashin mutuncin? Ya mutane za su zo tayaka farin cikin karuwa ka dinga hanasu suga dan.?" Nan dai tayi masa tatas! Ta ce ya bata dan ya bar gidan, in ba haka ba ta hada shi da Alhaji. Sannan aka sami sa'ida. Bayan munyi arba'in ne naje gida na dawo. Ina zaune da Sadik little wanda Sadik naji yana kiransa 50 Sharrin Jinni 3 da only one ban san me yake nufi da wanann sunan ba. Sai nima na ke gaya masa hakan. Muna zaune Sadik na gefen mu shima a zaune. Ban san yadda aka yi ba sai naji yaro ya tsandare da kuka. Ashe wai hannun ne ya sarkafe daya daga jikin hudu jin lessidin dake jikina. Shi kuma Daddy ya ja a rashin sani. Habawa Sadik na tashi sai ya kifa masa mari. Yaro ya yi taga-taga a firgice ya kwala kara. Take naji raina ya yi mugun baci. Cikin 6acin rai na ce "Haba Sadik dan rashin imani me za'a daka anan.?" Ya ce "An daka ya ya kina kallonsa yana jamin hannun da sai ya karya ya cuceni.?" Na ce "Ya za'ayi ya karyashi yana sani ne. Kar ka kara dakar min da daga yau." Ya ce "To ki gaya masa kar ya kara dakar min da daga yau." Nan na dire jaririn, wato only one na dauki Daddy muka yi cikin daki na bar ma sa shi a nan zuciyata kamar ta fashe dan bakin ciki. Shi kuma ya daukeshi suka nufi nasa dakin. Yauma din dai kamar kullum, muna zaune ni da yarana muna ta wasa, suna abin dariya ina yi sai ga Sadik ya fito zai fice. Ya karaso inda yake ya yiwa only one wasa yana ta bangale masa baki. Shi kuma Daddy ya koma gefe daya ya yi tsuhu yana kallonsu. Sadik ya ce da only one "Zanje kasuwa me zan taho maka da shi.?" Sai ya kara kunnensa 51 Amina A. Sharada dai-dai bakinsa ya ce "Okey in sayo maka keke da mota ko...... ?" "To duk zan sayo maka." Daddy yana jin haka ya taso da sauri ya ce "Nima za'a siyo min.?" Ya ce cikin hantara "Da Allah can waye zai siyo maka.?" Yana jin haka sai ya koma bayana ya boye fuskarsa abayana saboda tsoro. Yana fita sai ya zago ya sani a gaba ya zuba min ido ya yi gwalam da shi, tausayinsa ya kamani. Na ce "In Allah yaso zan siyo maka kaji Daddyn Umma." Ya gyada min kai. Na yi shiru ina tunanin irin kiyayyar da Sadik yake nunawa yaron nan kamar ba jininsa ba. Na ce a raina "In Allah yaso sai Sadik ya yi dana sanin kin da yakewa yaron nan. Da izinin Allah sai ya yi kuka da hawaye sharab-sharab. Domin musgunawar tayi yawa, sai kace agola ko shege. Yaro shi da gidan ubansa ba shi da ikon watayawa.? Na ce "Wallahi da ade agola na zo da shi da tuni na mai da shi gidansu, domin in huta shima yaron ya huta. Haba wannan bakin cikin har ina.?" Sadik karami rarrafensa yake yi. Ya saba da Sadik. Ko ina 72 shi in ba aiki, to tare suke da only one dinsa. fa yin da ni kuma nake farantawa Daddy, domin ko dinkin Sallah Sadik baya yi masa, 52 Sharrin Jinni 3 ni nake saya masa, sai kuma gidan Alhaji, domin Alhaji na yi masa Mamy na yi. Hakama Ibrahim nayi masa. Hatta Nusaiba tana yawan daukarsa ta tafi da shi tayo masa shoping. Kuma wani ikon Allah sam ba ruwansa da Sadik karami, suyi ta kyararsa ko kadan bana jin haushi domin na san suna yi ne dan su kona zuciyar Sadik. Sadik kuwa yaji haushi sosai, har cewa ya yi in daina zuwa da shi gidan tun da ba sansa suke yi ba. 53 Amina A. Sharada TOFA, KARSHEN TIKA-TIKI TIK! Wata rana ina zaune a falo ni kaďai ina tunanin abin da yake wakana a rayuwata, duk burin 'ya mace dai baya wuce gidan mijinta, to ni gashi na samu, amma na kasa jin dadn zaman gidan miji. Kuma auren so muka yi da shi bana ki ba, to why? Na tambayi kaina. "To ashe dai wannan rana ita zata zame min ranar warwarewar duk wani bakin cikina da kuma cudewar al'amarin ma baki daya. Ku biyoni a sannu. Ina nan zaune sai ga Sadik ya fito sanye da wani boyen dari tas mai kyan gaske. To ashe iri daya suka dinka shi da Alhaji. Shima Sadik har da babbar riga, kuma aikin ma iri daya. Na dube shi na ce "Daddyn only one ina za'ane aka yi wannan irin shiga kamar za'a gaisuwar surukai.?" Ya yi dariya ya ce "Aure zan karo shi yasa yanzu ma gidan iyayen yarinyar zamu." Na yi dariya "To Allah ya kiyaye hanya. A gaishe su in sunyi maka maraba." Ya ce "Au baki yarda ba kenan.?" Na ce "Yarda ma ai daya ce." Ya yi dariya "Shi kenan tun da baki karaya ba. Yanzu kyaji inda zanje." Na yi murmushi kawai. Ya ce "Gidan surukan Ibrahim zamu." Na ce "A ina ne kuma." Ya ce "Can kauye." Na ce "Wace matar shi kuma? Duk gayun nan nasa ya rasa inda 54 Sharrin Jinni 3 zai yi aurc sai a kauye?" Ya cc "Ai ba'a can take da zama ba. Anan Kano take, kin san ma kowace matar.?" Na girgiza kai "Ban sani ba." Ya ce "Haula ce fa kawarki." Na rike baki cikin mamaki. Na cе "Au dama Haula ce yake so.?" Ya ce "Iyi, gashi har ma zamuje gidan su." Na cc "Au shi ya sa na ce ta gaya min waye angon rannan da tazo ta ce wai ba yanzu zan ji shi ba. Ashe ma facala ta ce. Yanzu kuwa zan yi mata tsiya san raina." Ya yi dariya ya e "A to ita ku." Muna cikin wannan hirar ne sai ga Daddy da gudunsa, ya yin da Sadik ya juya baya zai yi tafiyarsa, sai ya cakumeshi ta baya yana zaton Alhaji ne. Habawa! Sai ya gambareshi ya ya kwada masa mari yana cewa "Haka kawai dan sangarta ka zo ka bata min kaya.?" Yaron nan ya gigice, ya taho da gudunsa ya rungumeni saboda tsananin rudewa da zafin mari. Ta ke naji zuciyata tana faman tafasa. Namike cikin bacin rai na ce "Haba Sadik ka gaya min idan dannan ba naka bane wallahi ayau zai bar gidan nan, zan fita da shi, duk wanda na samu akan

Chapter 3 of 5