Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 5
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels SHARRIN NA AMINA ABDULLAHI SHARADA (MRS.AHMED YUSUr Sharrin Jinni 3 SHARRIN JINNI 3 NA AMINA ABDULLAHI SHARADA (Mrs Ahmad Yusif Hadejia) 1 Amina A. Sharada HAKKIN MALLAKA Amina Abdullahi sharada GODIYA SHEKARAR BUGU 2008 Ga Allah Subahanahu wata'ala da ya bani ikon kammala wannan littafi. Allah ka karawa Anabi S.A.W. daraja da daukaka. Amin summa amin. GAISUWA > Ummi Sulaiman Hajiya Sulaiman Nafisa Kawu Fati Ya'u Maryam Alhaji Sakina Tasi Saude Balarabe Aisha A. Kurawa Hajiya Ali Dukkanku gaisuwa ce daga Zainab Sulaiman (Dangadi) Zeee Babu Maiduguri. 2 Sharrin Jinni 3 FATAN ALKAIRI Fatan alkairi gareki. * Nafisa Muhammad Sheka. (Marubuciyar Mariyatu) Wasila Muhammad Jamila Muhammad Hadiza Bashir Dandago Ummi Usman Hadiza Ciroma Hadiza Baba Sagir Muhammad Sheka Hauwa Muhammad Binta Muhammad Nayi muku fatan Alkairi daga Numan Adamawa State. GAISUWA TA MUSAMMAN Ga dukkan Masoyana masu aikon min da sakwanni tedt ko waya. Na gode sosai. Allah ya kara kauna Amin summa amin. GAREKU KAWAYENA NA KAINA • Bilkisu H. Muhd (Mrs Auwal by force Zage (MULKIN MALLAKA) . Nafisa Muhd Sheka (ZUHURIYYA) Sa'adatu Ahmed (SALEEMAT) 3 Amina A. Sharada Zahra'u Baba Yakasai (TARKON SO) Safiya Sani Ahmed (DUK ABINDA КА KE SO) Bilkisu Garba Maiagogo (IN SHARRANSHARRAN) JINJINA GARELA KANINA NA KAINA Shitu Sa'id Cross River State (Calaba) GODIYA GAREKU Sumayya Baita Yahaya D/Dutse Khadija K/Marusa KT Aunty Sa'a Zuru Deejat S/Sharubutu Jamila Zaryya Gamawa Zabba'u Tambuwal Maryam (Meran) Tambuwal Baraka shiru Lawan (Nakirki) Katsina Maman Fati Katsina H.M.A. Fagge Kano Rukayya Y. Adamawa P.T.O. Tsara rubutu a na'ura mai kwakwalwa (COMPUTER) MUBARAK M.B. GADON KAYA 07039170556-07039034583 Sharrin Jinni 3 SHARRIN JINNI 3 S adik ya yi matukar karfin hali ya ce "Kai waye da za ka shigo min gida haka kawai ka hana ni sakewa.?" Ya sake jin an cc. "Ni ba ka isa ka san ko ni waye ba. Amman da sannu nan gaba za ka sani." Ni ko ina kudundune a jikin Sadik na kasa fito da kaina ma daga kirjin Sadik. Sadik ya ce "Koma wayc kai Allah ya fika, domin mu da shi muka dogara." Nan ya fara karanto wasu addu'o'i masu karfin gaske, maganin duk wasu shaidanun aljanu. Ya dinga tofawa a dakin, kudu da arewa, gabas da yamma, sama da kasa. Duk wannan abun abu dake faruwa har yanzu ina jikin sa a dukunkune. Ya ce "Zo muje mu kwanta." Na ce "Wa? A ina.?" Ya ce "Muje dakina." Na ce "Sam ba dai a gidan nan ba, mu je dai kawai ka maidani gidan Alhaji." Ya ce "Kar fa ki manta duk inda muke Allah yana tare da mu.?" Na ce "Duk da haka ba zan iya zama ba. Haba Sadik kana fa jin abinda aka ce. To kai kuwa wonne tsautsayine zai sa mu kwana a gidan nan.? Ni dai uke ka maida ni." Hankalin Sadik a tashe ya ce "Mu koma falo." Kememe naki yarda in banbaru daga jikinsa. Ya rasa yadda zai yi dani, domin kuka nasa masa. A haka muka je falo ya dauko kaset na karatun Alkur'ani kira'ar Sidi 5 Amina A. Sharada Abdurraman Madina, da yake dama can Sadik ma'abocin son wannan karatun nc. Ya kunna tare da Kurc karar rediyon. In ka fita tun daga get ana jiyo sautin muryar, sannan ya kuma zauna a falin kan doguwar kujera. Dangwargwar har gari ya waye babu wanda ya rintsa, duk abin nan ina jikin Sadik lamo muna ta sauraron karatun Almur'ani, sannan kuma Sadik na ta faman yin addu'o'i. Tun assalatu Sadik ya ce in tashi muje muyi sallah. Na ce ya bari gari ya yi haske. Ya ce "A'a shi zuwa zaiyi ya yi sallarsa." Na ce "Ai ko ba zai barni ni kadai ba a falon, sai dai mu tafi tare. Haka muka shiga toilet. Tare muka yi alwala, sannan muka yi sallar tare. Kayan namu ma tare muka je muka dauko saboda tsananin tsoro. A inda muka yi sallar nan muka zauna muna karatun Kur'ani har gari ya karasa wayewa. Ya san ma in ya ce inje in hada abin karyawa ba zuwa zanyi ba, dan haka da kansa ya mike. Zumbur! Na kama gefen rigarsa na bishi. Na kasa komai dan tsabar tsoro, shi ya shirya mana abin karyawa, muka fito falo tare, muka zauna tare, muka kwashe kayan ma tare bayan mun gama karyawa. Ya ce "To yanzu in zan fita ya za'ayi kenan.?" Na ce "Ka fita ina.?" Ya ce "To zanyi ta zama a cikin gidane? Ai dole ne in fita." Na ce "Ai sai dai mu fita tare." 6 Sharrin Jinni 3 Ya yi shiru yana tunani. Can ya ce "Kin ga fa wannan magana ba ta shiru ba ce, dolene in sanarwa da Alhaji halin da ake ciki." Na ce "Au wai da kai shiru zaka yi? Ai ba zai yiwu ba. Domin kuwa wannan bau bana shiru bane. Ta shi mu tafi kawai gurin Alhajin.?" Ya ce "To muje.' Muka kukkule gidan, muka fito muka nufi gidan Alhaji. Da yake ba nisa a kasa muka je, saboda layi daya muke da shi. Da zuwan mu muka same shi a zaune a tsakar gida shi kadai. Muka yi masa sallama ya amsa gami da duban mu cikin mamaki. Ya ce cikin fada. "Yau zan ji shakiyancin banza. Daga gama bikin jiyajiyan nan sai ka dauko ta ku fito yawo.? Yanzu ina za ku je.?" Sadik ya rusuna ya ce "Alhaji ba yawo muka fito ba, wata matsala ce ta faru jiya." Ya ce "To me yake faruwa." Nan Sadik ya kwashe yadda aka yi ya fadawa Alhaji. Wani mamaki firgitacce ya kama Alhaji. Ya ce "Yanzu ya ya aka yi." Ya ce "Zuwa mukai domin mu sanar maka halin da ake ciki." Alhaji ya ce "shi kenan, muje cikin gidan, gani nan zuwa." Muka shiga ciki. Mamy na ganin mu ta bude baki da salatin ta baki daya. ta ce "Ku kuma ina zaku..." Kafin mu bata amsa Alhaji ya shigo, ya ce "Wani abun 7 Amina A. Sharada mamakine kuma ya samu. Anya kuwa Hajiya Lami babu wani bakon al'amari tare da yaran nan.?" Takc ya sanar da ita halin da ake ciki baki daya. Ta dafe kirji gami da salati, ta cc "Hakika akwai wani al'amari a tarc da su. Anya kuwa ba'a dajin nan suka kwaso aljanu ba.?" Alhaji ya cе "Nima dai abin dana ke tsammani kenan. Amma ko ma mcyc Allah zai mana maganinsa. Yanzu dai ku zauna ba inda za ku jc. Ma'ana ba za ku koma ba har sai an tabbatar an tsare gidan naku tukunna, kar suje su sabauta ku." Takc murna ta kamamu har Sadik din. Alhaji fa ya shiga hada Malamai manya domin su taimaka a tsare gidanmu. Sai da ya hada Malamai goma sha uku suka dukufa da karatun Alkur'ani ba dare ba rana. Sai da suka yi sauka sau uku, sannan suka dinga bayar da kafin miyagun mutane da Aljanu shaidanu ana binnewa a gidan. Sannan muma aka hadamu aka yi mana rukiya, domin ana zaton ko yana tare da mu. To ba abinda ya bayyana a tare da mu, sannan aka tabbatar mana da zamu iya shiga gidan yanzu ba wani abu. Muka yi matukar farin ciki. Alhaji da kansa ya rakamu gidan. Muka yi masa godiya mai tarin yawa, sannan ya zauna a falon gidan. Ya fara min fada akan abin da ya kamata in dinga yi dan 8 Sharrin Jinni 3 gudun samun mafakar wani shadanin Aljani а jikina. Dama dai aljani yafi samun sararin shiga jikin 'ya mace fiye da da namiji, saboda ita mace tafi sakaci, domin ita aka umarta da ta suturcе jikinta domin duk wani abu na daga jikin 'ya mace al'aura ne. Ba'a kuma ce ya suturce dan mazan mutane kawai ba, har ma da mazan Shaidanun Aljanu, wadanda bayan sha'awa ma, sukan auri mace ba da sanin ya ba, kuma suyi ta biyan bukatarsu da ita ba tare da an ankaraba, sai tura ta kai bango sannan suke bayyana kansu, azo ayi ta kai ruwa rana kafinb su bar jikin mace." Na ce "To Alhaji. Ta ya ya suke shiga jikin mace.?" Ya ce "Hanyoyin da suke shiga jikin mace yana da yawa, amma mafi sauki shi ne ta inda 'ya mace yafi sakaci da wurin. Misalin barin kai a bude da kitso, ko tsefaffen kai. sannan yawo da daddare a tsakar gida kafa ba takalmi. Zaman bakin kofa ko kan turmi. Shiga bandaki kai babu dauri, da surutai a bandaki, sannan kuma bayyanar da tsiraici ta hanyar sanya matsatstsun dunkuna. To wannan ma bayo ga mazan mutane yake tasiri ba, har ma da na Al anu baki daya, domin fidda tsiraici yana taka muhimmiyar rawar gani wajen jawo su. Kuma dan Allah ki dinga yawaita addu'a da karatun Alkur'ani mai girma. Ta wannan hanyar ma 9 Amina A. Sharada zaki iya nisantarsu, ba za su sami damar shigarki ba muddin kina kiyaye wadannan dokokin." Na yi matukar farin ciki da jin wannan shawarwari da Alhaji ya bani. Muka yi masa godiya mai yawa ya tashi, muka rakashi har bakin get ya tafi. *** Zama ya kankama tsakanina da Sadik. Ba wata fargaba ko hayaniya, sai zuba soyayyarmu muke yi hankali kwance, domin ba wani abu da yake damunmu barema ya firgitamu. Muna baiwa fulawowin gidan ruwa ni da Sadik da tiyo, ta hanyar jonota a jikin fanfon dake tsakiyar gadin din gidan. Dama abin ban ruwan a a hannun Sadik yake, yana ta jika fulawoyin. Sai ya dan watso min ruwa, naji sanyi ya shigeni, gashi kuma dama lokacin sanyi ya dan fara shigowa. Na ce "Lala-lala! Ka zuba min ruwa? Wallahi sai na rama." Ya ce "To rama din." Na shammace shi na fisge tiyon na feshe shi da ruwa ina dariya. Sai da na jike shi. Ya biyoni da gudu muka shoga cikin gida da gudu. Na fada dakina ina kokarin rufe kofa, sai ya rigani, ya danno kofar ta bude, na afka kan gadona, shima ya bini yana cewa "Yau sai kin gaya min wanda kika jika." 10 Sharrin Jinni 3 Ni kuma ina dariya ina cewa "Dan Allah Yaya kayi hakuri, wallahi na daina." Ya dauki filo yana maka min. Ni muma ina kukan kагуа. Na kukuta na janyo kwalar rigarsa na sabule da karfi, ni kuma na ware rogar barcina mai tsaga a gaba. Kallo daya ya yi min na rikita masa zuciya. Take ya afka min muka saka labule. Muna zaune a falo, na ce "Yaya Sadik." Ya ce "Na'am." Na ce "Ina son in koyi mota wallahi." Ya ce "Ai ba wani abu, zan dinga koya miki. Kullum da yamma ma dinga fita." Ina jin haka nayi tsalle da ihun murnata, na afka masa a jiki ina dariya. Na ce "Dan Allah Yaya Sadik mu fara daga yau." Ya ce "To shi kenan, in an jima sai ki shirya mmu fara, amma fa da sharadi. Ko kin iya ba zan barki ki dinga tuka kanki ba, domin dai kin san ina da kishi, shi yasa na ke shakkar koya miki, kar ki sami kafar yawo. Sai dai muyi da wajewa, in kin fara tuki da kanki ba shiga ba fita sai in ta kama dole.?" Na ce "Na yarda." Ya ce "Shi kenan, ki shirya da yamma zan fara koya miki." Na ce "To." Kwanci tashi kullum sai mun je da yamma Sadik ya koya min, har na fata gwanancewa, na kan dan yi tafiya mai nisa na dawo da kaina. Sadik dan murna sai ya tafa min, in na fito ya rungumeni yana min karka. Nima murna a guna b bayani. 11 Amina A. Sharada Sadik ya ce "In Allah ya sa ya fara aiki ya sami kudi zai saya min mota tawa ta kaina." Nan ma murna a guna kamar me. Yaua dai kauye muka nufa domin mu gaishe da su Dagaci, su Inna da Babba Tasallah. Alhaji yana yawan yi mana fada akan cewa mu dinga yawan zuwa muna gaishesu, shi ne zamu dinga samun albarkarsu akowanne lokaci, kuma zamu dinga ganin budi a rayuwa, domin iyaye ba abin wasa ba ne. Shi yasa a kowanne wata sai munje mun gaishe su. Gidan Dagaci muke fara zuwa, sannan muje gidan Baba Tasallah sai mu karkata gidan Inna. Bamu taba kwana ba, duk san da muka je a ranar zamu dawo, sai dai mukan kai dare. Dagaci ne ma ya ce zuwan da muke yi duk wata ya yi kusa. Ya deba mana wata uku-uku in ba so muke da ma muyi ta yawo a hanya ba. Haka muka hakura akan sai bayan wata ukun ma dinga zuwa. Rannan ina kwance a dakin Sadik da daddare muna hira har wani lokaci. Sadik ya fara jangwalata na son mu kebe. Ni kuma bana bukatar komai a wannan lokaci. Sai na yi masa karya na ce cikina yana ciwo. Ya ce "To shi kenan Allah ya sauwake." Na ce "Amin." Sannan ya mike ya kawo min 12 Sharrin Jinni 3 magani. Ala dole na sha, domin kar ya dagoni. Haka muka kwanta har kusan asuba. Da asuba naga ya fara dan lalube-lalube. Kawai sai na yi fuska, na ce "Nifa ban warke ba." Ya ce "Wallahi karya ne." Na ce "To shi kenan, bara in bar maka dakin." Na tashi na yi tafiyata dakina, na yi kwanciyata. Sadik na dakinsa, can kusan assalatu sai yaji kamar an bude get din gidan. Dan haka sai ya yi sauri ya daga labulen dake windown dakinsa. Yana kallon harabar gidan ne ya hango wani kamar Ibrahim ya fita da doguwar rigar barci. Ya fara mamakin meya kawo Ibrahim gidan sa a asubar nan. Wuf! Sai ya mike domin ya je dakina ya gaya min abinda ya gani. Yana shiga ya sameni ina ta sharar barci. Ya dagani da zummar ya dorani akan cinyarsa. kawai sai yayi ido biyu da gajeran wandan Ibrahim a karkashina ina kai a kwance. Ya yi saurin fusgoshi dan gasgata abinda idon sa ke barazanar nuna masa. Hakika babu makawa idonsa ba gaibu yake ba shi ba. Wandonsa ne!. Juyawar da zai yi sai ga agogon Ibrahim shima a yashe bisa gadon. Duk abin nan idona a rufe yake, ban san me ke faruwa ba, dan haka ban ko bude idona ba ma na sake gyara kwanciyata a cinyar Sadik. 13 Amina A. Sharada Ya janyeni a hankali ya dauke wadannan kayan. Wato agogo da gajeran wandon ya fice abinsa. A zatona zuwa zai yi ya dawo domin idona a rufe yake na ci gaba da kwanciya abina ina sauraron dawowar Sadik. Shiru bai dawo ba, na tashi na yi sallah, na koma na kwanta abuna har gari ya yi haske, sannan na fito na nufi kitchen domin in dora mana abin kalacin safe. Har na gama banga Sadik ba, sabanin yadda ada muke ta aikin tare, muna yi muna wasa da juna. Na jera mana abincin mu akan daning table na koma dakin Sadik domin inga in barci yake in tashe shi. Na jima a tsaye ina kwankwasa kofar, amma shiru bai ta shi ba bare ya bude. Na yi kira, na yi kira shiru. Sai na zaci abin da na yi masa a daren jiya ne ya bashi haushi har ya ki fitowa. Na koma kan kujerar falo na kwanta ina tunanin lallai ma Sadik, wato rana daya ta mai kaya, rana dubu ta barawo, wato dan yau daya na nuna masa haka shi ne zai yi fushi dani? Ko da yake ta wajen wannan fa Sadik ba shi da hakuri. Haka zan bashi hakuri in ya fito, domin ni ce da laifi." Ina nan kwance sai naji yana bude kofa. Na tashi da sauri na dubeshi bayan ya fito. A shirye yake tsaf! Ga alama ma fita zai yi. Ganin fuskarsa ta sani bugun kirji tafi sau ashirin masaki domin ban 14 Sharrin Jinni 3 taba ganinsa a wannan yanayi ba. Yazo zai giftani ya wuce. Na yi wuf! Na mike na shiga gabansa. Na ce "Sadik ina zaka je ko karyawa fa ba muyi ba." Ya kewayeni. "Kina iya karyawa in kin ga dama." Ya sa kai ya fice. Na yi turus dani a tsaye. Na sake binsa kafin ya kai kofa, na ce cikin sanyin murya. "Sadik ka yi hakuri, na san na 6ata maka rai. Wallahi ba zan kara ba." Ya juyo a fusace ya ce "Ya rage naki kuma." Ya fice abinsa ya barni a tsaye. Ban san cewa hawaye na zubo min ba sai da na ga ya digo min a hannu, sannan na lura. Na koma na kwanta akan doguwar kujera nima na kasa cin komai. Haka na kwanta ina tunani har azahar tayi ban iya kulla komai ba. A daddafe nayi abinci na ma, na ajiye ina jiran ya dawo ko kafin loka a huce daga fushin da yake yi. A lokacin da ya dawo ina dakina ina sallah, dan haka banji dawowarsa ba. Da na gama na fito domin in duba ko ya dawo. Na duba dakinsa akulle yake, sai na zaci ko bai dawo ba. Na koma na zauna na kasa cin komai. Tun safe ban karya ba, na yi wani rangwam dani kamar mara lafiya. Domin komai ma ba dadinsa na ke ji ba. Can sai naji shi ya bude kofa zai fito. Na zuba ido saitin kofar. Ina ganin ya fito na ce "Sadik ashe ka dawo? Wallahi ban sani ba, ina daki ina sallah." Ko kallona ma bai 15 Amina A. Sharada yi ba. bare ya san abinda na ce. Na bishi da sauri "Sadik na gama abincin rana fa, kai na ke jira mu ci. "Bani da muradi." Wani dunkulallen bacin rai ya tsaya min a wuya. Na sunkuya a gurin ina kuka. Ya yi ficewarsa abinsa Sai da na jima ina kuka a gurin sannan na tashi. Naji sam cikina ma ya cika bana jin yuwan bare kishirwa. Na koma dakina na kwanta ina ta tunanin anya ko wannan laifin da nake ganin na yiwa Sadik shi ya janyo wannan fushi kuwa? Kai ina ga dai akwai wanì laifin na daban, domin da ace wannan ne kawai da yanzu mun shirya, duk kuwa da cewa bamu taba koda musu da shi ba bare in san irin fushin zuciyarsa Dare ya yi, na shiga wanka na shirya tsaf kamar yadda na saba in zanje gurin Sadik, na feshe jikina da turare, na sanya kayan dana san Sadik na matukar kaunar in sanyasu. Na nufi dakinsa a lokacin ba abinda ya ga cikina sai ruwan shayi, domin abinci ba zaì ciwu ba a gurina. Na tsaya a bakin kofar sa na yi ta kwankwasawa, shiru ya ki budewa. Ni kuma na fi barin gurin, sai da na kai kamar awa guda ina bugun kofar har hannuna ya fara radadi Sadik bai bude min ba. Ina nan tsaye sai gashi ya bude a fusace, ya 16 Sharrin Jinni 3 dubeni sama da kasa. Da dai kamar ya ce in shigo, to ko mai ya tuna sai kawai naga ya yi wani kicinkicin da shi, ya ce "Wai yama za'ayi ki dinga buga min kofa haka kin hanani barci? Karki kara!." Na durkusa ina cewa "Dan Allah Sadik kayi hakuri, na tuba wallahi ba zan sake ba. Sadik kayi hakuri." Idanuna hawaye sharab-sharab. Kawai Sadik sai ya maida kofarsa ya rufe, ya ce "Zancen ki ke so." Nan na kwanta ina ta kuka." Nai masa magiya ya bude min, amma ko a jikinsa. Haka na kwanta a gurin nan har gari ya waye.ban tashi ba. Da ya bude kofarsa ya ganni sai ya tsallakeni kawai ya yi gaba abinsa. Sai kamshin turaren sa ne ya bugeni. Na yi zumbur na mike ya yin da ya kai bakin kofar fita. Na bishi da guduna ina cewa "Sadik ka yafe min dan Allah. Sadik kar Allah ya kamani da laifin saba makа." Ko kallona bai yi ba ya wuce yaja kofar da karfi ya barni tsaye ina ta faman kuka. Wasa-wasa sai da muka share kwanaki uku muna haka da Sadik. Duk nabi na rame, na lallace. Sai kawai na yanke shawarar in hakura in daina kula shi nima, domin dai duk wani rarrashi da zanyi ma sa na yi, haka kuma duk wani ban hakuri nayi. To gara nima in kama kaina tunda abin hakane. 17 Amina A. Sharada Saboda haka nima sai na shiga boye kaina ba ruwana da shi, in kuma mun hadu a falo baya kulani nima bana kulashi, sai dai ya wuce nima na wuce, ko kallonsa bana yi. Hakan ne ya sa shi matukar fadawa wani sabon bakin cikin. In na fito daga dakina yana cikin falon, sai inga ya yi sauri ya dago kai ya kalleni. Ni ko sai in dauke kai abina. Haka muka yi ta yi da shi ko zai sauka. Amma ina! Sai ma abinda ma ya yi gaba. Rannan ina zuane a dakin, sai naha Sadik ya yi sauri ya banko kofa ya shigo yana huci. Ya tsareni da ido da alamar tambaya a bakinsa, amma baiyi magana ba. Nima kuma ban yi masa magana ba na kauda kai. Ya shigo cikin tsananin bacin rai ya cakumeni ya jijjigani yana cewa "Wato Hamdiyya abin da zaki dinga yi kenan ko? Dan na kyalki da halinki shi ne zaki dinga cin amanata ko?" Take naji yawun bakina ya dauke. Naji ina jawo numfashina da kyar, domin barazanar daukewa da yake yi. Da kyar na bude bakina na ce "Sadik me ka ke neman doramin.?" Y ace "Kina nufin kice karya nake? Da fa idona bai gani ba bane. Shi yasa na bishi da gudu na rasa lungun da ya shiga, wallahi da sai na sassarashi, in yaso duk abinda za'ayi sai dai 18 Sharrin Jinni 39 ayi. Kuma ai duk kece cikakkiyar munafukar da kika cuceni kika yaudareni!!". "Wai Sadik na ce maka me kake zargina da shi? Kana nufin ina kawo maka mazan banza cikin gida.?" Ya yi tsaki da karfi ya ingizani waje, ya juya abinsa. Ina ban sami damar kuka ba, domin wannan lamarin yafi gaban kuka. Na bishi da gudu har dakinsa, na afka na tsaya a gabansa. na ce "Ban fa gane abinda ka ke nufi ba........." Kyawawan marirrika guda uku da naji sun sauka akan fuskata sune suka katseni. Ya zaro belt ya fara tafkata, ina ihu da neman taimako. Sai da ya gaji da dukana sannan ya fice ya barni anan jikina duk ya yi tsami. Na mike da kyar, na nufi dakina na kwanta. Take zazzabi ya rufeni na kwanta ina ta jin jiki. A maimakon jikin Sadik ya danyi sanyi. Sai lissafinsa ma ya kara dagulewa. Ya fice a hasale ransa a bace ya dauki motarsa ya fice, ko ganin gabansa baya yi, ya dauki hanyar air port yana tsula uban gudu. Yana cikin wannan hali ne kan motar ya kwace ya saki hanya (kan titi) ya daki wata katuwar bishiya dake gefen hanya ya tintsiro. *** 19 Amina A. Sharada Ina kwance jikina duk babu dadi. Sai na dan fito falo domin in dauki magani, in na gama shan maganin sai in kwanta. Anan falon ina tunanin abinda ke faruwa a tsakanina da Sadik. Na ce a raina "Wai Sadik me yake nufi da ni ne? Ko yana zargina ne da kula wani namijin? To in ko hakane na shiga uku, ya zanyi ya gane gaskiyar bana kula kowa.?" Na yi shiru ina yunno amsar. Sai naji Alhaji na sallama. Na ce a raina "Shi kenan ta faru ta kare, wai an yiwa mai dami daya sata. Na san ma zuwa ya yi ya gayawa Alhaji. Amma ko Sadik bai kyauta ba, mai makon ya sameni ni da shi ya fuskanci gaskiya shi ne ya je ya fadawa Alhaji...?" Ina cikin wannan tunani sai ga shi ya shigo falin. Na yi masa sannu da zuwa, na tashi zan kawo masa lemo da ruwa. Sai ya ce in zauna baya bukatar komai. Na dawo na zauna na gaishe shi kaina a sunkuye. Ya ce "Wai ina Sadik ya ce za shi ne.?" Na yi shiru, domin ban san inda ya yi ba. Na ce "Wallahi bai ce min ga inda za shi ba." Ya yi tsaki, sannan ya ce "Shi kenan, tashi ki shirya, za ku je asibiti dubiya ke da Hajiya Lami." Na ce "To Alhaji ai baya nan, kar kuma ya dawo ya yi min fada in ya ga bana nan." Ya ce "Ai nine na 20 Sharrin Jinni 3 cc kije. In ya yi magana ma kicc nina zo da kaina na ce

Chapter 1 of 5