Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 5
kijc." Na cc "Shi kenan bari in shirya." Ya tashi ya ce "In zo yanzu fa." Na ce "To." Na shiga na dauki mayafina da mukullan gidan na fito na kukkule gidan ina ta faman tunanin abin da yake faruwa tsakanina da Sadik." *** Hajiya Lami ce (Mamy) ta ke tukin. Ni kuma ina gaba a zaune. Na dubeta na ce "Mamy wai waye bashi da lafiya ne.?" Ta ce "Wani ne." Na се "Mе ya same shi.?" Ta ce "Nima ban sani ba sai in munje ma gani." A haka muka isa asibitin, muka shiga gurin mara lafiyar. Da isarmu sai na ga wani a kwance a nannade kansa da bandeji har fuskarsa. Ban shaida kowaue ba, domin idanunsa ne kawai a waje, kuma suma a rufe suke. Na sami guri na zauna na ce da Mamy "Wannan shi ne marar lafiyar.?" Ta ce "Shi ne." Na yi shiru kawai ina kallon dakin. Gado daya ne tak, sai kujeru biyu na maziyarta, wadanda suke dab da gadon. Shiru marar lafiyar bai farka ba, muna zaune kawai ni da Mamy. Na dubi Mamy na ce "Mamy wai waye ne.?" Ta kalleni kawai ta kauda kai, ta ce 21 Amina A. Sharada "Ai yanzu zai farka, ina jin in ya farka za ki gane ko wayc." Na yi shiru kawai ina tunanin ko waye oho. Mun fi awa uku a zaune bai farka ba. Na mike na ce "Mamy zan tafi gida, na san yanzu Sadik ya koma, kuma zai tarar bana nan." Ta ce "Ba wani abu zauna, in muje na yi masa bayani." Na се "То shi kenan." Na koma na zauna. Jim kadan sai naji wannan marar lafiyar yana wasu sambatu. Na ce da Mamy "Lah! Kin ga zai farka." Ta ce "Eh, dama a yadda likitan ya gaya mana sai wannan lokacin zai farka." "Hamdiyya!." Ta kira sunana a hankali. "Na'am." Na amsa mata ina tattara hankalina kanta. "Ina so duk a irin halin da kika sami kanki, walau na bacin rai ko tashin hankali, ki kasance mai tawakkali, ki saka Allah a al'amuranki kin ji ko.?" Na ce "To Mamy. Me ya ke faruwa.?" Ta ce "Ni dai na gaya miki kawao domin ki zama mai yadda da kaddara mai kyau da mara kyau.......... Ta ci gaba "Ina son in gaya miki wata magana. Amma fa sai kinyi min alkawarin ba za ki tashi hankalinki kan abin da zan fada miki ba." Tun daga lokacin naji gabana ya fadi ras! Na ce "Na yi miki Mamy, fada min." Ta ce "Kin san ko waye wannan akwance.?" Na dafe kirji cikin firgici na ce "A'a." Ta ce"To ai 22 Sharrin Jinni 3 kinji irinta, tun kafin in gaya miki har kin tsorata, shi yasa ma Alhaji ya ce kar in fada miki." Na matsa kusa da marar lafiyar na kare masa kallo sama da kasa. Ta 'yan yatsun kafarsa na gane ko waye, domin da ban lura ba sosai. Ai ina gane ko waye sai zuciyata ta buga dum! Numfashina yana fita sama-sama. Da kyar na kakalo sunansa. "Sadik!" Na ambata da karfi, na yi baya. Mamy ta rafka salati. A dai-dai lokacin da Alhaji ya turo ya shigo. Yana ganin abin da ke faruwa ya karaso da gudu yana cewa "Hajiya me ya sa kika gaya mata? Ai kinga irinta ko? Abin da akc gudu ya samu." Mamy ta ce "Alhaji taimaka ta suma, ayi kiran likita." Da gudu Alhaji ya fita, ya nufi ofishin lıkitan. Sai ga su tare cikin gaggawa, tare da wasu Nas guda biyu suna tura dan keken daukar marar lafiya. Suka karaso inda nake har Hajiya suka kamani suka dorani akan wannan keken. Nas din nan biyu suka tura shi suka nufi wani daki da ke kusa da dakin Sadik. Anan Likita ya auna, sannan ya bani gado. Shima dakin gado daya ne da shi tak, sai toilet. Ba'a dau wani lokaci na na farka. Bayan agajin hahawa dana samu. Hajiya tana wajena, shi kuma Alhaji yana wajen Sadik. 23 Amina A. Sharada Na dubi Mamy na ce a hankali. "Mamy me ya sami Sadik.?" Ta ce "Hatsari suka yi." "A ina.?" Na sake tambayarta kwalla na zuba daga idanuwana. Ta ce "Ban san a inda suka yi ba Na lumshe idona ya yin da barci ya yi awon gaba da ni sakamakon allurar barcin da aka yi min. Wani irin tafkeken dajinc, ba gida gaba ba gida baya, sai rukunan bishiyoyi da suka taimakawa dajin matuka wajen kara masa duhun gaske, gami da jerin duwatsu manya-manya da suke kewaye da dajin. Wasu maka-makan duwatsu sun kewaye wani katon tafki sun masa kawanya, sannan ga wani irin yanayi bai ban tsoro. Kallo daya zakaiwa dajin kasan cewa yana dauke da miyagun namun daji da aljanu. Adai-dai wannan lokaci ina tsaye a bakin tafki ina haki sakamakon gudun da naci. Zuciyata a bace ina kokarin taka dutsen dake gefen tafkin da nufin in zunduma ciki in huta da bakin ciki. Yunkurawar nan da zan yi na buga wani uban tsalle da niyyar in zunduma ciki. Sai naji wani shuu! Tik! Na jini a ksa maimakon inji ni a ruwa. A firgice na bude ido inga me yake faruwa. Sai na yi tozali da wani kyakkyawan saurayi baki, jikinsa 24 Sharrin Jinni 3 babu riga, sai wani warki na fata da ya daura, sannan da wata jaka ratayc a jikinsa. Na dube shi a firgice na fara ja da baya. Ya yi murmushi ya ce dani "Na ga har yanzu ba ki gane waye ni ba ko." Ban iya ce masa komai balle har ya samu amsar tambayarsa. Ya ci gaba "Yanzu ne naga ya dace in bayyana miki gaskiyar kaunar da nake miki. Allah ya saka min kaunarki. Tun kina yarinya ina biye da ke, ina lura da ke, bana bukatar duk wani abu da zai taba ki. Kowa ya bata miki sai na bata masa. Shi yasa kuka ga mutane suna shiga matsala a kanki. Ko uwar da ta haifekice ta ce za ta batamiki sai na nuna mata kuskurenta. Saboda haka ki jawa mijinki kunne. Wannan hadarin da ya yi kadan ne na taba shi, duk lokacin da ya kuskura ya dakeki sai na wulakanta rayuwarsa. Sannan kuma in kasheshi in daukeki." Duk wannan bayanin da ya ke yi ina jinsa kawai. Sai da ya kawo karshen bayanin nasa, sannan na ce "To kai waye?" "Ni ba mutum bane aljani ne. Tun da kina da dakakkiyar zuciya zan nuna miki asalin surata yanzu." Yana rufe baki sai ya yi wata irin girgiza gami da haniniya da kugi. Baki daya nan take suffarsa ta sauya daga ta mutane ta koma ta wani irin bakin 25 Amina A. Sharada maridin Aljani, wanda acikin aljanun ma shi irin bakaken shaidanun nan nc. Girmansa kuwa ya kere duk bishiyoyin da ke gurin. Kansa irin na miciji ne, sai dai yafi na miciji girma sosai. Ina ganin wannan halitta ban san sanda na fadi kasa sumammiya ba. Wuf! Na tashi daga barcina, gami da kwala wata razananniyar kara. Mamy ta tashi da gudu, ya yin da na ke ta kokarin dirowa daga kan gadon da na ke kai. Na fiske robar ruwan da akai min karin ruwa. Na nufi hanyar fita ina kiran "Sadik!" Mamy ta jawoni iya karfinta. Na tureta can gefe ta fadi. Ina kokarin ficewa sai ga Alhaji da Ibrahim. Suna ganin abin da yake faruwa, sai Alhaji ya rikeni yana tambayar me yake faruwa.?" Mamy da take kokarin tashi cikin tsamin jiki na kayan da nayi mata, ta ce "Wallahi Alhaji tana kwance tana barci sai naga ta tashi a razane tana kara, shi ne fa ta diro tana ihu." Ba dan Alhaji ya yi min rikon tsauri ba, da tuni na fisge. Ya dubeni yaga ba acikin hayyacina na ke ba, ina ta faman sambatu. Sai ya fara yi min addu'a yana tofamin. Mamy ma na yi. Alhaji ya ce Ibrahim ma ya taso ya yi min. Shima ya taimako. Haka dai suka dinga yi min addu'a, da haka har na fara nutsuwa. Da na komo cikin hayyacina, sai na mike kyam na koma kan gado. Na yi tagumi ina 26 Sharrin Jinni 3 tunanin abinda na gani a mafarki. Ban san lokacin da hawayc ya fara zubo min ba. Alhaji ya matso kusa dani, ya ce "Kiyi hakuri, Sadik din ya farko, yanzu ma daga gurinsa nake, yana shaida nautanc, har ma yana magana. Dan haka Ibrahim zai zzauna a wurinsa, ke kuma ga Nusaiba nan zata zauna tare da ke." Na ce "Alhaji nifa lafiyata kalau." Ya ce "Ai na sani, so na ke ki huta tukunna sai kije gurin nasa." Na koma na zauna, ina mamaki, wai lafiyata kalau amma ace wai bani da lafiya. A zaune Sadik yake, domin ya fara samun sauki, ya yi tagumi kawai, ya yin da Ibrahin yake gefensa a zaune shima yana kallonsa, zuciyarsa cike da mamakin irin tsanar da Sadik ke masa. Shi kuma baiga abinda ya yi masa ba, amma a yadda ya daukeshi, sai ka ce abokin gaba. Ko dai a hatsarin da ya yi ya samu buguwa a kansa ne? Irin tunanin da Ibrahim yake kenan. Ya yin da ya ke zaman jinyar Sadik. "Ibrahim na gaya maka bana son zaman ka, gara ka koma gida a turo wani. Kai ni a kyaleni haka ma, ni kadai ma zan iya komai da kaina." Ibrahim ya ce "To na ji, ka baro Alhaji yazo, yau sai in gaya masa ya kawo maka wani." Sadik ya yi tsaki ya juyar da kansa gefe daya kawai. 27 Amina A. Sharada "Nusaiba zo muje in ga jikin Sadik." Ta се "То taso muje tun da kin na ce sai mun je din." Na mike muka fita, muka nufi dakin Sadik. Yana kwance Ibrahim na gefe daya. Na karasa inda yake na kira sunansa a hankali "Sadik!". Ya bude ido ya kalleni. Sai naga ya tashi zaune ya Kurawa Ibrahim ido. Ya sake maida kansa gareni ya girgiza kai kawai, ya koma ya kwanta ya rufe idonsa. "Sadik ya jikin.?" Na ce da shi cikin sanyin murya. Ko kallona bai yi ba, ya ma juyar da kai kawai. Na zauna kusa da shi, na sa hannu na dafa shi, na cc "Sadik ka daina saka bacin rai a zuciyarka kar wan i ciwon ya kamaka." Baice dani kala ba. Na dubi Ibrahim na ce "Ibrahim ko baya magana ne.?" Ya ce "Wallahi nima haka yake min. Amma yana magana." Na girgiza kai kawai. Na zauna na yi tagumi, banda hawaye ba abinda ke zubo min daga idanuna. Haka muka yi ta zama a asibitin har Sadik ya samu sauki baya mun maganar komai, sai dai yasa Nusaiba tayi masa wani abun idan yana bukata. Baya sani, baya sa Ibrahim. Abin yana bamu mamaki, amma sai muka zuba masa ido kawai, domin in mun ce zamu tambaye shi dalili ma ba magana zai yi mana ba, sai dai akwai ya zubo mana na mujiya. 28 Sharrin Jinni 3 A haka aka sallamomu gaba dayan mu, domin Sadik ya samu lafiya. * Tunda aka sallamemu muka dawo gida ba abinda ya sauya dangane da fushin da Sadik ya ke yi dani. Idan abinci nayi baya ci, in gaisheshi nayi baya amsawa. Duk abin da na yi masa baya saurarona. Hakan ne ya sani matukar damuwa, koda yaushe ina zuane nayi tagumi, ko barcin kirki bana iyawa. Muna nan a haka rannan sai na tashi da jiri da ciwon kai. Ina kwance a dakina ban fito ba, ko karyawa ban yi ba, domin ba zan iya cin komai ba. Wajen sha daya da rabi na rana na samu jirin ya dan sakeni. Sai na fitoa falo domin in danji dadin jikina. Sai na sami Sadik a falon azaune yana shan tea. Anan na tabbatar shima sai yanzu yake karyawa. Na sami guri na zauna, na dubeshi na ce "Ina kwana.?" Ya dan kalleni. "Lafiya." Ya amsa min a ciki da gajeriyar amsa. "Dan Allah ko zaka je ka ce da Nusaiba tazo ta dan tayani wasu abubuwan. Wallahi bani da lafiya." Bai ce dani komai ba, ya ci gaba da abinda yake yi. Hakan da yake min ba karamin kona min rai yake yi ba. To amma dolene in yi hakuri har Allah ya kawo karshen wannan lamari, domin dai na san ba 29 Amina A. Sharada AUREN KI aka yi mana, AUREN SONE tsakanina da shi, bare yace dole aka yi masa auren. Ina nan kwance sai kamshin dankali da kwan da ya soya ya ke karyawa da shi ya bugeni. Take amai ya fara taso min. Ina kokarin tashi in fita da gudu sai aman ya rigani. Anan na fara kwara amai. Yana kallona kawai ba abinda ya ce da ni har na gama aman. Ciwon ciki kuma ya ce gani nan. Na dinga birgima ina rike da cikina ina kiran "Wayyo Allah! Sadik ka taimakeni. Wayyo Allah Sadik zan mutu!" Kawai sai ya yi tsaki ya dauke flet din da kofin shayin ya nufi kitchen ya barni a kwance anan ina juyi da kiran Wayyo Allah na zan mutu!. Ya dawo ya yi shigewarsa daki abinsa. Haka na yi ta murkususu, ga ciwo ga bakin ciki. Can jimawa sai ga Nusaiba ta shigo da saurinta. Ta karaso inda nake kwance tana cewa "Sannu Hamdiyya. Tun yaushe baki da lafiya." Da kyar na bude baki na ce "Da safen nan." Ta ce "Oh Allah ya sauwake, dama nima yanzun nan Yaya Sadik ya yi min waya, ya ce inzo baki da lafiya." Duk da nayi mamakin abinda tace. Sai na 6oye dan kar ta gane, na ce "Uhm." Kawai. Nan ta taimaka min nayi wanka, ita kuma ta gyara falon. Bayan na sauya kaya ina kwance sai gata ta gama, ta ce "Hamdiyya Yaya Sadik ya ce wai ki fito 30 Sharrin Jinni 3 muje asibiri." Na ce "Shi zai kaimu." Ta ce "A'a ya bani mukullin motarsa, ya cc in kaiki." Na cc "Au an gyara motar nc." Ta cc "A'a baki san Alhaji ya sauya masa sabuwar mota bane.?" Na yi shiru kawai ina tunani, dan ban san Alhaji ya sauyawa Sadik wata motar ba sam-sam. Amma dan kar ta ganc sai na cc "A'a dama ina a tsohuwar ta da yake fada." Та ce "A'a." Na tashi na shirya muka tafi. Na ce "To kin karbo kudi ko haka zamu tafi." Tа сс "Ya ce muje can Hospital din da akc zuwa." "Kin san wurin." Na tambayeta. "A'a ba kin sani ba.?" Ta ce dani. Na ce "Ke dai in kin sani kawai muje." Ta ce "Ban sani ba sai dai in tambayeshi. Ya dai ce Privete ne asibitin." Na ce "Kije ki tambayeshi." Na fita, ita kuma ta wuce dakin Sadik. Ta juyo ta kalleni, sannan ta maida hankalinta ga tuki, ta ce "Niga mamaki kika bani, gashi dai kina a halin rashin lafiya, amma sia naga kina murna bayan kinga likita. Wai me ke gudana ne.?" Na yi murmushi na ce "Sauki na smau shi ya sa kika ga ina ta murna." Tayi dariya, "To Allah ya karo sauki." Na ce "amin." Adai-dai lokacin da muka yi parking a kofar get dinmu, ya yin da Maigadi ya ke kokarin bude mana get. Muna shiga cikin gidan sai ta tsaya, na 31 Amina 4. Sharada fito ina yamutsa fuska, Daga k "an nan da zanyi sai muka yi ido hudu da Sadik yana kallona ta windownsa dake fuskantar harabar gidan. Na yi saurin dauke kaina nayi shigewara ciki na bar Nusaiba na kukkule motar. Ta sameni a falo a zaune, ta ce "Ungo ki kaima sa key dinsa." Na ce "Ba zan iya tashi ba, kai masa." Ta shiga ta kai masa. Ta dan jima sannan ta fito, ta ce "Hamdiyya ya ce ki bani katin in kai masa." Na yi kamar ba zan bata ba, amma dai sai na mika mata kawai, na sami guri nayi kwanciyata, Anan ta dawo ta sameni ina kwance da katin a hannunta ta miko min. "Gashi." Na ce "To." Na Каrба. Та zauna kusa dani, ta ce "Hamdiyya ina son in yi miki wata tambaya, amma ina gudun kar kice nayi miki shishshigi a lamarinki." Na yi murmushi, na ce "Nusaiba kenan, ai tsakanina da ke ba maganar shishshigi, gaya min duk daya ne." Ta ce "Dama so nake inji, wai me yake kaiwa da komowa a tsakaninki ke da Sadik ne.?" Na kalleta na yi murmushi. "To ke me kika gani.?" Ta ce "Ba komai, gani na yi dai ba kamar da ba." Na ce "To ai ba wani abu. Ke ce dai kika ga hakan." Ta ce "A'а Hamdiyya kar fa a dinga wahalarmin da Yayana." Na yi murmushi, na ce "Ko dai shi ya wahalar dani, domin in shi ba'a wahalar da shi ba ai shi ya wahalar." Tayi dariya, ta ce "Ki gode Allah 32 Sharrin Jinni 3 muje asibiri." Na ce "Shi zai kaimu." Ta ce "A'a ya bani mukullin motarsa, ya ce in kaiki." Na ce "Au an gyara motar ne." Ta ce "A'a baki san Alhaji ya sauya masa sabuwar mota bane.?" Na yi shiru kawai ina tunani, dan ban san Alhaji ya sauyawa Sadik wata motar ba sam-sam. Amma dan kar ta gane sai na ce "A'a dama ina a tsohuwar ta da yake fada." Ta ce "A'a." Na tashi na shirya muka tafi. Na ce "To kin karbo kudi ko haka zamu tafi." Ta ce "Ya ce muje can Hospital din da ake zuwa." "Kin san wurin." Na tambayeta. "A'a ba kin sani ba.?" Ta ce dani. Na ce "Ke dai in kin sani kawai muje." Ta ce "Ban sani ba sai dai in tambayeshi. Ya dai ce Privete ne asibitin." Na ce "Kije ki tambayeshi." Na fita, ita kuma ta wuce dakin Sadik. Ta juyo ta kalleni, sannan ta maida hankalinta ga tuki, ta ce "Niga mamaki kika bani, gashi dai kina a halin rashin lafiya, amma sia naga kina murna bayan kinga likita. Wai me ke gudana ne.?" Na yi murmushi na ce "Sauki na smau shi ya sa kika ga ina ta murna." Tayi dariya, "To Allah ya karo sauki." Na ce "amin." Adai-dai lokacin da muka yi parking a kofar get dinmu, ya yin da Maigadi ya ke kokarin bude mana get. Muna shiga cikin gidan sai ta tsaya, na 31 Amina A. Sharada fito ina yamutsa fuska. Daga k "an nan da zanyi sai muka yi ido hudu da Sadik yana kallona ta windownsa dake fuskantar harabar gidan. Na yi saurin dauke kaina nayi shigewara ciki na bar Nusaiba na kukkule motar. Ta sameni a falo a zaune, ta ce "Ungo ki kaima sa key dinsa." Na ce "Ba zan iya tashi ba, kai masa." Ta shiga ta kai masa. Ta dan jima sannan ta fito, ta ce "Hamdiyya ya ce ki bani katin in kai masa." Na yi kamar ba zan bata ba, amma dai sai na mika mata kawai, na sami guri nayi kwanciyata. Anan ta dawo ta sameni ina kwance da katin a hannunta ta miko min. "Gashi." Na ce "To." Na Karba. Ta zauna kusa dani, ta ce "Hamdiyya ina son in yi miki wata tambaya, amma ina gudun kar kice nayi miki shishshigi a lamarinki." Na yi murmushi, na ce "Nusaiba kenan, ai tsakanina da ke ba maganar shishshigi, gaya min duk daya ne." Та се "Dama so nake inji, wai me yake kaiwa da komowa a tsakaninki ke da Sadik ne.?" Na kalleta na yi murmushi. "To ke me kika gani.?" Ta ce "Ba komai, gani na yi dai ba kamar da ba." Na ce "To ai ba wani abu. Ke ce dai kika ga hakan." Ta ce "A'a Hamdiyya kar fa a dinga wahalarmin da Yayana." Na yi murmushi, na ce "Ko dai shi ya wahalar dani, domin in shi ba'a wahalar da shi ba ai shi ya wahalar." Tayi dariya, ta ce "Ki gode Allah 32 Sharrin Jinni 3 Hamdiyya, irin yadda Yaya Sadik ya dauke ki, in kika ce haka kinyi masa butulci, domin babu yarinyar da yake kauna fiye da ke." Na ce "To in ma cutarsa nake yi ai zaku gani ne yau da kullum ko.?" Ta yi murmushi, ta ce "Amai da wukar, Allah ya huci zuciya, ban fada dan rai ya baci ba, na fada ne dan a gyara." Na ce "Nima ai ba ran nawa ne ya baci ba, gani nayi za'a fidda min kokon usuli, wato ke mai dan uwa.?" Tayi dariya "Kema tawa ce ai." "Yo ba dole be. Ni kinga ki kyaleni inji da abin da ya dameni." Tayi dariya, "Ai abinda ya dameki ba wani abu ne na bacin rai ba, dan haka sai ki san yadda zaki alkinta mana dakon da ko 'ya." Na yi murmushi "Ku kai ku alkinta." Ta mike, "Kinga ni yanzu ma zuwa zanyi inb kaiwa Mamy albishir." Na harareta. "Kin ga ni fa bana son gunzugulu." "Koma me zaki ce nayi sai na fada." Na се "Kanki ake ji." Tayi waje tana dariya. Har ta fita ta dawo. "Au na manta zan dawo in dora miki girki ne Aunty Hamdiyya." Na ce "Kya santa dai." "Allah ba da wasa nake ba." Na ce "Ke ni ba zan ci ba." "To in bakya ci Yayan fa.?" Ma be "Jeki ki tambaye shi, in yana da bukata." Ta nufi dakin 33 Amina A. Sharada Sadik. Ta dawo ta ce "Ke in mun gama na gida a kawo masa." Na ce "Ke kika sani sautin mahaukaciya." Ta fice ta barni anan akwance. *** Yau watan cikina shida, har ya bayyana, kowa ya san da shi. Amma Sadik tun ranar da aka kai masa katunan nan har kawo yau bai taba cemin ashe ciki gareki ba. Na karaci laulayina na gama yana ji yana gani kamar wanda ba na saba. Hakane yake firgita ni. "To wai meye nufinsa ne? Hakuri dai iya hakuri nayi shi, koma ince ina kanyi, domin duk halin nan da muke ciki ba wanda na taba gayawa. Nusaiba ma dan ta fuskanta ne da ba zata san me ake ciki ba, kuma gidan mu gurin zuwanta ne yau da kullum. Irin wannan tunani shi ne abokin hirata kullum. Yauma kamar kullum ina zaune ni kadai a fali, duk na saki labulayen, da yake lokacin sanyi ne, irin hunturun nana. Na kwanta gami da jan tattausan bargona bayan na duba agogon da ke manne a falon. Daya saura minti biyar na rana. Na yi lami kamar mai barci. Can sai na mike kamar an mintsineni,. domin bin umarnin abinda tunanina ya sana'antamin. Na nufi dakin Sadik kai tsaye, na sameshi shima a kwance, duk da yake fuskarsa a 34 Sharrin Jinni 3 bude idanunsa na kallon sama, ya tsurawa silin din dakin ido kawai yana tunani. Na je kansa na tsaya da jiki tirtsitsi, fuskata a daure. Ya juto a hankali ya zubo min ido. Sai da muka share mintina kusan uku muna kallon-kallo da ni da shi, sannan ya ce cikin sanyin murya. "Me ya kawo ki dakina.?" Na ce "Eh kace mai ya kawoni mana tunda ba aurena ka ke yi ba. Ni dama zuwa na yi in shaida maka cewa na gama hada kayana zan tafi gida, na gaji da zaman da bashi da amfani. Ban san cewa baka aurena ba sai yanzu." Ya mike zaune a hankali "Wa ya ce bana aurenki.?" Na ce "Oho! Kai ka sani." Na juya zan fice. Ya ce "Zo nan Hamdiyya." Da dai kamar ba zan koma ba, sai dai na koma dan inji abinda zai ce min. Na tsaya a gabansa. Ya kalleni sama da kasa, ya ce "Yanzu baki ji kunyar tsayawa a gabana kina fadamin wannan maganar ba.?" Na ce "Kunya!? Kana wasane da abin da bana wasa ba? Kar ka manta wannan cikin fa dake jikina naka ne, amma duk irin wahalar da na ke sha akansa baka taba saurarena bama bare ka tausayamin. Hasalima tun lokacin da Allah ya bayar da cikin baka taba cewa yau banzar nan cike gareya ba bare in san ka san da shi. Ai ko zuwa nayi da shi ka tausayamin bare kuma naka." 35 Amina A. Sharada Ya yi shiru kawai yana saurarona. daga can kuma ya ce "Yanzu to ya kike son inyi miki." Na ce "Kawai gida zan tafi, in na haihu a aiko maka da jaririnka ko jaririyarka. Ban zaci baka kaunata ba sai yanzu!!". Ina gama fadin haka na saka kuka na fice daga dakin na barshi ya kasa katabus. Ina shiga dakina na hau hada kayana a cikin akwati ina ta faman kuka. Sai ga Nusaiba ta shigo sanye da riga da wando na sanyi masu kaurin gaske, ta sanyo hijabi. Da hucinta ta fado dakin, ta dauka na tafi, ta sameni a zaune hawaye na shatata daga fuskata. Tayi turus ta ce "Haba Hamdiyya, wai menene na tada hankalinki ba, ke kuma baki kwantarwa da Sadik nasa ba. Wai ya kuke son nayi muku ne.?" Sai da ta gama maganganunta, sannan na dago kaina ina share hawaye, na ce "Wato dai ku laifina ma kuke gani. In haka ne ke da Sadik din ya yi muku wayar ba sai ya fada miki abinda na yi masa ba. Ni wallahi tafiyata zanyi ba zan iya zama ba a cikin bacin rai." Ta ce "ni dai wannan lamari naku ban gane masa ba. Wallahi Alhaji zan gayawa." Nan da nan ta bugawa Alhaji waya. Yana amsawa ta ce "Alhaji kazo gidan Yaya Sadik, ina ta fama da Hamdiyya wai sai ta tafi gida. Nayi-nayi ta gayamin abinda ya faru taki...." 36 Sharrin Jinni 3 "Yauwa to muna jiranka......" Ta kashe wayar. Ta kalleni "Alhaji ya ce ki jirashi yana zuwa yanzu." Ko kallo bata isheni ba, na ci gaba da hada kayana. Itama kuma bata yi min magana ba. Daga nan ta koma falo ta zauna. A falo na samesu zaune tare da Sadik, nazo zan giftasu, sai Nusaiba tayi saurin kamo akwatin dake hannuna ta rike, ta ce "Ke yanzu in ance ki tafi sai ki tafi a yadda kike din nan.?" Na ce "A'a sai in tafi mana tunda ba'a Kaunata." Ta mike ta kama akwatin ta ce "Alhaji ya ce ki jirashi zai zo yanzu." Tana rufe 6aki sai Alhaji ya yi sallama ya shigo. Muka amsa masa baki dayanmu, ya sami guri ya zauna, ya dubeni ya ce "Zo nan Hamdiyya in ji me ke faruwa." Na koma na zauna bayan na sakarwa Nusaiba akwatin. Na sunkuyar da kaina, ya yin da hawaye ke zubo min kamar ruwa. Alhaji ya nisa ya ce "Ya aka yi ne.?" Cikin kuka na ce "Wallahi Alhaji ban san abinda na yi masa. Kusan watanni takwas baya min magana, kullum sai haushina yake ji." Alhaji ya ce "Sadik me yake faruwa har haka ta samu.?" Ya yi shiru kawai. Alhaji ya ce "Da kai nake magana kayi shiru." Kansa a sunkuye ya ce 37 Amina A. Sharada "Alhaji yarinyar ce dai kawai bata da kirki, shi yasa naga ya dace in daga mata kafa." Alhaji ya ce "Kamar yaya bata da kirki? Ai ka bani a rufe." "Alhaji ai ita ta san laifinta,

Chapter 2 of 5