Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 4
na ma lura bakin halinki ya hanaki sabo da matan gidan". Ta inda ya ke shiga ba ta nan yake fita ba. tana jinsa ya na ta miota a haka har bacci ya dauke shi. ita kam bata rintsa ba a haka har a ka yi sallar asuba. ** Da sanyin safiya dai-daikun mutane ka ke ga ni Umaima cikin kayan makaranta, A nutse suke tafiyarsu saboda tabbacinsu na cewar sammakon da suke daka na iya kaisu mkaranta ba tare da sun makara ba, duk kuwa. 77 Hadiza Ado Yalwa Garari Nisan da ke tsakaninsu da makaranta. 1 Asiya na tsokanar Umaima da ta zama sabuwar dalibar ajin farko na babbar Secondary (SS1) rawar kannan na ki ke damu na Umaima, satin nan sam kin hana ti baccin safe da asuba, kin fara shirin makaranta ni na rasa me yake dibanki ko dokin sabon kayanne oho". Ta dubi farin hijab din Umaima da yake daukar ido ga gurgar da yasha, su ka yi dariya gaba daya. Umaima ta ce "Ba za ki gane ba ne yaya shigata ss 1 din nan kuma ajin da na fi so (Science class), yanda na fitar da rai da karatun nan kuma na same shi ai dole... 78 Garari Hadiza Ado Yalwa Ta kasa karasa abin da take fada idanuwanta na kan Hijabdinta da wani mai mota ya watsa wa jikakkiyar jar kasa. Allah ya isa ba za mu taba taba yafewa ba, mugu, yanda ka bakanta mana ka cutar da mu a sanyin safiyar nan Allah ya hada ka da mummunan bakin ciki, Asiya ke nan da take ta jerowa me motar manyan alkaba'i wadanda ita ma bata san ta na fadar su ba saboda Gacin rai. Umaima dai kasa magana ta yi saboda takaici sai ga hawaye na silalowa daga idanunta, jar kasa ce ta yi face face a jikin farin jijab din, ganin hawaye a idon Umaima ya sake nunka bacin rai a wajan Asiya ta dago kai don ta nuna masa wata mai 79 Hadiza Ado Yalwa Garari dacin, ga mamakinta sai ga ni ta yi yana ja da haya, "Wallahi bazan saurara maka ba kama dawo din”. Ta zubawa motar ido har ya dawo dai dai in da suke kakin dake jikinsa kadai ya isa ya yi mata kwarjini, bare shi kansa, kwarijin da ta hanga a idonsa bai sanyaya jikintaba, shirye ta ke ta gaya masa koma menene in dai shi ma zai ji zafi a ransa. Ya sauke ajiyar zuciya ya jima bai ga wanda ya dubi tsabar idonsa ya yi masa irin wannan kallon ba bare wannan muguwar addu'ar da bai taba cin karo da ita a rayuwa ba, wannan dalili ya sa shi juyawa kalma daya ya yi niyar fada musu ku yi hakuri, to 80 Hadiza Ado Yalwa Garari amma yanayin kallon da take masa cike da tsiwa da tsana. "Ke ashe ba ma ke na bata ba kike wa mutane tsiwa da surutu kamar tabaбbiya". Cikin dakiyar murya ta cе "Gwara ka 6ata ni da ka 6ata Umaima a sabon Hijab dinta dubi abin da kai mata, ita kam Umaima tunda ta ganshi kwarjininsa ya firgita ta wannan ko dan sandane babbane, ko custom ne ko dai wane ne me damarar me kuma babban matsayi, ga yanayinsa da ya nuna hutu zalla ne a jikinsa, tun tsayawarsa wani kamshi da yake ta shi, gaba daya kwarjininsa yasa tsoro ya kama Umaima ta ja hannun Asiya da take ta zazzaga masa 81 Hadiza Ado Yalwa Garari masifa "Dubi abin da kai mata haba malam". "Kyale shi Yaya Asiya kin san masu mukami a kasar nan ba adalci gare su ba, kada ya samu abin da ba zamu iya fitar da kanmu ba". "Ko ma me zai mana sai dai ya yi mana amma ba zai yiwu ya yi mana laifi mu ja baki mu yi shiru ba, saboda muna tsoron sharrin da zai mana agaba". Umaima ta share kwalla da bayan hannunta don Allah ki yi shiru yaya kada hankalin mutane ya koma kanmu wallahi duk gaskiyar da muke da ita şhi za a bawa hakuri, mu kuma duk abin da zai faďa a kan mu dole a yarda. 82 Hadiza Ado Yalwa Garari Asiya ta yi shiru ita ma share kwallar take, har lokacin yana tsaye ya kuma tsira musu ido yana kuma juyo maganmganun Umaima da take yi kamar rada, ya dinga jin wani irin yanayi na shigarsa wanda yasa ya gaza kowane irin tunani komansa ya tsaya cak!, kalaman yaran kadai ke yawo a tsakiyar kansa, sai zuciyarsa dake tsananta da ci, yanayin kasala kuma na hana shi yin wani katabus. Da nannauyan jiki ya soma tafiya cikin motarsa har zuwa gidansa da ke kan titin Airport road cikin rukunin gidajen 'yansanda yana shiga harabar gidan ya hango yaransa a shirye tsaf suna ta tsalle tsallensu tana taku kadan kamar wadda jiri ke dibarta ya fito daga mota da sauri ya 83 Hadiza Ado Yalwa Garari taro ta hade da fadin "Subhanallah kamar dole Jidda ba ki da lafiya dole ne fitar. Amir Abba". Ya kwalawa yaransa kira "Ku zo 99 nan. Ya rungume ta a hankali ya rada mata "Is ok." Za ta yi magana ya dora danyatsanshi a a kan leßanta "Ki yi shiru na ce miki mu shiga ciki ko". Ba ta musa masa ba amman sai ga hawaye a fuskarta, bai hana su zuba ba saboda ya san yanda take ji a yanzu ko da kukan bakin ciki har da nå farin cikin don bata taba tsammanin dawowarsa yanzu ba, basu tsaya ko ina ba sai akan gadon baccinta. Da kanshi ya janye mayafin da ta yi lullubi da shi ya gyara mata 84 Hadiza Ado Yalwa Garari filo ya kwantar da ita, kamar dama kwanciyar take bukata ta takure ta rukunkume pillow hannunta daya a kan goshinta. "Ciwon kan da yake addabarta bai saurara mata ba, su Abba suka shigo suna cewa "Mama ki zo mu je unguwar" Ya dora hannunsa kan lebansa alamar su yi shiru sannan ya nuna musu kofar fita, suka fita daga dakin. Ya riko hannunta "Yunwa ko?" Ba ta ba shi amsa ba, sai ido da ta bi shi da shi na tsananin mamaki wai Muktar ne wannan ko mafarki nake. Ya san abin da ke damunta don haka bai jira amsarta ba ya mike hade da cewa "Ina zuwa". 85 Hadiza Ado Yalwa Garari Yana fitowa ya hadu da yaran sun nutsu a kan kujera suna murza ido alamun kuka suke ya duruksa а gabansu ya rike hannun Abba, wanda shine babba zai kai shekaru shida, wanda shine Babba Umar shine ainihin sunansa saboda ya ci sunan mahaifinsa yasa ake kiransa da Abba, sai Amir Kaninsa dake shekararsa uku wanda ya ci sunan kawunsa Usman. Ya ce "Haba Abbana kai ne babba kuma kasa. kanninka a gaba kuna kuka" Ya mike "Ina ku ke son zuwa?" Da sauri suka hada baki "Gidan gwaggo". "To na ji kirawo min driver, ya kai ku". 86 Hadiza Ado Yalwa Garari Nan da nan suka fita suna tsalle. Ya bi bayansu yana murmushi Bilya direba ya kara so suna rike da shi Abdul ya mika masa mukullin bude store. "A debo shinkafa buhu da mai roba daya ka shigo nan a daukiw asu kayan a kai gidan Gwaggo tare da yara nan. Bilya ya sara masa "To ranka ya dade". Sannan ya juya shi kuma ya koma ciki dauko lemoka ruwa da sauran kayan bukata ya sa kudi a embelope ya bawa Bilya ya kaima Gwaggon. Wani rin dadi ya dinga ji rabon da ya yiwa gwaggo wata kyauta irin haka har ya manta. Kichin ya koma 87 Hadiza Ado Yalwa Garari ya dafa indomie sannan ya hada mata tea mai kauri. Har baccinta ya soma nisa ya zubowa fuskarta ido ba karamar rama kyakkyawar fuskarta ta yi ba, sai wani irin haske. Gashi kwance a gefean fuskarta dan karamin bakinta a tsoke ko cikin bacci Jidda kyakkyawar gaske ce mai matukar hakuri. Ya sauke ajiyar zuciya sam ta rasa kulawa daga gare shi lokuta da dama anya kuwa bata yi masa mummunar addu'a cikin ranta kamar yanda yarinyar dazu ta yi masa karara yake hangen rashin adalcinsa, a kanta lallai Allah na karbar addu;ar wandá aka zalunta. Yanayin da yake ji ya ci 88 Hadiza Ado Yalwa Garari gaba da mamayar sa irin yanda bai taba ji ba. Ta so ta dan juya jikinya ya bata kamar akwai mutum kusa da ita ta dan bude ido dan tuni ma ta manta da Muktar a a gefe ya na gidan domin rabonta da ya shigo ya zauna tare da ita tsayin lokaci har ta manta. Ta dora idanuwanta a kansa yanda ya zuba tagumi yana kallonta sai ta ji har gabanta ya fadi. Anya kuwa ba wani abu ya faru da Muktar ba, sai ta ji ba ta iya komawa bacci ta mike zaune ya dan yi murmushi hade da sauke ajiyar zuciya "Dama dai ba bacci ki ke yi ba, gara ma da ki ka mike wannan ramar da ki ka yi haka, duk na san rashin cin abinci ya janyo ta, ba ainihin ciwo ba". 89 Hadiza Ado Yalwa Garari Ya so ma hada mata tea da kanshi ya dinga bata har sai da ya tabbatar da ta koshi bai bar gidan ba har zuwa karfe biyar na yamma da ma aikin dare ne da shi cikin kwanakin nan wanda ko ita Azimar bata san da haka ba, duk kowa da tana matsayin matarsa ya haranta mata shiga dukkan cikin wasu al'amura nasa. Yau rana ce da a rayuwarta da ba zata manta da ita ba ita rana ce da ta dade da fitar daren za ta sake dawowa a rayuwarta da. Ranar da ta samu kulawa daga Muktar kulawa da soyayya abin tamkar almara haka a office din sama din sama jama'a da yawa kė mamakin laushinsa a yau wanda har wasu ke kasa hakuri garin 90 Hadiza Ado Yalwa Garari canjin daga gare shi su ce "Oga yau kuwa kana lafiya". Amsa daya ya ke basu ta lafiya kalau. Shi da kansa ya tantance da cewar lafiya yake, wannan yanayi da ya ji jinin da tsoka gabоbinsa da ilahirin jikinsa yake sanyaya shi yafi masa kama da shigar ciwo sai dai bai jin wani ciwo a cikin jikinsa, wanda zai dauka ya zama ya tabbatar da cíwo ke damunsa.. Abu daya ya san na yawo a tsakar kansa nadamar rashin bawa yaran nan hakuri bayan sun yi masa miyagun addu'o'i, ba wai girman laifin da ya aikata musu ne ke damunsa ba, usili shi mutum ne da kansa kadai ya sa ni baya daukar matsalar wani a matsayin abin da zai 91 Hadiza Ado Yalwa Garari dame shi mutum ne wanda ya dauki tausayi ba a matsayin abin yinsa ba in har ka ga murmushinsa a kan fuskarsa to ba karamin abu ne ya faru ba, abu daya yake bawa muhammanci a rayuwarsa aikinsa. Sannan abu daya ya fi so a rayuwa a yi masa addu'ar alkairi. Sannan abin da yafi tsana zalunci bai da abokin hira ko me ba shi shawara yana dauka tunda ya rasa iyayensa bai da sauran gata shiru shi kadai ne ba wanda zai tausaya masa shi ne gatan kansa shine dangin kansa, shi kadai ne kansa, ka dan ya sa ni da rayuwar da ya ta shi ke nan tun farko shi yasa wadannan akidu suka zama hallayarsa. 92 4 - Hadiza Ado Yalwa Garari Abinda ya faru a yau ya dinga hasakaka masa wasu abubuwa da suka zamewa rayuwarsa duhu ya kas agane shi yake ta tafiya cikin duhu fitilar da ta haske su, kalaman yân matan nan, rayuwarsa ta baya ta zame masa rayuwar da komai ya yi ba dai dai ya yi ba, makusantanshi kan aibata shi laifi da nasa da ba na sa ba duk akansa a ke dorawa ya zama abin har tara abin kyama ba dai ya na da wani aibu ba na rashin kyawun hali gudun da ya yiwa Illa maraici da talauci. Dalili talauci neya mai da shi maraya maraici kuma ya mai da shi mara galihu wadannan abubuwan suka kangarar da shi suka tafi da murmushi da dariyarshi suka dauke 93 Hadiza Ado Yalwa Garari tausayi daga zuciyarsa ya zamo bai ganin girman kowa har lokacin da ya kawo wannan matsayin wanda a yanzu wadanda ma ba jininsa ba suke son kasancewa da shi danginsa suke alfahario da shi bakunan kowa ke fadar alkairinsa duk a yau ya hango aibiunsa da mutane sun san da shi sun kuma san yana munana musu amma saboda matsayinsa ba wanda zai tunkare shi da fada masa gaskiya, ko nuna 6acin ransa bare har ya gyara duk abin da yake yi. Addu'ar alkairice ake masa a gaban idonsa a bayan idon kuma fa mai duniya ta dauke shi? Duk wannan bai da sani ba kuma ya tunanin sanin sai a yau da 94 Hadiza Ado Yalwa. Garari haske ya haskaka duhun da yake tafiya a cikinsa. Lallai akwai abin da ya kangara zuciyar 'yammatan da suka dinga zazzaga masa masifa batare da ganin girmansa ba, karshe suka raka da yi masa mummunar addu'ar, to mene ne ya tunzuro su haka? Wane kuncin ne wanda ya tuno da ta shi rayuwa haka. Su ma nan gaba in sun girma suna iya zama masu halayya mara kyau saboda kangarewar zuciya, sun dauki dukkan masu mukamin mara adalci, ćiki har da shi, kuma ba karya su ka yi ba, aikata rashin adalci ya zamo dabi'unsu da hannu biyu ya ja tagumi bai san lokacin da hawaye ya soma zuba daga idanunsa ba, adadin 95 Hadiza Ado Yalwa Garari mutanen da za su yi masa Allah ya isa da mummunar addu'ar bai san yawansu ba, bai kuma san inda zai gansu ya nemi gafararsu ba, ina zai kai tarin hakkin. Da yake kansa ya zai yi da munana ayyukansa Gaba daya zaman office din ne ya ji yana neman gagararsa yanayin da yake ji na neman kwantar da shi mike wa ya yi yana sharar hawayen fuskarsa ya dauki rigarsa da ke jikin kujera ya kira wani Sajan "Zan wuce gida bana jin dadi ne in akwai wata matsala ka kira ni a waya". "To Oga". Ya sara masa haka ya dinga wuce su suna sara masa shi ma yana daga musu hannu suka cika da 96 Hadiza Ado Yalwa Garari mamakin don abin da bai taba yi ba kenan. Kyautarsa ce ma ke sawa suke ganin kimarsa dan shi mutanne mai yawan kyauta amma ba shi da sauki ko kaďan zafi ne da shi kamar zazzabi baya jin ban baki ko magiya Sajan din su biyu da suka kame suka kalli juna bayan ya wuce. "Oga Allah yasa ciwon nan nasa na yau ba kamun mala'iku ba ne" Dayan ya kwashe da dariya "Mala'ikun ka ga ni tare da shi ko me?" Ya sake fadin haka sajan Bala na kokarin zama akan benci kamar dai yana tare da su "Ka ga yanda ya yi laushi har yake iya daga mana hannu abinda ban taba gani ba tunda 97 Hadiza Ado Yalwa Garari na zo wannan gidan kuma ai yana cuta katuna kwanaki har kwanciya ya yi a Asibiti amma fuskar nan ta shi bata sauya da komai ba, in ka ga ka yi masa magana sau dubu wacce bata shafi aiki ba ko da kuwa gaishe shi kake yi ba zai saurare ka ba, dayan ya ce "Na yarda da maganarka. In dai hake ne kila saukin mutuwar ne ya zo masa. "Ni dai addu'ata koda koda ya mutu Allah ya kawo mana mai dan sakin fuska duk walwalar da na ke ciki da na ga fuskarsa sai na ji ta kau, lallai ne murmushi ga dan uwanka musulmi shi ma sadaka ne manzon Allah ya yi gaskiya" "Kuma shimfidar fuska tafi ta tabarma" in ji Bala 98 Hadiza Ado. Yalwa Garari ** Lokacin da su Umaima ke tafiya ba ta fasa sharar kwalla ba, ita kuwa Asiya nata dudduba inda za su samu ruwan da za ta wanke wa Umaima domin a ganinta har da ma ganin da take yiwa Jijab din yake kara tunzura zuciyarta take ta faman kuka, ita kuma da ta tsani ganin ta na yi a zuciyarta na tafarfasa hanyar titi ne sosai. Daga kamfanoni sai shaguna sam ba ta hangi wani gida ba, don haka bata hangi inda zata sami ruwa ba, wata mota ta hango ta tsaya kusa da su ta nata horn, sam basu kawo mai motarsu ya tsayawa ba, sai da suka zo daf da motar sannan suka ga glass din motar na sauka a hankali". 99 ر Hadiza Ado Yalwa "Ke sarkin makara”. Garari Sannan ta juya sai kuma ta yi murmushin ganin principal dinsu cе wadda saboda tsabar yawan makararta ta gane ta har tasa mata suna Sarkin makara, ta kuma yi bincike a kan yarinyar ta gane tafiyar kasa take yi da kuma halin yau yasa take yawan makaran, yanzu ko ta makarama ta hana a tsaida ita sun durkusa don gaishe ta ta ce "To ku shigo mu karasa". Nan fa suka shiga kokawar yanda za su bude motar don wannan karo na farko da suka fara shiga karamar mota, Asiya ta yi nasarar budewa ita kuwa Umaima ta zauna a gaban inda Hajiyar ta bude mata. 100 Hadiza Ado Yalwa Garari Hajiyar na tuki "Ke kuma me ya same ki ki ke kuka”. Ta kalli Umaima da har yanzu yanayinta na mai kuka ne ta ware Jijab dinta inda ta cukuikuye inda ya baci "Ba wani ne ya 6ata min sabon hijab di na ba". Hajiyar ta kalli Hijab din sannan ta mai da kanta kan titi "Saboda ke kuma 'yar sarkin shagwababа6бuce shine ki ke kuka". Bata sake magana ba har sai da suka isa makaranta ta dubi Asiya "Mu je office ki karbar mata wani, ke kuma wuce ki wanke a wancan famfon". Ta dauko sabon Hijab ta bawa Asiya tare da cewa "Kanwarki cе”. 101 Hadiza Ado Yalwa Garari Nan da nan annurin fuskar Asiya ya bayyana "Knwata cсе" Sannan ta durkusa ta nanata godiya. Principal ta ce "Ba komai ku yi maza ku je aji kar a fara darasi" Ta window ta mika wa Umaima sabon Hijab din saboda kiran da monitar ajinsu ke yi mata a yau ita ce da sharar aji. Sai da aka fito sannan suka hadu nan fa hirar dadin motar principal da karamci da ta yi musu duk da tsabar kwarjininta da ya yanda take dakawa yara tsawa, mamakin yanda ta yi musu suke yi, tuni ma sun manta da takaicin da suka hadu da shi a hanya. orSu dawo gida suna bawa Ummansu labarin abinda ya faru, duk yanayinta ya koma tamkar na mara 102 Hadiza Ado Yalwa Garari lafiya duk tambayar da suke damunta da ita na mai yake damunta ba komai shine amsarsu sai dai abin da ke cin zuciyarta yanda suka yi jiya da Lawan kan maganar Alhaji mai icce, sai yanzu ne ta gama gane Lawan sam bai dauketa a macen aurensa ba, tunda ba zai ma iya kare mata mutumcinta ba, shawara daya ta gama yankewa gobe da safe ta je garinsu kawai ta fadawa yayanta ta gama gajiya da aurensa 'ya'ya kuma zata bar masa su in ya so ya dafa ya cinye su ai 'ya'yansa ne. Da sanyin safiya ta shirya ranar Asiya ce bata je makaranta ba, tana ganin Ummansu nasa kayanta a leda duk jikinta ya bata akwai wata damuwa tana son tambayarta, amman 103 Hadiza Ado Yalwa Garari ba ta ga fuskar hakan a wajenta ba, don ko magana bata son yi babu walwala kwata kwata a tare da ita. Zargin Asiya bai gama tabbata ba sai lokacin da ta ga har sun kwanta Ummansu ba ta dawo ba sun kasance cikin tashin hankali wanda ya hana kowacce su rintsawa sabanin Lawal da ya yi baccinsa har da munshari. Bai yi tsammanin wannan 'yar magana zata iyasa Harira ta bar gidan ba. Duk da ba wannan ne karo na farko da suka fara samun sabani tana kai kararshi ga iyayenta ba, amma dai wannan karon ransa ya yi matukar baci abin da ya dauka rashin godiyar Allah ne kawai iri nata yasa ta gaza ta biyo masa ta wannan hanyar don haka 104 Hadiza Ado Yalwa Garari ya dauki alkawari shi ba zai taba bin bayanta ba bare wan nan nata ya cika shi da surutu na rashin kan gado duk ranar da ta gaji da zama ta dawo. Washe gari da safe haka suka gudanar da duk abubuwan da suka saba yi amma dukkaninsu jikinsu a sanyaye, Lawan kuwa da sanyin safiya ya fice ya bar gidan, yau da Hansa'u da Umaima ne kadai suka je makarantar, a hanyarsu ta dawowa sun shagala sosai wajen hirar matsalar tafiyar Ummansu wadda suka tabbatar cewa ba tafiyar shiri ba ce, Umaima ce ta hango lawal tare da wani babban mutum a tsaye a kofar wani gida da ake gini ma aikata nata kai kawo suna aikinsu, Umaima ta ce 105 Hadiza Ado Yalwa Garari "La kin ga kamar Babanmu a can gurin tsaye shi da wani mutumi". Hansa'u ta kai dubanta gurin "Tbbas shine to ko Baba me ya zo yi nan gurin?" Ta fada a sarari. "Dago kafa mu tadda shi ko Allah ya ci da mu ya ba mu wani abu mu kai gida". Umaima ta dan 6ata fuska "In kuma ya yankwanamu a cikin mutane ke kika jamana". Hansa'u ta ce "Ke kin fiya tsoro wallahi kawai daga mun ganshi mun gaishe shi sai ya yi mana wani abu ai ba cewa za mu yi ya ba mu wani abu ba". Suna kara tunkarowa gabansu. Suka kara tattara nutsuwarsu har 106 Garari Hadiza Ado Yalwa magana suka kowacce na tsoron yanda zai amsa musu gaisuwar ta su. Tun daga nesa Ahmad Ahuta ya hango 'yan matan da ke tunkaro su. Gaba daya ya shagala da kallansu, har bai san lokcin da suka kara sa idowa ba, sai ji ya yi suna cewa "Baba ina wuni". Ya dubi Lawan da ya hada fuska "Ku makarantar ce sai yanzu kuke dawowa tun dazu nake ganin yara na wuce Ya yi sauri yas abaki "Ai ba jima da tasowa ba" Sannan shima suka soma gaishe shi ya ams ayana murmushi "Yaranka ne wadannan Lawal? Don na ga kamanin musamman wannan babbar". Ya nuna Hansa'u. 107 Hadiza Ado Yalwa Garari Nan da nan Lawal ya washe baki "Eh wallahi alhaji ai ita babbar ita се Hansa'u wannan kuma Umaima". "To madallah" Inji Alhaji yasa hannu a aljihunsa ya dauko kudi ya mika musu. "Aka karasa mai karba tsakanin Umaima da Hansa'u sai kallon juna da suke yi daga karshe suka ce mun gode Alhaji suka bar shi da kudin a hannunsa. Lawal da ya kurawa kudin ido yaga cewa tafiya za su yi sai ya yi maza ya daka musu tsawa "Ke ya za ku dinga jayayya da Alhaji". Hansa'u ce ta juya da sauri ta durkusa ta karba sannan ta yi godiya. 108 Hadiza Ado Yalwa Garari Suna tafiya amma a rude suke da tsawar da babansu ya daka musu. Ba su bar fargabar ba har sai da suka tabbatar sun yi masa. Nasa baya iya gane su, saboda tsoron kada ya kira su ya balballasu da fada sun yi masa laifi dan su a iya tsawon rayuwarsu da Lawan basu tantance mene ne in an yi mas alaifi ne mene ne ba laifin ba sai dai idan bai gansu ba. Kusan a tare suka sauke ajiyar zuciya Hansa'u ce ta dubi Umaima a Hijab dinta ya karkace idanuwanta su ka yi muzu muzu ta yi dariya "Kin ganki ke kuwa lallai kin rikice. Ita ma ta kwashe da dariya "Na rikice ko mun rikice kin ga yand 109 Hadiza Ado Yalwa Garari amuke gwara kai kuwa kai Baba ba shi da dama komai fada". Hansa'u ta bude hannunta da kudin suka cike sababbin kudi ne takardar dariyar biyar biyar har guda shida. Tu ni idanuwansu suka firfito na mamaki sam ba su yi zaton kudin sun kai haka ba, nan da nan suka kara sauri sai gidan gaban Asiya suka zube kudin lokacin da take daurin gyada mai 6awo "Yaya kin ga wani mutum da suke tare da Baba ya ba mu". Asiya ta ajiye gyadar hannunta tana kirgawa suna bada labarin abin da ya faru kawai sai jin muryar Lawal su ka yi yana sallama Umaima ce ta yi saurin dibar kudin biyu suka zube 110 Hadiza Ado Yalwa Garari a farantin gyada suara kuwa ta daga tabarma ta cusa suna amsa sallama wadda ya yi ta hade da shigowa dakin. "Ina kudin da mutumin nan ya ba ku? Maza ku miko minsu". Nan ya zuba dubu dayan dake kan farantin gyadar ido Umaima ta dauka ta mika masa ya kirga "Sunfi haka munafukai ku fito min da sauran duk wahalar ta ku ba a kaina take ba, maza ku fito min da su". Umaima ce ta dake zuciyarta wajan iya furta masa "Duka abin da ya ba mu ke nan yanzu ma muka ajiyewa Yaya ko tabawa ba mu yi ba" "Yaran banza to da kuka kawo mata me za ku yi da kudi har haka? 111 Hadiza Ado Yalwa Garari Cefane zan je na yi muku tunda ita uwar ta ku ta watsar da ku ta tafi ta barku yana wannan gorin ya fita". Dukkansu suka kalli Umaima yand ata iya wannan karfin hali. Asiya ke cewa "Amma fa ba ki kyauta ba ni dai zan ajiye masa kudin tunda ya bukata ba ko abin da zai yi mana da su ba, tund akin ga yanzu ya יי san Umma ma bata nan". Umaima ta sauke ajiyar zuciya "Ni yaya gani na yi da zai yi wani abu da bai ma bukaci mu ba shi kudin ba sai dai ya ce mu siyo abin da muke bukata kawai amma me ye amfanin karyar da ki ka yi yanzu ai da mun ce masa ya ba mu mu siyo yafı karyar'. In ji Asiya ranta a bace. 112 Hadiza Ado Yalwa Garari "To ki yi hakuri Yaya idan ya kawo sai mu ba shi ko haka su ka yi ta zuba idon ya aiko musu da wani abu har dai Asiya da kanta ta fitar da tsammani ta dauko kudin ta bayar suka yi cefane da goyawa wannan bayan ba za su ba shi ragowar kudin ba, har sai dai idan ya kawo musu abin da za su ci. Tun kafin Harira ta gama shiga cikin garinsu mutane ke ta jajanta mata rashin lafiyar wanta wadda bata sani ba, jikinta ya yi sanyi kalau domin ta kula da cewa ciwon ba karamar kwantarwa ya yi masa yanda kowa ya sani ita ce dai labarin bai jewa ba, haka ta shiga cikin gida sai kusan hudu tana sallama ba wanda ya amsa mata sai can ta jiyo muryar inda 113 Hadiza Ado Yalwa Garari matarsa a shake da sauri ta shiga dakinsa Indo. Na bakink ofar tana sharar kwallah yayin da abokansa guda biyu ke zaune a gefansa dayan na tallafe da kansa dayan na shafa masa ruwa a fuska saboda sau biyu yana suma ta kara gabansa tuni muryarta ta soma rawa na son yin kuka. "Yanzu jikin nasa har ya kai haka ba a gaya min ba, da banzo ba shi ke وو nan. Yana jin muryarta ya dan bude ido "Harira" ya fadı sunan a wahale. "Yaya Allah ya ta shi kafadunka" Ya riko hannunta da kyau "Ina tausayinki Hararia ki yi hakuri da rayuwa ki zama jarumar kanki mai dogaro da kanki kafin ya karasa tari ya turnokeshi. Daga nan kuma sai shakuwa nan da nan numfashinsa ya soma kaiwa 114 Hadiza Ado Yalwa Garari da komawa, sai kuma bacci ya dauke shi haka suke zaune a gabansa masu tofa masa addu'a na yi masu kuka na yi kamar Harira da ta kasa jurewa kallonsa ta fito tsakar gida ta hada kai da gwiwa tana rasgar kuka lokacin sallah azahar ne ya yi don haka duka suka fita yin sallah, sai dai ashe ciwon bana tashi bane kafin ma, su idar rai yayi halinsa ..dukkan mai rai mamaci ne wannan mutuwar ba karami kada Harira ta yi ba, domin shi ne wanta daya tilo kuma marikinta da . ya rage mata a rayuwa wannan ya dakusar da kudirin da Harira ta taho da shi domin ta kasa bayyanawa wani ma abin da ke cikinta. Alhaji Ahmad kani ne ga Alhaji Madu wanda Lawai ke tukawa a mota. Tun ranar da ya dora idon a kan Umaima ya ji yarinyar ta kwanta masa 115 Hadiza Ado Yalwa Garari ya na son ya mai da gurbin matarsa da ta rasu tsayin lokaci yana zaune babu aure. Kudirinsa kuma na son yarinya ne karama sam baya sha'awar ya auri yarinyar da ta kai

Chapter 3 of 4