Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 4
shekaru Ashirin a duniya. Alhaji Ahmad na da tarin arziki amma bai taba haihuwa ba, ya dan yi aure aure mata kala kala har ya zamo ya fitar da rai da samun haihuwa, mutum ne mai matukar neman mata kamar wani dan akuya duk matar da ta yi masa sai ya yi kokarin wajan mallakarta, baya jin kyashin kashewa mace kudi ko nawa ne. Bai yi kauran baki ba wajen bayyanawar Lawai bukatarsa, shi kam Lawan ji ya yi kamar an tsunduma shi a aljanna saboda farin ciki, godiya ya 116 Garari Hadiza Ado Yalwa dinga yiwa Alha Ahmad kamar shine ya bukaci wani abu a wajensa, shi ma Alhaji Ahmad ya nuna masa cikin gaggawa zai yi abin a cikin sati uku kadai ya ke son Umaima ta zamo matarsa, ya daice masa zai je wajen 'yan uwansa su yi magana ba wai dai yana son ja da maganarsa ba ne sai dai ya na son samun wani abu a waje. Ya kuwa sami yanda yake domin kuwa Alhaji Ahmad dubu ashirin ya ba shi sannan ya yi masa alkawarin cewa tsintisya baya bukatar asaiwa Hansa'u ya na da komai a gidansa. Lawai bai taba hango amfanin haihuwa mata ba irin wannan lokacin ba dare ya yi amma bai iya rintsawa ba, yana tunanin abin farin ciki da yanda za a gudanar da shi sai dai duk inda ya hanga ya hango sai yaga dole sai da 117 Hadiza Ado Yalwa Garari Harira abubuwan za su tafi yanda yakamata iyaye mata su ya dace su yi irin wadannan maganganun da yayansu don haka washe gari ya yi sammako zuwa doka dan ya lallaßa Harira ta dawo dakinta su shirya yoeda bikin zai kasance, ya na zuwa kuna sai ya tarar da mutuwa yayan Harira nan fa ya zauna zaman makoki. Har sai da yamma bayan mutane sun rago ya aika aka kira masa ita suka zauna a soron gidan, bai damu da yanayin da fuskarta ke ciki ba, ya suma da yi mata gaisuwa ta amsa ashe kuma ba shi da lafiya ki ka taho baki gaya min ba, kin ga ai dana biyo ki Allah ya raba ganawarmu". Ta gyara mayafi ni bama wannan ne ya kawo ni ba, na dai zo ne na tarar" 118 Hadiza Ado Yalwa Garari Ya yi murmushi "Koma mene ne ya dace a ni me iznina kafin a fito Allah ya ji kanshi da rahama" Ta amsa da amin. Ya mike "Ni zan koma gobe idan an yi sadakar uku sai ki taho gida in ya so ranar bakwai din ba baki kudin mota ki dawo saboda yara su kadai sai su yi ta abin da su ka ga dama" Ashe ina da rana ta fada a zuciyarta ya yin da ya fito da kudi daga aljihunsa har naira dubu uku "Ga wannan ki shiga mota". Ba ta da wani zabi dole ta sa hannu ta karfa kudin domin ba ta da zabin da yafi haka, ko da ta koma gida ta kirga kudi ta yi matukar cika da mamaki rabon da Lawan ya bata irin wadannan kudade har ta manta ta san baya yi ne don bikonta ba, lallai akwai 119 Hadiza Ado Yalwa Garari wani dalili haka ta yi ta tunani cikin ranta don haka ta dokanta gari ya waye a gama komai ta taho gidan. Dukkansu suna yin sallar magariba a cikin daki, su ka ji sallamar Ummansu aikuwa suna yin sallama suka zagayaeta ita kuma fuskarta cike da murmushin ta rungume Sayyada take binsu da kallo. Ta fada musu rasuwar wanda duk suka jimanta duk da ba wani shakuwa su ka yi da shi sosai ba, tunda bakasafai take zuwa da du doka ba, in ma zata a a daren ranar Lawan ya bayyana mata duk yanda abubuwan suka faru. Abin da ya fadar mata da gaba sati uku da ya bukaci asa ranar bikin. "Amma Lawan kamar an yi gaggawa a cikin lamarin nan kuma gaggawa na daga shaidan" 120 Hadiza Ado Yalwa Garari Ya katse ta "Ni tsiyata da ke duhun kai, na gaya miki mutumin nan ba mace a gidansa yanzu haka mutuwa ta yi kin ga kuwa dole akwai bukatar ya ajiye mace a gidansa da gaggawa a matsayinsa na babban mutum kuma ma ban da abinki ai talaka ke bukatar shiri me kudi kuwa a shirye yake ko yaushe ya ke da bukatar yin abu ya kawai zai yi kawai ki gawa Umaima na yi mata miji kuma gobe ya ce zai so su yi hira Harira ta yi shiru amma zuciyarta bata gama kwanciya da maganar auren nan na gaggawa da kwadayi, ta ma shiga zargin anya kuwa Lawan ba tallan 'ya'yanta ya ki ga masu kudi ba. Aure irin wanda su za su yi komai daga karshe in da zai girbi wulakanci da kaskanci a saboda kwadayi ka dauka masa farin ciki har karshen rayuwarsa, 121 Hadiza Ado Yalwa Garari duk cikin yaranta tana jin auradda Hansa'u yarinya ee da bata da wayo ga ta da zurfin ciki kuma bata da hakuri tana da taurin kai a kan abin da bata so shi yasa take ciki da fargabar fada mata har zuwa yammacin ranar zuwan Alhaji. Sai da ta bari suna zaune duk su ukun suna ta hira abinsu sannan ta zauna a cikinsu ta yi shimfida da gabatar da abubuwan da suke ciki na damuwa da suke ciki sannan, ta sako maganar da ta ta so wadda ta ke nuna musu alkairi ce ga Hansa'u tun kafin ta karasa ta saka kai cikin goyoyinta ta na rasgar kuka fuskar mutumi kadai ta ke hangowa da ta kaicin wai ita ya ke so babansu ya fi shi kuruciya ga muni. Wai ma ga Asiya a ce ita za a urar dukkansa suka zube mata ido kukanta ya tabbatar musu da cewar bata so dole 122 Hadiza Ado Yalwa Garari Harira ta shiga lallashinta Asiya kamar ta hadiye zuciya ta mutu don bacin rai ita kan ta tsani ganin abin da zai sa. kannenta duk sai duniya tai mata zafi. Da kyar suka shawo kanta da lallami abin da tasa a ranta za ta yi komai don farin cikin Ummansu kin amincewa auren nan tamkar rugaza farin cikin Ummanta ne kamar ta tunsar da ita. Shiryen shiryen biki ya kankama a cikin shiri har da na barin gidan domin Alhaji Ahmad ya basu wani gida su zauna a ciki a cewarsu baya son 'yan uwansa su zo kawo lefe su ga wannan kazamin gidan da suke ciki, ba lawan kadai ba, hatta Hansa'u wannan barin gidan ya yi mata dadi gida ne mai dakuna cike da flour guda biyu da kichin da bandaki gida mai kyau, sun 123 Hadiza Ado Yalwa Garari tarar ya sa an shimfide musu leda da labulaye har da gado. Sabuwar duniya inji Uwani dake shafar ledar tsakar dakin. Yau ne ranar kawo kayan manyan akwatuna da set cike d akaya na gani na fada. Bayan 'yan kawo kaya sun tafi. Jama'a sun rago Umma na idar da sallar magariba,w asu mata gud abiyu suka yi sallama Umaima ta basu masauki suka zauna duk da bata gane su ba ta karbe su da fara'a sannan ta basu tabarmar da ke shimfide wadda baki suka ta shi daga kai suka zauna kallo take musu na son sanin daga ina ko su waye domin bata tuno inda ta taba ganin fuskokinsu ba, matar daya dattijuwa ce domin ko bata haifeta ba, yanayinta ya nuna ta soma manyanta. 124 Hadiza Ado Yalwa Garari Dayar kuwa yarinyar mace ce da alama amma bushewar da ta yi da ramamman jiki yasa bata fahimci wanda zai iya girmewa wani tsakaninsu ba. "Ba ki san mu ba kamar yanda mu ma ba mu sanki ba, dattijiwar ta katse mata tunani, "Eh wallahi ina fatan ke ce mahaifiyar yarinyar da Alhaji Ahmad a huta ya kawo yake neman aurenta". Gaban Harira ya yi wata irin faduwa. Ta ce "Ni ce na haifeta". Dattijuwar ta nuna yarinyar kusa da ita "Kin ga wannan ni ma 'ya ta ce, ta cikina kuma matar da Alhaji Ahmad Ahuta ya aura ya saki, shekarunta basu wuce sha takwas ba yanzu ita ce ta tara da na haifa ita 125 Hadiza Ado Yalwa Garari autata take bi, abin da ya kawo ni shine sanin darajar haihuwa domin kuw ana haifa kuma na san darajar da kamar kowace uwa à takaice dai kin ga yarinya rnan. tawa shekarunta shidda kacal a duniya Alhaji Ahmad ya aureta, bata cika shekaru biyu ba ya sake ta Labari ya yi ta zuwar mana yana dauke da cutar kanjamau, don haka muka kaita asibiti a ka yi mata gwaji take likitoci suka tabbatar dacewar ta kamu da ciwon shekaru biyu ke nan da suka wuce tana jinya duk da magungunan da ta ke karba a Asibiti, wannan ya sa na yi tattaki don fada muku gaskiya yanzu ya shafawa 'yan mata sama da biyar da ya aura masu Kanannun shekaru kamar na 'yarki". 126 Hadiza Ado Yalwa Garari sharar Yarinyar ta soma kwalla,"Wallahi son zuciya ya kai ni ga aurensa, ga shi yanzu ya cuce ni, labarin ina da cuta ya baza gari,kuma ku yi bincike sosai, za ku ji a bakin jama'a yawan aure -aurensa ya sa an gane don Allah mama ki cici rayuwar 'yarki." Harira ta sauke ajiyar zuciya daga suman zaunen da ta yi, zuciyarta kuma ta shiga rarraba mata maganganu tsakanin gaskiya ne ko karya. Ta dai yi musu godiya daga nan suka bar gida ta zabga tagumi yanda ta ji labarin auri-sakinsa a bakin Lawal da yadda ya ke son a yi komai cikin gaggawa da yadda ya ke ta nanata mata sai son tushe kuma daga surutun mutane lokacin da ya zo gaishe ta. Duk sun nuna mata akwai abin da yake son boyewa,in kuwa ma ga shi dama yarinyar sam ba ta so ita da kanta hankalinta ya kasa kwanciya da 127 Hadiza Ado Yalwa Garari al'amarin,lallai ya kamata ta yi bincike sosai don tabbatar da gaskiya. Shin idan ta binciki gaskiyar Lawal zai yarda da maganarta a fasa auren. In kuma ya yarda da ina su ke da kudin da za su biya shi wahalar da yayi ta neman aure, ciki har da zamansa a wannan ni'imataccen gida. Shin haka za ta aura wa 'yarta me cutar kanjamau, saboda yana da kudi? Shin yaya aka yi Asiya ta samu cikin jaririn hannunta? In gararin rayuwa zai kai su ? duk amsoshin tambayoyin na gaba mu hadu a cikin littafi GARARI na 2 wanda suka fito tare da na dayan nemi naka ba jira. Yanzu labarin ya soma. Daga mai debe muku kewa Khadija Ado Yalwa(Khadija Adamu Shitu) don yabo ko ba da 'shawara 09065291030 sai na ji dga gare ku. 128 IBB BOOKSHOP NOJ, SABON GARI MARKETKANO 07037690966 LITATTAFAN MARUBUCIYAR 1. KOFAR RAGO 2. KARSHEN KIYAYYA 3.GARARI 1-4 4. AUREN DANGI 5.AUREN MATSALA 6. AUREN GATА 7. DA WALAKIN... 8. BAGIDAJIYA 9. BAKUWAR FUSKA 10. KARAR KWANA 11.BA HUJJA 12. DA BAMBANCI 13. DA RABON WANI 14. DINKIN KWALBA 15. BAKON AL'AMARI Graphics And Computer Services 08099685635 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 4 of 4