Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 5
na zaune a cikin kuryar turakarsa yana bincike a eikin hallarar tsafinsa sai kawai yaga wani abu da ya yi matukar firgitashi ya razana ainun ya kurma wani uban ihu ya ja da baya. Adaidai wannan lokacin ne sarki Ridwan ya Karaso cikin turakar a guje, cikin firgici ya kama boka Rimasu ya tashe shi zaune ya zauna daf da shi yace Jarumi da Gimbiya "Ya kai dirkar birnin kilmaz me ka gani yanzu a sakamakon binciken da ka yi. Tabbas dama na ji a jikina wani abu na tafiya ba daidai ba" Boka Rimasu yace. "Yarka gimbiya sazira ta ci amanarmu, a halin yanzu ta sace akushinmu na sihiri ta gudu daga nan a cikin siffar kuyanga Dulus kuma taje ta hada kai da dakarun sumame na birnin samhar wadanda suka zo saceta domin su je can birnin samhar su sace na su akushin sihirin, suna so ne za su hada akushin guda biyu su jefasu a cikin wutar ibilisai dake karkashin dutsen zulus. Idan hakan ta faru Karshen mulkinka dana sarki muraka ya zo karshe, masarautun guda biyu duka sai sun fadi, babu wani sarki da zai sake gudanar da mulki yadda ya ke so a wannan nahiyar" Koda sarki Ridwan ya ji wannan jawabi sai ya fusata ya mike tsaye ya kurma uban ihu. Ihun ya cika gidan sarauta gaba daya. Kuyanga Dulus na ji wannan ihu na sarki sai data firgita ainun ta gane cewa asirinta ya tonu. Don haka sai ta mike zumbur daga kan kujera a falonta ta fito da gudu tana kokarin ficewa daga cikin gidan sarautar gaba daya al'amarin dayai matukar baiwa dukkanin hadiman gidan sarautar mamaki kenan, kuyanginta suka biyota da gudu a baya, tana cikin wannan gudune kawai aka ga ta tsaya cak! Ta kame kamar gunki, kawai sai aka ga kanta ya cire ya fado kasa daga jikin wuyanta. Jini ya yi tsartuwa daga jikin wuyanta. Jini ya yi tsartuwa daga cikin wuyan. 72 Jarumi da Gimbiya Kan na faduwa kasa sai ya koma fuskar kuyanga Dulus sarki Ridwan na tsaye a gaban gangar jikin rike da takobinsa jini na diga a jikin takobin kawai sai sarlo Ridwan ya dubi kuyangi da dukkanin dakarun tsaro dake wajen yace. "Wannan ba 'ya ta bace gimbiya sazira kuyanga Dulus ce ta rikide izuwa kamanninta, gimbiya ce duk ta shirya wannan al'amarin ina sarkin yaki kinana yake maza aje a gaya masa ayi gagarumin shirin yaki zuwa birnin samhar zamu tunkara yanzu" Yana gama fadin haka sai ya juya da sauri ya nufi turakarsa domin ya je ya yi shigar yaki. Al'amarin jarumi Lurwan da gimbiya sazira kuwa cikin kankanin lokaci suka yi shiri-tare da yaransa guda shida suka hau dawakansu suka nufi birnin samhar gimbiya sazira na goye a bayan jarumi Lurwan bisa dokinsa, wato su biyune akan doki guda. Lokacin da ya rage sauran baifi tafiyar rabin saaba su isa birnin samhar sai suka tsaya jarumi Lurwan ya dubi jaransa guda shidan yace "Abinda nake so da ku shi ne ku tafi izuwa can dutsen zulus inda wutar ibilisai take ku jirani a wajen. Zan sameku a can bayan na sami nasarar sato akushin sihiri na masarautarmu, kamar yadda na yi muku alkawari idan har muka sami nasara akan wannan kudurin ku ne za ku zamo manyan fadawa a wannan kasa tamu, kada ku manta cewa kowannanku ya rantse da gemun iyayensa bisa 73 Jarumi da Gimbiya alkawarin rike amanarmu" Jaruman shida suka ce tabbbas rayuwarmu fansace akan wannan babban Kuduri. Koda jin haka sai farin ciki ya kama gimbiya sazira ta dauko akushin sihiri na birnin kilmaz daga cikin jakarta yana nannade a cikin wani jan tsumma ta mikawa daya daga cikinsu tace "Ku tafi da wannan ku adanashi da kyau har sai mun zo da dan uwansa sannan za'a hadasu a lokaci guda a jefa a cikin wutar ibilisai" Batare da bata wani lokaci ba dakarun shida sua karbi akushin sihiri suka kada linzamin dawakansu suka nufi hanyar da zata kai su inda wutar ibilisai take har sai da su jarumi Lurwan suka daina hangosu sannan gimbiya sazira ta dubi lurwan tace da shi. "Yanzu sai ka daure hannayena ta baya ka barni akan doki ka kama linzamin dokin kaja ka kai ni gaban sarkinku a haka" Ba tare da wata gardama ba kuma sai jarumi Lurwan ya aikata hakan suka durfafi fadar birnin samhar kai tsaye ba tare da wata fargaba ba. Sarki muraka tare da dansa Yarima Andaz na zaune akan kujerar mulki fadar ta cika makil da fadawa, dakaru da mutanen gari ana gudanar da harkokin mulki, kawai sai aka ji takun sawun doki a cikin fadar. Hankalin kowa ya kai izuwa kofar shigowa da kakarun tsaro suka bude hanya kawai sai aka hango jarumi Lurwan rike da dokinsa sun runkaro inda karagar mulki yake. Gimbiya sazira na zaune akan dokin an daure hannayenta ta baya kuma an rufe mata idanunta 74 Jarumi da Gimbiya Cikin tsananin mamaki da farin ciki sarki muraka da yarima Andaz suka mike tsaye suna kallon ikon Allah abinda ya fara baiwa su sarki muraka mamaki shi ne ta yaya jarumi Lurwan ya sami wammam gagarumar nasarar ya sato gimbiya sazira cikin sauki haka? Sai da ya rage saura baifi taku bakwai a tsakanin dokin lurwan da karagar mulkin sarki muraka ba sai sarki muraka ya dakawa jarumi Lurwan tsawa ya tsaya cak, kawai sai sarki muraka ya yi wa wasu dakarunsa inkiya su kimanin dari cíkin hanzari dakarun suka zare makamansu suka ritsa jarumi Lurwan da gimbiya sazira dake daure akan dkin sarki muraka ya dubi dansa yarima Andaz kawai sai suka bushe da dariyar mugunta a lokaci daya. Sarki muraka ya turbune fuskarsa ya dubi jarumí Lurwan yace "Kana zaton bansa duk abinda kuka shirya bane a kaina, Lurwan ka ci amanata ka hada baki da wannan yar sarki domin ku rushe masarautunnan guda biyu. Naga komai da kuka shirya a cikin madubin tsafina, ya ke gimbiya sazira kiyi sani cewa komai sammakonki ni a tafe na kwana" Koda jin wannan batu sai gimbiya sazira ta bude hannayenta, igiyar data daureta ta kwance tasa hannu ta bude idanunta ta dubi sarki muraka a fusace tace. "Ya kai wannan -sarkin kayi sani cewa koda a yanzu bamu sami nasarar cika kudurinmu a kan ku ba kai da mahaifina to nan gaba sai an samu wadanda za su kawar da ku saboda shi zallunci baya dorewa a doron kasa, bamu da wata damuwa idan ka kashemu a yanzu kai ma ka jira ranar taka mutuwar Dajin 75 Jarumi da Gimbiya wannan batu sai yarima Andaz ya bushe da dariyar mugunta ya dubi gimbiya sazira yace. "Wannan shi ne iyakar abinda zaki iya fada? Dakaru ku kama su ku kai su cikin kurkuku ku kullesu, a daren nan na yau za mu cika burinmu na amfani da akushin sihiri bayan nan kuma zan cika alkawarina akanki yake lallai sai na daddatsa wannan kyakkyawan jikin naki na aikawa da mahaifinki kanki ya gani da idanunsa, nasan yana gani zai hadiyi zuciya ya fadi ya mutu" Sarki muraka ya bu she da dariyar mugunta yace. "Zancenka dutsene maza dakaru ku hanzarta kai su cikin kurkuku a je a kirawo mun babban boka domin mu fara shirin kaddamar da tsafin akushin sihiri" sarki na gama fadin hakan aka kama jarumi Lurwan da gimbiya sazira da karfin tsiya tunda sarkin yawa yafi sarkin karfi aka kai su cikin kurkuku aka kullesu. ** Al'amarin dakarun sumame su shida kuwa lokacin da suka isa inda kogin ibilisai yake suna dauke da akushin sihiri na birnin kilmaz sai suka daure dawakansu suka zauna a gefe guda. Dukkaninsu sai suka yi shiru suna tunani dayansu baice uffanba. Daga can sai babban cikin su wanda ake kira da suna barde awaisu ya dube su su duka yace. "Kunsa wani abu kuwa? Suka ce "Bamu san komai ba face ka fadi abinda yake ranka" Yace "Ina ji a jikina gimbiya sazira da barde Lurwan ba za su iya gudanar da wannan aikin ba a cikin gidan sarki face sun samu matsala saboda duk shirinsu sarki 76 Jarumi da Gimbiya muraka ya fi su, ai duk wanda ya rigaka kwana dolene ya rigaka tashi, ya zama dole mu rabu biyu wasunmu su kai musu dauki a yayin da dare ya raba, dolene mu san yadda zamu shiga cikin gidan sarautar domin muga halin da suke ciki ku sani cea nasararsu itace tau. Idan ba su yi nasara ba dukkaninmu nan sai an kamomu anyi mana kisan gilla" Lokacin da barde Awaisu ya zo nan a jawabinsa sai dukkaninsu jkinsu ya yi sanyi suka gamsu da abinda ya fada awaisu ya sake dubansuyace. "Nasan kuna tunanin hanyar da zamu bi mu shiga gidan sarauta ba tare da asirinmu ya tonu ba to ina so ku tuna da yadda muka yi muka shiga cikin gidan sarautar birnin kilmaz har muka isa bangaren turakar gimbiya sazira ba tare da kowa ya ganmu ba. Dakaru dari uku muka kashe a wajen kuma muka fito lafiya to yanzuma irin wannan shirin za mu yi saboda haka yanzu mutum biyu kacal zamu bari anan wajen kowa ya yi shiri lallai a darennan za mu ratsa gidan sarautar garinnan". Jarumi Lurwan tare da gimbiya sazira na zaune a cikin kurkuku har dare ya soma yi basu ci komai ba basha wani abu ba saboda takaicin yadda dukkanin shirinsu ya wargaje. Tsawon wannan lokaci dayansu baice uffanba sai dai su kalli juna su kauda kai. Sau goma sha daya gimbiya sazira tayi kokarin amfani da sihirin tsafinta domin su kubuta daga cikin kurkukun amma sai tsafin nata yaki ya yi tasiri, shima jarumi Lurwan haka ya yi ta jarrabawa sau ba adadi har ya gaj Jarumi da Gimbiya Sai da dare ya raba sosai suna zaune su basu kwanta ba kuma ba su rufe idanunsu ba kawai sai gimbiya sazira ta taso daga inda take zaune ta dora kanta akan kirjin jarumi Lurwan tace "Lokaci ya yi wanda zamu yi bankwana da duniya"Cikin mamaki ya janye jikinsa daga cikin nata ya dubeta yace "Gimbiya ban fahimce ki ba ya za'ayi muyi bankwana da duniya alhalin ba a zo kashe mu ba" Koda jin wannan tambaya sai hawaye ya zubo mata tace. "Da dai mu bari wannan azzalumin sarkin ya kashe mu gwara mu kashe kanmu kawai, idan fa na mutu tsafin da zai yi da akushin sihirin ba zai yi aiki ba, ina son ka kashe ni da hannunka nima na kashe ka da hannuna sai dai su zo su iske gawarmu wannan ce kadai hanyar da za mu bi mu hana sarkina da sarkinku cika burinsu na ci gaba da yin zallunci a wannan nahiyar idan baka manta ba ka daukar mini alkawarin cewar ranka da jikinka fansane akan wannan babban kuduri na alkhairi" Sa'adda da gimbiya sazira ta zo nan a zancenta sai shima hawaye ya zubo masa yace. "Tabbas na yi miki wannan alkawari kuma dolene na cika shi" Yana gama fadin hakan sai ya zaro wuka a jikinsa, itama gimbiya sazira sai ta zaro wukar jikinta, duka su biyun suka yunkura za su cakawa juna. wukaken akan makoshinsu kawai sai suka ga barde Awaisu ya duro daga sama tsulum! Ya bayyana a gabansu. Nan take yasa mukuli ya bude kofar kurkukun suka fito daga ciki duk su ukun suka kamatafiyar sanda da labe a cikin gidan sarautar. 78 Jarumi da Gimbiya A daidai wannan lokacine suka ji an busa kahon yaki, koda jin hakan sai gimbiya sazira ta yi murmushi tace "Ga mahaifina nan tare da rundunarsa ta yaki sun iso garinnan, yanzu nan za a yita ta kare, maza ka nuna mini inda aka ajiye akushin sihiri na wannan masarauta” Dajin haka sai jarumi Lurwan ya wuce gaba da sauri suka bishi a baya. Nan danan gidan sarautar ya hargitse da guje- guje na dakaru suka yi ta debo makaman yaki ana ta shirya dawakai domin tuni labari ya zo cewa ga dakarun yaki can na birnin kilmaz suna daf da isowa kofar birnin samhar jarumi Lurwan da gimbiya sazira tare da barde Awaisu suka tunkari dakin tarihi inda aka ajiye akushin sihiri amma sai dakaru suka taresu aka ruguntsume da azababben yaki da karfin tsiya su gimbiya sazira suka kwaci makaman yaki a hannun dakarun suka rinka ragargazarsu sai da suka shafe sama da sa'a uku suna bakin artabu da dakarun har ya zamana duka su ukun sun samu raunuka a jikinsu kuma sun sha bakar wuya kamar ba za su rayu ba sannan suka samu da kyar da sidin goshi suka shiga cikin dakin tarihin suka dauko wannan akushin sihiri. A can kofar birnin samhar kuwa yaki ya yi tsanani sai ragargazar maza ake yi suna zubewa kasa matattu. Saboda yawan gawarwaki a wajen kai kace yabanya ce a gona duk inda ka duba jinine ke malala bisa kan Kasa. Sarki Ridwan da sarki muraka ke jagorantar wannan yakin. Sai da gari ya waye ana ta gwabza wannna yaki har rana ta fito sosai sannan gaba dayan dakarun yakin suka kare aka yi ragas ya zamana cewa mutum biyune kacal suka rage a tsaye 79 Jarumi da Gimbiya suna kallon junansu suna haki kamar zakaru. KКо wannen su jikinsa ya yi kaca-kaca da jini, ba wadansu bane wadannan mutanen face sarki muraka da sarki Ridwan ya yin da kowannansu ya dubi dubun gawarwakin dakarunsa sai bakin ciki ya turnukesu suka kwarara uban ihu suka yunkura domin su ruga da gudu izuwa kan juna kawai sai sukaji an tsala tsawa a sararin samaniya mai matukar firgitarwa suka daga kawunansu sama suka ga ko alamar hadari babu hankalinsu ya dugunzuma ainun ba don komaiba sai saboda sun gane cewa an jefa akushin sihiri guda biyu a cikin wutar ibilisai. Koda suka fahimci hakan sai kowannansu ya kurma ihu suka durkushe kasa bisa guiwoyinsu cikin matsanancin bakin ciki nan take ko wannansu yasa takobinsa ya soka a cikinsa suka bingire kasa matattu. Kamar yadda Gimbiya sazira ta yi alkawari haka abin ya kasance domin an daura aurenta da jarumi Lurwan. Shi kuma Yarima Andaz an tsinci gawarsa a filin yaki anyi gunduwa-gunduwa da ita. An sare kansa an ajiye shi kusa da gawar mahaifinsa. Daga wannan rana aka sami zaman lafiya da kwanciyar hankali a wannan nahiyar gaba daya. Sarakuna suka rinka tabbatar da adalci gami da tausayi da jin kan talakawansu. ALHAMDULILLAH ABDUL-AZIZ SANI MADAKIN GINI KARSHЕ 80 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 5 of 5