Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 4
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels IBB PUBLISHERS GARARIHADIZA ADAMU SHITU (Matar Muhd.Nuhu Namarwa) Hadiza Ado Yalwa GARARI 1 Garari maima ta fito cikin Utashin hankali da tsananin 6acin rai, sauri sauri take tafiya har ta iske Asiya da jaririnta a hannun wadda dama tafiyar tata kamar ta me sanda takeyinta. Shi yasa Umaima bata wahala ba wajan tadda ta. Shesshekar kukanta kawai ka ke iya ji cikin sanyi asubar "Yaya yaya Asiya". 'Umaima ta kirata cikin dakusasshiyar murya da ta doshe sabodakuka. Ta na jin muryar ta gane ta kanwarta Umaima ce, amma sai ta kasa juyowa ta hada ido da kanwar tata inda wanda zai fahimce ta bai 4 Hadiza Ado Yalwa Garari wuce kannen nata ba, amma sai ga shi a yau tana jin kunyar hada ido da Kanwarta Umaima tana matukar jin kunyar kannenta da abin da ta aikata ina ga sauran mutanen gari da wanne ido zata kalle su yayin da gari ya waye mata da jaririn shege a hannunta, abin kunya ga al'adarta babban zunibi ga addininta. Ta ci gaba da sharar kwalla Umaima ta ci gaba da binta tana sharar tata kwalla tafiya suke yi ba mai wa wani magana, ba kuma wanda ya san takamaimai in da za su dosa a tsakaninsu. Abin da yafi tsayawa a kai Asiya abin da ta aikata ba laifinta ba ne amma babu yanda za ta yi ta kare kanta, duk duniya ta san ba wanda zai 5 Hadiza Ado Yalwa Garari gamsu da cewar ba laifinta ba ne, ba itace a bar kyamarba ba mugun halinta ba ne, ba rainuwa ko son jin dadi, ko shi wanda ya aikata mata bata hanglaifinsa a cikin faruwar wannan babban al'amari ba,, to wa za a dorawa laifin? Ta dubi kanwarta ta wadda duk in da ta sa kafa nan take mayarwa da alama ba da niyar komawa ashirya take ta bita duk in da ta nufa. Tana son ta yi maganā amma wani abu mai daci ya nauyaya bakinta. Ta sake dauke kanta zuwa daya gefanta iska mai sanyi na ratsa dukkan kofafin jikinta ta sake rungume jaririn hannunta. 6 Hadiza Ado Yalwa Garari ..Ta dinga jin kamar daga ita sai Umaima dake biye da ita sai kuma jaririn hannunta suka rage a fadin duniya iskar da sanyin asuba na sake horowa ta sauke ajiyar zuciya tana kallon hanyar da zata sa da su da titi. Tunaninta ya lola can baya abin da yafi tsaya a ranta. ** Ga Umma ga umma yara biyu suka shigo da gudu suna fada Aisya dake kwance a tsakar daki ta mike da sauri ta fito. ta shigo gidan da sallama cikin sanyin muryar yanda ba me iya jin sautin muryar tata sai dai la66anta da suke motsa. Uwani dake tankade a tsakar gidan ta daga kai ta kai dubanta 7 Hadiza Ado Yalwa Garari bakin kofar tana murmushi dai dai lokacin da Harira ke cire mayafinta. "Sannu kunsha hanya" in ji Uwani ganin yanayinta kadai ya nuna halin gajiyar da ta yi Asiya dake tsaye ta ce "Umma Sannu da zuwa?" Bata amsa ba saboda wani irin jiri da yake dibarta ta zube a kofar dakin. Asiya ta juya da sauri ta debo ruwa a randa ta mika mata ba musu ta karba ta shanye tana sauke ajiyar zuciya ko bata fada ba yunwa da gajiya sun rufar mata. Zaman da ta yi da ruwan da ta sha ya saukar mata da 'yar nutsuwa ta dubi Uwani "Tun safe da na fita nake gararanba”. 8 Hadiza Ado Yalwa Garari 'Ai ko ba ki baďa ba ice ko an dace?" "An dace, mun samu daki daya a gangaren 'yan garuwa". 'Kai madalla" Asiva dake jinsu sai ta washe bakin tana murmushi, yanda Asiya ta karanci fuskar ta san akwai wata damuwar shi yasa bata fadada fara'arta ba, burinta su kebe da mahaifiyarta ta ji mene ne damuwar, tana alwala ta ce "Ina su Umaima,?" Asiya ta ce "Sun je gidansu Rabi'a". Tana cikin maganar sai ga Umaima ta shigo tare da karamar kanwarsu sayya sayya ta tafi wajan Umma da gudu tana cewa "Mun je gidansu Aunti Rabi'a ta ba ni" 9 Hadiza Ado Yalwa Garari Masarar da take ci ta mika mata. Na ga Umma ta shigo An dace kuwa?" In ji Umaima. "An dace Asiya ta bata amsa a takaice. Hamdala Umaima ta yi "Wallahi na gaji da zaman gidan nan musamman idan aka yi ruwa babu mai rintsawa a cikinmu" Asiya ta ja ajiyar zuciya "ni ina ga ba mu ma taba zaman ukuba irin wannan ba a hakan me kin ga tausaya mana aka yi ita kanta uwani fa a takure take kawai dai babu yanda ta iya ne ga zafi, musamman in an yi ruwa bata da in da za ta yi girkinta fa sai a daki”. 10 Hadiza Ado Yalwa Garari Uhm "Yau da gobe sai Allah ni dai na ji dadi da a ka samu dakin nan. Umaima ta sake maimaitawa "Amma fa da sauran rina a kaba tunda ba a gama biyan kudin ba akwai ragowar kuma Umma ba ta da su". Nan da nan fara'ar da Umaima take yi ta dauki "Baban fa har yau bai zo ba" "Bai zo ba?" Asiya ta bata amsa a takaice. Shiru ya gilma na tsawon lokaci kowacce da abinda take sakawa a zuciyarta har Hansa'u ta yi sallama dukkansu babu ji ta ba ta sake maimaitawa sannan Umaima ta dago tana amsawa Hansa'u ta dubi 11 Hadiza Ado Yalwa Garari fuskokinsu da gani akwai damuwa gabanta ne ta ji ya fadi amma bata iya tambayarsu ba ta dai ce "Umma ta dawo ne?" "Еh". Asiya ta amsa mata "Tun yaushe, bata jima da dawowa ba ta shiga ciki. Da sauri fargabarta kar a ce yau ma basu samu hayar gidan ba, tana shiga ta hange Ummansu na gyangyadi a kan buhun da take sallah don haka ta juya wajan 'yan uwanta. Yara marasa mafadi ku kadai kun damu mutane da guje gujen banza da na wofi. Muryar mahaifinsu ce ta karade soron gidan su Ahmad da Mahmud suka shigo da gudu ko wanne ya 12 Hadiza Ado Yalwa Garar rakuße jikin koafar soron jikinsu ya yi budu-budu kamar wadanda aka tono daga rami, sai raba idanu suke yi kan yayyensu dake soron cikin tsananin tsoro da firgitar fadan da mahaifinsu ke yi. Ko sallama bai samu damar yi ba fada yake yi kamar ya ari baki, yana kwalawa Hairara kira kamar ba cikin dakin zai shiga ba. Tana cikin gyangyadinta wannan sababin na shi ya farkar da ita kafin ta yunkura ta ta shi ya karasa shigowa ya tsaya dai dai kanta. "Barci ma ki ke yi? kowa ya yi abin da ya ga dama, kowacce uwa na kokarin koyawa 'ya'yanta tarbiya ke kina kwance kina barci kin bar duniya su wancan dan banza Aminu yana can 13 Hadiza Ado Yalwa Garari ramin da 'yan iskan abokansa suna shaye shaye su kuma wadannan 'yan kananun na kan yashi mutane suna musu ta adi, wadan nan kuma da suka koshi da rashin tarbiyar har na shigo ban samu wadda ta iya daga baki ta gaishe ni ko yi min sannu da zuwa ba, yanda ki ka raina ni haka kika koyar da su su raina ni" "Haba Lawan ai dukkansu ka na da ikon yi musu fada kai ma a matsayinka na mahaifinsu, ba sai ni kadai ba”. "Ka da ki zage ni Harira ki iya bakinki, kin ji ko”. Ya ajiye bakar ledar da ya shigo da ita yana gunagunin. 'ya'ya mata Gare ki abinda kake yi min shi za su je suna yiwa 14 Hadiza Ado Yalwа Garari mazajensu ba namijin da zai iya zama dasu". Takaici ya hana ta sake yi masa maganar har ya fita. A soro dukkaninsu suna iya jiyo maganganun da yake basu kadai ba duk ma wanda yake cikin gidan yana iya ji. Ya zo wucewa kamar kobubuwa Umaimace ta iya cewa "Baba a dawo lafiya". Ko kallo bata ishe shi ba ya fita. Gaba dayansu suka nufi dakin da Umma take ciki ta hada kanta da gwiwa kuka take mai sautin ban tausayi. Su duka suka duruksa a gabanta Umaima da Asiya take su ma na su idanu ya fara zubar da kwalla ban da Hansa'u. Ita dai ta hada rai ne kamar 15 Hadiza Ado Yalwa Garari bata taba dariya ba ko magana bata iya yi muryar Umaima na rawa ta cе. "Umma dan Allah ki yi hakuri mu kukan nan naki muka fi tsana". Umma ta dago kai idanuwanta cike da kwalla cikin muryar kuka "Kuntsani kukan nawa kuke jamin magana". Su duka suka kalli juna cike da mamakin wacce magana kuma suka ja mata. "Yanzu ban da rashin mutumci ace mahaifinku ya shigo kun kasa ko da gaishe shi, in ba son kuja min magana ba me zai sa ku yi haka so kuke yi a dinga zagina a gari ana cewa duka 'ya'yana basu da tarbiyya kun min adalci kenan ta sake fashewa da kuka." 16 Hadiza Ado Yalwa Gararf Asiya ce cikin raunin tata muryar ta ce "Ki yi hakuri Umma ba nufinmu kenan ba wallahi ya shigo yana fada ne shine duka muka ji tsoron yi masa magana amma ki yi hakuri ba za mu sake ba" "Ku ta shi ku ba ni waje" Ta fada akagauce ba wadda ta iya yunkurin ta shi ganin har yanzu Ummansu kuka take yi "Ku ta shi na ce Ta sake maimaita musu. Umaima ce ta ce "To Umma kin yafe mana Ba wannan ke cin ranta ba tana dai so ne kawai ta nuna musu kuskurensu duk abin da ubansu yake yi mahaifinsu ne ba ta son Allah ya kama su da rashin yi masa biyayya. 17 Hadiza Ado Yalwa Garari Kalaman Umaima na yanzu ya dada karyar da zuciyarta hade da godiyar Allah daya bata su a matsayin yaya musu biyayya. Ta dube su "Dukkansu na yafe muku Allah ya yi muka albarka ya inganta rayuwarku". Cikin sauri suka amsa da Amin Ummanmu. Asiya ta yi saurin amsawa ta goge idanuwanta da bayan hannunta, duk suka mike cikin sayin jiki suka bar Sayyada da ke gefanta tana sharar barcinta da guntuwar masararta a hannun. Komawa ta yi kan buhuta ta kwanta wannan karon babu alamun bacci a idonta sai kuna da radadinn da zuciyartą take yi ta dora hannu a saman fuskarta tunanin alamuran 18 Hadiza Ado Yalwa Carart bayan suka ci gaba da kai komo cikin zuciyarta Hamisu yayan lawan shi ne mazaunin cikin garin Kano, unguwar Yakasai Usulin dalilin zamansa a cikin kano almajiranci aka kawo shi ya yi karatu sosai daga karshe ya soma taba 'yan sana'o'i Allah ya sa mishi albarka a sana'ar sai da kayan miya yana da babban teburi dinsa na siyar da danyan kayan miya wani lokacin ma har da busassu da sanar'a ya yi aure 'yar nan unguwar ce Habiba. Ganin ayyukan na yi masa yawa kuma Lawan kaninsa ya na zaune a kauye ba abin da yake yi yasa ya dauko shi ya ci gaba da taya shi 19 Hadiza Ado Yalwa Garari harkokin sana'ar shi kuma ya sa shi a makarantar Islamiya da Boko tun kafin lawan ya baro kauyen sun hadп da Harira a lokacin ya na da shekaru goma sha takwas da Haihuwa ita kuma bata fi shekaru sha biyu zuwa sha uku ba, Lawan da Harira suna matukar kaunar junansu, ya zamo dukkan kauyen ba wanda bai san wannań soyayya ba, ta kasance marainiya da ba ta da uwa da uba tun tana wata bakwai mahaifinta ya rasu, aifiyarta ita ce ta shayar tana da ckara biyu, mahaifiyarta ta rasu wanta ya ci gaba da rikonta. Dawowar Lawan birni bai sa ya manta da Harira ba domin duk wani marin neman aurenta an ci gaba da yi Hamisu kuma shine ya dauki dawainiyar yin komai tun daga karatu da neman auren 20 Hadiza Ado Yalwa Garari lawan ci da shansa da suttura duk ya na masa. Shi ma kuma yana kokarin taimakon 'ya'yansa da matarsa wadda ya ke cewa Adda har yau lokacin Allah bai bawa Hamisu Haihuwa ba shi yasa yake jilawan da kuma kani a ransa. Abu daya yake damun Hamisu da Lawan shi ne shigewa masu kudin unguwar, duk abokansa masu kudi ne ya ke harka da su ga shi da karya da son nuna shi ma fa wani ne, Hamisi yasha nuna masa illar wannan dabi'a amma ya gagara dainawa. Kodayaushe cikin kawowa Hamisu bukato yake yi shi kuma baya iya hana shi kudi sai dai yana yawan yi masa nasiha daga karshe da ya ga ba ya jin nasiya kawai sai ya yi shawarar 21 Hadiza Ado Yalwa Garari aurensu da Harira Yana ganin idan ya ajiye iyali zai yi zuciyar neman na kai da rage buri. Wata bakwai aka saka rana dakin da yake kusa da na shi yasa aka fete shi tsaf bayan an gama biki amarya ta tare a cikinsa, komai na gidan Hamisu ne ke yi yawan abokai wajan lawan abin sai Kara gaba da ya yi idan a hanya ka gan shi za ka yi zaton dan wani hamshakin mai kudi ne a yanzu har mota lawan ya iya yana kumawa hawa ta abokansa sosai ya kan yi musu rakiya duk in da za su. Yamma na yi ya ta shi daga siyar da kayan miya zai dawo gida ya dau wanka a shiga gari a dole yake ma zaman siyar da kayan miyar 22 Hadiza Ado Yalwa Garari domin idan bai zauna ba bayan da za a yi ya dan samu kudin kashewa. Harisa hankalinta a kwance saboda bar a shi ci bare na sha sam yawon maigidanta ma bai cika damunta ba saboda kodayaushe tana wajan Habiba idan ya zauna ma a gida gwaliyarsa ke 6ata ranta komai ta yi sai ya nuna mata ta cika kauyanci bata iya ba ko Habiba da take haifaffiyar birni ba ta gwale ta kamar yanda yake yi. Kwanci ta shi watan Harira bakwai sai gata da karamin cikin wata hudu wanda ita kanta Harira bata san da shi ba, sai da ya bayyana kansa, ta yi wani irin haske fatarta ta muje ta yi wata irin cika daga kasa duk da dama tana da dirin jiki. Ga ta da shegen 23 Hadiza Ado Yalwa Garari kwadayi sabanin da da ba ruwanta komai ci take yi. Habiba ce ta gano nan da nan ta fadawa malam Hamisu farin ciki a wajensa abin ba a magana. Haka su ka yi ta yi ta kula da Harira har Allah ya sauke ta lafiya ta samu da namiji. Lawan ya so a sama masa sunan Hamisa amma sai ya yi dariya ya ce sai dai a gaba, amma wannan dai sunan mahaifinsu z a asaka masa Mustafha. Haka kuwa a ka yi Mustafha ya sha gata kulawa a tsakanin iyayen nasa Habiba da Hamisu,. Suna kiransa da Dan baba watan dan Baba goma a ka samu cikin Asiya bai sha wahala ba saboda dama 24 Hadiza Ado Yalwa Garari shan mama bai dame shi ba, ga shi yana gudunsa ko ina. Asiya na da wata uku wata rana ta ame musu bakar rana da la'asar aka shigo musu da Hamisu a galabaice yana ta kwara a mai, Lawan ya na can wajen abokansa bai dawowa sai wajan tara na dare yana zuwa ya ga yanda jikin yayansa ya ke ya samo mota sai asibiti nan aka ba su kwanciya saboda yagalaibata har ya suma fita daga hayyacinsa, kafin wayewar gari ya ce ga garinku Hamisu Allah ya yi masa cikawa. Ba karamin dokan Lawan mutuwar Hamsiu ta yi ba, sai bayan an yi arba in Habiba ta kira shi ta yi masa nasiha sosai sannan ta dauko jarin kayan miyar da su kadai ne 25 Hadiza Ado Yalwa Garari Hamisu ya mallaka ta ce "Ga shi Lawan ka ci gaba da kasuwancin nan kamar yanda ka saba saboda ka samu ka kula da iyalinka kullum Malam zancensa ke nan na kamai da hankali kan iyainka in mu ne yau watarana ba mu ba ne. Ashe malam ba zai tsahon rai ba ta soma goge kwalla ta na kuka yana yi da haka yakarbi kudin yana godiya. Ita kam ta hada yan komatsanta ta koma ga iyayenta tun da babu da bare jika a tsakaninsu. Lawan ya maida hankali ga sana'ar yana kuma samun rufin asiri sai dai burinsa ya dinga kara yawaita yana daukarwa kansa abin da yafi karfinsa. 26 Hadiza Ado Yalwa Garari Sam bai damu da iyalansa ba, duk abin da ya samu a harkar karya da abokai kawai suke karewa. Rayuwa ta yi wa Harira kunci, daga ita har yaranta, Lawan bai damu da su ba, balle sauran al'amura na yau da kullum. Harira ta yi rama, ta yi baki, ga karamin ciki Harira. fada hantara da kyara a wajen Lawan sai abin da ya yi gaba, domin babu mai tsawata masa yanzu ma ji yake ya fi karfin zama da Hansa'u saboda yadda 'yan matan birni ke matukar son shi, shi ma yake kasha musu kudi,kamar bai san zafin neman suba. Abin na dada zuga shi,da sannu ya kwashe 'yan kudadensa da yake Tarawa ya sayi sabuwar motar hawa. Al'amura suka kuntata wajen Harira, ba ta da damar ta fada masa gaskiya da abin ya ishe ta,sai ta kwashe yaranta ta tafi kauye wajen yayanta. Ta shafe kimanin watanni biyu, Lawan bai zo ba,dole ta sa yayanta ya je wajen kanin mahaifinsa ya fada masa,idan ya saki auren Harira ne ya sani. Hankalinsa ya tashi sosai,ya ba wa yayan Harira hakuri, sannan ya tashi da kansa ya je har wajen Lawan yayi masa fada sosai,ya kuma nemi lalle ya zo bikon Harira da kansa. Bayan ya gama cinikinsa na yamma suka tafi tare da karya da gaskiya Lawan ya tsara, amma ba 27 Hadiza Ado Yalwa Garari wanda ya goyi bayansa,saboda su ma sun fara ganin halin Lawan na rashin daukansu da daraja. Ba kamar dan uwansa Hamisu ba,nauyi ma yake ji ya kalle su a wajen wadansu, shi ya sa ko zuwa digansu ba sa son yi saboda yadda yake nuna musu halin ko-in-kula da nuna rashin jin dadin zuwansu Kiri-Kiri. Sun dai yi masa nasiha, ya yi kamar ya ji, saboda shi da kansa ya ji jiki a rashin Harira a kusa da shi. Yayanta yayi mata nasiha sosai ya kuma ba ta kudi da kayan amfanin gona masu yawa, matarsa ta hada mata su Kuka, Daddawa, Kubewa suka dawo. Da farko kamar da gaske Lawan ya dinga kulawa da su amma ko wata biyu ba a yi ba ya watsar. Ba ma ya dawowa cikin gidan,sai ya raba dare, haka da Assuba yake fita sarin kayan miya. Zara ba ta barin dami, tuni jarin kayan miyar ya karye, ya soma haya da motar da ya saya. Nan ma ba a jima ba ya siyar da motar haka kudin suka lalace. Lawan rayuwar manyan masu kudi ya dora kansa a kai,ko hularsa da agogon hannunsa sun isa jarin wani mai karamin karfin. Bayan haihuwar Hansa'u Umaira ta ga lamari Lawan ba na kare ba ne, hatsin da yayanta ya aiko mata da shi na gonakinta na gado, ta siyar da buhu daya jari ta ja jarin basassun kayan miya,dayan kuma ta soma sayar da gasara. 28 Hadiza Ado Yalwa Garari Nan da nan ta samu saukin al'amura ta shiga kula da kanta da 'ya'yanta ba ji ba ga ni. Har ta haifi Umaima matsalar da tafi damun Harira tun wancan lokacin har zuwa yanzu bai wuce yawon haya ba, saboda dai lawan tun bayan rasuwar Hamisu biyan kudin hayar gidan ma ya gagare shi saboda dama can Hamisu ne yake biya masa wannan ya zama dalilin da yasa a ka tashe su, daga gidan ke nan ya zama dalilin da yasa aka tashe su daga gidan ke nan bayan barinsu gidan zuwa yanzu sun zauna, a agidajen da ban daban sama da kusan goma sha daya, domin wani gidan ma basa rufa shekara saboda basa iya biyan kudin shekara sai dai naw ata shida shi ma idan watanni ya 29 Hadiza Ado Yalwa Garari cika basa iya biyan wani sai dai a tashe su. Jarin kayan miyan lawan tuni ya dade da rushewa har gonar Harira ta gado ta matsawa wanta sai da ya ba da gonarta aka siyar kusan har fushi ya yi da ita mai tsananin saboda siyar da gonar da ta yi ko watanni shida kudin basu yi a hannun Lawan ba ya cinye su tsaf. Yawan cudanya da yara marasa tarbiya Dan Baba yake yi shine ya gurbata rayuwarsa tun yana dan shekara goma sha uku ya soma shaye shaye hankalin Harira ya yi matukar ta shi amma babu yanda ta iya saboda daki daya suke iya kama haya, da 'yammantan yayanta dole shi sai dai ta nemi alfarmar kwananshi a shagon 30 Hadiza Ado Yalwa Garari makota ko gidajen abokan arziki da haka tarbiyarsa ta gurbata a yanzu haka sai ta shafe wata guda ma bata sa shi a idonta ba, irin ma ta ganshi gani ne na bakin ciki da takaici saboda kullum yana cikin maye. Bola ta zame masa gida da sunan sana'ar jari Bola yake yi baya iya tsinanawa kansa komai kayan maye ne abokin rayuwarsa. Wannan rayuwar ta dan Baba ita ce ta tsorata da ita wajan dagewa a akan karatun sauran yara da anta ta saka su a makaranta boko da islamiya duk da yanayin rayuwar da suke ciki baya barinsu zuwa makaranta kullum kamar sauran yara amma suna cikin dalibai kuma suna maida hankali 'yan mata yaran sun zame mata sanyin 31 Hadiza Ado Yalwa Garari idaniya suna matukar yi mata biyayya da tausayin da kaunar. junansu ta tsaya tsayin daka wajan kula da tarbiyarsu daga makaranta sai sana'arsu suna da juriyar da jarumta. Suna tsara komansu ta yanda zai yi dai da da rayuwarsu. Mutum biyu ne ke fashin makaranta na kwana biyu saboda suyar awara da ta yi kwana biyu tana zuwa sannan wata ta zana kwana biyu da haka sukan kare satin karatunsu basa zuwa makarantar yamma sai ta magariba da ta dare saboda aikin awarar yamma. Bakaramar tangarda suke samu ba saboda canje canjen wajan zama wani lokacin a wannan dalili sai jarin 32 Hadiza Ado Yalwa Garari ya kare tas sun yi zaman neman sabo sannan su dora. Umaima ce ta iya kitso sosai a cikinsu yara na zuwa ta na yi musu ko ta je har gida ta dan yiwa matan aure ta na samu sosai wani lokacin ma d kudin kitson suke ta da jari. Sun so zama sosai a gidan da suka baro saboda sana'arsu ta bunkasa sosai a gidan har suka samu faragar su ma tara kudin haya. Sai dai kudin bai cika ba har lokacin karbar kudin ya yi dama suna da labarin rashin mutumcin mai gidan don haka Ummansu ta je da kanta ta kai masa rabin kudin ta ba shi hakuri a kan za a ciko kamar gaske ya nuna mata ba koma da kudinta idan ta ciko ta kawo masa. Ta ji dadin hakan ta yi 33 Hadiza Ado Yalwa Garari ta yi masa godiya yanda ta ke tsammaninsa ba ta taba tunanin sauki haka daga gare shi ba, amma me ta na komawa gida ta tarar da ya datsawa dakin wani katon kwado gaba daya yaranta na tsakar gida ta rasa in da za ta saka ranta dan bakin ciki da takaici daga karshe dai ta kira me yanke dan mukulli ya yanke suka shiga. Washe gari kuwa sammako ya yi da manyan mutane suka fitar musu da kaya titi. Lawan yana gidan a lokacin ya yi ta ba shi hakuri bai saurare shi ba, sannan ya ce da Harira su tsaya anan yana zuwa, ya tafi Lawan bai dawo ba har rana ta tarar da su sai asoron makotansu suka zauna ganin yanda garin ya yi bakikkirin wani 34 Hadiza Ado Yalwa Garari gangamemen hadari na tasowa ya sake ta da hankalinsu ta soma kaiwa da komawa a cikin unguwar ga yara sun yayyame kayan sunata tsallae tsallaensu a kai, a nan ne suka hadu da Uwani wadda sun taba zaman haya da ita a wani gida danta a yanzu ya gina mata gida mai dakuna biyu da kichin da bandaki, ita ce ta tausaya wa Harira ta kwashe kayan kichin dinta ta hada a daki daya suka zauna a kichin din da yake ya na da dan girma makota kuma suka yi mata alfarmar ajiye kayanta a soron gidan su kafin su samuw anda za su zauna. Komai da sauri suka yi shi saboda ruwa ya soma sakkowa sun haďu a cikin dakin da aka basu ruwa ya tsoge sai dai babuw anda ya samu 35 Hadiza Ado Yalwa Garari zama c ikinsu saboda yan da ruwa ke shigowa dakin cikin ta jikin kofa gara shi wadatar gurin zaman a hakan sun cika da godiyar Allah saboda ruwan bai sauka a kansu da kayansu ba. Lawan ba shi ya shiga in da suke ba sai washe gari ya yiwa uwani godiya sosai ya zauna har ya ci abinci ya na ta nunawa Harira shi ma ajiyan yana can ne ya na nema musu in da zasu zauna ruwan jiyan nan ma a kansa ya kare. Kwanan gida ba zai yiwu a gare shi ba sai dai lokaci zuwa lokaci ya shigo ya

Chapter 1 of 4