Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 4
gansu ya kawo musu dan abin da ya sauwaka kamar yan da suka saba, basu dogara da shi ba, ta ci gaba ne da siyar da gasarar a kadai amma aikin awara a gidan mutane ba 36 Hadiza Ado Yalwa Garari zai yiwu ba, da kwanaki suka soma turawa Lawan sai ya daukie kafarsa gaba daya daga gidan, ta koma fitar da rai da zai nema musu wani gidan tunda ta samu labarin a dakin abokinsa yake kwana kuma har abinci matar abokin nasa take ba shi, ya mike kafa sosai a gidan abokin nasa ga shi su duk ranar da a ka yi ruwa basa iya bacci abincin ma ya zama sai uwani idan ta yi ta sama musu jarin awara tuni ya karye. Dole ta fito nemar mus hayar da kanta saboda idan har suke cinye ragowar kudin hayan to fa bata san in da za su samu ba, don haka ta dinga fita ba ji ba gani nema musu gida duk in da ta je sai a ce mata babu, sai da ta yi sati guda ta na yawo ba a dace ba, 37 Hadiza Ado Yalwa Garari ranar kwana na takwai ta na dawowa take fadawa Uwani ba a samu ba, Uwani ta nisa. "Maganar gaskiya Harira samun haya a nan kusa zai yi muku wahala saboda yanda ake yamididin bakwai biyan kudin haya, sai dai ki yi can wajejen Remin kebe nan ne ba sanku sosai ba kila a dace". a Wani irin nauyi kirjin Hairara ya yi tabbas ita ma ta yi tunani haka don ta samu dakunan da babbu kowa amma tana zuwa sai a ce wai an ba da su. Shawara Uwani ta dauka ta sake fita sannan ta samu dakin ga matsalar rashin cikon kudi ta yi burinta fita idan rana ta yi sanyi ta nemo Lawan duk in da yake ya taimaka ya bada 38 Hadiza Ado Yalwa Garari cikon kudin sai ga shi ya shigo da bala'in da ta kasa yi masa ko wacce magana. Wai yaushe ne Lawan zai ji kanta yaushe zata burge shi a rayuwa yaushe ne zai kyautata mata. Wannan tunani take yi tana fitar da kwalla zuciyarta na sake daukar zafi ba don tausayin 'ya'yanta ba da ta gudu ta bar Lawan ta nuna masa ita ma fa babu digon kaunarsa a zuciyarta, to amma yaranta ta san in ta bar masa su haka zai barsu su watse su lalace tunda kaf danginsu babu mai daukar masa babu ma wanda ya dauka da mutumci da kima balle a rabe su. A soron gidan Kamar ba mutum a cikinsa sai yawan ajiyar zuciyar da 39 Hadiza Ado Yalwa Garari suke yi daya bayan dayan Uwani се ta fito daga dakinta wadda kusan duk hayaniyar da yake yi babu wani abin da bata ji ba, abin da yafi konawa Uwani rai yadda yake wa Harira a gaban yaranta. Ya leko sorön gidan "A'a 'yammata duk kuna nan kuna shan iska" A tare suka dago kai dan duk sun ji motsin fitowarta. Umaimata ta dan yi yake "Muna nan". "Ga wannan ku dan taba kuma bari na kaiwa Ummanta ku, wannan" Ta meka musu robar hannunta da 'yan farantin kuma ta nufi dakin Ummansu. Da shi danwake ne, da ya sha ya ji yana ta kamshi man zallar Kulikuli duk da yunwar da ke 40 t Hadiza Ado Yalwa Garari addabesu babuw adda ta yi gigin dauka, takaici da tunani kadai ke yawo a tsakiyar kansu, har sai da su Ahmad da Muhammad suka shigo sannan Asiya ta ce su dauka su ci batare da ta yi shawara da kowa a cikinsu ba, kallo daya ta yi waa Kannen nasu ta tabbatar sun fisu jigata da jin yunwa, ga shi ba shi da yawan da zai ishe su, ma gaba daya. Kudin kitson da Umaima ta samu shi ta cire ta meka wa Asiya "Ga shi yaya me za mu yi da daddare?" Asiya ta ja ajiyar zuciya tana juya kudin hade da tunanin sai lokacin Hansa'u. Та се "Akwai sai a yo cefane faten tsaki kawai". 41 Hadiza Ado Yalwa Gararf Har lokacin da suka gama girki Harira bata nukurkusarta wanda ya hadda masa ciwon kai mai tsanani. Dama tuni 'yanmatan sun sabarwa kansu aikace-aikace gidan in har Ummansu tasa musu hannu to, ita ta so taimaka musu. Har washe gari da yamma Lawan bai dawowa ba kuma bata hangi wata hanyar da za ta bi ta samu kudin ba ga wani abin da yafi tayar da hankalinta a yau ruwan ranar da a ka yi tun safe ake kwara ruwa har sai wajen sallah azahar sannan ruwan ya soma raguwa daga ita har yaran sai da suka je ke sharkaf saboda feshin ruwan da yake shigowa dakin duk da asabarin da suka sake a bakin kofar. 42 Hadiza Ado Yalwa Garari Ga a zababbiyar yunwa dake addabarsu saboda babu wannda ya samu damar fita bare ya samo musu dan abin da za su saka a bakunanus, garin kwakin da bai wuce gwangwani biyu ba ta jikawa yaran suka karya da shi har zuwa rana ana idar da sallar la'asar ta fito daga gidan duk da ana dan yin yayyafi. Ba kuma yanke shawarar in da yakamata ta soma nufa iska mai sanyi ce take kadawa cikin sararin samaniya ruwa ya jika ko ina, ni'ima ta sauke har lokacin babu alamun rana sai haduwar saboda hadari ta sauke kanta daga kallon yanda gabas take dada duhu hadiye ajiyar zuciya. Take ta yanke shawarar neman Lawan a wajen abokansa ta san zai zo 43 Hadiza Ado Yalwa Garari har gida ya ci mutumcinta saboda abin da za ta yi masa, amma tana da tabbacin zai iya nemo kudi duk in da suke ya yi mata duk yanda ta so ko don karta sake biyo shi wajan abokansa ta ba shi kunya sai dai rashin sa'ar da ta yi ta samu duk in da yana zam ata je bata same shi ba. Jikinta a sanyaye ta juya da nufin komawa gida har ta soma tafiya sai kuma ta canza shawara ta nufi rumfar mai icce in da a nan ne wanda zai basu hayar gidan yake sana'arsa ta sai da icce. Koda ta isa bata same shi a cikin rumfar ba bata yi mamaki ba saboda tasowar hadari da iska mai hade da digowar kwayayyen yayyafi ta zubawa iccen ido kamar wadda ke 44 Hadiza Ado Yalwa Garari jiran amsar in da mai su ya shiga daga gare su. Katuwar rumfar kwano ce idan ka dauke tabarma da bencin da ke cikinta, to fa babu komai sai iccen tana da girman gaske akwai itatuwa masu yawan gaske duk wadanda aka faskara da wadanda aka daure aka kasa ne a cikin rumfar gunguma gunguman daba a faskara ba, kuma suna daga wajen rumfar. "A'a barka da zuwa Hajjaju" Ta ji an fada daga bayanta tana juyawa ta ga mai iccen bota ce a hannunsa "Ke ce da hadarin nan?" Ta dan yi murmushin yake "Wallahi dole ce ta fito da ni". Ya zauna a kan bencin dake cikin rumfar ita kuma ta durusa a kan 45 Hadiza Ado Yalwaа Garari tabarmar shifede bayan sun gaisa shiru ta ratsa na wasu 'yan mintuna, tana juya kalaman da ya kamata ta yi amfani da su dan bayyana masa matsalar da take ciki, har dai ya kosa da shurin nata idanunsa na kanta "Kudin kika kawo?" Sai sannan ta girgiza kai "Har lokacin kanta na kasa dama na zo neman alfarma ne. "Alhaji Baban yaran ne baya gari kuma a takure muke a inda muke zaune saboda yanayin nan nadamuna, shine na zo a taimakamin; ka karbe rabin kudin nan in ya dawo zan kawo cikon insha Allahu a taimaka dan Allah Alhaji". Ba ta kula da irin kallon kurullar da yake yi mata ba, saboda har ; 46 Hadiza Ado Yalwa Garari lekacin kanta Rasa yake har ta kai karshen maganarta. "Wannan ba zai gagara ba kawo abin da yake hannunki". Kamar ta yi rawa don murna farin cikinta ya kasa 6oyowa take ta yi murmushin da har hakoranta suka bayyana takwanto kudin daga cikin bakar ledar da ta daure su, a ciki ta kirga sannan ta mika masa. Sai a lokacin ne ta kula da irin kallon kurullar da yake mata har sai da gabanta ya fadi take fara'ar dake fuskarta ta dauke. Cikin muryar kasa-kasa ya cе "Ai ba girmanki ba ne, kina yarinyarki da ke kina neman alfarma" Ta dago da sauri kafin ta ce wani abu. Ya mike "Babu damuwa, 47 Hadiza Ado Yalwa Garari ko yau ne ko na iya shiga, babu damuwa, ko yaune ko na iya shiga ga mukullin nan ya a jiye mata mukullin a gabanta. Wannan kalmomin na shi su kasa cewa komai sai godiya sai dai a cikin zuciyarta na cike da tambayar me yake nufi da furta su a gare ta har ta isa zuciyarta bata gama amince mata cewar ba shi da wata manufa a cikin kalamansa ba. Addu'a ta shiga yi ta Allah ya tsare ta daga dukkan wani mugun nufi ba karamin farin ciki yaran suka yi ba, da ta zo musu ba labarin ya karbe kudin da sanyin safiya ma za su tare a gidan, cikin dare suka kammala dukkan shirinsu guri na wayewa, ta shiga yiwa Uwani sallama da dimbin 48 Hadiza Ado Yalwa Garari Godiya Uwani taya su murna sosai ta ce," kuma taimakon wani ai taimakon kai ne." ta kuma dora da addu'ar Allah ya hore. Nan da nan suka dora tarkacen kayansu a kura suka dauki hanya. Daga 'ya'yan suke bin Ummansu da ta san gidan,jikinsu a sanyaye yake har babu wacce ta ke iya Magana cikin 'yan matan. 'ya'yan nata ban da su Mahmud da suke ta yin wasanni goge-goge a kan hanyar ita kuma Umman Harira tafiya kawai ta ke yi zuciyarta cike da sakesake da addu'a. A bakin wani lungu mai siririyar kofa suka tsaya Harira ta kuma sauke kayan suna taya ta said a suka shiga lungu sannan suka gane kofar gida ne 49 Hadiza Ado Yalwa Garari ba lungu ba, ba su yi tafiya mai nisa ba sai ga su a tsakar gidan. Ba su shiga gidan sosai ba, katuwar rumfa suka shiga wadda ta ke dauke da dakuna har guda takwas hudu na kallon hudu. Kowane daki daya iyali ne a cikinsa, suka yisallama har sau uku, amma babu wanda ya amsa musu.. Matasan 'yan mata ne suke casar fada kamar za su yaga naman jikinsu. Fada suke yi,su Umaima suka kalli juna har Harira ta fara bude kofar dakinsu sannan wata mata ta fito daga daki da buta a hannunta,ga mamakinsu ko inda 'yan matan suke bat a kalla ba,kamar ma bat a san wani abu na faruwa ba. Da fara'arta ta, ta ce," a'a, baki muka yi sannunku da zuwa." 50 Hadiza Ado Yalwa Garari Ta karasa fitowa da Sanda a hannunta "To kar na kuma jin bakin wata a cikinku" Su ka gaisa da matar cikin fara'a sannan Harira ta ture kofar dakinta ta shiga ba lefi dakin yana da dan girma, sauran yaran suka dinga shigowa da kyar suka barsu wajen shirya kayansu, duk basu wuce tabarmi da katifa guda daya ba,s ai wani tebur da gwandon kwanika da jakunkunan kayansu. Nan da nan suka kammala shirya komai. Dukkansu suna kwance a tsakiyar dakin ba wacce ke iya magana, kuma ba wacce ta rintsa a acikinsu, kowacce da abin 51 Hadiza Ado Yalwa Garari da ke sakawa a ranta, ta yanda za su fuskanci zaman gidan. Sun saba da zaman gidan haya tun tasowarsu, amma sun gaza sabawa da fargabar kalubalen da duk gidan da suke zama su kan zamo baki. Musamman irin wannan gidan da ya tara yawan al'umma ban da su Mahmud da tuni suka fice suna murnar samun sababin abokai. Rana na dagawa gidan ya dume da zafi hayaki, dole ce ta sa dukkansu fitowa ko don shekar daddadar iskar bayan gidan, in da anan suke tsammanin samin inuwar da za su tsugunna ba su yi mamakin ganin daukacin gidan wajen ba sai dai kowacce ba a zaune take ba kamar 52 Hadiza Ado Yalwa Garari yadda suka zo shan iska duk suna aikace aikacen kayan siyarwasu, wasu dambu wasu danwake, shi ya sama hayakin ke komawa dakunansu. Wata 'yar budurwa ce ta fito ta kalli Umaima ta sheke da dariya "Kunji turaren hayaki ko, ku ne kuka kunshe kanku a ciki daki". Asiya ta yi dariya "Akwai hayaki kam sannunku da aiki". Yarinyar ta soma gabatar da sunanta dana kannensu, abin da suka rike shine Laila wadda ke gabatar da kansu, wadda bata wuce sa'ar Asiya ba. 53 Hadiza Ado Yalwa Garari Daga nan ta fara musu hira wadda yawanci bugar ciki ne da tambayoyi mara alaka da ita. Su kam daga murmushi basa iya kara wani abu domin Ummansu me kwabarsu ce akodayaushe basa iyawa manya na magana suna sa baki ko shiga cikin maganar da bata shafe ka ba, wanda abin da suka lura da shi a wannan zamani sami yaran basa shayin fadar kowace irin magana gaban iyayinsu, wani lokacin ma suke kara musu haske a takaice kusan tare ma ake hirar. Wadda rabinta duk żancen mutane ne da batsa, wani lokacin su kan ji kunya kamar su nutse amma iyayen babu abin da ya dame su, 54 Hadiza Ado Yalwa Garari yaran kuwa dariyarsu suke yi ba wani alamun kunya ko damuwa a kan fuskokinsu. Haka suka ci gaba da zaman wajan ba don zaman na musu dadi ba, sai dan rage wahalar zafi da hayakin cikin dakinsu,w anda babu shi, sai ma iskar bishiyar dake makota ke kaďo musu. Suna zaune har zuwa lokacin da kowace ta mike ta wanko kafafu da hannaye sannan aka zo ana саба kwalliya. Iyayensu na zuba musu abinci siyarwa a roba da suke fita da su, tallah. Sannan ne fa Asiya ta mike dukkansu ma suka bi bayanta don 55 Hadiza Ado Yalwа Garari komawa cikin nasu dakin, Ummansu tunda safe ta fita nemar musu abinci za su ci duk da sun baro gurin duk wacce ta gama abinci ta zubo musu ko da suka ki karba sai su ajiye musu a dakin na su, sai su yi godiya, Asiya na sallaha Umaima na yiwa Sayyada tsifar kanta Hansa'u na wanke musu kwanuka. Ummansu ta ji sallama ta shigo Umaima ta amsa ta dube su, duka ta nisa ina so Muhammad yanzun nan su ka ci abinci suka fita ina kuka samu abinci Umaima ta yi mata bayani a takaice ta dauko ledar da ta shigo musu da ita Jalop din shinkafa ce a cikin cikin 56 Hadiza Ado Yalwa Garari zuciyarta ciki da tunanin yanda za ta yi ta samarwa su Mahamud makaranta, domin ta tsani yawon nan nasu tana ciki da farbar kada su zame mata yan da yayansu ya zama, duk yanda take son kulle su a daki abin gagararta yake yi ba kamar yaranta ba, ga shi dai a cikin idon ta ma har ta manta rabon da ta ga wansu ba ma ta tsammanin yasan zamansu gidan Uwani tun wani lokaci suna wancan gidan da ya shigo mata daki kamar mahaukaci yana layin buguwa ta matan gidan suka dinga gudawa suna rufe dakunansu da kyar ta tura shi waje ta kuma gargafe shi kada ya sake shigowa cikin idan 57 gidan Hadiza Ado Yalwa Garari ita yake son ga ni ya tsaya daga waje ya tura a kirata. Bai yi magana ba ya juya kawai ya tafi bata sake ganinsa ba a idanuwanta. Duk zancen zucin da take yi tana juye musu abincin a cikin kwanika, da ddadan kamshin abinci ya gauraye dakin wanda rabon da su ji irinsa har sun manta. Hansa'u će ta kasa hakuri ta ce "Umma ina kika samu wannan abincin me yawa haka, ga kamshi" Dukkansu suka sa dariya. Ban da Umma da tunanin da ta ke yi ya sauke mata da dakin zuciya ta dai sauke ajiyar zuciya. "Tun bayan fita ta gidan Kubra na nufa yayar Yahanasu" (Yayar 58 Hadiza Ado Yalwa Garari wata ce da suka taba zaman gidan haya da ita) Tun da na ga ba mu da abin da za mu ci na soma tunanin sai ta fadomin a rai, na santa macece mai tausayi da kara, kuma daga nan zan iya zuwa gidan akafa ta na can Jaba gidajen 'yansanda nan, wallahi ira ce da wannan aikin abincin har kudi wai na yi jari" Gaba daya suka yi mata addu'ar Allah ya biyata da aljannah. Sun gama cin abinci suka fara shawara sana'ar da yakamata su yi don neman tudun dafawa. Sun tsaye ne a kan shawara da Umaima ta kawo wato yin Awara da safe da 59 Hadiza Ado Yalwa Garari rana kuma wake da shinkafa da Kunun tsamiya tunda akwai masu yin awara a gidan basu 6ata lokaci ba wajen siyo kayayyakin da niyar gari na wayewa za su tashi da aikin. Misalin karfe tara na dare Hansa'u na yiwa su Mahmud shimfida, Umaima da Asiya na dafa Awara, Ummansu na zaune da sauran matan gidan ana taba hira, suka ji gyaran muryar hade da sallama. Harira ta dauka mijin daya ne daga ciki ne ya dawo ta dan janye jikinta don tafi kusa da hanya ga mamakinta sai ta ji kamar muryar Lawal ya na nanata sallama ta dago ido babu tantama shi dinne 60 Hadiza Ado Yalwa Garari ya soma duru-duru na rashin sanin ina ne dakinnasu. Muryar Hansa'u ta ji ta fito daga dakin ya yi saurin shiga dakin, ba don a bakon guri suke ba babu abin da zai sa ta biyo shi, fushi take yi da shi sosai, amman gudun kada 'yan gidan su gane akwai matsala yasa ta mike ta shiga dakin amma ta tsaya a bakin kofar bata iya furta masa kowace kalma ba. Shiru ya ratsa tsakaninsu ya dai kula da yanda ta hade fuska, ya yi kasa kasa da muryar "Na je can gidan Uwani ta hada ni da yaro ya rako ni nan ashe an samu dakin amma baki neme ni ba." 61 Hadiza Ado Yalwa Garari Duk kame kamen da yake yi tana jinsa bata iya cewa komai ba saboda kalmar da zata fada ba mai dadi bace, kafin su fara raba abin fada a bakon waje. Ganin ba zata tanka mushi ba ya soma kiran Hansa'u ta shigar da sallama. ya mika mata ledar hannunsa "Ga wannan ku je ku ci ke da kannenki". Kawunan kifi ne da gyada me gishiri. Hansau'u na fita Umman ta bi bayanta ta koma gun matan gidan su ka ci gaba da hirarsu. Lawan ya rage kayan jikinsa sannan ya haye katifar ya yi kwanciyarsa ya na jero tsaki na jin 62 Hadiza Ado Yalwa Garari haushin yanda ta tafi ta bar shi shi kadai a daki. "Ke su Mahmud ma ba wanda ya leko bare ya yi musu 'yan tambayoyin da suke ransa. Asiya ce ta shigo don dibar tabarmin shimfidarsu kamar yanda ta ga ni kowacce mata na shifida a koafar dakinsu, ta ji magana ta juya ta ji wanda ke makotaka da dakinsu na cewa "Ai sai kin fara shimfida kwali, yanda rumukan nan ba za su hanaku bacci ba" "Asiya ta sauke ajiyar zuciya yanzu ina zamu samu kwali?" Yarinyar d ahar a lokacin Asiya ba ta rike sunanta ba ta ce "Siyarwa 63 Hadiza Ado Yalwa Garari ake yi kantunan dake kusa da gidan nan Dole Asiya ta aje shimfidar ta koma ta gayawa Umma don ta hango matsalar da 'yar budurwar ke fada mata. Harira ta shiga dauko kudi a daki tana kallon yanda Lawan ya yi dai-dai akan katifa ta dinga jin kamar ta rufe shi da duka, haka ta hadye takaicin ta fita ta bawa Ahmad kudin ya tafi siyowa. Duk yanda Lawan ya yi ya shawo kan Harira abin ya gagara don haka shima ya dau gaba da ita, sai dai hakan bai hana mishi kwanan gidan ba da cin duk wani abinci da ya ga ni a dakin bai canza ba, duk da ya samu 64 Hadiza Ado Yalwa Garari aikin tuka wani babban mutu a mota wato driber. A cikin 'yan kwanakin duk da bai fadawa Harira ba ta dai lura da yanda yake canza kayan sawarsa da daduwar tsabtar jikinsa ta yi tunanin akwai in da yake zuwa koma dai me ya ke ciki bata damu da tunanin halin da yake ciki ba. Harkokin sana'arta yanda zata taimaki yaranta shi tafi mai da hankali a kai musamman cikin 'yan kwanakin nan da take hada kudin da zata sa su Mahmud a makaranta da Islamiyya. Ga dai shi anata ciniki sosai fiye ma da zatansu sai dai hidimar gabansu tana da yawa. Umaima da kudin da take tarawa na kitso ta biyawa Asiya kudin 65 Hadiza Ado Yalwa Garari jarabawar shiga aji shida (qualifying). Daga ita har Hansa'u kuma basa zuwa saboda ba su biya kudin makaranta ba, ganin wannan ne ya sa ta dagewa don neman kudi har wankau take zuwa duk sati ake biyanta ko yaran nata ba wanda ta gayawa tana yi, don ta san halinsu karshe su matsa a kanc ewa su za su yi ita kuma bata san yaran su dinga shiga gidajen masu hali saboda tsoran abin da zai je ya ZO. Daga ita har yaran ba wanda ya fadawa Lawal halin da suke ciki saboda sun manta ranar da Lawal ya magance musu matsalarsu. Wata ranar Lahadi Alhaji Manman tafiya zuwa Abuja sai ranar litinin za su dawo, cikin dare yake 66 Hadiza Ado Yalw a Garari sanarwa Harira tafiyarsu, ta yi addu'a da fatan alheri. Sai lokacin ta san Lawal yana wannan aikin shi ma don lawal ya na tsoron hanya kada wani abu ya same shi, su ce basu sani ba, aibunsa ya fito sarari, shi yasa ya yi shawarar fada ya kuma shigo musu da shinkafa kwano daya manja gwangwani daya ya bata dari biyu wai ta yi cefane, ragowar kudin ya adana abinsa sannan ya yi musu sallama suka dauki hanyar Abuja. Washe gari litinin da safe Hansa'u ta gama awara da safe ta shigar da ragowar tana irga kudin, Umaima ta gamaiwa sayyada wanka tana shaifa musu mai Ummansu na 67 Hadiza Ado Yalwa Garari kan sallaya tana lazimi bayan ta idar da sallar walha. Lawan ya yi musu sallama gaba daya suka amsa tare da yi masa sannu da zuwa, suna kokarin ta shi ya ce "Yau me ya hanaku zuwa makaranta?" Saboda rashin sabon jin irin wannan tambayar daga bakinsa yasa ya rasa me fara ba shi amsa a cikinsu sai kallon juna da suka yi na mamaki har sai da ya maimaita musu tambayar. Duk da murmushin a fuskarsu Umaima ta ce "Kudin makaranta ne ba mu biya ba" Ya ci gaba da taku zuwa kan katifar sannan ya kalli Harira dama aurar da su ki ka yi kika huta". 68 Hadiza Ado Yalwa Garari Saboda takaicin maganar Harira ba ta iya cewa komai ba, su kuwa kowacce ta yi nadamar tsayawa don jin kalaman nasa, nan da nan annurin fuskokinsu suka gushe, kamar walkiya suka fice daga dakin. Ya zauna yana nanatawa "Ke Harira wataran rashin daukar shawararki ce take sawa na ke rabuwa da ke, amma ban da haka kya sa yara a gaba kuna kallon juna ai gwara ki aurar da su ita fa babbar Asiya sha bakwai ta ke Hansa'u sha biyar Umaima sha huďu ko ke sanda na aure ki ai shekararki basu fi na Karamar ba" Gudun ka da ya ce bata bi shawararsa ba ya sa ta tankawa duk da wani abu ya zo ya tsaya mata a 69 Hadiza Ado Yalwa Garari cikin shakewar murya ta ce "To wa zan aurarwa su, tunda ba su da ma nemi kuma in ma suna da mane min da me zan aurar da su". Ya mike kafafuwansa "Ke dai Harira ki dinga godewa Allah ko da kudin da suke neman miki ai kya yi musu kayan daki." "Da shi mu ke ci mu ke sha har na biya kudin haya" Ta fada a zafafe, domin ya gama kaita makura. "To ni na zame hoto ke nan ba nayin komai". Wani kallo ta watsa masa maimakon amsar ya janyo robar awara ya soma ci "Ke dai ki dinga godewa Allah". 70 Garari Hadiza Ado Yalwa Ta dauke kwanan awarar ya bita da kallo ai kuwa aiki na gabanki" Zuciyarta na kuna ta shiga cikin matan gidan wadanda suka rage a wajen duk yanda ta so goge takaicin maganganun nasa sun kasa fita daga ranta. ke yi Duk hirar da matan gidan sai dai ka ga murmushinta da yawa bata gane abin da suke fada ba jinsu kawai take yi, abin da bata sani ba kuma shirunta ba karamin bakanta ran matan gidan ke yi ba, suna mata wani irin kallo ne mai girman kai, kamar tana nuna ta fi karfin yin magana da su, ko tafi karfin yin mu'amala da su, daga ita har yaranta basa sakewa da kowa a gidan in ka ji hirarsu isu isu ne kawai, in ko suna 71 Hadiza Ado Yalwa Garari cikin yaran gidan sai dai murmushin in ko a ka yi abin dariya su yi dariya, na jaje su ce Allah ya kyauta. Ga karatun bokon da suke yi wanda duk cikar gidan da batsewarsu babu wanda yake zuwa makaranta sai su. Wannan yasa suka sa musu ido sosai cikin al'amuransu da haka har suka gano ba fa wani abu suka fisu da shi ba tsabar girman kai ne a tasu fahimtar. Wannan ya janyo muguwar tsanar ya zamo ko magana suka yi a gidan ba mai tanka musu. Da farko abin ya da mu Harira ta same su cikin tausasawa take tambayarsu ko ta yi musu wani laifi ne ko yaranta sun bata musu ba 72 Garari Hadiza Ado Yalwa wadda ta yi magana saboda ba takamaimai abin fadar sai tsabar hassada. Tun daga wannan lokacin ta fita daga sha'aninsu za dai ta gaida kowa da safe haka ma yaranta za su gaishe su daga nan basa kara shiga sabgar kowa harkokin gabansu kawai suke yi duk da hakan ma bai rage ko da digon abin da suke yi musu ba, sai ma abin da ya dadu. Wani yammaci ta dawo daga gidan da take yiwa wanki agajiye take sosai saboda yau wanki mai yawa ta yi tafiyar ma kamar dole take yi ga ciwon kai, sai ta dinga jin kamar kira daga bayanta sai ta juye ta tabbata ita din ake kira, tabbas ita din yake kira da murmushi a fuskarsa a gabanta ya 73 Hadiza Ado Yalwa Garari yi wata irin faduwa tun ranar da ta baro rumfår shi ko hanyar bata kara bi ba, Alhaji Mai ice ne ta dan rage tsaho don ta gaida shi gaba daya fuskarta babu walwala. "Kin buya ina ta cigiyarki" Ta dan dauke kai ta ci gaba da tafiya "Wallahi ban yi ta wajejenku ba ne". Ganin tana tafiya ne yasa ya се "Harira tsaya magana nake son mu yi". Ta dan tsaya tana kallon kasa, "Haba Harira kamar baki gane abin da nake nufi ba, bakya nuna min kulawa.".ta dago da sauri ta watsa masa wani irin kallo irin na kyama "Ban gane abin da kake nufi ba Alhaji Ina tsammanin an fada maka ina da 74 Garari Hadiza Ado Yalwa aure, in ma ba a gaya maka ba to ka sa ni ina da aure na, ya dago hade da sauke ajiyar zuciya, na sani amma irin aurenki ba zai hanamu soyayya ba Harira" "Zuciyata ta kamu da son ki tm ranar da na ganki, shi kuma mijinna ki ai bai mai da ke mace ba, idan har kin ba ni dama ni zan hana zuciyarki da hannuwanki wahala zan mai da ke macen so ke maida aurenki yanda ya mai da shi". Maganganun suka dinga yawo a kanta zuciyarta na dada tafarfasa ta dai kasa magana har ya kai karshen maganarsa. Ya sa hannu a aljihu ya zaro kudi ya mika mata, sannan ta samu karfin fara tafiya batare da ta kallo kudin ba, hawaye ne suka zubo 75 Hadiza Ado Yalwa Garari mata duk wannan tozarcin lawal ne ya ja mata, kafinta isal gida haki ya fara ta so mata saboda 6acin rai. Ranar haka ta wuni ta na juya abin a ranta tana kuma tunanin abin da yakamata ta yi don dakatar da wannan al'amari. Hanyadaya ce wadda zata samu sauki barin gidan Alhaji mai icce sai dai matsala daya kudin da zasu kama hayar wani gidan daga karshe ta yanke shawarar fadawa Lawal ko ya samar mata mafita a cikin wannan BAKON AL"AMARIN. Cikin darre bayan ya kammala duk abin da zai yi ya kwanta, ta same shi ta fada masa tun kafin ma ta karasa ya katse cikin fada. "Wai me ki ka dauki kanki Harira indiya ko balarabiya mai 76 Garari G Hadiza Ado Yalwa Alhaji Zai yi da ke, kawai salon ki janyo abinda za ki ce muta shi daga wannan gidan tunda

Chapter 2 of 4